Tag: yadda ake

  • Yadda Sunayen Wasu Hulunan Hausawa Suke

    Yadda Sunayen Wasu Hulunan Hausawa Suke

    1. Bakwala
    2. Dara gajera
    3. Dara doguwa
    4. Dankwara
    5. Gurus
    6. Gurumfa
    7. Haɓar Kada
    8. Kalaɓus
    9. Kube
    10. Markiyo

    11. Mu-haɗu-banki
    12. Iya kwandishin
    13. Mangadara
    14. Saki
    15. Siniya
    16. Sallau Musa
    17. Tashi-da-kwakwa
    18. Zita
    19. Zanna Bukar

    FASIHIN KAITA

    Karanta Sunayen Wasu Kifin Hausa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Sunayen Wasu Kifin Hausa

    Sunayen Wasu Kifin Hausa

    1.Buku ( karfasa)
    2. Gaiwa
    3. Ramfai
    4. Kursa
    5. Ƙurungu
    6. Gwaski
    7. Milli
    8. Kala- kala
    9. Ragon ruwa

    WASU SUNAYEN MASUNTA

    1 Mali
    2.Koma
    3.Ƙugiya
    4.Taru
    5.Fatsa
    6.Kalli
    7.Ara (kwando)
    8.Suru
    9.Damal (kwalhe)

    FASIHIN KAITA

    Karanta Taron Makon Hausa FCE Bichi 23 Oktoba 2025

    Edita@rumasau-kallamu

  • Amfanin Kankana (Watermelon)

    Amfanin Kankana (Watermelon)

     SINADARAN DA KE CIKIN KANKANA:

    – Water (about 92%)
    – Vitamin C
    – Vitamin A
    – Potassium
    – Magnesium
    – Folate
    – Lycopene (antioxidant)
    – Citrulline (amino acid)

    FA’IDOJIN KANKANA A JIKI:

    1. Tana taimakawa wajen hana bushewar jiki.
    2. Tana rage haɗarin kamuwa da cututtukan zuciya.
    3. Tana ƙara ƙarfin jiki da rage gajiya.
    4. Tana sanyaya jiki, musamman a lokacin zafi.
    5. Tana kare ƙwayoyin ƙwaƙwalwa daga lalacewa.
    6. Ba ta ɗauke da kitse, don haka tana taimakawa wajen rage ƙiba.
    7. Tana taimakawa wajen daidaita hawan jini.
    8. Tana inganta narkewar abinci da motsa hanji.
    9. Tana taimakawa lafiyar ido.
    10. Tana kare fata daga illar rana da tsufa.

    Karanat Amfanin Ganyen Shuwaka Ga Lafiyar Ɗan Adam

    Edita@rumasau-kallamu

  • Malamai, Malanta Da Hanyoyin Sada Zumunta II

    Malamai, Malanta Da Hanyoyin Sada Zumunta II

    September 12, 2024

    ƁANGARE NA II: HANYOYIN SADA ZUMUNTA

    Musamman a wannan ƙasar Najeriya hanyoyin sada zumunta sun fara ɓulla ne daga shekara ta dubu biyu (2000) lokacin da aka fara amfani da wayar hannu mai amfani da layin waya.

    Da farko wayoyin da ake amfani da su, wayoyi ne da ba sa ɗauke da manhajar hanyoyin sada zumunta, da yawan mutane a lokacin ba hanyoyin sada zumunta ne a gaban su ba, kawai abinda su ka fi yi shi ne buga waya da amsa kira.

    Za a iya ce wa mafiya wayancin waɗannan hanyoyi ba a samar da su ba, balle ma a saka su a matsayin manhaja a wayar hannu. Misali, manhajar sada zumunta na 2go wasu ɗalibai na jami`ar Witwatersrand Johannesburge, suka ƙirƙire shi a 2007.

    Brian Acton da Jan Koum su ne suka ƙirƙiri manhajar Whatsapp a shekara ta 2009, Facebook kuma Nick Clegg, Sheryl Sandberg, Sean Parker, Mark Zuckerberg suka ƙirƙira a 2004 a Massachuset ƙasar Amurka. Twitter kuma a shekarar 2006 aka ƙirƙire shi, amma sai 2012 aka ƙaddamar da shi wanda Jack Dorsey, Noah Glass, Biz Stone da Evan Williams su ka ƙirƙira.

    Twitter (2006), Tiktok( 2016), Telegram (2012). Kafinsu akwai wasu hanyoyin na wasiƙu da sada zumunci kamar su hotmail, yahoomail (1997) da gmail (2004) da sauransu amma ba a samun su a manhajar wayar hannu. Waɗancan su ne aka fi sani a nan, amma akwai dubbansu suna nan ana ta amfani da su yau a faɗin duniya.

    A nan kasar, musamman a yankin mu na Arewa, da yawa daga cikin masu amfani da waɗannan manhajoji na sada zumunta ba su san waɗannan manhajoji ba sai kusan shekarar 2010 yau shekara goma sha –biyar ke nan. Sannan da yawa da ga cikin mutane ba su san babban dalilin samar da waɗannan manhajojin ba, balle su yi amfani da su ta hanyar da ta dace.

    Matasa na cikin `yan gaba dai gaba dai wurin amfani da waɗannan manhajojin. Ƙaramin misalin da zan bayar shi ne a cikin mutane miliyan hamsin (50M) da suka yi amfani da 2go a nahiyar Afrika miliyan 13 suna Najeriya kuma sama da kashi casa`in (90%) matasa ne.

    Wannan hasashe haka yake har yau a ko ina, matasa su ne kan gaba wurin amfani da waɗannan hanyoyi musamman a ƙasashe masu tasowa. Wannan ya na faruwa ne sakamakon rashin aikin yi da zaman banza da matasa suke fama da shi a ƙasashe masu tasowa wanda ci bayan tattalin arziki ke sabbaba shi.

    A yau ana ganin samari marasa aikin yi suna yin duk abinda za su yi dan su sami kuɗin da za su sayi data dan su sami damar amfani da waɗannan manhajoji na sada zumunta. Misali, Facebook idan mutum ba shi da data, idan kuma ba lite yake amfani da shi ba, toh a akwai abinda ake cewa “free mode” kwai za ka ga rubutu, amma hotuna ko bidiyo ba za su bayyana ba, sannan ba zai baka damar bin hanyar da za ka sami labari ba ko wani bayani ba wato “link”.

    Sau da yawa wannan yana hana mutane fahimtar asalin abinda aka yaɗa ko aka wallafa, sannan ya kan sa mutum ya yi sharhi na goyon baya ko akasin haka, ko ma ya yaɗa abinda ba shi ne ba.

    Abu mai mahimanci na gaba shi ne, mutane suna shiga abin da ba su da ilimi a kai. Wannan shi ne dalilin yin wannan rubutun. Sau da yawa babban malami zai yi bayani na ilimi mai zurfi a kan wani abu mai mahimmanci da ya shafi addini, a yaɗa shi ta hanyoyin sada zumunta, kwatsam sai ka ga wani matashi, ko wani ɗan tasha bai san dama ko hagu ba a kan abinda ya shafi ilimin addini, kawai sai ya ce wannan babban malamin nan “ƙarya” ya keyi, ko zai ci gyaran malamin.

    Ba don komai ba, kawai wannan hanya ta ba shi dama ya ga ko ya ji abinda wannan babban malamin ya faɗa. Wani babban abin takaicin shi ne shi, wannan matashi ko ɗan tashan ba zai iya kawo wata hujja na ilimi ba, sai soki-burutsu, jahilci da hayaniya.

    Misali ɗaya daga cikin misalai masu yawa shi ne mas`alar mutum ya ce ya saki matarsa da wasa ko da kuwa a shirin wasan kwaikwayo ne. Manyan malamai kamar Dr. Bashir Aliyu Umar, oon da Prof. Umar Sani Fagge sun yi fatawa a kan ce wa duk wanda ya aikata haka matarsa ta saku.

    Suka kafa hujja da hadisin Manzon Allah SAW ingantacce. Amma aka samu wasu waɗanda ba su wani abu na ilimin addini, kai wasu ma `yan tasha ne, suka rinƙa surutai na jahilci da rashin ladabi ga malamai da malanta da ƙoƙarin ƙaryata hadisin Manzon Allah SAW da molon ka.

    Ba abinda ya ba su wannan damar sai waɗannan hanyoyi na sada zumunta wanda suke ganin ilimi kamar abin banza da arhan malanta. Idan aka duba a baya za mu ga mas`aloli na addini, malamai da tsarekunsu su suke tattauna cikin girmamawa ta hanyar rubuce – rubucen ilimi.

    Amma yanzu saboda waɗannan hanyoyin na zamani sai a ci mutuncin malami, a zage shi, a faɗi munanan maganganu game da shi, ba tare da an kawo wata hujja ko wata magana ta ilimi ba saboda ba abin da za a iya faɗa da rashin ilimi.

    Sannan abu na biyu, wannan ya ba da dama kowa ya ga cewa zai iya zama malami saboda yawan yaɗuwar ilimin kayauta kuma cikin sauƙi. Kowa zai iya zama malami dare ɗaya. Wanda kuma ba haka ba ne, kuma ba ma zai yiwu ba.

    Abu na uku, waɗannan hanyoyin sun bai wa wasu `yan dagajin mutane damar yin sojan gona, su mai da kansu malamai, su tsoma baki a cikin abinda ya shafi ilimi, da ma faɗin duk abinda suka ga dama. Jahilai kuma suna nan birjik followers, masu sharing da masu like.

    Daga ƙarshe, waɗannan hanyoyin sun ba da gudumawa wurin yaɗuwar ilimi da wayar wa mutane kai game da addini, sannan a gefe ɗaya kuma sun ba da damar raina malamai da ilimi, rashin ganin girman ilimi da mahimmancinsa. Malamai sun zama ba komai ba, sannan malanta ta zama arha.

    Duk wanda baya ganin wanɗanda suke riƙe da tushen addininsa, (ilimi) da girma ta yaya zai ga girman addininsa? Gimama malamai yana daga cikin abinda zai sa mutum ya san daraja da girman addininsa.

    Whatsapp: 08039290267

    Karanta Malamai, Malanta Da Hanyoyin Sada Zumunta A Yau (1)

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Hawan Jini Yake (HYPERTENSION)

    Yadda Hawan Jini Yake (HYPERTENSION)

    Jini ruwa ne mai launi ja-zur da ke kewaya sassan jikin dabbobi masu ƙashin baya (vertebrates), kamar mutane (humans), mage (cats), ƙadangare (reptiles), tsuntsu (birds), kwaɗo (amphibians), kifi (fish), da sauransu.

    Bincike ya tabbatar da cewa banda mutum, akwai dabbobin da suke kamuwa da matsalar hawan jini. Amma wannan matsalar tana maganar hawan jinin mutum ne.

    Jini yana gudu da ƙarfi a cikin jijiyoyin jikin mutum idan zuciya ta feso shi. Aikinsa shi ne isar da kayan abinci zuwa sassan jiki, da fitar da ruwan dattin jiki ta hanyar fitsari ko zufa.

    Ƙarfin tafiyar jini yana buɗe jijiyoyi (arteries), kuma shi ne “blood pressure”. Akwai adadin blood pressure da ake buƙata wanda ba zai cutar da jiki ba. Idan ya yi yawa shi ne “hypertension”, kuma matsala ne. Idan ya yi kaɗan shi ne “hypotension” shi ma matsala ne. Idan ya yi daidai shi ne “normotension”, kuma shi ake buƙata.

    NA’URAR AWON GUDUN JINI (BLOOD PRESSURE MEASUREMENT DEVICE)

    Na’urar awon gudun jini ita ce “sphygmomanometer”. Tana da jakar ledar “polyester” da “nylon” mai suna “inflatable arm cuff”, wacce ake hura ma iska da ƙwallon roba mai suna “bulb pump”. Sa’annan tana da fuska (screen) mai nuna sakamakon awon, wato “pressure gauge”.

