Tag: yadda ake

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Uku

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Uku

    Ba a daɗe da sallacewa ba kuma aka buɗe gari, a hankali kowa ya koma harkokinsa. Ranar Lahadi da daddare bayan yara sun yi bacci; suna zaune a parlor shi yana kallon ball a TV yayin da ita kuma take chatting a waya; ta ɗago daga kallon wayar ta dube shi tace ‘Babe gobe fa za a koma makaranta.’

    Ba tare da ya ɗauke kai daga kallon TV din ba yace ‘Kin gaya min fa tun last week, kuma na siyo duk wani abu da ake buƙata. Ta gyara zama ta ajiye wayar tace ‘Ni ma zan shiga school ɗin na gano, wata ƙila an kafe timetable, amma sai wajen goma zan fita.’
    ‘Ok, to za ki dawo kafin 12:30pm kenan ko? Saboda ɗauko ‘yan makaranta tunda ni kin ga ina office.’

    ‘Eh, zan yi ƙoƙari na dawo kuma idan ban dawo ba ma kafin na fita zan je da Rashida ta ga makarantar tasu idan lokaci ya yi ban dawo ba sai ta je ta ɗauko Nasreen. Ya gyara zama ya kalle ta kamar a firgice ‘Wai wannan yarinyar ce za ta dinga ɗauko yaran daga
    makaranta kuma ta zauna ta zauna da su a gidan ita kaɗai?’

    Cikin halin ko in kula tace ‘To ya za a yi, ai ka ga dai ni ma dole na je makaranta ko? They will be fine fa, yarinyar tana da hankali sannan kuma ka ga ga Afaf tana nan idan ta dawo. Su ma ita da Habib na gaya musu idan an tashi daga makaranta su taho tunda na ga ko ni ce ma na je ɗauko su idan muka rasa napep a ƙasa muke tahowa.’

    Ya ƙare mata kallo sanna yace ‘Wai me kike faɗa ne? Su Afaf ɗin ne kike so su dinga tahowa daga makarantar su kaɗai kuma a ƙas, sannan har da Nasreen? Wadda sai an tashe ta da minti talatin sannan a tashe su? To babe ya za mu yi? Ai ka ga dai kamar Afaf ba shi da wani amfani a ce sai Rashida ta je sannan za su taho tare ko?

    Ni kuma duk lokacin da ta kama ina gidan zan je na ɗauko su. Suka yi shiru na ɗan lokaci kowa da abinda yake tunani. Jimawa kaɗan yace ‘Ni barin wannan yarinyar taki ma a gidan ita kaɗai gaskiya bai yi min ba, ya za a yi duk mu fice a barta ita kaɗai kuma a bar mata mukullin gidan? Ai idan muka dawo sai abinda muka gani kenan, za ma ta iya fara shigo da maza gidan ko a yi mata wayo a yi mana ɓarna idan aka gane ita kaɗai ake bari a gidan.’

    ‘To yanzu ya kake so a yi? Ka ga dai da ni da yaran ai dole duk mu je makaranta ko?’
    ‘Ni ma ban sani ba, kece za ki san yanda za ki yi. Za ki ma iya fita da ita ki rufe gidan in ya so sai ku dawo tare ki ɗauko yaran, duk yanda dai kuka yi. Amma dai gaskiya wannan tsarin na barinta a gidan bai yi min ba.’

    Ranta ya fara ɓaci; me yake nufi ne? So yake yace ta bar makarantarta kawai saboda ta zauna masa da yara ko kuwa mai aikin yake so ya korar mata? Wannan bayanin da yake yi ma sam ba zai yiwu ba gara dai ya sake lissafi ko kuma shi ya dinga baro office yana zuwa yana ɗauko su.

    Tace ‘Uhm, to ai ka ga ba ni nake rubutawa kaina timetable ba, wani malamin ma sai 1pm yake fara lecture kuma dole na yi attending idan dai ina son na gama degree ɗin. Sai dai ko ka kawo wata dabarar da kai kake ganin za a yi da ɗauko su in ya so ita Rashida idan zan fita sai na fita da ita duk lokacin da na gama lecture sai mu dawo tare.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan ya tashi ya jefar da remote ɗin TV ɗin da yake hannunsa ya shige ɗaki. Ta bi bayansa da kallo tana mamaki; wai me mutumin nan yake nufi ne? Shikenan sai ta jingine rayuwarta ta zauna ta kular masa da yara? To ai ita ko ‘yayan da ta haifa ma haka ko tana so ko ba ta so za ta dinga barinsu da mai aikin ta tafi makaranta tunda dai haka ta ga masu yaran suna yi.

    Ko kuwa da yake ta auri tuburarre haƙura za ta yi da komai ta zauna sai yanda suka yi da ita? Haka suka kwana a wannan daren kowa da abinda yake ransa. Ko da gari ya waye tun asuba ta tashi ita da Rashida wadda ta taya ta nan da nan suka shirya
    yara sannan suka haɗawa kowa abinci.

    Kamar yanda ya saba sai ƙarfe bakwai da kwata sannan ya fito, zuwa lokacin sun shirya suna jiransa; ya kwashe su ya kai su ya dawo. Sai wajen ƙarfe tara da rabi sannan ya gama shirinsa, lokacin fitowarta kenan daga wanka saboda sai da ta tsaya ta gama abincin rana ta juye a flask sannan ta fara shirin. Ya same ta a ɗaki tana shafa mai riƙe da mukullin motarsa, yana daga tsaye a bakin kofa yace ‘Ni na fita.’

    Ta juyo da sauri tana cewa ‘La! Babe don Allah bari na yi sauri na saka kayana sai ka ba ni lift. No ba ta hanyarku zan bi ba, ki wuce kawai sai na dawo. Kada ki manta min da yara.’ Ya faɗa yana ficewa daga ɗakin. Ta bi bayansa da kallo da baki buɗe; lallai ma mutumin nan.

    Ƙiri-ƙiri dai shi baya son ya ɗauke ta a motarsa idan dai makaranta za ta, in banda haka ai ko ba hanyar makarantarsu zai bi ba ya sauke ta a bakin titi ya rage mata tafiya. Ta juya ta cigaba da shiryawa cikin sanyin jiki tana tunanin son kai irin na Mustapha. Allah ya so ta ma Baffa magana ya tura mata kuɗi kuma ya sanar da ita duk wata zai dinga turo mata kuɗi saboda karatunta, idan tana son wani abu sai ta yi masa magana.

    Tabbas ta san da a ce da Mustapha ta dogara da sai dai ta haƙura da karatunta ta zauna ta kular masa da yara. Nan da nan ta ƙarasa shiryawa ta fito ta sallami Rashida wadda ta bar su tare da Shukra bayan ta yi mata duk wani bayani da take buƙata sannan ta kama hanya zuciyarta cike da damuwa da wasi-wasi.

    Kafin sha biyu ta gama duk wani abu da take yi a makarantar sai dai ba ta son ta dawo ta ɗauko yara; ba wai yaran ne ba ta son ɗaukowa ba amma ba ta son ta ɗauko su Mustapha ya ga kamar faɗansa ne ya sa don haka duk lokacin da za ta fita ya za ta zai yi mata faɗa ta dauko masa yara.

    Don haka suka nemi inuwa ita da ƙawayenta suka zauna suna hira, sai wajen 1;30pm sannan suka ƙarasa masallaci suka yi sallah kowacce ta kama hanyara gida. Ko da ta zo gida ba ta tarar da wata matsala ba, Rashida ta kai Shukra gidan su Ummi ta ɗauko
    Nasreen daga makarantar kamar yanda ta ba ta umarni. Su kuma Afaf da Habib kusan tare da ita suka shiga gidan.

    Ko da ya dawo tana jin sa yana tambayar yaran wanda ya ɗaukosu daga makaranta suna ba shi amsa, musamman Shukra wadda yake ta tambayarta me suka yi ita da Rashida a gidan bayan Anti ta fita. Haka ta yi banza da shi ta cigaba da harkokinta.

    Haka suka cigaba da yi, sai ya zama kuma da yake ba a fara lecture sosai ba sati biyun farko kullum Khadeeja ba ta fita da wuri sanna kuma tana dawowa kafin ya dawo gidan, don haka matsalarsu da sauƙi tunda zai zo ya tarar da ita tana ta hidimar yara.

    Sati ɗaya da komawa aka kafe wa su Khadeeja timtable, kuma da yake babu lokaci sosai timetable ɗin a matse take. Haka dai suka cigaba da karatun. Ranar Alhamis shi ne take da lecture 8am to 6pm, don haka ta san dole ta shirya ta fita tare da yara. Tun dare ta gama komai, ta yi rabin aikin abincin safe sannan ta fitowa da kowa kayansa.

    Ta yi wa Rashida duk wani bayani da take buƙata tunda yaran idan sun dawo daga makarantar boko babu islamiyya don haka nan za su wuni a gidan. Tun kafin asuba ta tashi suka fara aiki tare da Rashida. Bayan Mustapha ya dawo daga masallaci
    sallar asuba ya same ta a kitchen, tana ta fama kai wa da kawowa tsakanin dankalin da take soyawa da kuma haɗawa yara abincin makarantarsu a lunch box.

    Bayan ya amsa sannu da zuwanta yace ‘Wai kin yi sallah kuwa? Na ga kamar a nan na bar ki fa. Ta yi ‘yar dariya tace ‘Haba dai, na yi sallah mana. Sauri nake na gama saboda yau 8am to 6pm ne da ni kuma 8am din nan idan Prof. ya riga ni shiga aji rufe min ƙofa zai yi wallahi shi yasa nake ta sauri don kullum sai ya yi attendance.’

    ‘Oh kenan yau sai 6pm za ki dawo gidan? Eh.’ Ta amsa a gajarce tana kwashe dankalin da ya riga ya soyu. Ya ƙara haɗe girar sama da ƙasa sanna yace ‘To a ina za ki bar yara wuni guda? Ba ta son hayaniyarsa don ba ta son abinda zai ɓata mata rai, ba tare da ta bar abinda take yi ba tace ‘A nan mana gidansu; Rashida za ta ɗauko Nasreen su kuma su Afaf idan suka dawo za su same ta a gidan sai su yi zamansu kafin na dawo, they will be just fine.’

    ‘Haba ai daɗewar ta yi yawa, kenan haka za su zauna su yi duk abinda suka ga dama ba tare da wata kulawa ba.’ Ya faɗa a fusace. ‘Kada ka damu Rashida za ta kula da su.’
    Kafin ya ba ta amsa suka jiyo ihun Nasreen daga ɗakinsu tana cewa ‘Wayyo Anti.’
    Ta riga ta san rigimar Nasreen, idan dai aka tashe ta da sassafe zuwa makaranta sai ta yi kuka ko ma waye ya tashe ta, shi ma kuma ya san da haka.

    Amma ba tare da ɓata lokaci ba ya nufi ɗakin da sauri. Ganin haka ita ma Khadeejan ta ajiye abinda take yi ta bi bayansa, kusan a lokaci ɗaya suka shiga ɗakin. Nasreen tana zaune a kan gadonsu da hawaye shaɓe-shaɓe a idonta yayin da Rashida take tsugune a gaban gadon tana riƙe da towel. Me aka yi miki kike kuka Nasreen?’ Ya tambaya kafin ya karasa shiga ɗakin.

    Khadeeja tana shiga ɗakin ta sauko daga kan gadon ta rungume ta tana cewa ‘Anteee.’
    Ya shafa kanta ‘Me aka yi miki? Cikin shagwaɓa tace ‘Rasheeda ce. ”Ya juya ya dubi Rashidan a fusace yace ‘Me kika yi mata? Nan da nan jikinta ya hau rawa tana gyara tsuguno, kafin ta yi magana Khadeeja ta shafa kan Nasreen tace ‘Nas me Rashida ta yi miki?’

    ‘Tashi na ta yi daga barci. To ai kin ga shirya ki za ta yi ki tafi school ko? Ko kina son ki makara Uncle ya koro ki gida ne? Ya yi tsaki ya fice daga ɗakin ba tare da ya sake cewa komai ba. Ta lallaɓa Nasreen ta tura ta banɗaki sannan ta juyo za ta fito, kafin ta fito ta jiyo shi yana dawowa ɗakin yana cewa ‘Dankalin da kika bari a wuta ya kone, ki je ki duba na kashe miki wutar.’

    Ta wuce shi ta ƙarasa kitchen ɗin da gudu inda ta sami dankalin ya ƙone, ta kwashe sannan ta sake kunna wutar ta ɗora. Ya ƙaraso ya tsaya a kofar kitchen ɗin, ya ɗan ɗauki lokaci yana kallonta tana zubawa yara abincin rana wanda ta sauke a babban flask. Jimawa kaɗan yace ‘Kin ga irin abinda yasa bana son ki bar su da yarinyar nan ita kaɗai ko?

    Ya za a yi ta iya kula da yara tunda ga shi nan ba ta ma iya tashinsu daga bacci ba?’
    Ta kalle shi cike da mamaki tace ‘Nasreen ce fa, ko kai ne ma ka tashe ta sai ta yi rigima, ko ka manta ne? Kuma kai ne ka ce ba ka son Rashida ta dinga yi maka girki kuma ka ga dole abu ɗaya zan yi a lokaci guda ba zai yiwu ina girka muku abinci ba kuma ina shirya yara.’

    Ya juya ya fice ba tare da ya ce komai ba. Ta ja tsaki ta share ƙwallar da ta taru a gefen idonta sannan ta cigaba da aiki. Ba ta ma san me take ji ba, ƙoƙari kawai take ta fita daga gidan idan ta je makaranta ta samu ta yi tunani ta fahimci me take ji. Bayan ta gama abinci ta wuce ɗaki ta same shi bayan ta zubawa yara abinci suna ci.

    Yana kwance a gefen gado yana fama latsa waya ta wuce har ta kusa shiga wankan yace ‘Idan na kai yara dawowa zan yi kin sani, sai wajen 10am zan fita, ita wannan yarinyar taki haka za ki bar min ita a gidan daga ni sai ita? Cikin halin ko in kula tace ‘Eh, ita da Shukra za su zauna idan za ka fita kawai ka gaya mata don ta san cewa ka fita ta cigaba da aikinta.’