    A maƙale da ita akwai na’urar jin sautin bugun zuciya da jin gudun jini (stethoscope). Lokacin yin awon, ana ɗaura inflatable arm cuff ɗin a damtsen hannu, a hura iska a ciki. Cuff ɗin zai matse damtsen. Hakan zai sa na’urar ta iya ɗosano ƙarfin gudun jinin, ta nuna shi a screen, kuma za a ji sauti bugun zuciyar ta stethoscope.

    Nau’rar awon iri biyu ce:

    1. Ta farko ita ce na’urar da ake sarrafa ta da hannu (manual blood pressure monitor): Tana da stethoscope, inflatable cuff, da pressure gauge, kuma iri biyu, kamar haka:

    a. Mercury sphygmomanometer, wacce ake ganin sakamakon awon a jikin tsinken ruwan “mercury” a tsakiyarta.

    b. Aneroid sphygmomanometer, wacce take amfani da “spring” da “gauge”.

    2. Ta biyu ita ce na’urar da ke sarrafa kanta: (digital blood pressure monitor): Tana da maɗosanin bayanai (sensor) wanda yake ba ta damar yin aiki da kanta (automatic). Tana da inflatable cuff, amma ba ta da stethoscope. Idan aka ɗaura inflatable cuff ɗin, za ta hura iska da kanta ta hanyar motorized pump. Sai screen ɗin ya nuna sakamakon awon.

    KARANTA SAKAMAKON AWON GUDUN JINI (READING OF BLOOD PRESSURE MEASUREMENT)

    Sakamakon awon yana da lambobi biyu ne.

    1. Lamba ta farko ita ce ta sama, kuma ana kiranta “systolic”. Tana nuna ƙarfin gudun jini ne lokacin da zuciya ta kumbura domin ta feso shi.

    2. Lamba ta biyu ita ce ta kasa, kuma ana kiranta “diastolic”. Tana nuna ƙarfin gudun jini ne lokacin da zuciya ta sace bayan ta feso shi.

    Lambobin awon suna fitowa ne da alƙaluman millimetre of mercury (mm Hg).

    Tun farko na faɗi cewa sakamakon awon blood pressure iri uku ne:

    (a) Gudun jinin da ya yi sama, wato hypertension.

    (b) Gudun jinin da ya yi daidai, wato normotension.

    (c) Gudun jinin da ya yi ƙasa, wato hypotension.

    Matsakaicin gudun jini da ake buƙata (normal range of blood pressure) ya danganta da shekaru ko yanayin mutum ne. Wato ana buƙatar lambar sama (systolic) da lambar ƙasa (diastolic) su kasance tsakanin da’irori kamar haka:

    1. Jariri: Systolic = 72 mm Hg zuwa 104 mm Hg.

    2. Ɗan shekara 1 zuwa 2: Systolic = 85 mm Hg zuwa 113 mm Hg. Diastolic = 37 mm Hg zuwa 69 mm Hg.

    3. Ɗan shekara 3 zuwa 5: Systolic = 91 mm Hg zuwa 120 mm Hg. Diastolic = 46 mm Hg zuwa 60 mm Hg.

    4. Ɗan shekara 6 zuwa 12: Systolic = 96 mm Hg zuwa 131 mm. Diastolic = 55 mm Hg zuwa 62 mm Hg.

    5. Ɗan shekara 13 zuwa 17: Systolic = 80 mm Hg zuwa 120 mm Hg. Diastolic = 45 mm Hg zuwa 80 mm Hg.

    6. Ɗan skekara 18 zuwa 50: Systolic = 120 mm Hg zuwa 130 mm Hg. Diastolic = 80 mm Hg zuwa 85 mm Hg.

    7. Mace mai juna biyu: Systolic = 120 mm Hg zuwa 130 mm zuwa. Diastolic = 80 mm Hg zuwa 85 mm Hg.

    8. Tsoho: Systolic = 120 mm Hg zuwa 140 mm. Diastolic = 80 mm Hg zuwa 90 mm Hg.

    TASIRIN HAWAN JINI KO SAUKAR JINI DA ALAMOMINSU (EFFECTS AND SYMPTOMS OF HYPERTENSION OR HYPOTENSION)

    Tasirin hawan jini ko saukar jini yana bambanta a tsakanin mutane, kamar haka:

    1. Jarirai: Ba a cika samun hawan jini ga jarirai ba. Idan aka ga jariri da hawan jini, to, lallai an haife shi da nakasar zuciya ne (heart defect), ko matsalar ƙoda (kidney problem). Alamominsa su ne yawan kuka, kasa shan nono, da rashin girma. Sa’annan ba a cika samun saukar jini ga jarirai ba.

    Idan aka samu, lallai dalilinsa zai zamo rashin ruwan jiki (dehydration), ko zubewar jini (blood loss), ko ciwon zuciya (heart disease). Alamominsa su ne rashin shan nono, rashin walwala, da koɗewar fata (pale skin).

    2. ‘Yan shekara 1 zuwa 10: Ba a cika samun hawan jini ga yara masu wannan shekarun ba. Idan kuwa ya same su, alamominsa sune ciwon kai (headache), gajiya (fatigue), riƙewar numfashi (shortness of breath), haɓo (nose bleeding), sanƙarewa (seizures), da rashin gani (vision problems). Idan ba a magance shi ba, zai iya lalata zuciya, ƙoda, da ƙwaƙwalwa.

    Haka nan ba a cika samun saukar jini ga yara masu wannan shekarun ba. Idan aka samu, alamominsa su ne jiri (dizziness), suma (fainting), saurin bugawar zuciya (rapid heartbeat), da rashin ƙwarin jiki (weakness). Rashin magance shi zai iya lalata aikin ƙwaƙwalwa (impaired brain function), tsumburewa (growth retardation), da rikicewa (hypoxia).

    3. ‘Yan shekara 11 zuwa 17: Ana samun hawan jini ga matasa masu wannan shekarun. Alamominsa su ne ciwon kai (headache), zafin kirji (chest pain), da zafin jiki (abdominal pain). Idan ba a magance shi ba, zai iya lalata zuciya, ƙoda, da ƙwaƙwalwa, da jijiyoyin jini.

    Kuma zai iya kawo shanyewar tsagin jiki (stroke). Haka nan ana samun saukar jini ga matasa masu wannan shekarun. Alamominsa su ne ciwon kai (headache), zafin ƙirji (chest pain), da zafin jiki (abdominal pain). Rashin magance shi zai iya lalata zuciya, ƙoda, ƙwaƙwalwa, da jijiyoyin jini.

    4. Baligai ‘yan shekara 18 zuwa 50: An fi samun hawan jini ga masu wannan shekarun. Alamominsa su ne ciwon kai (headache), jiri (dizziness), da rashin gani sosai (blurred vision). Idan ba a magance shi ba, zai iya haddasa ciwon zuciya (heart disease), shanyewar tsagin jiki (stroke), da lalacewar koda (kidney failure).

    Haka nan an fi samun saukar jini ga baligai masu wannan shekarun. Alamominsa su ne jiri (dizziness), suma (fainting), da gajiya (fatigue). Rashin magance shi zai iya lalata ƙwaƙwalwa (impaired brain function), rikicewa (hypoxia), da gigicewa (shock).

    5. Tsofaffi: An fi samun hawan jini ga tsofaffi. Alamominsa su ne ruɗewa (confusion), mantuwa (memory problems), kasa tafiya (difficulty in walking). Idan ba a magance shi ba, zai iya haddasa ciwon zuciya (heart disease), shanyewar tsagin jiki (stroke), da cutar mantuwa (dementia).

    Haka nan an fi samun saukar jini ga tsofaffi. Alamominsa su ne jiri (dizziness), suma (fainting), da ruɗewa (confusion). Rashin magance shi zai iya lalata ƙwaƙwalwa (impaired brain function), rikicewa (hypoxia), da gigicewa (shock).

    6. Masu juna biyu: Ana matuƙar samun hawan jini ga mata masu juna biyu har yakan kai matakin farko na ciwon jijjiga (preeclampsia). Alamominsa su ne kumburin jiki (abdominal swelling), ciwon kai (headache), rashin gani sosai (blurred vision), da ciwon jiki (abdominal pain).

    Idan ba a magance shi ba, zai iya haddasa haihuwar bakwaini (preterm birth), haihuwar ƙanƙanin jariri (low weight of newborn), da matsaloli masu yawa ga uwa da jaririnta. Haka nan ana matuƙar samun saukar jini ga mata masu juna biyu. Alamominsa su ne jiri (dizziness), suma (fainting), da gajiya (fatigue).

    Rashin magance shi zai iya hana samar da isasshen jini ga jariri a cikin mahaifa (impaired blood flow to fetus), ƙanƙancewar jariri (fetal growth restriction), ko ɓari (miscarriage). Idan ciki ya tsufa, to, saukar jini alama ce ta preeclampsia.

    RABE RABEN HAWAN JINI (TYPES OF HYPERTENSION)

    Hawan jini ya rabu gida biyu:

    1. Hawan jini na asali (primary or essential hypertension): Shi ne wanda ba a san asalin abinda yake kawo shi ba, amma tsarin rayuwar mutum take haɓaka shi, kamar cin gishiri da yawa, rashin motsa jiki, tsufa, shan giya, ƙiba, gado, da sauransu.

    2. Hawan jini mai dalili (secondary hypertension): Shi ne wanda wasu cututtuka ko amfani da wasu magunguna yake kawo shi, kamar matsalolin ƙoda, zuciya, ƙwaƙwalwa, da magungunansu.

    MAGANI (TREATMENT)

    Magance hawan jini yana da matuƙar alaƙa da tsarin rayuwar mutum, kamar motsa jiki, rage ƙiba, cin abinci mai kyau, da shan magani bisa umurnin likita. Shi ma saukar jini magance shi yana da alaƙa da magance abubuwan da suke kawo shi, kamar yawaita shan ruwa, da kauce ma abubuwan da jikin mutum yake bijire musu.

    Karanta Bayani A Kan Budurci Da Kuskuren Da Ake Yi A Kan Rashinsa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Shida

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Shida

    Tana jiyo motsin shigowar Mustapha gidan amma ba ta yi zaton zai tafi da sauri ba, don haka ma ta jira sai da ta gama abinda take yi tunda ta jiyo shi da Baffa a tsakar gida. Sai dai ga mamakinta ko da ta fito Baffa ta tarar shi kaɗai, yana shirin shigewa mota ta yi sauri ta karasa.

    Tace ‘Na ji kamar kai da Mustapha ne, ko har ya tafi ne? Ya tsaya yana riƙe da murfin mota yana cewa ‘Shi ne, matar tasa ce ta fara gwada masa tutsun nata shi ne ya taho kawo ƙara da sassafe. Ikon Allah, Khadija Iya-rigima. Me ta yi kuma?’

    Nan ya ba ta labari kamar yanda Mustapha ya ba shi, ya ƙara da ‘Na ce su zo bayan Magriba don ita ma yanzu zan kirawo ta na sanar da ita kada ta yi taurin kai, kin san hali. Ta yi dariya ‘To Allah ya kai mu, ai an auna arziƙi ma da aka ɗauki lokaci haka ba ta fara rigimar ba. Suka yi dariya ta yi masa a dawo lafiya ya wuce sannan ta koma ciki.

    Sai da yamma ta yi sannan ta kirawo Khadeeja a waya, bayan sun gaisa tace ‘Me ya haɗoki da Mustapha ne ya kawo ƙararki da sassafe ne? Ta yi dariya sannan ta ba ta labari, bayan ta gama ji tace ‘Ikon Allah, to neman mata Mustaphan yake yi kenan ko kuwa dai aure yake nema?’

    ‘Ni ma ban sani ba Mommy, amma dai ko ma menene ai da akwai cin fuska a ce ina yawo a taxi ita kuma tana yawo a motar mijina; at least ya bari ta aure shi sai ya ba ta wannan ikon. Kuma sannan idan ita ce za ta dinga yi masa hidimar yaransa ai sai ta karɓa gaba ɗaya ni kuma na huta gaba ɗaya.’