    Har za ta shige banɗakin yace ‘Gaskiya ba na so, kuma ke ma kin san bai dace ba ki bar ni a gida daga ni sai mai aikinki mace. Irin haka ne kuma idan an ce za a auri mai aikin ku ce ba ku yarda ba. Duk ɓacin ran da take ciki sai da ya ba ta dariya, duk da dai dariyar takaici ce tace ‘to ai ga ka nan ga ta nan ka aure ta mana, ai ita ma mace ce.’

    ‘Ni dai na gaya miki bana son ki bar ta a gidan idan ina nan tunda ke ba kya nan, ki sami inda za ki ajiye ta idan na fita sai ta dawo gidan. ‘Uhhm!’ Ta amsa sannan ta shige wankan cike da takaicinsa, har ji take kamar zuciyarta tana turiri. Zuwa makaranta lecture kawai ya zama wata drama.

    Nan da nan ta ƙarasa shiryawa ta shirya yaran, ta haɗa tea ta zauna tana sha. A haka Mustafa ya fito ya same su lokacin 7:15am. ‘Ku tashi mu je.’ Ya faɗawa yaran.
    Ta miƙe riƙe da kofin shayinta tace ‘Bari na ɗauko hijab dina na saka ku rage min hanya.’
    ‘A a za ki makarar da mu ne fa, ga shi ko shayi ba ki gama sha ba kuma kin san idan suka makara koro su za a yi.

    Ya juaya ga yaran wadanda sun riga sun miƙe kowa da kayansa a hannu yace ‘Mu je.’
    ‘Anti sai mun dawo.’ Suka faɗa sannan suka juya suka fice ya bi bayansu. Ta bi bayansa da kallo cike da mamaki; ta kasa gane motarsa ce ba ya son ta dinga shiga ko kuwa tsabar baƙin ciki ne a kan za ta fita yake hana shi rage mata hanya.

    To amma kuma yana kai ta unguwa, kodayake wannan fita ce da shi ya ga dama kuma kusan duk inda za ta tunda ta aure shi tare yake kai ta da yaran suna biye da ita. To me yasa idan dai makaranta za ta tafi sai ya san yanda ya yi ya tafi ya bar ta ba tare da ya ko da rage mata hanya ba?

    Haka har ta gama shirinta ba tare da ta samo amsar tambayarta ba; ta fito ta sami Rashida a kitchen tace ‘Idan babansu ya dawo ki koma ɗaki ki zauna in ya fita sai ki fito ki cigaba da aikin; idan Shukra ta zauna a wajensa shikenan idan kuma ta taho wajenki to don Allah kada ki bari ta yi kuka ya ji.’

    Ta yi mata sallama ta fice tana sauri saboda 7:20am ta riga ta yi kuma ba ta da tabbas ɗin za ta iya kai wa BUK kafin 8:00am. Ta kusa isa titi Mustapha ya karyo kwana ya shigo layin, ta ɗauke kanta daga kallon inda yake; ba ta sani ba ko ya ganta ko bai ganta ba.

    Ta ƙarasa titi cikin sanyin jiki ta hau Napep tambayoyi daban-daban suna ta yawo a kanta; wai ina babe ɗinta ne? Wanda yake son ta? Wanda kafin aurensu har so yake ya ɗauko ta daga makaranta ya kai ta unguwa ko ya kai ta gida don dai tana hana shi ne saboda ta san Baffa ba zai bari ba a lokacin. To shikenan soyayya ta ƙare ko me
    Mustapha yake nufi da ita? Shekara ɗaya fa kenan da ‘yan watanni da aurensu.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyu

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyu

    Ranar Sallah yana tashi ruwan shayi kawai ya sha ya shirya ya fice; bayan an idar da sallar idi kai tsaye gidan Mama ya wuce wajen yaransa. Yana gamawa da su ya wuce gidan Mommy wajen Khadeej; ko da dai ya ji haushin yanda ta yi zamanta a gidansu ta ƙi dawowa amma ya san ya yi kewarta.

    Duk wani haushi nata da yake ji ya riga ya huce, abu ɗaya yake so a yanzu shi ne ta dawo gida ya samu ya daina fama yawo shi da yaransa sai kace wasu waɗanda ba su da gata. Ya kalli kayan sallarta waɗanda ya taho da su ya kai mata ko za ta ƙara, ya kau da kai ya cigaba da tuƙinsa.

    Shi ya ga ma kamar ba ta damu da kayan sallar ba tunda da ita aka kai ɗinkin amma da yake ta so ta yi sallah a gida ko bi ta kansu ba ta yi ba sai ma ce masa da ta yi Baffa ya yi mata kayan sallah. Haka dai ya yi ta tunani kala-kala har ya ƙarasa gidansu Khadeeja.

    Lafiya ƙalau suka gaisa cikin mutunci kamar babu wanda yake jin haushin wani a tsakaninsu; ya shiga ya gaida Mommy sannan ya gaida Baffa. Suka dawo ita da shi suka zauna a parlor ɗin baƙi inda ba tare da ɓata lokaci ba ta kawo masa tuwon sallah da lafiyayyen zobo mai sanyi. Suka zauna yana ci tana yi masa hira.

    Bayan ya gama ya huta ya yi wa Baffa sallama inda Baffan ya sanar da shi jibi ya zo ya ɗauki matarsa. Suka fito tare da Khadeejan ta rako shi bakin mota. Tana tsaye riƙe da murfin kofar motar yayin da shi kuma yake zaune a kujerar direba ya juya kujerar baya ya ɗauko ledar da take ajiye a kan kujerar ya miƙa mata yana cewa ‘Ga kayan sallarki duk da na ga ba ki damu da su ba.’

    Ta yi ‘yar dariya tana tura masa ledar tace ‘Ka koma da su ka ajiye min a ɗakina tunda jibi zan dawo. Shi ma dariyar ya yi yana mayar da kayan yana cewa ‘Ko dubawa ma fa ba ki yi ba. Haba kayan da na riga na sansu, idan na dawo zan duba sannan na yi kwalliyar sallah ta.’

    Cike da farin ciki da walwala suka yi sallama sannan ya wuce gidan Hajia. Yana shiga gidan ya tarar da Hajia a parlor ɗinta suna hira ita da Yaya Jidda, yaranta kuma suna ta kai wa da kawowa a tsakar gidan. Bayan ya gaida Hajia ya yi mata barka da sallah ya juya suka gaisa da Yaya Jidda wadda take ta faman shan kunu tana basarwa saboda kar ya yi mata wata magana.

    Bayan sun gaisa sun ɗan taɓa hira da hajia ya dubi Yaya Jiddan yace ‘Yaya bari na ba ki account number ki turo min 10k ɗin da na tura miki ta yi wa yara sayayyar kayan shayi; tunda sun ce min ba a saya ba ko? Ta sake haɗe girar sama da ƙasa ta kalli hajia sanna ta kalle shi tace ‘Ban gane ba a siya ba, an siya mana.

    Kawai dai ba ranar da ka bayar ba don kafin ka turo kuɗin masu kantunan sun rufe. Shi yasa ba a samu an saya ba har sai ranar da aka sake buɗe gari, ranar da ka zo kenan ka kwashe su. Da safen da ka tafi da su ai da sun zo za su tarar da kayan komai an saya don har ciko ma nayi.’

    Hajia tace ‘Ai kuwa ka ga babu maganar dawo da kuɗi tunda an sayi kaya.’Takaici ya kama shi don ko ɗaya bai yarda da wannan zancen nata ba, ya kawar da kai sannan ya sake dubanta yace ‘Haka ne, to shi kenan, sai a ɗauko min ragowar na tafi da su tunda jibi yaran za su dawo har Khadeejan kuma ko suga babu a gidan sai na sake siya.

    Ki aika a ɗauko min su tunda kusan ma ba a yi amfani da su ba kenan tunda ranar da aka siyo ranar suka tafi. Kafin ta yi magana Hajia tace ‘To su sauran yaran gidan ba ‘yayanka ba ne da ba za a ba su ba, kayan shayin kawai ba wani abu.’ Ta dubi Jiddan tace ‘Ko da yake bari na barku wataƙila suna nan ki ba shi ya kai gidan nasa.’

    Ta sake kicin kicin sannan tace ‘Hajia kema dai kin san yaran nan ba za su bari ga kayan shayin har da Indomie su bari na ajiye ba tare da na ba su ba. Sai dai kawai idan biyansa zan yi na yi wa babansu waya ya biya abinda ‘yayansa suka ci tunda yana kallo suna ci kuma ya san ba shi ya siyo ba.’

    Hajia tace ‘A a ba za a yi haka ba, sai kace a garin matsiyata ake.’ Ta dubi Mustaphan tace ‘Kai Mustapha ka yi haƙuri, ba na son wannan rigimar taka. Wannan ma ai ba wani abu ba ne da za a ɗaga tunda daga yaranta har nakan duk ‘yayanka ne. Muryarsa a maƙogoro yace ‘Shikenan Hajiya.

    Ya miƙe tsaye yana cewa ‘Bari na je wajen Alhaji mu ci tuwon tare, ko da yake ma a ƙoshe nake me sanyin kawai zan sha. Yana shigewa Jidda ta kalli Hajia tace ‘Kin gani ko Hajia, a kan kayan shiya zai yaga min rigar mutunci, wallahi yaron nan har yanzu bai yi hankali ba.’

    Tace ‘Ya fi ki gaskiya, ya za ki karɓi kuɗinsa kuma ki dinga bar masa yara da yunwa?Hajia wallahi na gaya miki ƙarya yaran nan suke yi, kawai don sun san za a biye musu ne suke abinda suka ga dama. Idan banda haka ya za a yi na hana su abinci na ba wa su Nawwara tunda ai duk tare suke wuni suna wasansu; kawai dai suna so su nuna su ubansu mai kuɗi ne.’

    ‘Ki dai bi shi a hankali kin ji na gaya miki. Bari ma ya fito na ji sai yaushe zai kawo min yaran yawon Sallah ko kuma ni ma laifin naki ne ya shafe ni ya kai yaran wajen wadda da ba ya son ya bar mata su?’

    Haka yana ji yana gani ya haƙura ya ƙyale Yaya Jidda; daman ya riga ya san Hajia ba za ta taɓa bari a ga laifinta ba. Kamar yanda aka yi alƙawari ranar uku ga sallah tun wajen ƙarfe tara na safe ya tafi ɗaukan Khadeeja; da yake sun riga sun yi waya a shirye ya same ta don haka ba tare da wani ɓata lokaci ba ya ɗauko ta ita da mai aikinta Rashida suka kama hanya.

    Sai da suka tsaya a gidan Mama suka kwashi yara sannan suka wuce gidan Hajia. Nan suka zauna a parlor ana ta hira yayin da yara suke ta kai wa da kawowarsu. Jimawa kaɗan Yaya Jidda ta dubi Khadeeja tana nuna Rashida tace ‘Wannan yarinyar taki kuwa za ta iya wani aikin kirki? Kada fu ku je a kama ku da child abuse?’

    Ta yi dariya duk da yanda maganar ta ɓata mata rai tace ‘Ah haba dai, shekarunta fa sha biyar yaya don dai kawai ba ta da girma ne. Aiki kam ta iya sosai ko a gida ma Mommy ta koya mata.’‘To amma idan Habi ta dawo sai a mayar da ita ko? Tunda na ji Habi ɗin tace baku da wata matsala da ita kuma tana nan ita ma tana shirin dawowa.’

    ‘Uhm, sai a haɗa biyu ma tunda kin ga ga hidimar gida ga ta yara, kuma ina zuwa makaranta. Haba wace hidima ce sai an haɗa ‘yan aiki har biyu a wannan gidan? Hidimar har nawa take? Kafin ta ba ta amsa Mustapha ya shigo yana cewa ‘Ku tashi mu tafi ko, don na san kuna da aiki a gidan nan don duk ya yi ƙura.’

    Suka fara shirin miƙewa yayin da ita kuma Yaya Jidda ta kalli Mustaphan tace ‘Na ga kun samo ‘yar aiki, Baba Habi ma fa tana nan tana shirin dawowa. Yace ‘Ah ai kawai sai ki ce mata ta yi zamanta tunda dai gaskiya ba mu da inda za mu ajiye ‘yan aiki har biyu. Da nace ta mayar da wannan ɗin idan Baba Habi ta dawo?’

    ‘To ga ta nan ku yi magana idan ta fi son Baba Habi ɗin sai a mayar da wannan ɗin.’

    Ba tare da ɓata lokaci ba Khadeeja tace ‘Uhm ai gara a bar wannan ɗin, in ya so in da wata matsala sai na yi magana a nan ɗin a kawo wata. Haka dai dole Yaya Jidda ta bar su suka tafi ba tare da ta iya gamsar da su cewa Baba Habi za ta dawo ba.

    Kamar yanda ya faɗa kuwa kaca-kaca suka tarar da gidan, sai dai suna shiga suka fara ƙoƙarin gyarawa. Kuma da yake yana ajiye su ya sake fita har da Afaf da Habib aka yi aikin, don haka cikin ƙanƙanin lokaci suka gama.

    A haka rayuwa ta cigaba; sai dai a ɓangaren Mustapha idan dai yana gidan ba a saka masa yara aiki, sai dai su su yi ta gara Rashida komai ita za su aika ko su saka. Khadeeja tana son ta tsawatar musu amma tana tsoron abinda ubansu zai ce tunda ta ga sun ɗan sami natsuwa babu wata hatsaniya, ba ta so ta ja rigima. Don haka haka ta zuba musu ido; abu kaɗan sai a ƙwalawa Rashida kira ko da kuwa aikin Khadeejan take yi dole ta bari ta je ta yi musu yanda suke so.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 31st Octoba 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 31st Octoba 2025

    Fassarar huɗubar Juma’a kai daga Masallaci mai alfarma, ta yau Juma’a 9 Jumadal Ula, 1447 H / 31 October, 2025 M

    Mai Huɗuba: Sheikh Dr. Mahir bin Hamad Almu’aiƙili

    Mai Fassara: Usman Muhammad Ahmad

    Huɗuba ta farko:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Wanda Yake afuwa da yafiya kuma Yake gafarta zunubai, kuma Yake saka wa ma’abota kyautatawa, kuma Yake tunkuɗe musu tsanani da damuwowi, kuma Shi ne wanda Yake talala kuma Yake jinkirtawa don mai laifi ya tuba.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai Yake ba Shi da abokin tarayya, Tsarkakakke daga tawaya da aibuka Wanda Ya ce: ((Haƙiƙa kuma Mun halicci sammai da ƙasa da abin da yake tsakaninsu cikin kwana shida, kuma wata gajiya ba ta shafe Mu ba)).