    Mommy tace ‘Um! Da wannan, amma dai ki bari a bi abun a hankali. Saura kuma idan kun zo ki yi shiru ki ƙi yi wa Baffa bayani ya yanke miki hukunci in ma ya ga dama yace ki ba wa Mustaphan haƙuri. Ta yi ‘yar dariya ‘Ba zan yi shiru ba Mommy. Suka yi sallama suka ajiye wayar.

    Sai dab da magriba ya dawo gidan, ya yi mamaki da ya jiyo Rashida da Afaf a kitchen suna ƙoƙarin dafa abincin dare; a tunaninsa tunda ya san Baffa ya gaya mata yana nemansu ya kamata a ce ta shiga hankalinta. Bayan ya amsa sannu da zuwansu ya wuce ɗakinta; ƙofarta a rufe take, ya saka mukullinsa ya ji har yanzu ba ta cire mukullin ba don haka ya daure ya ƙwanƙwasa.

    Sai da ta gama yauƙinta sannan ta buɗe ta rige hannun kofar ta matsa ya shige. Ya so ya zare mukullin kofar to amma sai ya ga idan ya zare ai duk da haka ba lallai ta dinga fita daga ɗakin ba balle ma ta dinga yin hidimar da ta saba; tunda dai wulaƙanci ne kawai ta shirya za ta yi.Don haka ya bi bayanta suka shige ɗakin, tun kafin ta gama zama a inda ta tashi yace ‘Baffa ya gaya miki mu je yana nemanmu ko?’

    Cikin halin ko in kula tace ‘Ƙarfe nawa za mu je? Ya so a ce ta ba shi dama su yi magana su kashe wannan rigimar in ya so ya kirawo Baffa yace masa sun shirya amma sai dai ga alama ta fi so su je wajen Baffan. Yace ‘Da na dawo daga masallaci sai mu je.’

    Ya juya ya fice daga ɗakin ba tare da ya saurari amsarta ba. Ta bi bayansa da harara tana dariya; wato shi uban ‘yan son kai har yanzu bai ga laifinsa ba don haka ita yake tsammani ta ba shi haƙuri kenan. Tabbas yau sai ta ƙure wannan son zuciyar na Mustapha duk da har yanzu wata zuciyar tana gaya mata kada ta je ta yi wa mijinta tonon asiri a wajen iyayenta.

    Yana dawowa daga masallaci ya same ta a shirye, ko zama bai yi ba suka sallami yara suka fice daga gidan. Suna shiga gidan suka sami Mommy wadda ta ba su umarni su ƙarasa parlor ɗin baƙi domin Baffa yana can yana jiransu. Yana zaune a kan kujera 3-seater don haka Mustapha ya zauna daga gefen damansa jikin 2-seater ita kuma Khadija ta koma ɗaya gefen jikin single seater ta zauna.

    Bayan Baffa ya amsa gaisuwarsu ya dubi Khadeeja yace ‘Dije, me ya haɗa ki da maigidanki ne kika daina kula shi shi da yaransa? Ta sunkuyar da kai cikin sanyin murya tace ‘Baffa ba daina kula su na yi ba. Kafin Baffa yace wani abu Mommy ta shigo da sallama Nabila tana biye da ita ɗauke da tray wanda aka jera ruwa da lemo a kai, don haka Baffa ya tsaya ya amsa sallamarta.

    Ta nunawa Nabila inda za ta ajiye tray ɗin daga kusa da Mustapha, ta ajiye ta gaida Mustaphan sannan ta miƙe ta fice daga parlor ɗin ita kuma Mommy ta kara ta zauna a kan kujerar da Khadija take zaune a ƙasanta. Ya juya ya gaida Mommy, bayan ta amsa Baffa ya sake duban Khadeeja yace ‘Ya aka yi Dije ina saurarenki.’

    Tace ‘Baffa ba daina kula su na yi ba fa. To ai ya ce kusan kwana uku kenan ba kya kula kowa sai dai kawai ki kulle kanki a ɗaki kin bar yara da mai aiki sannan kuma gari yana wayewa sai ki fice ki tafi makaranta. Kawai saboda ya tura sakatariyarsa ta je makarantar yara kun haɗu.’

    Ta faki ido ta share ƙwalla; ya riga ya ba wa Baffa kanun labaran don haka duk yanda take son ta kare mutuncinsa ba zai yiwu ba domin ita ma dole ta kare kanta a wajen mahaifinta. Ta gyara zama tace ‘Wallahi Baffa ina bakin ƙoƙarina wajen kula da gidan da yaran, kuma babu laifi duk mun sami fahimtar juna da yaran gaba ɗaya.

    Duk wata hidimarsu ni nake yi, kuma ni ce nake ɗauko su daga makaranta ranar da ba na nan kuma sai mai-aikina ta ɗauko su. To shi ne ranar Monday suka yi open day a makaranta; ni ce na saba zuwar musu don haka tun weekend suka gaya min, shi kuma na manta ba mu yi maganar ba.

    Don haka gari na wayewa da na shirya zan tafi school sai na tsaya makarantarsu. Shi ne sai na ga har ya tura sakatariyarsa ta je musu. Baffa ya yi dariya yace ‘To ai babu komai Dije, wataƙila don ba ku yi maganar ba ne kuma kin ga ita ɗin ai sakatariyarsa ce zai iya saka ta wannan aikin duk da dai personal ne.’

    ‘Ni Baffa ba zuwanta ne ya ɓata min rai ba…’ nan ta ba shi labarin yanda ta ga sakatariyar a motar Mustapha ɗin da kuma yanda tunda ta aure shi sau ɗaya ya taɓa kai ta makaranta a motarsa da kuma yanda ko ta shirya ba ya yarda ya fita da ita. Da kuma yana wasu lokutan tana tsaye a bakin titi yake dawowa daga kai su; ba ta sani ba ko yana ganinta amma ita dai tana ganinsa.

    Baffa ya kalli Mustaphan ya kalli Mommy sannan ya kalli Mustapha wanda ya yi tsamo-tsamo don bai za ta Khadija za ta kawo wannan maganar ba; shi da ya ga ta daina damuwa ya rage mata hanya ma ya zata ta haƙura gaba ɗaya don haka bai san tana jin haushinsa a kan wannan ba.

    Yace ‘Ikon Allah, yanzu a ce a ki ragewa mutum hanya sai ka ce wani wanda ake jin haushi? Ko dai akwai wata matsalar ne Mustapha?’ Nan da nan ya fara gyara zama kansa a ƙasa cikin rawar murya yace ‘Babu wata matsala, em… dama yawancin lokutan ne ai ba ta shiryawa da wuri su kuma yaran idan 7:30am ta yi rufe musu gate za a yi.

    Umm.. shi yasa dole muke tafiya, kuma wasu lokutan ma idan na kai su gidan nake dawowa sai daga baya nake fita. Tace ‘Baffa ai ko ya dawo zai fita idan nace ya rage min hanya sai ya san abinda zai faɗa wanda zai sa ba zai tafi da ni ba don haka ma tun tuni na daina tambayarsa.’

    Suka ɗan yi shiru na ɗan lokaci Mustapha yana ta ƙoƙarin haɗa ido da ita yayin da ita kuma take ta ƙoƙarin kauce masa don ko gefen da yake ba ta kalla ba. Baffa yace ‘Shikenan abinda ya saka ki fushin ko akwai wani abun?’ Kana jin muryarsa kuma ka kalli fuskarsa za ka san ransa ya sosu matuƙa, domin karsashi da rahar da ya fara wannan tattaunawar da su duka babu.

    Har ta gyaɗa kai Mommy ta zungure ta da kafa, ta dago suka haɗa ido. Ta sunkuyar da kanta tace Baffa ita sakatariyar tasa kuma na tambaye shi menene a tsakaninsu; idan ma aurenta zai yi ai sai ya gaya min ba wai kawai na dinga ganinta a motarsa ba tana yawo a gari ni ina yawo a tasi.

    Saboda ni dai yanda na ga ta nuna alaƙarsu ta fi ƙarfin ta office kawai, don yaran ma duk sun santa ni kaɗai ce a gida na fara ganinta ranar. Baffa ya mayar da idonsa kan Mustapha wanda ya yi sauri ya sunkuyar da kansa ƙasa, ji yake kamar ya zura da gudu don bai taɓa zata Khadeeja za ta kawo waɗannan maganganun a gaban Baffa ba.

    Suka yi shiru na ɗan lokaci kowa yana sauraron abinda Mustaphan zai ce, shi kuma ya sunkuyar da kai ya yi shiru kamar wanda ruwa ya ci. Mommy ce ta gaji da shirun ta yi gyaran murya tace ‘Uhm, ai gara ka gaya mata idan auren sakatariyar za ka yi ka ga tunda dai na san cewa ta san ka kai ka ƙara auren.’

    Ya gyara zama yana shafa ƙeya yace ‘A a ba ma shi ba ne, kawai dai da na aiketan ne to kuma ana ɗan wahalar mota shi ne na ce ta je a motata tunda ta iya tuƙi. ’Jimawa kaɗan Baffa yace ‘Allah ya sauwaƙe. ’Mommy tace ‘Amin dai.

    Suka sake yin shiru na ɗan lokaci, sannan Baffa ya kirawo sunan Khadeeja, ta amsa ta dube shi suka haɗa ido sannan yace ‘Ki yi hakuri Dije, kin ji. Ta gyada kai shi kuma ya ɗan numfasa sannan ya cigaba ‘Ki yi hakuri ki bi mijinki, kin ji bayanin da yayi. Kuma idan ma yace zai auri waccan yarinyar wannan bai kamata ya zama matsala ba tunda dai kin san duka wani namiji mijin mace huɗu ne.

    Ki yi haƙuri ki cigaba da hidimarki kamar yanda kika saba, kin ji. Batun kai wa makaranta kuma kin ga shi ‘yayansa yake zubawa a mota yake kai su a makaranta kuma tabbas haka ya kamata uba nagari ya kasance, don haka idan kika gama shirya masa nashi yaran ke ma ki shirya ki yi min waya sai na zo na kai ki tunda dai ke ma ‘yata ce; kai ki makaranta kuma ba baƙon abu ba ne a wajena.’

    Ya gyara zama ya ɗago kai a razane ‘A a Baffa a yi haƙuri ai ba sai an yi haka ba, in sha Allahu za mu dinga tafiya ma. Dama ai ba ta gaya min ne shiryawa kawai take tace ta tafi. Kada ka damu, zan dinga zuwa ina kai ta wannan aikina ne.’ Baffa ya ba shi amsa rai a ɓace.

    ‘A yi haƙuri Baffa, in sha Allahu ba za sake ba, ni ɗin ma zan dinga kai ta. A yi haƙuri.’ Mommy tace ‘Ke kuma ki yi haƙuri da yaranki tunda su ba su yi miki komai ba, ki kula da su ku zauna lafiya. Shi ma kuma kin ji bayaninsa, ki je ku yi zamanku lafiya kamar yanda kuka saba saboda Allah. Ita rayuwar aure haƙuri ce, ku dinga haƙuri da juna.

    Kuma nan gaba ko wata matsala ta taso muku ku yi ƙoƙari ku kashe ta a tsakaninku. Toh.’ Ta amsa cikin sanyin murya. Jimawa kaɗan suka yi wa Baffa da Mommy sallama suka fice; Khadeeja ta so shiga cikin gidan wajen Nabeela amma Mommy tace kada ta shiga ta bar shi yana jira idan ta shirya ta dawo su yi hirar.

    Tunda suka shiga motar bai ce komai ba sai muzurai kawai yake, don haka ita ma zuciyarta wasai take. Ta ji daɗin yanda Baffa ya nunawa Mustapha cewa ita ma da gatanta; duk da dai har yanzu tana jin cewa ba za ta ɗorawa kanta jiransa ya kai ta makaranta ba balle ta ɗorawa kanta damuwa.

    Suna shiga gidan ta wuce ɗakinta shi ma ya wuce nashi ɗakin. Sai da ta yi sallah sannan ta fito wajen yaran; zuwa lokacin Shukra har ta riga ta yi bacci. Bayan ta tabbatar sun ci abinci ta wuce kitchen, ta kirawo Rashida tana tambayarta me suka dafa da daddare. Ta gaya mata indomie suka dafa saboda haka Afaf tace, ta nuna mata indomie ɗin da ta saka a flask ta ajiyewa Abbansu.

    Ta riga ta san ba ya son indomie, musamman idan ta fara sanyi kuma ita ma yunwa take ji ba ta son cin indomie mai sanyi. Don haka Rashida ta taya ta ta gyara busasshen kifi ta dafa musu jollof sphageti mai rai da lafiya. Nan da nan gidan ya ɗauki ƙamshi; zuwa loakacin yaran duk sun kwanta.

    Ta jera abincin a dining table sannan ta haɗa masa shayi mai kayan ƙamshi irin wanda yake so sanna ta wuce ɗakinsa ta tura ƙofa ta shiga. Saura kaɗan ta yi dariya saboda ganin yanda ɗakin ya yi kaca-kaca; ga ƙura ga kaya da tarkacensa ko ina. A ranta tace mutum sai kace kuturu, ya sa hannu ya gyara makwancinsa kawai ya gagare shi.

    Ta ɗan yi gyaran murya tace ‘Ga abinci can na saka a dining,’ Dama tunanin abincin yake don yunwa yake ji sosai; ya riga ya san indomie suka dafa tunda jiya ma ita suka dafa don haka ya riga ya fara tunanin yanda zai yi sai kuma tace masa ga abinci. Ya dube ta ya ɗan sassauta fuskarsa yace ‘Yanzu zan fito.’

    Ba tare da ta ba shi amsa ba ta juya ta fice, ya bi bayanta da kallo yana murmushin yaƙe. Ya rasa daɗi zai ji ta ba shi abinci wanda hakan yake nuna za ta cigaba da hidimarta; ko kuwa haushinta zai ji saboda yanda ta yaga shi a gaban Baffanta. Haka dai ya taso ya fito, babu kowa a parlor ɗin don haka ya zauna ya ci abincinsa ya ƙoshi; irin ƙoshin da ya kwana biyu bai yi ba.

    Sai da ya gama cin abincinsa ya huta sannan daga baya ya je ya kullo gidan ya shiga ɗakinsa; har ya kwanta kuma ya tashi ya bi bayan Khadeeja. Ya kula idan ya biye mata ba za ta neme shi ba, ko ba komai kuma yana so su yi magana ya ƙara kwantar mata da hankali game da maganar Naja don ba yanzu yake so ta sani ba. Sannan kuma yana so ya nuna mata rashin jin dadinsa game da yanda ta je ta kunyata shi a gaban Baffa.

    Duk yanda yaso ta taso su koma ɗakinsa su kwana kamar yanda ya saba bai samu ba, daga haka ya gane idan ya fiye takura mata zata sake ɗauke musu wuta; don haka sai ya haƙura ya zubar da duk maganganun da ya taho da niyyar gaya mata. Ya haƙura suka kwana a nan ɗakin nata tunda tace ta fara bacci ba ta son canza ɗaki.

    Tun asuba ta tashi kamar yanda ta saba, nan da nan ta shiga hidima da yara da taimakon Rashida. Ba ƙaramin daɗi ya ji ba da ya dawo daga masallaci sallar asuba ya jiyo ta a kitchen, don haka cike da walwala ya wuce ɗaki ya koma bacci kamar yanda ya saba.

    Ƙarfe bakwai na safe yana fitowa kowa ya shirya yayin da Khadeeja take kai wa da kawowa tana jera masa nasa abincin a dininga table. Bayan ya amsa gaisuwar yaran yace ‘To kowa ya ɗauki kayansa mu wuce ko? Nan da nan suka miƙe suka fara ficewa. Ya dubi Khadeeja wadda take fitowa daga kitchen yace ‘Ba ki shirya ba ke, ko sai an jima za ki tafi?’

    Da murmushi tace ‘No, yau ba mu da lecture ba zan je ba. ‘Ok.’ Ta yi musu a dawo lafiya suka wuce. Bayan ya dawo haka ya yi ta tambayarta idan ta san za ta je makaranta ta gaya masa ya jira ta ya tafi da ita ya kai ta; sai da ta tabbatar masa ba za ta fita ba sannan ya fita ya tafi office.

    Washegari ranar Juma’a ce; kamar yanda ya saba yana kwance a ɗaki bayan ya dawo daga masallaci yana rage bacci kafin a gama shirya yara ya kai su makaranta. Wayar Khadeeja ce take ta faman ringing a ɗakin tana katse masa bacci, baya son tashi don haka ya yi tsaki ya gyara kwanciyarsa.

    Sai dai wayar da ta tsinke sai a sake bugowa; to waye ma yake kiranta da wannan safiyar bayan ko wayewa garin bai gama yi ba? Wayar tana fara ringing a karo na uku ya mirgina ya miƙa hannu ya ɗauko wayar daga kan durowar gefen gado. Ya kallin screen ɗin inda sunan wanda yake kiran ya bayyana “Baffa” ya karanta a fili yana wattsakewa.

    To me yasa Baffan Khadeeja yake kiranta yanzu? Allah ya sa dai ba wani abun ne ya faru a gidan nasu ba. Nan da nan ya sauko daga kan gadon ɗauke da wayar ya nufo kitchen inda Khadeejan take faman zubawa yara abinci suna tsaye kowa yana karɓar nasa. Ya miƙa mata wayar wadda take ringing yana cewa ‘Ki amsa Baffa ne yake ta kiranki kin baro wayar a ɗaki.’

    Tana karɓa ta amsa ta kara a kunnenta; yana tsaye yana kallonta yana tsoron kada a ce wani abu ne ya faru a gidan nasu. Bayan sun gama gaisawa da Baffan tace ‘A a Baffa, ina nan ne muna shirin makaranta ni da yara.’

    Daga ɗaya ɓangaren Baffa yace ‘Ƙarfe nawa ne lecture ɗin naki Dije? ’Tace ‘Karfe takwas. Idan nazo 7:30am ai kin gama shiryawa ko? ‘Eh Baffa. ‘To ki shirya idan na ƙaraso zan yi miki waya ki fito na kaiki makarantar sai na wuce office. ’Cike da girmamawa kamar wadda za ta tsuguna a wajen tace ‘To Baffa na gode, Allah ya ƙara lafiya.’

    Ta ajiye wayar bayan ya amsa, kafin ta yi wani abu Mustapha yace ‘Lafiya ƙalau dai naga Baffa yana kiranki da safe. Ta miƙawa Habib shayinsa da ta haɗa masa tana cewa ‘Uhm zai zo ya kai ni school ne shi ne yake tambayata ƙarfe nawa zai zo. Habib ya karɓi shayinsa ya fice yayin da Mustaphan ya matsa kusa da ita cike da kulawa da damuwa yana cewa ‘Makaranta kuma?

    Ba nace zan dinga kai ki ba? Yanzu ke saboda rashin tausayi sai ki taso shi da wannan safiyar kawai don ya kai ki makaranta? Ke abu ba zai wuce a wajenki ba? Ta juya cikin halin ko in kula tana cewa ‘Shi ne ya karɓi timetable ɗina yace zai dinga zuwa yana kai ni ko? Ai a gabanka ya faɗa.’

    ‘Kuma a gabanki na ba shi haƙuri ai; wannan wanne kalar abin kunya ne ina nan kuma ina da abin hawa amma za ki taso Baffa ya zo ya kai ki makarnta don Allah? Dariyace take son ta ƙwace mata saboda yanda duk ya muzanta kamar ma Baffa yana tsaye yana kallonsa. Kafin ta ba shi amsa ya ɗauki wayar tata ya dannawa Baffa kira ya miƙa mata waya yana cewa ‘ki gaya masa zan kai ki ba sai kin yi min wulaƙanci ba.’

    Kafin ta yi magana har Baffan ya ɗauka, don haka ta kara a kunnenta tace ‘Um Baffa ka bari ma Abban Afaf zai kai ni makarantar. ’Yace ‘Ah, kin tabbata dai ko? ‘Eh Baffa, ga su ma tare za mu fita gaba ɗaya shiryawa muke.’

    Ya zare wayar daga hannunta kafin ta sake magana ya kara a kunnensa cike da girmamawa yace ‘Baffa za mu tafi tare in sha Allahu, zan dinga kai ta. A yi haƙuri. Yace ‘To, to babu laifi. Allah ya yi muku albarka. Ya ajiye wayar yana harararta yana cewa ‘Yanzu zan je na shirya, ke ma ki shirya sai mu fita gaba ɗaya ko kuma idan na kai su sai na dawo kafin nan kin ƙarasa sai mu wuce.’

    Tace ‘Um, ka ga babu komai fa, za ku iya tafiya ma sai na wuce kawai ba sai na gayawa Baffan ba.’ Ya kakkafe ta da ido yana harararta har sai da ta sunkuyar da nata idanun, ya juya yana cewa ‘Ki shirya nace. ’Ya fice ya bar ta a nan. Ta yi dariya ta cigaba da aikinta.

    Ba ta da zaɓi haka ta shirya suka fita tare, kuma daga wannan lokacin ya zama ko da wanne lokaci zata makaranta haka yake barin abinda yake yi ya zo ya kai ta. Sai dai idan ta gama abinda take yi kawai sai ta hawo motar haya ta dawo.

    Karanta  Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyar

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyar

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyar

    Da asubar fari ya tashi, bayan ya gama alwala ya fito da niyyar tafiya masallaci ya ƙarasa ƙofar ɗakinta ya murza hannun ƙofar ko zai ji ta a buɗe amma sai ya ji ta a rufe, sai dai ya hango fitila ta ƙasan ƙofar ɗakin a kunne. Don haka ya kaɗa kai ya wuce masallaci ya san ta riga ta tashi.

    Tun kafin ta tayar da sallah cikinta yake ƙugi saboda jiya ba ta ci abincin dare ba ta kwanta, don haka tana idar da sallah ta gama azkar ɗinta ta buɗe ƙofar ɗakin ta fito ta wuce kitchen; a lokacin Rashida da su Afaf babu wanda ya tashi domin dama ita ce take tashin Rashida kafin ta yi sallah su kuma su Afaf bayan ta idar da sallar.

    Tana shiga ta ɗora ruwa kofi ɗaya ta jira ya tafasa, ta haɗa shayinta mai kauri a babban kofi ta ɗauki burodi ta gutsura ta ɗauka ta nufi ɗaki. A falo ta ci karo da shi ya shigo daga masallaci, ya dube ta yace ‘Shayi za ki sha da sanyin safiya kuma.’

    ‘Um.’ Ta ba shi amsa sannan ta wuce ɗakin. Da hanzari ya bi ta don kada ta rufe ƙofar, ya cimmata a daidai lokacin da take zama a kan dadduma tana ajiye shayin nata. Ko kallon inda yake ba ta yi ba balle ta nuna ta san mutum ya shigo. Ya ƙarasa ya zauna a gefen gado yana cewa ‘Sai kin gama za ki taso yaran ne? Akwai school fa.’

    Ta gutsiri burodi ta tsoma a shayin sannan tace ‘Ba ni da lecture sai 9am so idan na gama zan ɗan koma ne na rage bacci zuwa kamar 8am sai na tashi na shirya. Ya ɗan yi dariya a kaikaice don ya san kwanan zancen, yace ‘Haba dai, ai kya daure ki shirya yaran kafin ki koma ki kwanta ko?’

    ‘Oh, ai kuma ka cire al’amarinsu daga hannuna ka saka a hannun sakatariyarka kamar yanda ka sanar da ni a aikace jiya don idan ban manta ba ma ita ce ta kawo muku dinner. Ko ba komai ma ka huta da mita ta. Ta ɗauki kofin sahyinta ta cigaba da kurɓa.