    Kuma ina shaidawa lallai Annabinmu kuma shugabanmu Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa, ma’abocin tafkin nan da za a tuzga masa, da matsayin nan da za a masa baiwarsa, duk wanda ya masa biyayya ya tsira, kuma duk wanda ya saɓa masa za a jefa shi a wuta, Allah Ya yi salati a gare shi, da alayensa, da sahabbansa, da matansa, da waɗanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar da halittu za su koma zuwa ga Ubangijinsu a cikinta, kuma Ya yi masa sallama mai yawa.

    Bayan haka:

    Ya ku taron muminai! Ina muku wasici da ni kaina da tsoron Allah, ku ji tsoron Allah Maɗaukakin Sarki kuma ku masa biyayya, kuma ku sani cewa a gaba gare ku akwai mutuwa da ƙabari, da tashi daga ƙabari da taron filin alƙiyama da sakamako, wasu za su kasance cikin ni’ima da farin ciki, wasu kuma za su kasance cikin azaba da halaka – Allah Ya tsare mu – ((Lallai masu taƙawa suna cikin gidajen aljanna da ƙoramu () A mazauni na gaskiya a wurin Mai mulki, Mai iko)).

    Ya ku al’ummar musulmi!

    Lallai zuciya ita ce abin da Ubangiji Yake la’akari da shi daga bawa, don haka, duk wanda ya haɗu da Allah da zuciya kuɓutacciya, to haƙiƙa ya rabauta kuma ya tsira, kuma duk wanda ya haɗu da Shi da zuciya mara lafiya, to haƙiƙa ya taɓe kuma ya yi asara, kuma cututtukan zukata suna da yawa, kuma daga cikin mafi hatsarinsu akwai cutar ƙeƙashewa, saboda ma’abocin ƙeƙasasshiyar zuciya, yana kawar da kai daga tuba da komawa zuwa ga Allah, har ma a lokacin saukar bala’i da masifa, sai zuciyarsa ta zama makiyaya ce ta Sheɗan, kuma ba ta karɓar wa’azozin Alƙur’ani.

    Allah Maɗaukaki Yana cewa: ((Kuma lallai Mun aika da (manzanni) zuwa ga al’ummomin da suka gabace ka, sai Muka ɗora musu tsananin talauci da cutuka ko sa ƙasƙantar da kai To me ya hana lokacin da musibarmu ta zo musu, su ƙasƙantar da kai? Sai dai kuma zukatansu ne suka ƙeƙashe, Shaiɗan kuma ya ƙawata musu abin da suka kasance suna aikatawa)), kuma Allah Mai girma da ɗaukaka Ya ce: ((To tsananin azaba ya tabbata ga masu ƙeƙasassun zukata da ba sa ambaton Allah. Waɗannan suna cikin ɓata mabayyani)).

    Kuma daga cikin sabuban tausasan zuciya da khushu’inta akwai dawwama a kan ambaton Allah, da tuntuntuni cikin ayoyinsa, da tuna mutuwa da magaginta, da ƙabari da matsansa da duhunsa, da ziyartar maƙabartu, da nazari game da lamuran ranar alƙiyama, ya zo a cikin littafin Ɗabaƙatul Hanabila cewa, wani mutum ya ce wa Imamu Ahmad: “Ta yaya zuciyata za ta yi taushi?”, sai ya ce: “Ka shiga maƙabarta, kuma ka shafa kan maraya”.

    Ya ku ‘yan’uwa masu imani!

    Ita rayuwa gajera ce duk yadda ta yi tsawo, kuma kwanakinta ‘yan kaɗan ne ko yaya suka yawaita, mai dace shi ne wanda ya rayu a cikinta a kan biyayya ga Ubangijinsa, kuma ya yi guzuri a cikinta don ranar haɗuwa da Mahaliccinsa, asararre kuwa, shi ne wanda ya bi son zuciyarsa, kuma ya yi burace-buracen samun kyakkyawar sakamako a wajen Allah, har mutuwa ta afka masa alhali yana cikin gafalarsa.

    Kuma bai mata shiri da aiki nagartacce da zai zama sababin kuɓutarsa ba, kuma masu barin wannan duniya iri biyu ne: Mamaci da zai huta daga wahalar wannan gida ta duniya, ya isa zuwa ga hutu a gidan matabbata, da kuma mamaci da bayi da ƙasa za su huta daga sharrinsa, kuma zai tafi ne zuwa ga mammunan makoma, kuma tur da makwanci.

    Hadisi ya zo a Sahihu Muslim, daga Abu Ƙatada Allah Ya ƙara masa yarda cewa: Lallai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya bi ta wajen wata gawa, sai ya ce: (Wanda zai huta, da wanda za a huta daga gare shi), sai suka ce: Me kake nufi da wanda ya huta da wanda aka huta daga gare shi? Sai ya ce: (Bawa mumini zai huta daga cutarwar duniya da wahalarta zuwa rahamar Allah, shi kuma fajirin bawa bayi da ƙasa, da bishiyoyi, da dabbobi za su huta daga gare shi).

    Ya ku ‘yan uwa masu imani!

    Idan mutum ya mutu, to haƙiƙa alƙiyamarsa ta tsaya, domin ƙabari shi ne farkon matakan lahira, Allah Ya sanya shi ya zama wa’azi da izina, wacce zuciya za ta tausasa da ita, kuma ta tunkuɗe gafala, ta kuma taimaka wurin ƙoƙarin aikata ɗa’a, don haka, babu abin da zai amfanar da mutum a ƙabarinsa face aikinsa, hadisi ya zo a Bukhari da Muslim cewa: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Abubuwa uku ne suke bin mamaci, sai biyu su dawo, ɗaya kuma ya wanzu tare da shi: Iyalansa da dukiyarsa da aikinsa za su bi shi, sai iyalansa da dukiyarsa su dawo, sai aikinsa ya tsaya tare da shi)).

    Don haka ne Usman Allah Ya ƙara masa yarda ya kasance idan ya tsaya a kan ƙabari, sai ya yi kuka, har sai ya jiƙa gemunsa, sai aka ce da shi: Kana tuna aljanna da wuta ba ka kuka, amma kana kuka saboda wannan? Sai ya ce: Lallai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Ƙabari shi ne farkon matakan lahira, idan ya tsira a cikinsa, to abin da yake bayansa ya fi shi sauƙi, idan kuwa bai tsira ba, to abin da yake bayansa ya fi shi muni). Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Ban taɓa ganin wani abu mai firgitarwa ba face ƙabari ya fi shi firgitarwa). Tirmizi ne ya rawaito a Sunan ɗinshi.

    Ƙabari ya fi shi firgitarwa; saboda mutum yana kasancewa a cikinsa shi ɗaya tilo, ba tare da aboki, ko masoyi, ko mai ɗebe kewa, ko abokin zama ba, kuma akwai matsa a cikinsa, da akwai wani da zai kuɓuta daga wannan matsar, da Sa’adu ɗan Mu’azu ya kuɓuta daga gare ta.

    Ƙabari ya fi shi firgitarwa; saboda akwai fitina a cikinsa, kamar fitinar Dujal koma wacce ta fi ta tsanani, ƙabari ya fi shi firgitarwa; saboda shi ko dai ya zama dausayi ne daga cikin dausayoyin aljanna, ko kuma rami ne daga cikin ramukan wuta – Allah Ya tsare mu – saboda haka, duk wanda ya kasance mai kyautatawa, to ƙabarinsa zai zama yalwa da farin ciki a gare shi, duk kuwa wanda ya kasance mai mummunan aiki, to zai zama kewa da baƙin cikin da damuwa a gare shi.

    Hadisi ya zo a Bukhari da Muslim, Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Shi bawa idan aka sanya shi a ƙabarinsa, kuma abokansa suka juya suka tafi suka bar shi, har ma zai na jin ƙaran takun takalmansu, sai mala’iku biyu su zo masa, sai su zaunar da shi, sai su ce da shi: Me ka kasance kana cewa game da wannan mutumin, wato Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi?

    Sai ya ce: Na shaida cewa shi bawan Allah ne kuma Manzonsa, sai a ce da shi: Ka duba mazauninka a wuta, Allah Ya musanya maka shi da wani mazauni a aljanna), Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare ya ce: (Sai ya gan su gaba ɗaya, amma kuma kafiri ko kuma munafiki sai ya ce: Ban sani ba, na dai kasance ina faɗin abin da mutane suke faɗi ne, sai a ce da shi: Ba ka sani ba, kuma ba ka karanta ba, sannan sai a dake shi da guduma ta ƙarfe da ƙarfi a tsakanin kunnuwansa biyu, sai ya yi ihu da ƙarfi ihun da duk wanda yake kusa da shi zai ji ban da mutane da aljanu).

    Don haka ne ya zama daga cikin shiriyar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi akwai neman tsari daga azabar ƙabari a kowace salla, kamar yadda ya zo a Sahihu Muslim, daga hadisin Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda cewa: Lallai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Idan ɗayanku ya yi tahiya, ya nemi tsarin Allah daga abubuwa guda huɗu, ya ce: Ya Allah ina neman tsarinka daga azabar wutar jahannama, da azabar ƙabari, da fitinar rayuwa da mutawa, da sharrin fitinar Dujal).

    A’uzu billahi minsh-shaiɗanir-rajim: ((Har sai idan da mutuwa ta zo wa ɗayansu zai ce: “Ubangijina, Ku mai da ni (duniya) mana  “Don in yi aiki na gari game da abin da na bari (a rayuwata).” Ina! Lalle wannan kalma ce da yake faɗin ta (da bakinsa). A gabansu kuwa akwai shamaki har zuwa ranar tashinsu Sannan idan aka busa ƙaho to fa babu wata dangantaka (mai amfani) a tsakaninsu a wannan ranar, kuma ba za su tambayi juna ba

    To waɗanda ma’aunansu suka yi nauyi waɗannan su ne masu babban rabo. Waɗanda kuwa ma’aunansu suka yi sakayau waɗannan su ne waɗanda suka yi asarar kawunansu, suna masu dawwama a cikin (wutar) Jahannama)). Allah Ya albarkace mu da Alƙur’ani da sunna, kuma Ya amfanar da mu abin da ke cikinsu na ayoyi da hikima, ina faɗin abin da kuke sauraro, kuma ina nema mana gafarar Allah daga kowane zunubi da laifi, don haka ku nemi gafararsa, lallai Shi Ya kasance Mai gafara ne Mai jin ƙan.

    Huɗuba ta biyu:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, dukkan yabo ya tabbata ga Allah Mai tabbatar da zukata, Mai gafarta zunubai, ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah Shi, kaɗai Yake ba Shi da abokin tarayya, Mai yaye damuwa, kuma ina shaidawa lallai Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da Alayensa da Sahabbansa, da aminci mai yawa.

    Bayan haka, ya ku taron muminai!

    Lallai a cikin ziyartar maƙabartu akwai wa’aztuwa da ɗaukan izina da suke zaburar da mutum a kan tsoro da fargaba, da kuma gaggawa wurin ɗa’a da aiki, kuma duk wanda ya ji tsoro zai yi gaggawa, kuma duk wanda ya yi gaggawa zai kai ga matsayin da yake fata, saboda haka ne Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya kwaɗaitar game da ziyartar maƙabartu don wa’aztuwa da ɗaukar izina, ya zo a cikin Musnad na Imamu Ahmad cewa: Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce: (Na kasance ina hana ku ziyartar ƙaburbura.

    to ku ziyarce su domin za su tunatar da ku lahira), kuma ziyartar maƙabartu yana da hukunce-hukunce da ladubba, daga cikinsu akwai yin addu’a ga mamata, domin ƙaburbura cike suke da duhu, amma Allah yana haskaka su sakamakon addu’ar salihai daga cikin bayinsa, ya zo a cikin Sahihu Muslim daga hadisin Abu Huraira Allah ya ƙara masa yarda cewa: “Wata mata baƙa ta kasance tana hidima a masallacin Annabi, sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya daina ganinta, sai ya tambayi inda take, sai suka ce: ta rasu, sai ya ce: (Me ya sa ba ku sanar da ni ba?)

    Kamar dai sun raina lamarinta, sai ya ce: (Ku nuna min ƙabarinta), sai suka nuna masa, sai ya yi mata salla, sannan ya ce: (Waɗannan ƙaburbura a cike suke da duhu ga ma’abotansu, kuma lallai Allah Maɗaukaki yana haskaka musu sakamakon addu’ata gare su), kuma ya kasance daga cikin shiriyarsa tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi, idan ya zo maƙabarta, yana cewa: (Assalamu ala ahlid diyari minal muminina wal musulmin, wa yarhamullahul mustaƙdimina minna wal musta’akhirin, wa inna insha Allahu bikum lalahiƙun), Muslim ne rawaito shi.

    Ya ku taron ‘yan-uwa!

    Lallai ƙaburbura suna da alfarma, don haka ba ya halatta ga mutum ya taka su, ko ya zauna a kansu, ya zo a cikin Sahihu Muslim cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce: (Mutum ya zauna a kan wuta ta ƙone tufafinsa har ta kai ga fatarsa, shi ya fi alheri gare shi sama da ya zauna a kan ƙabari).

    Haka kuma, Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya hana fuskantar ƙaburbura yayin salla, da riƙar maƙabartu a matsayin wurin salla, ya zo cikin Bukhari da Muslim daga Aisha Allah ya ƙara mata yarda cewa: “lallai Ummu Habiba da Ummu Salama Allah ya ƙara musu yarda sun ambaci wani coci da suka gani a Habasha mai ɗauke da hotuna a cikinsa, sai suka ba da labarinsa wa Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi, sai ya ce: (Lallai su waɗannan mutanen idan wani mutumin kirki ya mutu a cikinsu sai su gina masallaci a kan ƙabarinsa, sannan su zana waɗancan hotunan, kuma waɗannan su ne mafiya sharrin halitta a wurin Allah a ranar alkiyama).

    Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce: (Ku saurara! lallai waɗanda suka gabace ku sun kasance suna riƙar ƙaburburan annabawansu da salihansu a matsayin masallatai, lallai na hane ku daga yin hakan). Muslim ne ya rawaito shi.