    Ya ɗan tsaya yana ƙare mata kallo saboda yanda ya kasa fassara yanayin fuskarta domin kamar ranta ba a ɓace yake ba kamar ma dai tana cikin yanayi na nishaɗi. Yace ‘Common Khadija, na riga fa na gaya miki cewa ban same ki a waya ba shi yasa nace ita ta je ko? Ko da wani abu ma ai sai ki shirya su idan na kai su makaranta sai mu ƙarasa maganar kin ga lokaci yana ƙurewa.’

    ‘Babu ma wani abu, na riga na fahimci saƙon. Ya miƙe yana cewa ‘To don Allah ki fito ki shirya su kin ga idan suka makara rufe gate za a yi. Ta cigaba da shan shayinta kamar ba da ita yake magana ba, ya fara kosawa don haka kamar a hasale yace ‘Kina ji ina miki magana ko?’

    Ta kalle shi suka haɗa ido tace ‘Na ji. Ya kalli agogon bangon da yake ɗakin ya ga ƙarfe shida saura kwata, ya juya ya fice ba tare da yace komai ba. Ya wuce ɗakin yaran don ya kula so take yi su makara. Idan ya taso su in ya so sai su zo da kansu su gaya mata ta taso ta shirya su.

    Yana ficewa ta tashi ta tura ƙofar a hankali ta mayar ta kulle ta bar mukullin a jiki, domin yau babu wanda za ta shirya sai dai a yi duk abinda za a yi. Tana zama a kan daddumar ta ji Nasreen tana buga mata ƙofa tana cewa ‘Anti mun tashi. Har ta gaji da bugun ta ruga banɗaki ba a buɗe mata ba.

    Ya fito daga ɗakin nasu Rashida tana biye da shi, ya dube ta yace ‘Je ki taya mana ku shirya yara, kun kusan makara fa. Ta wuce kitchen yayin da ya nufi ɗakin Khadeeja, ya murza hannun ƙofar yana turawa ya jita a rufe ‘Ya juyo da mamaki yana hango kitchen yana cewa ‘Ko kina kitchen ne?’

    Ya wuce ya nufi kitchen ɗin, yana shiga ya dubi Rashida yace ‘Ba ta fito ba? Tace ‘Eh. Ya yi tsaki ya juya ya fice. Ya koma kƙfar ɗakin nata ya ƙara ƙwanƙwasawa, sai sai har ya gaji da ƙwanƙwasawa ba ta buɗe ƙofar ba, yana kallo ta ƙasan ƙofa ya ga duhu alamar an kashe fitilar ɗakin. Ya ja tsaki ya wuce ɗakinsa, yana shiga ya ɗauki wayarsa ya fara kiran lambarta.

    Sai dai har ya gaji da kira ba ta ɗauka ba. Don haka ya ajiye wayar a kan gadon ya fito daga ɗakin ya wuce kitchen, yana shiga ya tarar da Rashida tana tattare fulawar da ta kwaɓa jiya za a yi shawarma wadda Khadija ta bar ta a nan a buɗe ta kwana har ta bushe. Yana shiga ta bar abinda take yi ta tsaya tana kallonsa.

    Yace ‘Ya ba ki fara komai ba kika tsaya kina kallona? Uhm ai ban san me zan fara ba. Me kuke yi ke da ita idan za ta shirya ‘yan makaranta? Um, ai ita ce take yin abincin ni taya ta nake yi, kuma yanzu ban san me za ta dafa ba. Mtsewww!’ Ya ja tsaki sannan ya juya kamar zai fice sai kuma ya dawo yace ‘Ki ɗora ruwan shayi mana da abincin tafiya makaranta.’

    Ya juya zai fita tace ‘Um to abincin makarantar me za a dafa? Ya kalle ta cike da takaici; wai wannan wacce irin daƙiƙiyar yarinya ce? Yace ta dafa abincin ma sai kuma ya gaya mata abincin da za ta dafa. Kamar zai fice kuma sai ya tsaya yace ‘Ki dafa indomie. ‘To.’ Ta amsa jikinta na rawa ta juya ta shige store domin ɗauko indomie.

    Yana dawowa parlor ɗin ya jiyo Afaf tana hayaniya da Shukra a kan shiryawa, har ya nufi ɗakin sai kuma ya fasa ya wuce ƙofar ɗakin Khadeeja ya ƙwanƙwasa ƙofar a hankali yana cewa ‘Khadija ki buɗe mana. Babu wanda ya ba shi amsa don haka ya koma parlor ɗin ya zauna yana jiyo hayaniyar yaran a ɗakinsu suna shiryawa.

    Jimawa kaɗan ya tashi ya nufi ɗakin inda ya sa hannu ya fara ƙoƙarin taya su shiryawa. Nan da nan suka gama sannan ya taso su a gaba suka fito inda ya saka su a gaba suka sha shayi da burodi sannan a gurguje Rashida ta zuba musu indmie ɗinsu a flask ya tasa su a gaba suka fice.

    Khadeeja tana jin fitarsu da mota ta fito daga ɗakin a shirye ta sallami Rashida ta sanar da ita idan ya dawo ta fice ta tafi maƙota in ya so idan zai fita sai ya yi mata magana ta dawo; Haka suka saba tunda Shukra ta shiga makaranta; idan dai ba tare da yara zai fita ba sai dai Rashida ta je maƙota ta jira idan ya gama zai fita sannan ta dawo ta shiga gidan.

    Bayan ta gama sallamar Rashida ta fice ta tafi makaranta. Suna dab da ƙarasawa makarantar aka rufe gate ɗin, gaba ɗaya masu gadi da sauran ma’aikatan suka shige ciki suka rufe ƙofa; wanda hakan yake nufi babu yaron da zai sake shiga. Ya tsaya ya cije leɓe na ɗan lokaci sannan ya kunna motar suka kama hanyar komawa gida.

    Nasreen tace ‘Mun makara, ga shi ba mu taɓa makara ba. Yace ‘E, kun tsaya kuna ta faɗa ba ku shirya da wuri ba. Afaf tace ‘Abba Anti ba ta da lafiya ne? Ya shafa kansa yana cewa ‘Eh, ba ta jin daɗi. Shigowa gidan suka tarar da Rashida a tsaye a bakin ƙofa kamar yanda ta saba jiransa, tana ganin su ta bi su suka shige.

    Shi kuma Abbansu ya ƙarasa ƙofar ɗakin Khadeeja ya fara ƙwanƙwasawa yana yi yana cewa ‘Khadeeja da Allah ki buɗe mana. Rashida ta fito daga ɗakin su Afaf tace ‘Antin ta tafi makaranta. Ya kalle ta da mamaki yace ‘Makaranta? Yaushe? ‘Bayan kun fita.’

    Ya wuce ɗakinsa ya bar ta a nan. To me Khadija take nufi ne? Daga yin abu ta ma ƙi ta zauna a yi magana tana ta wulaƙanci, ga shi har ta sa yara sun rasa makaranta. Yanzu ga shi dole ya fita ya bar su a gidan su kaɗai abinda ba ya so. Amma wannan wulaƙancin na Khadeeja fa ya fara yawa, ta ma ƙi ta saurare shi gaba ɗaya. Yanzu ya take so a yi?

    Haka ya wuce ɗakinsa ya zauna ya fara kiran wayar Khadeeja amma har ya gaji da kira ba ta ɗauka ba. Ya duba lokaci ya ga karfe takwas da rabi, ga shi yana da meeting ƙarfe tara. Don haka a gurguje ya tashi ya shiga wanka ya shirya. Ko abinci bai tsaya ci ba ya fice ya bar yaran.

    Babu wanda ta gayawa yanda suka yi da Mustapha, don ko su Rahma ba ta cewa komai ba; su kuma da suka kula ba ta son magana sai kawai suka ƙyale ta. Haka ta yi zamanta a makaranta har wajen ƙarfe biyar na yamma sannan ta kamo hanya ta dawo gidan. Tana shigowa yara suka fara yi mata oyoyo; da murnarta ta amsa sannu da zuwansu kamar yanda ta saba.

    Ta kalli Afaf tace ‘Bari na je ɗaki na sha magani na huta, kaina ciwo yake yi. Ba tare da ta saurari amsarta ba ta shige ɗakin ta turo ƙofa. Sai bayan sallar isha’i sannan ya dawo, lokacin Afaf ta sa Rashida ta dafa musu taliya sun ci abincin dare saboda Khadeeja tace kada wanda ya sake buga mata ƙofa.

    Yana shigowa gidan ita ya fara tambaya suka ce masa tana ɗaki, sai dai ga mamakinsa yana taɓa ƙofar ya ji ta a rufe. Nasreen ce ta sanar da shi cewa tace a daina buga mata ƙofa ba ta da lafiya. Don haka shi ma sai kawai ya ƙyale ta ya cigaba da harkokinsa har sai da yara suka kwanta.

    Wajen ƙarfe goma na dare ya sake ƙwanƙwasa mata ƙofar, ta yi banza da shi ba ta ce komai ba. Ya matsa jikin ƙofar yace ‘Wallahi Khadeeja idan ba ki buɗe ƙofar nan ba zan ɓalla ta. Tana daga ciki ta ɗauki ‘yar saman rigar baccinta ta saka sanna ta zo ta buɗe masa ƙofar tana riƙe da wayarta tana chatting.

    Ta koma ciki ta ƙarasa kan gado ta zauna ta miƙe ƙafarta ba tare da ta ce masa komai ba. Yana daga tsaye ya ƙare mata kallo sannan yace ‘Wai wanne irin wulaƙanci ne wannan kike yi ne Khadeeja? Kin bar min yara sun makara a makaranta kuma kin fice kin bar gida ba tare da wani bayani ba?’

    ‘To ai ka san dai yau ina da lecture ko?’ Ta ba shi amsa sannan ta sake mayar da hankali a kan wayarta. To don me ba ki tashi kin shirya yara ba kuma da kika dawo kika sake rufe ƙofa kika bar su. Au wai Najan ba ta zo ba? Ai na zata ta yi musu komai tunda yau ita ce da aiki.’

    Ya cije leɓe sannan ya ja dogon tsaki ya fesar da iska saboda yanda Khadeeja take ƙure shi ‘Na gaya miki babu komai a tsakanina da ita sakatariyata ce kawai, don Allah wai me kike so na yi miki ne a kan wannan maganar. Idan kuma don ta je makarantar yara ne to ki yi haƙuri ba za ta sake zuwa ba, babu wata alaƙa tsakanina da ita dama sai ta office.’

    ‘Ai na ga alama.’ Ta faɗa ba tare da ta daina kallon wayara ba. A fusace yace Khadeeja ni nake miki magana kina danna waya ko kallo ban ishe ki ba? Ta ajiye wayar a gefenta ta kalle shi tace ‘Shike nan, na ji duk abinda ka faɗa. Please kada ki sake rufe ƙofar nan, kuma ga yara can sun kwanta da safe ki tashe su da wuri kada su makara.’

    ‘Ok. Har ya juya zai fita ya ɗan tsaya yace ‘Kuma kin san ke ma ba a nan kika saba kwana ba. Ok. Ya fice ya bar ta.Ta murguɗa baki kamar yana kallonta tace ‘Ɗan rainin hankali, ba ka yi laushi ba tukunna ka je ka ɗauko Naja ta zo ta dinga yi maka hidimar kai da yaran. Yana fita ta zame ta yi kwanciyarta sai dai ba ta rufe ƙofar ba.

    Tana jinsa ya dawo ɗakin ya leƙa fuskarta ta yi kamar bacci take, don haka ya fice ya bar ta bayan ya kashe mata fitila. Ya yi zaton kamar yanda ta amsa masa da daddare za ta tashi ta shirya yara, sai dai abinda ta yi jiya shi ta sake maimaitawa. Ta saka mukulli ta kulle ɗakin, ya buga har ya gaji ba ta buɗe ba.

    Don haka ba tare da ɓata lokaci ba ya tsaya a kan yara suka shirya ya kwashe su ya kai su makaranta. Kafin ya dawo ta fice ta bar masa Rashida a gidan. Takaici ne ya sake kama shi; to me Khadeeja ta mayar da shi ne? Wannan wane kalar taurin kai ne take yi haka? Kuma me take nufi?

    Yanzu me take so ya yi mata; yaya ma zai yi da ita don gaskiya idan ba so take ya doke ta ba bai san me zai yi mata ba. Haka ya shirya ya fice ya nufi office. Har ya kusa ƙarasawa office ɗin dabara ta faɗo masa; ya karkata kan motar ya nufi gidan su Khadeeja.

    Gara ya je ya kai ƙararta waje Baffa in ya so su tsawatar mata don shi yanzu idan ba duka ba bai san me take so ya yi mata ba. Ya ci sa’a ya sami Baffa yana shirin fita, bayan sun gaisa Baffa yace ‘Lafiya kuke dai na ganka da sassafe ko?’ Nan ya mayar masa da abinda ya faru da kuma yanda Khadeejan take rufe kanta a ɗaki, sai dai ce masa ya yi ya rasa Khadeejan ne a waya shi yasa ya tura sakatariyar tasa.

    Baffa ya yi dariya yace ‘Kishi ne nasu na mata ya motsa, ka san a kan wata macen komai son da matarka take maka to za a ji kanku. Kada ka damu bayan Magriba ka ɗaukota ku zo nan. Zan kirawo ta don ma kada tace za ta yi taurin kai. To Baffa, na gode.’

    Ya yi musu sallama ya fice yana jin daɗin matakin da ya ɗauka tunda ya san ko babu komai Baffa zai yi mata faɗa kuma ya san dole ta shiga hayyacinta. Suna shirin shiga lecture wayarta ta yi ƙara, tana dubawa taga Baffanta ne don haka ta ja da baya ta nemi waje ta amsa. Bayan sun gaisa yace ‘Khadeeja, na cewa Mustapha ku zo bayan magriba ke da shi kin ji ko?’

    Tace ‘Um Baffa yau? Wani abu ya faru ne? Babu abinda ya faru, ku dai zo ɗin. To Baffa in sha Allahu za mu zo, in ya dawo zan gaya masa. Kada ki damu na gaya masa ma, yanzu ya bar nan. Ta amsa suka yi sallama da Baffa tana dariya, don ta san inda zancen ya dosa, ta gane Mustapha ƙararta ya kai duk da ba ta zaci haka ba.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Huɗu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Huɗu

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Huɗu

    Kwanci tashi cikin wannan rayuwar da Khadeeja take a gidan Mustapha har ta gama level 2 a karatunta ta shiga level 3, kuma shekararsu biyu kenan da Rashida mai aikinta. Zaman dai haka ake yinsa cikin dagewa da dagiya; idan Mustapha yana son buƙatarsa a wajenta sai ta ji kamar ba shi ba saboda yanda yake kwantar da kai ya samu buƙatarsa ta biya.

    Amma kuma da zarar ta yi maganar karatunta ko wani abu da zai sa ta fita daga gidan ba tare da ta tafi da yara ba to sai ya nuna ɓacin ransa. Domin a halin yanzu kowa a danginsu ya santa da ‘yayanta domin tare ake ganinsu ko bikin wa ake yi. Gidan Mommy kuwa sun mayar da shi kamar gidan kakarsu, kuma da yake sun sami karɓuwa sai suka sake sakewa.

    Karatunta yana tafiya daidai tunda ta saka auduga ta toshe kunnenta daga duk wata mita ta Mustapha, sai dai kawai kullum a gajiye take daga aikin gida da kuma aikin tunanin abinda za ta yi Mustapha ya daina nuna mata halin ko in kula. Yaran ba su saba ba ta matsala ba a da, amma zuwa yanzu duk tana neman ta rasa kansu; musamman Afaf da Nasreen.

    Idan dai aiki ta saka su ba za su ce ba za su yi ba amma idan ba su ga dama haka za su yi kunnen uwar shegu da ita sai dai ko ta yi aikinta ko kuma ta sa Rashida ta yi mata. Sannan kuma yanzu Afaf ta ƙulla ƙawance da Samira ‘yar wajen Yaya Jidda, don haka kusan duk wani motsi na Khadeeja Afaf sai ta gayawa Samira wadda take kai wa uwarta rahoto na kai tsaye; don haka ne ma matsawar da Yaya Jidda take wa Khadeejan ta ƙaru.

    Sai dai a yanzu ba wannan ne damuwar Khadeeja ba, babbar damuwarta ita ce rashin haihuwa. Tun bayan da ta yi ɓari a loakcin corona ko ɓatan wata ba ta sake yi ba ga shi ana neman shekaru biyu. Zaman gidan ba ya mata daɗi, ba ta jin daɗin yanda yaran suke mata, musamman Afaf wadda a da take tunanin sun zama ɗaya. Tana fatan ita ma Allah ya ba ta nata ‘yayan waɗanda za su kalle ta a matsayin uwa.

    Ta riga shi kwanciya kamar yanda suka saba saboda yanda ta kula idan ta zauna jiransa su kwanta tare ita ake cuta tunda dole ta tashi kafin asuba ta shirya yara. Sai wajen sha biyu saura sanna ya gama abinda yake ya kwanta a kusa da ita, ta juya ta gyara kwanciyarta.

    Yana kwance amma ya ɗaga waya yana chattinga kamar yanda ‘yan kwanakin nan ta kula kullum kafin ya kwanta sai ya yi chatting. Ta miƙe ta je ta yiwo fitsari, ta sha ruwa sannan ta dawo ta kwanta, zuwa lokacin ya gama chatting ɗin ya ajiye wayar yana azkar. Ta kwanta ta gyara kwanciyarta, bayan da ta kula ya gama azkar ɗin ta lalubo hannunsa ta riƙe cikin sanyin murya tace ‘Abban Afaf.’

    ‘Umm.’ Ya amsa yana kallonta duk da hasken da yake cikin ɗakin bai kai ya kawo ba. ‘Uhm, gaskiya ina son zuwa asibiti na ga gynae doctor.’ Ta faɗa tana wasa da hannunsa wanda ta riƙe. Ya riƙe hannunta a cikin nasa ya ƙara ba ta hankalinsa yace ‘Baki da lafiya ne?’

    ‘No ba wani specific issue. Ka san dai kwanaki nace maka ina son na je a duba a ga abinda yasa har yanzu ban sake samun ciki ba, kada na je wata matsala ce na yi ta zama gara na je a duba. Ya gyara kwanciya ya ƙara matsowa kusa da ita ‘Kina dai so ki ɗorawa kanki damuwa, har yanzu fa ba a yi shekaru biyu da ɓarin ba.

    Iya wannan ya isa ya sa ki san cewa lafiyarki ƙalau, kawai Allah ne bai kawo ba tunda wancan ɗin ma ba asibiti kika je kika samo ba ko? Na sani, amma dai gaskiya ina so na je a duba ni ɗin na sami nutsuwa. Tunda ka ga idan na je aka ce min lafiyata ƙalau ai dawowa zan yi kawai na cigaba da addua’a, idan kuma matsala ce sa na nemi maganinta.’

    ‘Babu wata matsala kina dai son tonowa kanki matsalar. Ke yanzu ma da kike neman ciki ido rufe ya za ki yi da karatun? Tunda ga shi kin shiga level 3 kuma ke da kanki kina cewa ya fi wahala. Ya za ki yi da laulayi ga karatu? Ko har kin mata ne? Ai zai fi sauƙi idan ma dole ne sai kin je asibitin ki bari ki gama karatun kafin ki kwantar da kanki.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, kowa da abinda yake tunani. Jimawa kaɗan tace ‘Ina son zuwa gaskiya, amma dai ina jin zan bari mu gama exams ɗin wannan semester in ya so kafin a koma hutu sai na samu na je. To Allah ya kai mu.  Tana son ta haihu duk da dai Mommy ma tace mata lafiyarta ƙalau amma ita gaskiya tana so ta je a duba ta.

    Kuma yanda Mustapha yake gwada mata halin ko in kula idan ana maganar haihuwa ya sa gaba ɗaya ta fara tunanin ko bai damu da ta haihu ba; to ya ma za a yi ya so ta haihu tunda shi masoyiyarsa ta haifar masa yara har uku? Haka ta yi ta saƙe-saƙe tana juyi, sai gefin asuba sannan bacci ya ɗauke ta.

    Kamar kullum yana shiga office ɗin yau ma damuwarsa ta yaye; musamman yanda ƙamshin turarenta ya yi wa ƙofofin hancinsa maraba bayan da ya shiga office ɗin nasa ya rufo ƙofar. Wannan ya tabbatar masa da cewa ta riga ta zo office ɗin wataƙila wani office ɗin ta je. Ya ajiye jakarsa a kan table ya ƙarasa ya zauna a kan kujerarsa cike da farin ciki.

    Sabuwar sakatariyarsa Naja’atu Musa Bello; watanta uku da fara aiki amma soyayya mai ƙarfi ta ƙullu a tsakanisu. Duk wata damuwa da Khadeeja za ta ɗora masa da ya shigo office ɗin ya ganta yake mantawa da ita, idan kuma an tashi daga office ko a ranakun da babu aiki ya kan je gidansu zance. Duk da dai manya ba su riga sun shiga zancen ba amma dai yana ji a jikinsa Naja’atu tasa ce.

    Bai daɗe da zama ba ta turo kofar ta shigo, daga tsaye ta sakar masa kyakkyawan murmushinta wanda ba ya gajiya da kalla. ‘Ranka ya daɗe barka da shigowa.’ Ta faɗa tana juya ƙwayar idonta. ‘Good Morning my dear.’ Ya amsa yana ta faman murmushin da yake barazanar ƙarawa bakinsa faɗi.

    Ta ƙarasa ta zauna a kujerar gabansa, sannan ta ɗauki file a kan teburin ta miƙa masa. Nan take ya buɗa ya fara karantawa yana mata tambayoyi tana yi masa bayani. Bayan sun gama ya ajiye file ɗin a gefe ya dube ta yace ‘To meye labari? Ta yi dariya ta sunkuyar da kai a kunyace tace ‘Komai normal. Good. So na yi mana order ɗin lunch ko? Don na san ko an ce ki zo mu je mu ci a waje ba kya son zuwa eateries, sai shopping ko?’

    Ta yi dariya tace ‘Gara dai a yi order ɗin. Ba damuwa, ki yi mana order ɗin sai ki turo min account number na tura kuɗin.’ Yes Boss, an gama. Suka yi dariya gaba ɗaya. Tana shirin tashi yace ‘Yauwa, gobe ana open day a school ɗin su Afaf, please idan kika shigo around 10am sai ki je musu, ki jiyo min duk bayanansu da performances ɗin su.’

    Ta gyara zama tace ‘Uhm, ok. But Madam ba ta nan ne ko ba ta jin daɗi? Ya gyara zama ya fara lilo a kujerar da yake kai yana kallonta sosai sanna yace ‘No, lafiyarta ƙalau but na dai fi son ke ki je ki jiyo min komai. Cike da farin ciki ta sake faɗaɗa murmushinta tace ‘Yes Sir, Allah ya kai mu. Kuma Allah ya sa kada ka sa yayata ta ba ni query saboda na shiga aikinta duk da dai ni ma ‘yayana ne.’

    Ya yi dariya ‘Kada ki damu, ba ki da matsala da ita. Suka sake ɗan taɓa hira sannan ta fice ta koma office ɗinta cike da farin cikin yanda alaƙarsu take tafiya ita da ogan nata. Ba za ta taɓa bari Mustapha ya kufce mata ba don ta ga mijin aure. Ta gama degree ɗinta har ta yi masters, saurayinta na ƙarshe har sun zo gaisuwa haka kawai ya daina zuwa sai ji kawai ta yi ana bikinsa da ‘yar uwarsa.

    Duk da ta san ba wasu shekaru ne da ita masu yawa ba domin shekarunta 28 kacal, amma dai ta san an matsu ta yi aure a gidansu; musammam ummanta wadda aikin ma so ta yi ta hana ta sai ta yi aure. Sai ga shi ashe mijin yana wajen aikin. A hankali suka saba, har suka kai yanzu da take jin za ta iya cewa ta fi matarsa sanin halin da yake ciki da inda yake a kowanne lokaci.