    Ya ku bayin Allah! Kuma hakan ya kasance ne saboda lallai shi wuce iyaka game da ƙaburburan salihai yana kai mutum ga yin shirka da Allah, ga babban malamin tafsirin nan, Abdullah ɗan Abbas Allah ya ƙara musu yarda, yana faɗi a ƙarƙashin fassarar faɗin Ubangiji Maɗaukaki: ((Kuma suka ce: kada ku bar ababen bautarku, kuma kada ku bar Wadda da Suwa’a da Yagusa da Ya’uƙa da Nasra)), ya ce:

    “Waɗannan sunaye ne na wasu mutane salihai daga cikin mutanen Annabi Nuhu, yayin da suka mutu, sai Shaiɗan ya yi wahayi ga mutanensu cewa su kafa hotunansu a wuraren da suke zama, kuma su sa musu sunayensu, sai suka yi haka, ba tare da suna bauta musu ba, har sai da waɗannan suka mutu, kuma ilimi ya bace, sai aka fara bauta musu”. Bukhari ne ya rawaito shi.

    Saboda haka, ya kai bawan Allah! ba ya halatta a girmama ƙaburburan salihai, ko a yi gini a kansu, bare kuma a riƙa kewaye su da ɗawafi, ko yanka ko bakance dominsu, ko kiran ma’abotansu, ko neman agaji a wajensu, a neman biyan buƙatu ko yaye damuwa, don haka mu ji tsoron Allah ya ku Musulmi, kuma mu taƙaita da abin da aka shar’anta ziyartar ƙaburbura saboda su, na wa’aztuwa da ɗaukan izina, da sallama ga mamata, da yi musu addu’a, kuma kada mu ƙirƙiro wani abu da zai fusata Ubangiji a wurin.

    Haƙiƙa ya zo cikin Musnad na Imām Ahmad cewa, Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce: (Na hana ku ziyartar ƙaburbura, to ku ziyarce su, amma kada ku faɗi abin da zai fusata Ubangiji), a wata ruwayar kuma: (Amma kada ku faɗi magana marar kyau), wato: maganar banza, kuma bai dace ga wanda ya je maƙabarta ya shiga cikin zancen duniya ba, ko yin dariya da barkwanci, bari dai, abin da ya dace shi ne ya yi tunani game da halin ma’abota ƙaburburan, haka kuma, ana so ya yi tunani a kan halinsa da makomarsa, da kuma cewa shi ma mai tafiya ne zuwa wurin da suka tafi.

    Sannan ku sani, ya ku taron muminai cewa, lallai Allah Ya umarce ku da wani umarni mai daraja wanda Ya fara da kansa, sai Ya ce: ((Lallai Allah da mala’ikunsa suna yin salati wa Annabi. Ya ku waɗanda kuka yi imani, ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

    Ya Allah Ka yi salati ga Annabi Muhammad da matansa da zuriyarsa kamar yadda Ka yi salati ga iyalin Annabi Ibrahim, kuma Ka yi albarka ga Annabi Muhammad da matansa da zuriyarsa kamar yadda Ka yi albarka ga iyalan Annabi Ibrahim, lallai Kai ne Sha-yabo Mai girma.

    Ya Allah, Ka ƙara yarda da halifofi shiryayyu, Abubakar da Umar da Usman da Ali, da sauran sahabbai da tabi’ai, da waɗanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar alkiyama, kuma Ka haɗa mu tare da su cikin afuwarka da karamcinka da kyautarka, ya Mafi tausayin masu tausayi.

    Ya Allah, Ka ɗaukaka Musulunci da Musulmai, Ka sanya wannan ƙasa ta zama mai aminci da kwanciyar hankali da wadatar arziki da yalwa, da sauran ƙasashen Musulmai.

    Ya Allah, Ka amintar da mu a ƙasashenmu, Ka shiryar da shugabanninmu da majiɓinta al’amuranmu, kuma Ka ƙarfafi shugabanmu kuma jagoranmu da gaskiya.

    Ya Allah Ka datar da shugabanmu hadimin masallatai biyu masu alfarma da gaskiya, tare da magajinsa amintacce zuwa ga abin da ɗaukaka ne ga Musulunci da gyaruwar Musulmai, da kuma abin da alheri ne ga ƙasa da mutane, tare da dukkan shugabannin musulmai.

    Ya Allah, Ka kiyaye mana addininmu, da shugabancinmu da tsaronmu, ya Allah Ka datar da jami’an tsaronmu da sojojinmu masu tsaro a kan iyakoki da fagage.

    Ya Allah, Ka tabbatar da aminci da zaman lafiya da kwanciyar hankali da nutsuwa ga ‘yan-uwanmu a Falasɗinu.

    Ya Allah Ka kiyaye Masallacin Ƙudus, kuma Ka sanya shi ya kasance mai ɗaukaka har zuwa ranar alkiyama.

    Ya Allah, Ka yaye damuwar masu damuwa daga cikin musulmai, Ka kwaranye baƙin cikin masu bakin ciki, Ka biya bashin waɗanda ake bi bashi, kuma Ka warkar da marasa lafiya daga cikinmu da na sauran musulmai.

    Ya Allah, Ka sanya ƙaburburanmu su zama mafi alherin masauƙanmu bayan mutuwa, Ka sanya su su zamto dausayi daga cikin dausayoyin aljanna, saboda rahamarka, ya Mai ni’imtarwa, ya Ma’abocin ɗaukaka da girma.

    Ya Allah, Ka gafarta wa Musulmi maza da mata, da muminai maza da mata, rayayyunsu da matattu.

    ((Ya Ubangijinmu! Ka ba mu mai kyau a duniya da mai kyau a Lahira, kuma Ka tsare mu daga azabar wuta!).

    ((Ya Ubangijnmu! Ka karɓa daga gare mu, lallai Kai Mai ji ne kuma Masani. Kuma Ka karɓi tubanmu lallai Kai ne Mai yawan karɓar tuba kuma Mai jin ƙai)).

    ((Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka Ubangijin buwaya game da abin suke siffanta Shi da shi () Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni () Kuma dukkan yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai)).

    Karanta Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 15th August 2025

    Edita @rumasau-kallamu

  • Taron Makon Hausa FCE Bichi 23 Oktoba 2025

    Taron Makon Hausa FCE Bichi 23 Oktoba 2025

    A ranar Alhamis 23 ga watan Oktoba 2025, Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Bichi (FCE Bichi) ta gabatar da taron makon Hausa karo na biyu don tunawa da shahararren mai karanta littattafai a radiyo, marigayi Ahmad Isah Koko. Taron ya gudana ne a babban ɗakin taro da ke Kwalejin.

    Taron ya samu halartar manyan marubuta ƙagaggun labarai irin su Ɗan Azumi Baba Ceɗiyar ‘yan gurasa, Nasir NID, Abdul’aziz Sani Madakin Gini, da sauransu. Haka kuma manyan malaman da masu gabatar da shirye-shirye a gidajen radiyo daban-daban sun samu halarta.

    Bayan gabatar da taƙaitaccen tarihin rayuwar marigayi Ahmad Isah Koko da na shirinsa na Rai Dangin Goro, an gudanar da shirye-shirye na al’adun Hausawa sannan wasu daga cikin marubuta sun yi sharhi a kan wasu daga cikin rubuce-rubucensu.

    Farfesa Isa Mukhtar daga jami’ar Bayero Kano, Ya gabatar da maƙala mai taken Gudunmawar Ƙagaggun Labarai Wajen Koyar da Tarbiyyar Al’umma.

    A ƙarshe an ba da ƙyaututtukan girmamawa ga iyalan marigayi Ahmad Isah da kuma sauran mashahuran mutane.

    RMK

     

  • Baɗi Ba Rai Kashi Na Biyu

    Baɗi Ba Rai Kashi Na Biyu

    Episode 2
    A short story by
    Sakina Yazid (Innar su Amal)

    Mutanen da suka fara dawowa daga maƙabarta ne suka gan ta, don haka ƙanin mahaifinta ya kama hannunta suka koma gidan tana biye da shi kamar wata marar hankali.

    Suna shiga farfajiyar gidan ta turje, ta ƙi ƙarasawa cikin parlor. Nan aka yi wa Ummanta magana inda suka fito ita da Maman Misbahu da ma wasu matan waɗanda suka haɗa da ƙawar Farida, Rabi’a wadda isowarta kenan.

    Ummanta ta ƙarasa kusa da ita ta kama hannunta cike da kulawa tace ‘Farida ki dangana mana, Allahn da ya karɓe shi zai ba ki wani. Ki taho mu shiga gida mu zauna. Ta fizge hannunta daga hannun Ummu tace ‘Ba zan shigo ba, ba zan sake shiga gidan nan ba in sha Allah.’

    Zuwa lokacin ragowar mazan sun ƙaraso har da Misbahu da babansa da Baban Farida. Suka tsaya suka yi cirko-cirko. Maman Misbahu ta ƙaraso ta dafa kafaɗarta tace ‘Idan ba ta son nan ɗin ai sai ku wuce gida. Ta sa hannu ta ture hannun Maman Misbahu daga jikinta tana mata kallo na ƙyamata.

    Ta dubi Umma ta tace ‘Ba zan je gidan ba, wane gidan zan je? Ba kwa buƙata ta ai tunda ba zan sake zama da Misbahu ba. Dole ya sake ni tunda ya kashe min yaro, kin ga kuma kuma ke da Abba ba kwa son bazawara. Don haka ba zan je muku gida ba, in sha Allah daga yau ba za ku sake ganina ba balle na janyo muku abun kunya.’

    Duk wanda yake wajen jikinsa ya yi sanyi, kowa ya kasa magana. Maman Misbahu ta daure tace ‘Ki yi haƙuri Farida a zauna a bi abin a hankali. Ta yi murmushi yaƙe ta juya tana fuskantar Maman Misbahun sannan tace ‘Dole ki ce na yi haƙuri tunda ke ɗanki yana raye, amma ni ya kashe min nawa ɗan.

    Kuma na san kamar yanda kika saba kariya za ki ba shi, sai dai ina miki albishir da cewa ba zai rayu har abada ba. Za mu tsaya a gaban Allah wanda shi kaɗai zai iya yi mana adalci. Ta juya ta yiwo tattaki ta ƙaraso gaban Misbahu ta tsaya, ta zuba masa ido har sai da ya gaji ya sauke nasa ƙwayar idon.

    Kana kallonsa ka san a jigace yake sannan kuma cikin tashin hankali. Ta share ɗigon hawayen da ya gangaro a fuskarta tace ‘Yanzu ka ji daɗi ko Misbahu? Ɗanka, kuma ɗana guda ɗaya ka kashe shi ka huta. Burinka shi ne ka cuzguna min ka saka ni a cikin ƙunci kawai saboda ni na nuna maka soyayya na aure ka. Yanzu ka ga sai ka je ka auri Shahida ka sake rayuwa.

    Na san cewa iyayenka za su ba ka kariya kamar yanda suke yi idan ka yi min wulaƙanci na kai ƙara, kuma na san duk taron mutanen nan da suke kallonmu ba za su iya yi min adalci ba tunda suma duka sun yarda da cewa duk abinda namiji ya yi ado ne; mace ita ce take laifi. Sai dai ina so ka sani daga rana irin ta yau duk lokacin da na yi sujuda sai na kai ƙararka wajen Allah; Allah ya yi maka abinda ka yi min kuma Allah ya saka mana ni da ɗana da ka kashe.’

    Ya runtse ido saboda yanda kalmar ka kashe ɗana take sukansa a zuciya. Yana matuƙar son Adnan, ya za a yi a ce shi ya kashe shi. Har yanzu ma ƙoƙari yake ya yarda cewa Adnan ɗin suka kai maƙabarta suka binne. Ta yi murmushi sannan ta cigaba ‘Ina jiran ka aiko min takardar saki na zuwa gobe. Ban san hukuncin da zan ɗauka ba amma tabbas duniyar nan ba za ta ɗauke mu ba ni da kai idan dai ka bari na sake ganinka ba tare da ka sake ni ba.

    Na tsane ka, bana fatan na sake ganinka a rayuwata. Ina fatan Allah ya hana ka farin ciki kamar yanda ka hana ni da kai da duk wanda yake goya maka baya. Ta matsa daga gabansa ta nufi waje; Ummanta ta bi bayanta da gudu ta sha gabanta tace ‘Ina za ki Farida, ki bari na ɗauko jaka ta mu tafi gida.’

    Ta kalleta tana share hawaye tana cewa ‘Ban san inda zanbi ba, amma wallahi ba za ni gidanku ba balle na janyo muku abun kunya a ce ‘ƴarku ta ƙi zaman aure. Na san dai ko gidan marayu na je za a karɓe ni a ba ni wajen da zan zauna na ƙarasa rayuwata wadda ina ji a jikina ba ta da yawa.’

    Ta raɓa ta gefen Umman ta wuce ta nufi gate. Umma ta tsaya a nan tana share hawaye ba tare da ta san abin yi ba. Gaɓa ɗaya mutanen da suke wajen duk an kasa motsi, kowa binta yake da kallo ana share hawaye. Rabi’a ce ta fito daga cikin matan nan tana riƙe da jakarta cikin hanzari ta ƙarasa ta dafa Farida; wadda ta kusa gate ta baya.

    Ta juya ta kalleta yayinda Rabi’an ta kama hannuwan Farida ta riƙe tana cewa ‘Ki zo mu je gidana Farida, don Allah ki zo mu tafi. Babu wanda zan bari ya ganki, kin ga gobe ma za mu wuce Abuja ba za su sake ganinki ba.’

    Ta kalli hannuwansu waɗanda suke a haɗe, cikin hawaye tace ‘Ba ki yi fushi da ni ba Rabi; ke da aka saka ni na daina kula ki saboda kada ki aure min miji kuma yanzu ba kya tsoron na biki gidanki, gidan mijinki? Ki bar ni kawai na shiga duniya Rabi, na gaji da kowa wallahi.’

    Ta jinjina hannuwansu tace ‘Ba zaki shiga duniya ba Farida, ai ni ba ki gaji da gani na ba ko? Shiru ta yi ta kasa ba ta amsa, don haka ta ja hannunta suka fice daga farfajiyar gidan kowa yana kallon su.

    ƘARSHE….

    EPILOGUE

    Mata da yawa suna zaune a gidajen aurensu cikin cin zarafi da ƙunci ba lallai duka ba. Wasu zagi ne da rashin girmamawa da kuma sauran nau’o’i na emotional abuse.