    Don haka ma take jin cewa ƙwace shi a wajen Khadeeja kamar ƙwace goruba ne a hannun kuturu, domin tun yanzu tana jin ta fara samun nasara tunda kullum ita yake kawowa ƙarar Khadeejan sai ta ba shi haƙuri, ta riga ta fahimci irin zaman da suke yi da Khadeejan don haka ta gama shirya musu; lokaci kawai take jira.

    Ƙarfe sha ɗaya take da lecture don haka sai da ta gama shirya yaran dukansu suka fita makaranta sannan ita ma ta ƙarasa ayyukanta ta shirya. Ƙarfe goma da minti biyar tana zaune a gaban mudubi tana gyara fuska ta tuna jiya da daddare Shukra ta ce mata Anty tace kowa ya zo da Mommy ɗinsa open day 9am to 11am sannan sai a zarce da sports.

    Kuma idan dai ba ta manta ba ma Afaf ta gaya mata duk da section ɗin su Afaf ɗin daban da na su Shukra. Sai dai ba su yi maganar da Abbansu ba, bai gaya mata ita ce za ta je ko shi ne zai je ba gaba ɗaya ta manta ba ta tambaye shi ba. Ta miƙe ta ɗauko wayarta wadda take ajiye a gefen gado ta dannan masa kira.

    Sai da ta kirawo sau uku duka wayar ba ta shiga ba, don haka ta yanke hukuncin idan ta fita sai ta fara tsayawa a makarantar tasu tukunna kada ta je sai ta wuce makaranta ya bugo waya yace ita ce za ta je ya jiƙa mata aiki. Nan da nan ta ƙarasa shiryawa ta saka jilbab ɗinta me kalar lilac sanna ta saka baƙin sneakers ɗinta ta sallami Rashida sannan ta wuce.

    Tana zuwa makarantar kai tsaye ajinsu Shukra ta wuce, duk malaman nasu sun santa saboda zuwa ɗaukansu don haka ba tare da ɓata lokaci ba aka ba ta bayanan Shukra da kuma results ɗinta na CA. Tana gamawa ta ja hannun Shukra suka wuce ajinsu Nasreen inda nan ma aka haɗa mata komai, Nasreen tana cikin waɗanda za su yi wasan tsere don haka ba ta samu ta fita daga aji ba Khadeeja ta ja Shukra suka nufi secondary section don ta karɓo sakamakon Afaf da Habib.

    Tun kafin su ƙarasa kofar secondary section ɗin ta hango Afaf tare da wata mata sanye da baƙar abaya da brown envelops a hannunta, suna tafe suna hira; ga dukkan alamu a dai malama ce a nan makarantar duk da ita Khadeeja ba ta taɓa ganinta ba. Da suka ƙara matsowa kusa Shukra ta zare hannunta daga na Khadeeja tana cewa ‘La, Anti Naja ce ga su nan ita da Yaya Afaf.’ Ta ƙarasa wajensu da gudu.

    Da fara’arta ta cimmusu, suna haɗuwa ta ƙara faɗaɗa murmushinta cike da girmamawa tace ‘Sannu Anti. Cike da mamaki ita ma ta ɗan yage baki mai kama da murmushi tace ‘Yauwa, sannunmu. Ya aiki ya yaran?’ ta kula da yanda ta ke magana kamar da ƙyar don haka kafin ma ta ba ta amsa ta mayar da hankalinta ga Afaf tace ‘Yaya Afafa mu je na karɓo muku CA report ɗinku ke da Habib na wuce don ni ma school zan je.’

    Ta ɗan ɗaga gira cikin halin ko in kula tace ‘Anti Naja ta karɓar mana ai, dama na su Shukra za ta je ta karɓa yanzu. Ta kalli Afaf ɗin sannan ta kalli malamar da aka kira Anti Naja tana mamaki tace ‘Me yasa? Anti ai da kin bar shi na zo gashi sun saka ki aiki. Ta kawar da kai ta ɗaga gira tana cewa ‘No ba wani aiki, ai Abbansu ne yace na karɓar musu.’

    Ita ma Khadeeja ta dan zaro ido tace ‘Oh, ya zo kenan ko yaushe yace a karɓar musu?’ Afaf ta fahimci Khadeeja ba ta san Naja ba kuma ba ta ma san da zamanta ba, sabanin ita da ƙannenta waɗanda a cikinsu za ta iya cewa Shukra ce kawai ba ta san Naja ba ko kuma ta santa amma ba ta san wacece ita ba. Ta ɗan yi gyaran murya tace ‘Anti ba fa malamarmu ba ce, sakatariyar Abba ce kuma shi ne ya turo ta daga office ta zo mana open day ɗin.’

    Mamakin Khaddeja ya ƙaru, ta sake ƙarewa Naja kallo na ɗan takaitaccen lokaci sannan ta buɗe baki za ta yi magana sai kuma ta fasa. Ta ɗan yi murmushi da gefen baki sannan ta kalli ƙasa ta ɗago suka haɗa ido da Najan wadda take mata kallon da ta kasa fassarawa sanna tace ‘Oh, ok, Umm.’

    Kafin ta ce wani abu Habib ya ƙaraso wajen yace ‘Yauwa Anti kin ƙaraso? Dama ke nake jira; don Allah zo mu je ki cewa uncle ni ba na son basket ball team ya bar ni na shiga football team. Haka kawai wai saboda ni dogo ne sai na yi basketball. Kafin Khadeeja ta yi magana Najan tace ‘Au shi ne ba ka gaya min ba Habib, ai da ka gaya min na yi masa magana.

    Dama Anti nake jira.’ Ya faɗa cikin halin ko in kula ya zari envelop guda ɗaya daga hannun Najan ya miƙawa Khadija yana dariya yace ‘Anti guess what? Ta ɗan yi murmushi yayin da suka bar Naja da baki buɗe, tace ‘What? Ya zaro takarda ɗaya ya miƙa mata yana cewa 38 naci a Hausa yau don haka yau da shawarma zan yi dinner ko?’

    Ta karɓa tana dariya sannan ta ba shi hannu suka tafa tace ‘Iyye, ai dole ka ci shawarma tunda yau ka wuce gori. Haba ko kai fa, kullum komai ka ci A da B amma a Hausa ka dinga cin D da F. Ya miƙawa Khaddeja envelop ɗin yana cewa ‘To za ki ga Uncle ɗin? Tace ‘No, tunda yanzu ka ga kun riga kun fara games ina jin ka bari sai gobe sai na zo na gan shi.

    Kafin nan mun tattauna a kan football da basketball ɗin kuma mun yi magana da Abbanka ko? Ya gyada kai ‘Eh, haka ne. Naja ta yi sauri tace ‘Idan kina sauri ne ai sai na je naga Uncle ɗin. Tace ‘No ba sauri nake ba, kamar dai goben zai fi dacewa kawai. Habib ya katse su yana miƙawa Khadeeja envelope ɗin yana cewa ‘Anti sai mun dawo, goben kya zo kawai.’ Ya wuce ya bar su a nan.

    Naja ta miƙawa Khadeeja hannu tana cewa ‘Ki kawo na tafi wa da yallaɓai takardun tunda office zan koma. Ta ɗan yi murmushi tace ‘No ina ga gara ni na tafi masa da su tunda a gidansa zan kwana. Ta ɓata rai tace ‘Um, sai an jima. Ta wuce riƙe da takardun Afaf da suke hannunta Afaf ɗin tana biye da ita suna hira.

    Khadeeja ta bi bayansu da kallo tana mamaki; to yaushe ya yi sabuwar sakatariya? Tunda da dai ta san sakatarensa namiji ne. kuma har yaushe sakatariyar ta kai matsayin ta zo wa yara open day har tana wani cewa a ba ta takardu ta kai masa? Tukunna ma; kamar dai yaran nan sun sa wannan sakatariyar, ita ce ba ta santa ba.

    To kenan har ya yi introducing ɗinta a wajen yaransa a matsayinta na wa? Me yasa suka kwana tare bai ce mata tazo open day ba kuma bayan ya fita ma ya kasa kiranta? Wanda tunda ta aure shi duk wata harkar makarantar yara ita ce take zuwa kuma shi yake saka ta ta zo. To me yasa wannan ya sa sakatariya? Naja? Ba ta son ta yanke hukunci cewa akwai wani abu tsakanin Mustapha da Naja amma dai tabbas tana da tarin tambayin da zai amsa mata.

    Sai da ta raka Shukra aji sannan ta nufi fita daga makarantar. Tun kafin ta gama fitowa daga cikin ginin makarantar zuwa farfajiyar wajen da ake ajiye motoci ta hango su, tana riƙe da hannun Afaf suna magana har suka ƙarasa bakin motar gefen direba ta sa mukulli ta buɗa motar; ta dan ja baya ta labe. Me take gani ne? Motar Mustapha? To shine ya kawo ta ko me? Tana nan a laɓe ta hango su; Naja ta buɗe motar ta zauna a kujerar direba sannan ta yi wa Afaf sallama ta ja motar.

    Sai da ta karanta lambar motar a fili domin ƙara tabbatarwa motar Mustapha ce; kanta ya ɗaure gaba ɗaya. To me hakan yake nufi? Ya aiko sakatariyarsa ta zo wa yara open day kuma a motarsa. To haɗa kuɗi suka yi suka sayi motar a tare? Ko kuwa dai tsabar ƙauna ce ko rashin hankali ya sa suke sharing motarsa da sakatariya? Me yasa bai aiko ta a motar haya ba ko a motar office? Wato motar da ita idan dai makaranta za ta ko a rage mata hanya ba ta isa ya yi ba ita ce ya ba wa sakatariya take yawo a gari.

    Kai! Gaskiya Mustapha ya raina ta. Ta yi sauri ta fito daga inda ta raɓe lokacin da ta hango Afaf ta nufo wajen. Ta yi mata sallama sannan ta wuce ta fice daga harabar makarantar. A bakin titi ta tsaya, motocin haya sai tsayawa suke ba tare da ta hau ba; gaba ɗaya ma ta manta inda za ta saboda yanda zuciyarta take zafi; me Mustapha yake nufi da ita?

    Har ta juya za ta koma gida saboda yanda take jin ba za ta iya zuwa lecture ɗin ba sai kuma ta tuna idan ta je gidan me za ta yi? Rufe kanta kawai za ta yi a ɗaki ta yi kukan da ba zai mata maganin komai ba; don haka ta sake juyawa ta koma bakin titi ta hau motar BUK. Ta kalli waje ta tagar motar, ta yi murmushi ita kaɗai; wai ita ce a motar haya yayin da ga wata can tana yawo a motar mijinta.

    Ta kawar da kai ta share ƙwalla. Ko da ta ƙarasa makarantar ta san an riga an yi nisa da lecture ɗin kuma ko ta shiga ma ta san babu abinda za ta gane, don haka kai tsaye ta wuce hostel ɗakinsu Rahma inda suka saba zuwa su huta; duk da dai ta san suna wajen lecture amma ta san inda suke ajiye mukullansu. Tana shiga ɗakin ta yi watsi da kayanta ta faɗa gadon Rahma ta kwanta ta fashe da kuka.

    Sai wajen ƙarfe ɗaya da kwata sanna suka shigo ɗakin suka same ta a kwance ta ci kuka ta ƙoshi. Suna shiga Farida tace ‘Haba Malama, tun ɗazu muke kiranki a waya kin ƙi ɗaga wa ashe kina nan abunki. Suka ƙarasa suka faɗa kanta Asiya tace ‘Ko dai abun ya zo ne a tanadi goro da ledar amai. Ta sake fashewa da sabon kuka.

    Suka yi tsuru-tsuru. Rahma ta shafa bayanta tace ‘Kawata kina faɗar mana da gaba fa, don Allah me ya faru? Ko Babe ba shi da lafiya ne? Haka suka yita jero mata tambayoyi, ita kuwa ta yi banza da su har suma suka gaji suka yi shiru, suka zauna kawai suna jiranta. Sai da ta yi mai isarta sannan ta ba su labarin abinda ya faru.