    Iyayensu ne ya kamata su ba su kariya a irin wannan lokacin to amma haƙuri kawai suke ba su; suna kuma mayar da su cikin halin da yake firgita nutsuwarsu. A mafi yawancin lokuta ma idan iyayen suka saka baki aka zauna da mijin matsalar za ta warware, sai dai idan iyayen ba su jajirce ba. To amma ba za a ko gwada ba. Haka ake zuba musu ido suna rayuwa cikin ƙunci – alone, sad and depressed.

    Iyayensu ba za su taimaka musu ba.

    Al’umma ba za su taimaka musu ba.

    But idan depression ya yi musu yawa har ya janyo suka aikata wani abu na assha a lokacin ne za ka san every single member of the society yana kallon su; domin kuwa za a yi assembly a tsine musu albarka.

    Ban sani ba, ba mu san depression ɗin ba ne ko kuma ba mu yarda yana iya saka mutum ya cutar da kansa ba ko ya cutar da wani. Da sun yi magana sai mu ce su yi haƙuri. Su fita daga harkar mijin su yi zaman ‘ƴa’ƴa. Idan sun matsa mu ce ƙaddararsu kenan.

    Haka za su ƙare rayuwarsu cikin damuwa. Babu abinda ban ji ba from real people
    “Mamaki nake idan na ga mutane suna walwala, su ba su san a cikin matsala ake ba ne?”

    “Mahaifina yace kada na kashe aurena na ba shi kunya, na yi zamana.”

    “Mahaifiyata tace ban isa na janyo mata magana a tsakanin kishiyoyi ba, babu me bazawara ba za a fara a kanta ba.”

    “Na rasa yanda zan yi da shi Anti, duk wanda na gayawa sai a ce na yi haƙuri. An ma rasa me yi masa ko da nasiha ne. To har tsawon yaushe ne zan yi haƙurin? Sai na mutu? Shikenan daga na yi aure nayi sallama da jin daɗi har sai na koma ga Allah?”

    Waɗannan maganganun fa real people ne suke faɗa, very young women; all less than 30.

    Are we alright? Is this fair? Idan muka cigaba da bari ‘ƴa’ƴanmu da ƴan uwansu suna azabtuwa a dalilin aure tabbas ba mu yi wa aure adalci ba kuma ba mu yi wa musulunci adalci ba.

    Ina mafita?

    Innar su Amal.

    Karanta Baɗi Ba Rai Kashi Na Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Baɗi Ba Rai Kashi Na Ɗaya

    Baɗi Ba Rai Kashi Na Ɗaya

    A short story by
    Sakina Yazid (Innar su Amal)

    Kamar duk lokacin da irin wannan abun ya faru yau ɗin ma haka ta shiga gidan cike da tashin hankali; duk da dai ta daina kukan ta share hawayenta. Hawayen iya na fuskarta ne kawai ta share amma tabbas ta san ba za ta iya daina kukan zuciya ba, ko za ta daina to ba ta san lokacin da za ta daina ɗin ba.

    Parlor ɗin shiru, da alama Umma da kuma su Maimuna suna ɗaki; wataƙila suna sallar la’asar domin lokacin sallar ne. Kai tsaye ta wuce ɗakin Umman ta tura ƙofar ta shiga da sallama.

    A kan dadduma ta hango Umman tana zaune tana azkar. Kallon da Umman ta yi mata ya sa duk wani karsashi da ta taho da shi ya zube kafin ta ƙarasa gabanta. Ta riga ta san amsar da Umman za ta ba ta guda ɗaya ce; wato wadda ta saba bata. Zuwa yanzu ma gani take yi gaba ɗaya kamar Umman nata ta ƙosa kuma ta gundura da jin matsalolinta.

    To amma idan ba wajen Umman ba ina za ta? Da wa za ta yi magana ta ji sanyi a ranta? Duk da dai yin maganar bai taɓa samar mata mafita ba. An riga an hane ta da yin ƙawaye tun lokacin da aka yi mata aure, don haka ta fita harkar ƙawayen har su ma suka rabu da ita. Mutum biyu ne a rayuwarta iyayenta da kuma mijinta Misbahu; su suka fi mata kowa muhimmanci a rayuwarta kuma su ne suke neman tura cikin halaka.

    Cikin sanyin jiki ta ƙarasa gaban Umman ta sauke goyon Adnan ta zaunar da shi; nan da nan kuwa ya rarrafa yana dariya ya haye jikin Umman wadda ta ɗauke shi tana dariya.‘Umma ina wuni.’ Ta faɗa cikin sanyin murya. Ta harareta sannan ta amsa ‘Lafiya ƙalau. Yanzu kuma me aka yi na ganki fuska duk a koɗe?’

    Ta sunkuyar da kai ta yunƙura ta haɗiye malolon da ya tokare mata ƙirji, ta buɗe baki da ƙyar tace ‘Umma duka na ya yi, kuma ya gaya min maganganu na wulaƙanci fiye da yanda ya saba gaya min. Ga neman mata Umma, a gabana zai yi waya da budurwa ya saka a loudspeaker wai na ko yi soyayya.’

    Cikin damuwa Umman ta sauke Adnan wanda ya kama rarrafe a tsakar ɗakin, ta dube ta cikin natsuwa kamar me nazari sannan tace ‘To in dai maganganu ne menene ba ki ji ba a bakin Misbahu? Ai tuntuni nace ki fita harkarsa ki mayar da hankali wajen wannan yaron da Allah ya ba ki. Kuma yau ya aka yi kika biye masa har ya kai miki duka?’

    Ta share hawayen da ya gangaro a kan fuskarta, ta yi ajiyar zuciya a karo na babu iyaka sannan tace ‘Hayaniyarsa ya gama yi ya shiga ɗaki ya kwanta shi ne na shiga maƙota dubiya. Shi ne ina dawowa ya hau zagina, kuma na ce ya yi haƙuri shi ne ya mammare ni yace wai zuwa na yi maƙota na kai gulmarsa.’

    Nan da nan ta sake fusata tace ‘To ke me ya kai ki maƙota kin riga kin san halin mutumin nan? Na riga na gaya miki ki fita harkarsa ki bar shi da mugun halinsa. Idan ba ya son shiga maƙota to ai sai ki bari. Umma bai taɓa hana ni shiga ba wallahi. Kuma na gaya miki idan ya tashi wulaƙancinsa bana ma sanin me na yi masa, tunda ko na saba yin abu wataran sai kawai ya hau zagina a kai.’

    ‘To ai sai ki kiyaye, tunda kin ga dai mahaifinki da kansa ya yi masa magana kuma yace ya daina. Ki je ki cigaba da lallaɓa shi ki mayar da hankali kan ɗanki. Bawa ba ya wuce ƙaddararsa, wata ƙila ke taki ƙaddarar kenan.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci; Farida tana ta faman share hawaye yayin da Ummanta take faman hidima da Adnan. Jimawa kaɗan tace ‘Umma na gaji da auren mutumin nan wallahi, son shi ya fice min daga rai. Bana son zaman gidansa; idan ina cikin gidan ji nake kamar an saka zuciyata a keji kuma an kunna wuta a cikin kejin. Wallahi Umma wulaƙancin da yake min ya ishe ni.’

    Ta kawar da kai tare da haɗe fuska sannan tace ‘Haƙuri za ki je ki yi, tunda dai mutumin nan babu abinda ya rage ki da shi; ci, sha sutura da sauransu. Ko muma nan kullum cikin hidima yake da mu. Kina kallo ga ƙannenki can a gidajensu amma ke kullum kina tafe kawo ƙara. Ni kaina da kika gani idan da ban yi haƙuri da ubanku ba da yanzu wani zancen ake ba wannan ba.

    Kuma ma idan dai maza ne na yanzu duk haka suke kowanne da tashi matsalar musamman neman matan; idan kin fito ba ki san gidan wanda za ki koma ba. Idan ma kin sami mijin kenan.’

    Haka dai Umma ta ƙare mata faɗa da nasiha sannan ta tursasata ta koma gidan; domin a faɗarta ba ta ma so a ɗaga maganar balle mahaifinta ya ji don ita ma sai ya yi mata faɗa. Don haka cikin matsananciyar damuwa ta goya Adnan suka kama hanya.

    Ƙwaƙwalwarta ta cushe gaba ɗaya; wace irin rayuwa ce wannan? Auren soyayya suka yi da Misbahu amma yanzu ba shi da aiki sai cuzguna mata; duk da dai ba wai kullum ba ne yake mata hakan. Sai suna zamansu lafiya kamar kowanne ma’aurata laifi kaɗan sai ya gaya mata maganganu masu zafi watarana ma ya mammare ta.

    Ga shi ba ta sanin wanne laifi ne za ta yi ya haifar da hakan don haka kullum a ɗari-ɗari take a gidan. In dai haka maza suke to idan ta samu ta rabu da Misbahu ma babu wani auren da za ta sake balle a ce ba a san wa za ta aura ba; tana ji a jikinta zawarci zai fi mata sauƙi da wannan rayuwar da take yi yanzu.

    Tana hango gidan bugun zuciyarta ya ƙara sauri, wata sabuwar fargaba ta shige ta. To amma idan ba nan ba ina za ta? Gidansu ne kawai ragowar gatanta kuma can ta je aka koro ta. Haka ta ƙarasa ta shiga gidan tana fatan idan dai har mutuwa ce za ta raba ta da Misbahu to tabbas ta shirya mutuwa don tana da yaƙinin Allah zai ji tausayin ta.

    Yana kashingiɗe a parlor ɗin a kan 3-seater ta tura ƙofar ta shiga; ƙasa-ƙasa ta yi sallama ta shige ba tare da ta saurari amsa ba. Tana jin ƙwayar idonsa yana bin ta da kallo na wulaƙanci irin wanda ya saba. Sai da ta kai tsakiyar parlor ɗin tana daf da shiga ɗakinta ya daka mata tsawa.

    ‘Daga ina kike? Akuya sarkin yawo.’ Ta ɗan diririce tana shirin komawa da gudu sannan ta dage ta lalubo nutsuwarta cikin in-ina tace ‘Gidanmu na je. Ya sake ƙare mata harara yana jan dogon tsaki ‘Mtsewww!’ Ta bi bango ta shige ɗakin ta turo ƙofar tana fatan kada ya zo yace zai doke ta.

    Haka ta lallaɓa ta yi sallar magriba sannan ta fito ta ɗora abincin dare tun kafin ya nema ya ɗaga mata hankali. Ya riga ya san babu abinda za ayi duk da kai ƙarar tasa da ta yi, don haka da ya fita ma bai dawo gidan ba sai da sha biyun dare ta gota; lokacin ta daɗe da yin bacci.

    A hankali suka ɗan shirya kamar yanda suka saba, sai dai ita duk a firgice take. Zama take na ɗari-ɗari a gidan saboda ba ta san me za ta yi ta tsokano shi ba. A bayan layinsu aka yi haihuwa, kuma da yake ya san maigidan tun jiya ya ba ta izinin zuwa suna da ake yi yau Asabar.

    Wajen 12pm maƙociyarta ta yi mata sallama a kan ta zo su je sunan don ita daga can za ta wuce cikin gari. Nan suka haɗu su uku maƙota suka wuce. Tun da suka shiga layin gabanta yake faɗuwa; akwai gidaje na ƴan jami’a a layin inda wasu ƴan mata ne suke zaman kansu wasu kuma samari.

    Akwai wata yarinya Shahida wadda Misbahu yake nema; ba ta taɓa ganin yarinyar ba amma an tabbatar mata a nan layin gidan yarinyar yake. Don matan layinsu ma sun sha gaya mata sun gan shi da yarinyar ya sauke ta nesa da unguwar. Sun yi magana sau babu iyaka har ma ta gaji; tunda yanzu ma a yanda ake ya gaya mata idan ta ƙara yi masa maganar wata daga cikin ƴan matansa sai ya kora ta gida ya kawo matan gidan ya ga idan akwai wanda ya isa ya hana shi.

    Haka dai ta dafe zuciyarta suka ƙarasa cikin gidan sunan; nan da nan kuma da suka haɗu da matan unguwa ta manta da komai aka ci gaba da hira cikin walwala. Sun kai kimanin awa ɗaya, ‘ƴan matan suka shigo gidan; da yake ba wani sosai aka cika tsakar gidan ba sai da suka tsallake suka zo kusa da Farida sannan suka zauna.

    Suka gaggaisa da mutane da alama wasu daga cikin matan da suke zaune a wajen sun san su. Ita ma Farida ta waiga ta gaisa da su. Suka tambayi maijego aka ce musu yanzu ta shiga canza kaya don haka suka zauna nan aka cigaba da hira.

    Jimawa kaɗan suka jiyo muryar maijego daga parlor tana magana da wasu matan. Ɗaya daga cikin ‘ƴan matan nan wadda take zaune kusa da Farida ta buɗe baki ta ƙwala mata kira bayan ta amsa tace ‘Da Allah ki zo ki nuna min matar masoyina na yi mata kallon ala tsine uwar mai ƙarya; ko da yake dai ya gaya min kalarta.’

    Ta fito daga parlor ɗin tana dariya ta nuna yarinyar tana cewa ‘Shahida ba fa na son wulaƙanci, duka nan babu sa’anki ƴar rainin hankali.’ Aka sheƙe da dariya gaba ɗaya wajen. Farida tana jin an ambaci Shahida ta sha jinin jikinta; ta juya ta kalle ta suka haɗa ido yayin da yarinyar ta tintsire da dariya. Maƙociyarta wadda suka zo tare ta taɓa ta tace ‘Tashi mu tafi Maman Adnan.’

    Suka miƙe a tare, ita ma Shahida ta miƙe tana dariya da kallon raini tana cewa ‘Ashe ma kusa dake na zauna, sannu fa. Mai jego tace ‘Ke Shahida ba fa na son raini… A a ku fa uwayen gidan nan haka kuke wallahi, ba ku iya kula da miji ba sai ikon tsiya. To komai baƙin cikinku sai mun shigo.’ Ta faɗa da shaƙiyanci tana dariya.

    Farida ta ja tsaki, ta raɓa ta gefenta ta wuce, maƙociyarta Anti Amina tana biye da ita. Ta ƙyalƙyale da dariya tace ‘A a fa kada ki bangaje ni idan ba haka ba wallahi na sa a baki red card a daren nan ki kwana gidan father ɗinki. Farida ta shammaci mutanen da suke wajen ta juya ta yi taku ɗaya ta ƙarasa gaban Shahida ta sauke mata mari a kumatunta.

    Nan take wajen ya yi tsit yayinda Shahida ta dafe kumatunta tana fitar da hawaye. Farida ta nuna ta da yatsa tana cewa ‘Idan ke ‘ƴar halak ce ki ba shi umarni kada ya bar ni na kwana a gidan yau.’ Ta sauke yatsan sannan ta cigaba ‘Ko da yake ba zan yi mamaki ba idan ke ɗin ba ‘ƴar halaka ba ce tunda ga shi nan kin mayar da kanki kamar public toilet.

    Kowa ya tashi juyen ƙazantarsa sai ya zo ya haye kanki. Ki bashi umarni yau kada ya bari na kwana a duniyar ba ma a gidansa ba. Ta juya ta fice ba tare da ta saurari kowa ba Anti Amina tana biye da ita. Nan ragowar matan da ke tsakar gidan suka haɗu da maijego suka fara ba wa Shahida haƙuri.

    Ta share hawayenta ta zauna, ta zari wayarta tana cewa ‘Wallahi sai ta gane kurenta, sai na saka ya ci ubanta tunda ta mare ni. Kuma wallahi ita da zaman lafiya da Misbahu har abada, sai na yi ajalin wannan auren nata.’

    Suka cigaba da ba ta haƙuri maijego tana cewa ‘Ki dai yi haƙuri ki bar maganar nan tunda kin ga kece ba ki da gaskiya, Please ki fita harkar ta.’ Ta goge fuskarta ta dubi matan tace ‘Ku yi shiru zan yi waya da Allah.’ Nan da nan suka yi shiru saboda son jin gulma.

    Ta lalubi lambar Misbahu ta danna masa kira; bugu ɗaya kuwa ya amsa yana cewa ‘Ƴan matana ya aka yi ne, har kin…’ Nan take ta rushe da kuka; abinda ya saka shi ya ruɗe ya shiga jero mata tambayoyi ‘Babe me ya faru? Kina ina ne? Ko accident kika yi ne?’
    Ta sassauta da kukan tace ‘Matarka ce ta mareni kuma ta zazzage ni a cikin mutane.’

    Cikin ƙosawa yace ‘Ban gane ba, Farida? A ina kuka haɗu? Ko gidan kika je? Ta sheƙe majina irin na me kuka tace ‘A gidan suna muka haɗu nan kusa da gidanmu, shi ne ƙawarta ta nuna mata ni suka haɗu suka yi min wulaƙanci a cikin mutane kuma ta mammare ni.

    Dole sai fitowa muka yi ni da Ikram saboda kunya. Wai ni take kira public toilet har da cewa ni ba ƴar halaka ba ce. ‘Ya isa, ki daina kukan mana. Kina ina ne na zo yanzu? Sai na ji yanda aka yi, kema kin san ba zan ƙyale ta ba.’ ‘Ni kada ka zo inda nake, ai duk kai ka janyo tunda kai ne kake zuwa kana ba ta labari na har ta sami damar yi min wulaƙanci.’

    Ta tsinke wayar ba tare da ta saurari amsar shi ba, ta mayar da wayar cikin jakarta ta kama hannun ƙawarta suka fice.

    Cike da damuwa Farida ta koma gida; ba ta nadamar marin da ta yi wa Shahida, amma dai tana fargabar haɗuwarta da Misbahu. Don ta san tabbas idan bai mammare ta ba to sai ya yi mata zagi na ƙasƙanci; idan ba ta yi wasa ba ma to sai ya ba ta red card kamar yanda budurwar tasa ta faɗa.

    Haka Anti Amina ta ɗauki lokaci tana ba ta haƙuri sannan ta bar ta ita ma ta wuce nata gidan. Ba ta jima da shiga gidan ba Maryam yarinyar da take mata aiki ta shigo; tunda dama tace mata ta zo bayan 2pm. Ta ji daɗin shigowar tata saboda ta san ko da Misbahu zai shigo yanzun to zai ƙyale ta a ƙalla zuwa lokacin da Maryam ɗin za ta tafi; kafin nan ta samu ta shirya yanda za ta ƙwaci kanta.

    A fusace ya shigo gidan wajen 2:30pm; tunda sai da ya tsaya a wajen Shahida ya lallaɓa ta yayin da ita kuma ta ƙara yi masa fanfo sannan ya huto gidan. A lokacin da ya shiga gidan Maryam tana kitchen tana aikinta yayin da ita kuma Farida take ɗaki tana kwantar da Adnan wanda ya yi barci.

    Ba ta rufe ƙofar ɗakin sosai ba don haka bai ma kula da mutum a kitchen ba ya shige ɗakin. Tana ƙoƙarin yi masa sannu da zuwa ya kama hannunta ya janyo ta daga ɗakin tana turjewa tana tambaya ‘Abban Adnan lafiya kake ja na haka? Ka bari na gyara masa kwanciya mana.’

    Bai saurare ta ba kuma bai fasa jan nata ba, har sai da suka fito ƙofar ɗakin sannan ta samu ta fincike hannunta. Cikin ƙarfin hali tace ‘Wai meye haka Misbahu, ya za ka kama ja na kamar wata yarinya.’

    Ya ɗan ja baya yana mata kallo na takaici da mamaki saboda bai taɓa zaton za ta iya yi masa magana haka ba. Ita kanta ba ta san ina ta samu ƙwarin gwiwar ba amma tabbas tana jin yau ba za ta saurara masa ba.

    Cikin huci yace ‘Ni za ki yi wa rashin kunya saboda ba ki da mutunci ko? Saboda kin haɗu da ƴan iskan ƙawayenki sun hure miki kunne ko?’ Ta sun kunyar da kai tana ja da baya saboda yanda yake nufo ta, sai dai kafin ta yi wani yunƙuri ya kwaɗa mata mari. Tana ƙoƙarin dafe kumatun ya sake kwaɗa mata a ɗayan sannan yace ‘Wace shegiyar ce tace ki mari Shahida? Kuma sannan ki zage ta?’

    Nan da nan hawaye ya wanke mata fuska, cikin ƙunan rai tace ‘Ita ba ta gaya maka abinda ta yi min ba kafin na mare tan, ko kuwa nice wadda ba ni da gata da za ka zo kana mari na saboda karuwa? Ya yi wata ‘ƴar dariyar mugunta sannan yace ‘An mare ki ɗin, ko akwai abinda za ki iya yi a kai? Shashasha kawai.’

    Cikin kuka tace ‘Babu abinda zan iya yi amma zan cigaba da kai ƙara wajen Allah. Duk wanda ya zalunce ni Allah ya isa ba zan taɓa yafewa ba.’

    A fusace ya fara ƙoƙarin kwance belt ɗinsa yana cewa ‘Lallai yau za ki gane kurenki, ni kike yi wa Allah ya isa saboda ba ki da mutunci? Jikinki zai gaya miki. Kafin ta yi wani yunƙuri ya zabga mata belt ɗin wanda ya bi ta wuyanta ya sauka a saman bayanta. Ta gantsare ta saki wata ƴar ƙara tana ƙoƙarin sosa wajen dukan; wanda tuni ya riga ya yi ja zur ya tashi.

    Ya sake ɗaga belt ɗin ya zabga mata. Ta ja baya kamar za ta faɗi bango ya tare ta; ƙoƙari take ta shiga ɗakinta ta turo ƙofa amma sai da ta wuce ƙofar sannan bangon ya tare ta. A nan ta sulale ta zube saboda zafin dukan da kuma gigicewa. Ya gyara belt ɗin ya riƙe ƙasan yanda ƙarfen belt ɗin zai sauka a jikinta; a daidai lokacin kuma Adnan wanda ya riga ya tashi daga bacci har ya sauko daga kan gadon ya rarrafo ya nufi jikin mamansa yana kuka.

    A lokacin Misbahu ya riga ya ɗaga belt ɗin zai zuba mata; tana ƙoƙarin ɗauke Adnan belt ɗin ya sauka a ƙeyarsa. Nan take jini ya wanke mata jiki yayin da Adnan ɗin ya yi wata gajeriyar ƙara ya faɗa ƙirjinta kamar wanda aka jefa.

    Ta jijjiga shi cikin matsananciyar firgita tana kiran sunansa; a dai-dai lokacin Misbahu ya saki belt ɗin ya nufo kanta yana ƙoƙarin karɓar Adnan ɗin yana cewa ‘Me kika yi masa? Inna lillahi wa Inna ilaihi raji’un!’

    Maryam wadda take tsaye a bakin ƙofar kitchen tana kallon su tana share hawaye ita ma ta zuba ihu ‘Inna lillahi wa Inna ilaihi raji’un!’ Kafin su yi wani yunƙuri ta zura da gudu ta yi waje ta ƙofar kitchen tana faman ihu tana kiran mutane.

    Nan da nan jikin Misbahu ya hau rawa suka miƙe tare da Farida wadda ita ma jikinta yake rawa tana ta wani gunji ta ƙanƙame Adnan saboda yanda hawayenta ya bushe ta kasa kuka. Kai tsaye waje Farida ta nufo rungume da Adnan yayin da shi kuma Misbahu ya juya kan center table inda ya ajiye mukullin motarsa yana cewa ‘Ki tsaya na fito mu kai shi asibiti.’

    Kusan a lokaci guda suka ƙaraso tsakar gidan inda suka ci karo da Maryam mutum uku sune biye da ita; maƙocinsu Dr. Abdul da wani mutum tare da shi sannan kuma da maigadin gidan. Dr. ya sha gaban Farida wadda ko ɗankwali babu a kanta yana cewa ‘Subhanallah! Me ya sami Adnan ɗin?’

    Cikin rawar baki tana waigawa tana kallon Misbahu tace ‘Ya fasa masa kai da belt, ya kashe min yaro. Maryam wadda take share hawaye ta tsomi baki tana cewa ‘Dukanta yake yi da belt ɗinsa wallahi yana ɗagawa ya kwaɗawa yaron, dukansa ya yi da belt ɗin. Shi ne baban nasa.’

    Dr ya ja su suka koma kan baranda sannan ya ba ta umarni ta kwantar da Adnan. Nan ta shimfiɗe shi ta janyo gefen rigar ta ta fara goge fuska ba tare da ta damu da jinin da yake jikinta ba. Ya dudduba shi sannan ya juya ya dubi mutumin da suka zo tare da shi yace ‘Inna lillahi wa Inna ilaihi raji’un! Wannan sai dai a yi haƙuri Allah ya karɓi kayansa.’

    Nan take Farida ta juya ta cakume Misbahu tana cewa ‘Ka kashe min yaro, sai ka kashe ni ni ma. Da ƙyar ya samu ya haɗa hannuwanta ya riƙe tana faman kuka. A hankali kuma kamar wadda aka zarewa laka ta sulale ta zauna kamar me zaman tahiya ta haɗa hannuwanta guda biyu ta rike tana fitar da numfashi a hankali.

    Maryam ta ƙaraso ta zauna a kusa da ita suka yi jugum suna bin mutane da kallo. Mutumin da suka shigo da Dr ya dube shi yace ‘Ai sai an kirawo police tunda ya zama case ɗin accident kenan. Ba tare da ɓata lokaci ba ya fidda wayarsa ya kirawo ‘ƴan sanda, a lokacin ne kuma Misbahu ya sami dama ya koma gefe ya kirawo mahaifiyarsa.

    Jimawa kaɗan ita ma Maryam ta miƙe ta koma cikin gidan ta ɗaukowa Farida hijab ta zo ta saka mata sannan ta kama hannunta ta dangwala a wayarta ta buɗe ta lalubo lambar Ummanta ta kirawo ta. Abinda kawai ta iya gayawa Umman Farida shi ne Adnan ya rasu, ta katse wayar ta riƙe a hannunta suka cigaba da kallon ikon Allah.

    Kusan a lokaci ɗaya ƴan sandan suka iso da mutanen gidan su Adnan, kafin wani lokaci kuma mutanen gidansu Farida suka iso. Mahaifin Adnan shi ya ja ƴan sandan ya sallame su, kusan ma babu wanda ya kula da lokacin da suka sulale suka fice.

    Tunda Umman Farida ta iso take fama da Farida a kan ta shiga cikin gidan su zauna amma ta ƙi, kuma ta ƙi yi wa kowa magana. Don haka suna nan tsaye aka yi wa Adnan sutura aka yi masa sallah yayin da Umma da Maman Adnan suke tsaye sun saka Farida a tsakiya suna lallashinta.

    Ana fita da gawar mata suka fara shigowa gidan domin ta’aziyya, sai dai har zuwa lokacin Farida ta ƙi shiga cikin gidan ga shi magriba ta fara kawo kai. Da yake maƙabartar babu nisa nan da nan aka kai shi aka dawo. Babu wanda ya kula da lokacin da Farida ta sulale ta fice daga gidan ta kama bin hanya.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Gamuwa Da Abokan Gaba Ko Wani Mai Iko 

    Yadda Ake Addu’ar Gamuwa Da Abokan Gaba Ko Wani Mai Iko 

    اللهُمَّ إِنَّا نَجْعَلُكَ فِي نُحُورِهِمْ وَنَعُوذُ بِكَ مِنْ شُرُورِهِمْ
    Allahumma ina naj’aluka fee nuhurihim wana’uzu bika min shururihim

    Ya Allah! Mu Muna sanya Ka a gabansu, kuma Muna neman tsarinka sharracensu.

    اللّهُمَّ أَنتَ عَضُدِي ، وَأَنْتَ نَصِيرِي، بِكَ أَحُولُ وَبكَ أَصُولُ وَبكَ أُقَاتِلُ

    Allahumma anta adudee, wa’anta naseeri, bika ahulu abika asulu wabika ukatilu

    Ya Allah! Kai ne Mai ƙarfafa ni, kuma Kai ne Mataimakina. Da ƙarfinka ne nake yin dabarun yaƙi, kuma da ƙarfinka ne nake kai hari, kuma da ƙarfinka ne nake yin yaƙi.

    حَمَّنَا اللهُ وَنِعْمَ الْوَكِيلُ
    Hammanal lahu wani’’imal wakeelu

    Allah ne Mai isar mana, kuma madalla da Shi abin dogaro.

    Karanta Abin Da Mutum Zai Yi Idan Ya Yi Mafarki Mara Kyau

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Ɗaya

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Ɗaya

    Duk da bai ce mata zai zo yau ɗin ba amma dai haka kawai zuciyarta take gaya mata zai zo tunda an buɗe gari kuma tun wancan lokacin da aka buɗe gari ba su haɗu ba. Ta san dai yana jin haushinta daga yanda yake amsa wayarta amma ta nutsu a zuciyarta cewa zai zo ɗin.

    Tun wuri ta tashi ta yi wanka ta shirya don ya same ta a shirye; sai dai ga mamakinta har azahar tana zaune a parlor tana ta faman duba waya, duk wanda ya buga gate da hanzari take tashi ta buɗe tana saka rai Mustapha ne amma har la’asar bai zo ba.

    Dab da la’asar tana zaune a parlor tana ta faman latsa waya tana duba whatsapp ko ya buɗe saƙon da ta tura masa amma ga mamakinta har zuwa lokacin bai buɗe ba. Mommy ce ta fito daga ɗakinta; har ta kama hanyar kitchen sai kuma ta kula da Khadeeja a zaune a parlor ɗin.

    Ta dawo ta tsaya tace ‘Ya na ganki a nan, ina Nabila PA ɗin taki?’ Ta yi dariya tace ‘Tana can tana abinda ta saba wato bacci. Ta wuce kitchen ta bar ta a nan, jimawa kaɗan ta fito ta dawo parlor ɗin ta zauna a kan three seater daga bangareb da yafi kusa da single seater din ta Khadeeja take zaune.

    Ta ɗan yi gyaran murya tace ‘Uhm, ai na zata Mustapha zai zo yau ɗin, ko sai da yamma zai zo?’ Ta ɗan gyara zama tace ‘Umm! Ina jin dai sai da yamman, wataƙila gidansu ya wuce tunda shi da yara ne.’ ‘Um to bari mu gani. Amma dai kuna waya ko?’ ‘Eh, jiya da daddare ma mun yi magana.’

    ‘Ai shikenan bari mu gani. Suka yi shiru na ɗan lokaci; jimawa kaɗan tace ‘Mommy kina neman Mustaphan ne da naga kamar jiransa kike yi? Ta jijjiga kai tana murmushi ‘A a me zai yi min; kawai dai na san ya kamata a ce ya zo ya duba ki ko, ai ko gaisawa ne a yi duk da dai da an sallace za ki koma.’

    Ita ma dariyar ta yi sannan tace ‘Zai zo Mommy in sha Allahu.’ Abu kamar wasa har aka sha ruwa babu Mustapha babu labarinsa’ haka dai ta lallaɓa ta ci abincin ba tare da tana jin daɗinsa ba. Tana kula da yanda Mommy ta saka mata ido sosai tana kula da duk wani motsinta tun ɗazu da suka yi magana.

    Sai da aka tafi sallar isha’i lokacin ‘yan gidan duk sun tafi masallaci sannan Mommy ta kirawo ta; ta riga ta san kiran don haka cikin sanyi ta tashi ta wuce ɗakin Mommy ɗin. A zaune a kan dadduma ta same ta don haka ta zauna daga gefenta a kan kafet. Sai da Mommy ta ɗauki lokaci tana kallon fuskarta kamar mai karanta littafi sannan tace ‘Wai ya aka yi Mustaphan bai zo ba?

    Gashi kin san ba za a sake buɗe gari ba sai satin sallah. Ko wani abu ne ya tare shi?’ ‘Umm! Kin san sai sun je office da zarar an buɗe gari. Sai da aka fara kiran magariba sannan ya kirawoni yake gaya min a lokacin yake barin office ga shi yana so ya isa gida kafin a fara tare hanya.’ Ta sharo ƙarya.

    Ta sake kakkafe ta da ido na ɗan loakci sannan tace ‘Umm! Ko dai fushi yake don an ce ba za ki koma sai bayan sallah? Na ga fa bai sake zuwa ba tun wancan lokacin da ya zo ɗaukanki ba ki bi shi ba.’

    Ta sunkuyar da kai tana ‘yar dariya tace ‘Umm, ya ma gama fushin ai. Da farko ne ya fara fushin ya zata zan fasa zama har bayan sallar amma daga baya da ya ga ba zai sami yanda yake so ba ya hakura.’ ‘Umm! To ko shi yasa bai zo ba?’

    ‘A a fa Mommy, na gaya miki ya je aiki ne shi yasa ya makara bai zo ba. Idan aka sake buɗe gari ko kuma ranar sallah zai zo.’ ‘To Allah ya kai mu. Idan dai da akwai wata matsala gara ki faɗa tun kafin ki koma a san matakin da za a ɗauka don na kula kamar akwai abinda kike ɓoyewa.’

    Ta ɗan yi murmushi sannan tace ‘Babu wani abu fa Mommy, aiki ne kawai da raino; kin san harkar yara. Bana samun lokacin kaina kullum cikin hidimarsu nake. Shi yasa tunda Biba ta tafi ban sami natsuwa ba. Kin ga yanzu kin ce kafin sallah za a samo min yarinya sai mu koma tare, daga wannan babu wata matsalar.’

    Ta kalle ta da alamomin tambayoyi domin jikinta yana ba ta kamar akwai abinda Khadeejan take ɓoye mata, amma babu wani abu da za ta iya yi a kai tunda ba ta ma san menene matsalar ba. Tace ‘To kuma shi Mustaphan ba ya baki wata matsala? Ta yi dariya ‘Mommy kema dai kin san da da matsala da tuni na gaya miki fa, babu komai.’

    Dole Mommy ta haƙura ta ƙyale ta da tambayoyin nan ba don ta gamsu da amsoshin da ta bayar ba. Sai da ta yi da gaske sannan ta hana kanta kiran Mustapha a wannan daren; ta yi wa kanta alƙawarin daga yanzu ba za ta sake kiran shi ba har zuwa bayan sallah. Idan ya zo su koma, idan kuma bai zo ba ita dai to ba za ta neme shi ba. Haka ta kwana tana matse ƙwalla.

    Duk yanda ya so ya daure zuciyarsa daga sharewar da Khadeeja ta yi masa zuwa yanzu ya gaza; ya riga ya saba tana kiransa tana lallaɓa shi da ba shi haƙuri amma shiru. Yana kallon kiranta ranar Asabar ya ƙi ɗauka don ya san za ta ce ya zo gidansu ne; shi kuma ba zai je ba in dai ba ɗaukanta zai je yi ba. Don haka ya ƙi ɗaukan kiran yana sa ran idan dare ya yi ma za ta sake kira, a lokacin sai ya ba ta uzurin dare ya yi.

    Sai dai har ya kai yaran gidan Mama ya wuto gida ya gama duk abinda zai yi ba ta sake kira ba; lokacin da ya tashi sahur ma wayar ya fara dubawa ya ga ko ta kirawo yana bacci amma ga mamakinsa babu kiranta ko ɗaya. Haka ya yi sahur ya gama ibadarsa ya kwanta.

    Sai da gari ya waye zuwa azahar sanna ya tuna akwai messages ɗinta na whatsapp da ta turo bai buɗe ba don haka ya je ya lalubo saƙonnin ya buɗe. Ya bi su ɗaya bayan ɗaya ya tura mata amsa, wanda tambayarsa take yi ko zai zo sannan tana gaya masa kayan da zai ɗauko mata a ɗakinta ya taho mata da su.

    Har zuwa la’asar ba ta amsa saƙonninsa ba sai dai sun nuna alamar sun shiga; ya buɗa whatsapp sau babu iyaka amma har zuwa lokacin ba ta karanta saƙonninsa. Ba ta taɓa share shi haka ba; to ko dai ba ta da lafiya ne? kada fa ya je wani abu ne ya same ta don idan dai Khadeeja ce ya san za ta neme shi.

    Zuciyarsa tana gaya masa wulaƙanci ne kawai take so ta yi masa don haka ya rabu da ita duk da yanda ya kasa cire tunaninta daga ransa. Haka suka zauna ba sa waya kuma ga saƙonninsa nan ta gani amma ta ƙi ta ba shi amsa. Ranar jajiberin sallah ya kasa jurewa shiru ɗin don haka ya kirawo ta; wayar tana dab da tsinkewa sannan ta amsa.

    Murya ƙasa-ƙasa cikin halin ko in kula tace ‘Bana kusa da wayar ne. Kwana biyu na jiki shiru ne, kuna lafiya? Lafiya Alhamdulillahi. Ya yarana?’ Suna nan ƙalau, suna gidan Mama. Allah sarki, don Allah in ka je kace ina gaida su maman.’ Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan yace ‘Kin yi zamanki a gida gaba ɗaya kin manta da ni ko?’

    Ta yi ‘yar dariya tace ‘Ka dai manta da ni. Ko kayan sallarki ma ba ki tambaya ba. Uhm, akwai wasu ma a nan da Mommy ta ɗinka min. To ya kike? Lafiya dai kike ko?’ ‘Lafiya ƙalau. Suka ɗan taɓa hirar haka wadda duk gaba ɗaya kusan shi ne yake ta daddagewa don ita ma ta ji haushin abinda ya yi mata, daga baya yace ‘Gobe fa Sallah, yaushe zan zo mu taho gida?’

    ‘Umm, in dai ka cire jibi duk lokacin da ka shirya za ka iya zuwa mu tafi, tunda an riga an samo min mai aiki ga ta har ta koyi duk wani aiki da nake so. Uhm, dole dai sai kin sani cin tuwon sallah a gidan hajia ko? To ina laifi, idan ka ci ni ma ka yi min take away.’ Haka suka cigaba da hirararsu a hankali suna sakewa, daga baya suka yi sallama a kan ranar sallah zai zo ya ci tuwo kafin ya wuce gidan Hajia.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma

    Karo na babu iyaka kenan da ta ɗauki wayarta ta buɗo whatsapp ta duba; har yanzu bai amsa messages ɗinta ba kuma bai biyo whatsapp call in da ta yi masa ba. To me yake faruwa ne? Allah dai yasa lafiya Mustapha yake da shi da yaran. Da farko da ta ga ta yi magana ta whatsapp bai kula ta ba kuma ta kirawo shi ta whatsapp ɗin bai ɗaga ba sai ta zata ko fushi ya yi, amma dai zuwa yau kwana uku abun ya fara ba ta tsoro kada ta je ko wani abu ne ya same shi.
    Ta riga ta san babu credit a wayar don haka ko balance ma ba ta duba ba; shi ɗin ba mutum ne mai son saka mata credit ba, idan ma ta yi magana sai yace wa za ta kirawo ko kuma me za ta yi da data ɗin. Idan aka yi albashi dai idan ta yi magana yana saka mata naira ɗari biyar, shi ne za ta samu ta raba ta sa data sauran ta ɗan yi waya.
    Don haka yanzun ma babu na wayar sai dai data ɗin da ta yi mata saura. Ta yi tsaki sannan ta sauka daga kan gadon Nabila inda take kwance ta wuce ɗakin Mommy.A parlor ta sami Mommy tana zaune tana kallon tafsiri a tashar Sunnah TV, ta zauna a kusa da ita bayan ta yi sallama ta amsa. Sai da suka ɗan yi jim kaɗan ta kula dai Mommy babu abinda za ta ce mata sannan tace ‘Mommy don Allah ki ɗan saka min 1k a waya mana.’
    Ta kalle ta tana dariya tace ‘1k kuma? Ina Mustaphan ko kuma yau ba nashi kike so ba tunda kina gidana nawa kike so?’ Ita ma dariyar ta yi ta ƙara langaɓe kai ‘A a Mommy, don Allah dai ki taimaka, wallahi ya saka min ƙararwa na yi kuma dai kin san ba ni da kuɗi. Ke kenan kullum ba ki da kuɗi?’
    ‘Mommy bari dai na fara aiki. Uhm, shi Mustaphan ko ɗan na kashewa ba ya yaga miki balle ga ki ‘yar makaranta?’ Ta ɗan marairaice ‘To ai kin ga yanzu an yi hutu Mommy, duk ‘yan sauran canjin ma na kashe. Shi yasa kike maula kuma? To ɗauko min wayata a ɗaki na saka miki a cikin wanda mijina ya ba ni.’
    Ta miƙe tana dariya tace ‘Mommy. Baffanta ba wai millionaire ba ne amma dai ta san yana da kyauta; duk da Mommy tana sayar da ‘yan kunnaye da sarƙoƙi amma duk wata sai ya tura mata kuɗin kashewa account ɗinta sai dai ko ya tura babu yawa amma fa sai ya tura.
    Kuma idan dai ta buƙaci wani abu bayan wannan to yana iya bakin ƙoƙarinsa wajen ganin ya yi mata sai dai ko idan babu hali. Ta yi zaton haka za ta je ta samu a wajen Mustapha, musamman da yake yana yawan yi mata kyaututtuka da saka credit a waya lokacin da yana neman aurenta.
    Sai dai bayan ta shiga gidan sai ta tarar ba haka ba ne; don wani lokacin a kan ya saka mata kati a waya ya gwammace ya ba ta aron wayarsa ta yi waya. Ko da ta koma makaranta ma ta yi zaton zai ɗan dinga ba ta kuɗin makaranta da kuɗin kashewa sai dai tun a ranar farko da gane ba zai jure ba.
    Domin da farko bayan ta gama shiryawa ta yi zaton zai kai ta ne, amma sai dai suna fitowa da aka zo inda zai ɗauke hanya ya wuce office ɗinsu sai yace ta sauka a nan ta hau motar haya. Da ta yi maganar kuɗin mota kuma sai yace mata wai ya zata tana da kuɗi; ta dai samu ya ba ta naira dubu kamar ba da son ranshi ba.
    Tun daga ranar ma sai ya zama ta daina damuwa ta yi sai ta shirya ta bi shi, yawanci sai ta jira idan ya fita sai ta kama hanya a motar haya. Kuɗin motar ma tana shirin ta tambayi Baffa ya dinga ba ta aka shiga lockdown; kuma har yanzu tana da niyyar kafin ta koma gida ta sanar da Baffanta kawai ya dinga tura mata kuɗin mota.
    Tana ta wannan tunanin ta je taɗdauko wayar ta kawo wa Momy; ba tare da ɓata lokaci ba ta tura mara katin naira dubu kamar yanda ta buƙata. Nan da nan ta koma ɗaki ta sake hayewa kan gadon Nabila sannan ta danna masa kira. Sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ya ɗauka, cike da isa yana magana da ƙyar ya amsa sallamarta, haka ma gaisuwarta kamar ba zai amsa ba.
    Wannan ya sa jikinta ya yi sanyi kuzarin da ta fara wayar da shi duk ya gushe. Cikin sanyi murya tace ‘Babe, ya na ji ka haka? Ko ba ka da lafiya ne?’ Sai da ya ɗan yi jinkiri sannan ya amsa ‘Umm, lafiyata ƙalau. Ke kin damu da lafiyata ne da kike wannan tambayar? Ba dole ki ji ni haka ba tunda kin zaɓi ki nesanta kanki da ni?’
    Nan ta fahimci inda zancen ya dosa, amma da yake so take ta waske sai tace ‘Haba Babe ya za a yi na guje ka? Tunda da kuka tafi daga nan nake ta yi maka message ta whatsapp, ba ka gani ba ne? Kuma wallahi wayar ma ka san ba ni da credit, yanzun ma da ƙyar na samu Mommy ta saka min ɗari biyu shine nake kiranka fa. Haba Babe ya za a yi kace ban damu da kai ba?’
    ‘To idan kin damu da ni ya za a yi na zo har gidanku ga azumi kin sani kuma ga shi ana lockdown? Amma kina kallonmu ni da yarana duk muna ta murna za ki dawo amma kika ce ba za ki dawo ba sai bayan sallah. To ai na gaya maka wannan ba ni na tsara haka ba, Mommy ce. Kuma ka san dai idan mace ta haihu dai ana yin gyara da sauransu, sallar nan fa kuma saura bai fi kwana goma sha shida ba.
    Haba Babe to meye na fushin?’ Shiru ya yi ba tare da yace mata komai ba suna sauraren numfashin juna. Ita ce ta gaji da sauraro tace ‘Ya na ji shiru ne? ina yara na?’ ‘Ai ba ki damu da su ba shi yasa suna ta cewa ki biyo su kika ƙi. ’Ta fara gajiya da wannan mitar tasa da duk abinda tace sai ya ce ba ta damu da su ba shi da ‘yayansa, to wai ita ba ta buƙatar a damu da ita ne ko me yake nufi?
    Shi ba zai iya kula da ita ba kuma ya bar ta ma cikin natsuwa a inda za a kula da ita ta ɗan sami natsuwa yana nema ya hana? Ta ɗan yi murmushi mai sauti ta danne fushinta sannan ta saita muryarta tace ‘To don Allah ka yi haƙuri ka daina cewa ban damu da ku ba, kai ka san na damu daku. Kamar yau ne za ka ga lokacin ya yi ai na dawo, ko ba shikenan ba.’
    ‘Umm, amma dai da za ki dawo yanzu ai da ya fi ko? Haka kawai ni ba gwauro ba kin saka ni azumi babu mata. Kawai idan an buɗe gari na zo na ɗauke ki mu tafi, shi ne kawai zan san kin damu da ni. Ta dan ɗaga murya tace ‘Ah, Babe to me zan cewa Mommy, ni daɗi miji zan bi mijina kenan ko me?’
    ‘Ba wani daɗi miji, ai aure ne kuma ita ma ta sani. To gaskiya dai ka bari sai bayan sallar kawai.’ Haka dai suka ɗauki lokaci suna waya ba tare da ta amince za ta dawo ɗin ba, maimaita masa kawai take sai bayan sallar. Don haka kusan a fusace ya katse wayar ba tare da sun yi wata sallamar kirki ba.
    Ta jefa wayar a kan gadon kusa da ita ta ja tsaki, sai kuma ta kifa kanta a kan pillow sai hawaye. Ta godewa Allah Nabila tana ɗakin Mommy tana bacci da sai ta gayawa Mommy tana kuka. Ta fara nadamar sakawa da ta yi Mommy tace ta zauna a gida har bayan sallah, yanzu gashi yana fushi da ita.
    Ita ba ta zata wannan abun zai sa ya yi fushi ba don da ta san zai yi fushi ma da ko gidan ba za ta taho ba za ta haƙura ya je ya ɗauko ta. Bata sani ba ko za ta iya jure jinsa a cikin damuwa har na tsawon sati biyu ko uku, amma dai za ta gwada. Don da kunya tace a barta sai bayan sallah sannan yanzu kuma ta zo tace za ta koma.
    Haka ta ƙarasa wunin ranar cike da damuwa da nadamar zaman da ta zaɓa za ta yi a gida. Haka ta cigaba da haƙuri tana buga masa waya wanda kullum idan ta buga gaisawa kawai suke yi babu wata magana mai daɗi, kamar ma shi dole take masa. Abun yana matuƙar damunta don haka ta fara rama wadda Mommy ta zata don ta cigaba da azumi ne tunda ta sami lafiya; idan ta yi zuru-zuru aka yi magana sai tace azumin ne da wahala.
    Tun da ya kai su gidan Hajia bai sake zuwa ba tunda garin a rufe yake ba a fita, sai yau Asabar a lokacin saura sati ɗaya sallah. Yana fita ya tsaya a shagon telansa ya karɓar musu ɗinkunan kayan sallansu wanda tun kafin a fara azumi ya kai; wanda har da na Khadeeja a ciki, ya tsaya aka ba shi leda ya ware nata waɗanda ba shi da niyyar kai mata gidansu.
    Ya dai yarda zai ajiye mata a ɗakinta duk lokacin da ta dawo ta gani. Yana karɓa kai tsaye ya wuce gidan Hajia cike da kewar yaransa. Tun daga nesa ya hango Habib a zaune a kofar gida tare da wani yaro, ba wasa suke yi ba a zaune suke kawai sun yi shiru kowa da abinda ya dame shi.
    Kafin ya ƙarasa tsayar da motar ya taso da fara’arsa; ya gyara tsayuwar motar ya buɗe kofa yana sake ƙarewa Habib din kallo wanda ya yi zuru-zuru kamar wanda ya kwana da yunwa. ‘Abba sannu da zuwa.’ Muryar Habib ta katse shi. ‘Yauwa Habib, ya naganka kamar kana jin yunwa ko azumi kake ya fara ba ka wahala tun da safe haka?’
    Idonsa ya ɗan yi rau-rau yace ‘Eh, azumi nake yi. To ba ka yi sahur ba ne?’ ‘Ba sosai ba, baƙin tuwo ne kuma ba na ci ga shi kuma babu wani abincin a gidan sai shi, na ɗan ci kaɗan dai. To ba sai ka fasa yin azumin ba? ɗa safe ka yi breakfast.’ ‘Hajia ma haka tace na fasa yin azumin amma ni nace zan yi, idan ma ban yi ba ba abinci zan samu ba sai an sha ruwa.
    Tunda muka zo ma sau ɗaya na sha azumi.’ Cike da tsananin mamaki yace ‘Ban gane ba abincin kake samu ba sai kace wani almajiri? Ba a ba ka abinci ne a gidan? Ina Baito? Ai Baito sai da rana take zuwa, kuma safiya tana yi Hajia take cewa mu tafi gidan Anti Jidda mu yi wanka a can mu ci abinci a can. Kuma idan mun je sai Anti Jiddan tace babu abinci sai dai kawai wata ran ta ba mu baƙin shayi da ragowar ƙosai ko doya.
    Idan kuma mutum ya dame ta sai ta yi masa faɗa, ita ma Shukra da Nasreen ragowar kunu ne kawai ko kuma idan an yi sa’a an rage abincin shan ruwa shi ne ake ba su.’ Mamakinsa ya ƙaru, yace ‘A a, ai na turowa Anti Jidda kuɗi a sayi indomie da cornflakes har da madara, ba a siya ba ko me ya faru da su.’
    Ya ɗan zaro ido ‘Tab, tunda muka zo ba mu taɓa cin indomie ba ko cornfalkes. In an sha ruwa dai da yake muna gidan Hajia shi ne aka haɗa mana shayi da madara har da ƙwai ma ake soya mana da kaza, amma dai da rana babu wanda yake ba mu abinci. A wajen Hajia ma muke shan ruwa tare da ita da Alhaji.
    Ya yi matuƙar mamaki kuma ya ji tausayin Habib; amma kuma yana matuƙar mamakin yanda za a yi a ce Yaya Jidda ta bar masa yara da yunwa. Ranar da ya kawo su bayan ya tafi ta kirawo shi tana tambayarsa kuɗi a sayi kayan shayi da indomie, kuma a take ya tura mata naira dubu goma don a siyo da wuri. To me ya faru da kuɗin da ake hora masa yara da yunwa?
    Tare suka jero da Habib ɗin suka nufi cikin gidan, suna daf da shiga suka ci karo da Afaf tare da Shukra da Nasreen kowacce sanye da hijabinta, nan da nan suka faɗa jikinsa suna murna ‘Abba, Abba. Bayan ya amsa gaisuwarsu yace ‘Ina za ku je?’ Afaf tace ‘Gidan Anti Jidda za su je su yi breakfast.’
    ‘Ke kina azumin ne?’ ‘Eh ina yi.’ ‘To ku zo mu wuce ciki ku yi breakfast ɗin a nan.’ Nasreen ta yi dariya tace ‘Tab ai babu abincin, da an gama shan ruwa Baito take juye duk wani ragowar abinci ta tafi da shi. Kuma Hajia cewa take mu je gidan Anti Jidda a dafa mana indomie amma idan mun je ba a dafa bana, baƙin shayi ake ba mu da ragowar ƙosai ko kunu.’
    Ya ɗauki shukra ya ja hannun Nasreen yana cewa ‘ku zo mu je. Bayan sun gaisa da Hajia tace ‘To ka bar su su je gidan Jidda ta dafa musu indomie ɗin su karya sai su dawo ko? Yunwa suke ji ga su nan.’ Nan suka yi wa Hajia bayanin abinda ake ba su idan suka je gidan yaya jidda; ita ma ta yi mamaki sosai. Tace ‘To me yasa ba ku taɓa faɗa ba?’
    Nasreen ta zumɓuro baki tace ‘Yaya Meena ce tace duk wanda ya faɗa sai ta ci ubansa ta karta masa rashin mutunci don ta san mu da tsinin baki.’ Daga Hajiyan har Mustaphan mamaki ne ya kama su, Meena ita ce babbar ‘yar Yaya Jidda. To amma me zai sa ta yi haka bayan Jiddan da kanta ta gayawa Hajia ya turo kuɗin indomie da kayan karin kumallon yaran?
    Tace ‘Lallai daga Aminan har Jiddan za su zo su same ni.’ Saboda tsabar takaici Mustapha kasa magana ya yi. A nan ya sake ba da kudi Habib ya fita kanti ya siyo musu indomie, yana kawowa Afaf ta dafa musu da ƙwai tunda dama da akwai ƙwai a gidan. Haka ya saka su a gaba duka sai da suka karya azumin suka ci suka ƙoshi.
    Nan ya zauna suka cigaba da hira wajen Hajia tunda shi ma Alhaji ya fice; sai dai har la’asar ta  kawo jiki Yaya Jidda bata zo gidan ba saboda yaronta Abdallah ya shigo gidan lokacin suna cin indomie shi ma ya zauna aka ci da shi kuma yana gamawa ya koma gida ya gayawa uwarsu Abban Afaf ya zo har ma ya sa an dafa musu indomie da ƙwai.
    Don haka tana sane ta ƙi zuwa saboda rashin gaskiya. Haka ya wuni a gidan ransa a ɓace yana tunanin mafita; tabbas duk Khadeeja ce ta janyo masa wannan wulaƙancin. To yanzu ya zai yi da yaran? Idan ya tafi da su ba za su bar shi ya zauna a nutse ba, kuma ma ya san Hajia ba za ta yarda ya tafi da su gida su zauna tare da shi ba.
    Sai dai kamar yanda ta riga ta faɗa ya je ya siyo abubuwan da suke buƙata ya kawo ita sai ta dinga dafa musu kafin Baito ta zo; domin ita ma Baito ɗin mijinta ne ba shi da lafiya take jinyarsa shi yasa ba za ta iya zuwa da safe ba. La’asar tana matsowa ranshi ya sake ɓaci, kuma har lokacin Yaya Jidda ba ta iso ba.
    Bayan ya idar da sallar la’asar yana zaune a kan dadduma yana tunanin mafita Habib ya shigo ya same shi. Bai daɗe da zama ba yace ‘Abba da ma ka kai mu gidan Mama, ka ga dama mun daɗe ba mu je ba tunda muka koma gida. Um, to ai da sallah za ku je ko? Ko ba kwa son zama a nan ɗin ne? Ai ka ga yanzu Hajia da kanta za ta dinga ba ku breakfast ɗin ko?’
    ‘Um, nan ɗin ma muna son zama amma can ɗin ma muna so, in ya so idan Anti Khadeeja ta dawo sai mu dawo.’ Nan sauran yaran suka shigo suka saka shi a gaba a kan su gidan Mama suke so su je; shi ɗin ma yana so ya kai su don ya san ba za a bar su da yunwa a can ba tunda ko babu mai aiki akwai ‘yan mata. To amma yanzu hakan yana nufin kenan ba za a iya riƙe masa yaransa a gidansu ba ko me?
    Ita kuma Yaya Jidda me take nufi? Gashi ta ƙi zuwa, shi kuma ba zai je gidanta ba don ya fi so ta zo su yi a gaban Hajia. Haka dai yaran nan suka saka shi a gaba dole ya amsa zai wuce da su. Ita ma Hajia da ya gaya mata zai kai su sai da ta nuna ɓacin ranta don gani take kamar fushi ya yi da yanda ya sami yaran, sai da Alhaji ya sa baki kuma suka ga Nasreen tana nema ta saka musu kuka sannan suka bari ya kwashi yaran suka wuce gidan Maman su Ma’u.
    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Tara
    Edita@rumasau-kallamu
  • Abin Da Mutum Zai Yi Idan Ya Yi Mafarki Mara Kyau

    Abin Da Mutum Zai Yi Idan Ya Yi Mafarki Mara Kyau

    Wanda ya yi mafarki mara kyau ko ya ga abu mummuna a mafarki, to sai ya yi waɗannan abubuwan:

    -Ya yi tofi ta gefen hagunsa sau uku.

    -Ya nemi tsarin Allah daga Shaiɗan da kuma sharrin abin da ya gani, sau uku.

    -Kada ya gaya wa kowa wannan mafarkin.

    -Ya juya daga kwuiɓin da ya kasance yana kwance a kansa.

    -Idan ya so, ya iya tashi ya yi salla

    Karanta Addu;ar Sanya Sababbin Tufafi

    Edita@rumasau-kallamu