    Rahma tace ‘kada fa na yi ashar ƙawata, kut! Wannan wanne kalar wulaƙanci ne mutumin nan yake miki? Farida tace ‘Motar da yake ƙyashin ɗaukanki ya je ya ba wa budurwa ko ma karuwa take yawo a titi? Lallai an gaida uban Afaf. Rahma tace ‘Gaskiya idan ya dawo yau ya kamata ya yi miki bayani na ganewa, duk da babu wani explanatin da zai sa na yarda babu wani abu a tsakanishi da ita ba sakatariya ba ko DG ce wallahi.

    Ya yi miki bayani kuma kema ki karanta masa; wannan ai zubar da mutunci ne kina yawo a motar haya wata side chick tana yawo a motar mijinki? Mijinki na sunna fa, Haba! Gaskiya dai ya kamata ki san yanda za ki yi ki ƙwaci kanki a hannun mutumin nana tunda shi ga alama bai san mutunci ba.’

    Amina tace ‘Don Allah ku bar ta ta bi abun a hankali. Ta kalle ta rai a ɓace ‘A hankali Amina? Shi a hankali kika ga yana yi min? Ni budurwarsa take cewa wai na kawo takardun yara ta kai masa saboda tsabar samun waje? Haba mana! Farida tace ‘Toh shi dai na gani, aure ai ba hauka ba ne. Wallahi ya kamata ki dage ki gaya masa abinda yake ranki tunda dai an daɗe ana ruwa ƙasa tana shanyewa, ai ba siyo ki ya yi a bakin rimi ba da zai mayar da ke kamar wata sokuwa.’

    Amina tace ‘Don Allah ku bari a bi abun a hankali, miji fa ba kamar saurayi ba ne haba!’ Rahama ta ja hannun Amina tace ‘Taso ‘yar uwa mu nemo abinci wannan batun na masu aure ne ba namu ba kin ji. Haka ta wuni a makarantar nan Amina tana ba ta baki yayin da Farida da Rahma suke ƙara jaddada mata ya kamata ta ɗauki mataki idan ba haka ba rainin zai wuce haka. Sai bayan la’asar sannan ta kwaso kayanta ta dawo gidan.

    Wunin ranar haka ta ƙarasa shi cikin ƙunci, sai da ta cewa yara ba ta da lafiya sannan suka ƙyale ta don kowa yana so ya ba ta labarin sports day. Rashida ce ta ƙarasa duk wata hidimar gida da ta yara, har abincin ma da ba ya so Rashidan ta girka yau cewa ta yi ta girka don a yanda take jin ko ta dafa ba zai yi daɗi ba.

    Sai bayan sallar magriba sannan ya dawo gidan, bayan ya gama hayaniya da yara ya wuce ɗakin ya same ta. Tana kwance ba ta ko juyo ta kalle shi ba don haka ya yi zaton bacci take yi. Sai kawai ya kintsa ya fice daga ɗakin. Ba ta son yi wa yaro alƙawari ta karya don haka tun da ta dawo ta sa Rashida ta haɗa mata duk wasu kayan da take buƙata na haɗa shawarma sanna ta kwaɓa mata fulawar, yanda idan ta fito bayan isha’i sai ta haɗa shawarma kamar yanda ta yi wa Habib alƙawari idan ya yi passing Hausa.

    Suna zaune shi da yaran ta wuce su ta shiga kitchen, nan da nan ta fara ƙoƙarin ɗorawa. Tana daga kitchen ta jiyo yana amsa waya yana kwatancen gida; ta ja tsaki a fili tana fatan Allah ya sa ba baƙo zai yi ba don ko me zai yi ba za ta gaisa da wani baƙo ba balle ta ba shi ko da ruwa. Sai dai ya yi duk abinda zai yi. Kafin ta gama wannan tunanin ta ji shi yana cewa yanzu zai fito, inda ba tare da ɓata lokaci ba ta ji fitarsa.

    Jimawa kaɗan ya shigo da leda ya wuce ya same ta a kitchen tana yayyanka fulawa za ta fara gasawa. Ya miƙa mata ledar yana cewa ‘Ga wannan shawarma ce; sakatariyata ce Naja ta aiko delivery man ya kawo a ba wa yara. Sai ki duba ki zubo a tray mu ci don na ji kamar da yawa’Ta kalle shi da jajayen idanuwanta waɗanda suka koɗe saboda kuka da tsabar mamaki; ta yi murmushi mai ɗaci sannan ta kashe wutar abinda ta ɗora a wuta ta nufo shi yayin da ya miƙa ledar a zaton za ta karɓa.

    Ta bigi kafaɗarsa ta wuce ta shige ɗaki ta bar shi a nan tsaye. Ya bi bayanta da kallo cike da tsananin mamaki saboda Khadeeja ba ta taɓa yi masa irin wannan wulakancin ba; kuma a gaban yara don duk biyo shi suka yi da suka ji yana maganar a juye a ci. Nan take ya ajiye ledar kan sink sanna ya bi bayanta ɗaki; yana shiga ya same ta a tsaye a gaban mudubi tana cika tana batsewa kamar ma jiransa take yi.

    ‘Wannan wane irin wulaƙanci ne ina miki magana za ki yi min tsaki a gaban yara saboda raini.’ Ya tambaya cikin jin kai da isa. Ta kalle shi ta ɗauke kai tana murmushin takaici tace ‘Ji na yi kamar zagina ka yi. Kallon takaicin da yake mata ya koma na mamaki, ya tsare ta da ido kuma ita ma ta ƙi ɗauke nata idon. Yace ‘Ni na zage ki? Ko kuwa dai ke kika zage ni?’

    Ba tare da ta ba shi amsa ba tace ‘Wacece Naja Mtseww!’ ya ja tsaki sannan ya cigaba ‘Sakatariyata ce; shi ne kike nema ki zage ni saboda nace ta kawowa yara abu? Ba ka gaya min ka mayar da ita wakiliyarka a makarantar yara ba, har sai da na je musu open day sannan sai na ganta wai kai ka tura ta. Har tana cewa wai na ba ta takardun yara ita kace ta karɓo.’

    ‘Eh, ai ni nace ta karɓo tunda na fita ban gaya miki ba. Kuma ka kasa yi mi waya kamar yanda kafin yau duk abinda kake so a yi na yaran kake min waya ko da ina sama jannati ne na je na yi? Ya fara hasala saboda yanda take maganar a tsiwace ga wani kallon raini da take masa.

    ‘Ba fa na son wulaƙanci khadeeja; ni na tura ta ta karɓo ko ban isa ba ne? Na zata za ki yi murna tunda kullum cikin ƙorafi kike da mitar hidimar yaran saboda kina gani ba ke kika haife su ba, ke naki karatun ne a gabanki. Ta yi murmushi tace ‘Ka isa har ka yi yawa, kuma alhamdulillahi tunda an sami mai karɓa ta yanzu kam zan huta da wasu abubuwan. Kuma na gane ni ce ban isa na shigar maka mota ba shi yasa ita da kake ganin mutuncinta ka koya mata mota har ga shi nan ta kai ta ɗauki motarka ta fita yawo.’

    Ta ɗaga ƙafa za ta shige banɗaki sai kuma ta tsaya ta kalle shi suka haɗa ido sannan tace ‘Bayan hidimar yaran sai kuma wacce hidimar take maka? Ko ma dai ka aure ta ne ni ce ban sani ba? Ba fa na son iskanci Khadeeja! Kina ji nace miki sakatariyata ce kike wannan maganar banzar. Na aike ta don haka na ba ta mota ta ta je ta dawo, shi ne kike wannan rashin kunyar?

    Idan da kina hidimar yaran ba tare da ƙosawa ba ai babu wanda zan nema. Na san idan na gaya miki sai kin yi mita don haka na nemi wadda za ta yi cikin walwala na saka ta, sai dai duk abinda za ki yi ki je ki yi amma idan kika zage ni wallahi ba za ki ji da daɗi ba. Ta yi murmushi ‘Hmmm! Ka fi ƙarfin zagi yallaɓai, amma tabbas ka yi yanda kake so don haka ni ma zan yi yanda nake so.’

    Ta juya ta shige banɗaki ta turo ƙofar ta bar shi nan tsaye. Haka ya gaji da tsayuwa ya juya ya fice daga ɗakin; tana jin fitarsa ta fito ta saka mukulli ta kulle ɗakin ta bar mukullin a jiki ta koma ta kwanta. Tun a office Naja’atu ta sanar da shi haɗuwarsu da Khadeeja, kuma ita kanta sai da ta nuna rashin jin daɗinta a kan ya san Khadeeja za ta je ya tura ta.

    Sai da ya yi ta faman ba ta hakuri sannan ya samo kanta. Bai taɓa zaton Khadeeja za ta ba shi matsala, don ya zata idan yace mata sakatariyarsa ce za ta fahimce shi, yanzu ga shi ita ma Khadeejan so take ya lallashe ta. Yana da niyyar auren Naja don sun ma yi magana da Alhaji kwanan nan ma za a kai kuɗin aure; kawai dai bai shirya gayawa Khadija ba saboda bai shirya ba, ya fi so sai magana ta tsaya an kusa biki sai ya sanar da ita.

    Kafin lokacin ya gama gininsa sai su tashi su koma don a can yake so amarya ta tare. Yanzun ma kuma da hakan ta faru ba gaya mata zai yi ba, idan ta gama fushin nata ya san me zai gaya mata. Tun yana saka rai za ta buɗe ƙofar ɗakin har dare ya fara yi ba ta buɗe ba, yara har sun gaji da tambayarta. Haka ya sa Rashida ta ba su abinci sannan ta taya su suka shirya suka tafi suka kwanta, shi ma ya shiga ɗakinsa ya kwanta yana sauraron lokacin da zai ji motsinta.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya daga Masallaci mai Alfarma 7th Nuwamba 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya daga Masallaci mai Alfarma 7th Nuwamba 2025

    Fassarar huɗubar Juma’a kai daga Masallaci mai alfarma, ta yau Juma’a 16 Jumadal Ula, 1447 H / 07 November, 2025 M

    Mai Huɗuba:  Sheikh Dr. Abdallah bin Awwad Aljuhani

     Mai Fassara: Dr Abdullahi Yunusa Machina

    Transcribe: Aminu Bashir

    Huɗuba ta farko:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, muna yaba masa, muna neman taimakonsa, kuma muna neman gafararsa. Kuma muna neman tsarin Allah daga sharrukan kawunanmu da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi, to babu mai ɓatar shi, kuma duk wanda ya batar, to babu mai shiryar da shi.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bautawa bisa cancanta sai Allah Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa. ((Ya ku waɗanda kuka yi imani! Ku ji tsoron Allah matuƙar tsoronsa, kuma kada ku mutu face kuna musulmi)).

    ((Ya ku mutane! Ku ji tsoron Ubangijinku wanda Ya halicce ku daga rai guda ɗaya, kuma Ya halicci matarsa daga gare shi, kuma Ya yaɗa maza da mata masu yawa daga gare su, kuma ku ji tsoron Allah wanda kuke yi wa juna magiya da shi, kuma ku kiyaye yanke zumunta, lallai Allah Ya kasance Mai kula da ku ne)).

    ((Ya ku waɗanda kuka yi imani! Ku ji tsoron Allah kuma ku faɗi magana wacce take daidai, Zai gyara muku ayyukanku, kuma Ya gafarta muku zunubanku, kuma duk wanda ya yi ɗa’a ga Allah da Manzonsa to haƙiƙa ya rabauta rabauta mai girma)).

    Bayan haka: Ina yi muku wasiyya da ni kaina da duk wanda ya ji maganata da jin tsoron Allah Mai girma da ɗaukaka, wanda Ya halicci bayi, kuma zuwa gare shi makoma take, kuma gare shi ake neman dacewa da shiriya, domin jin tsoronsa riba ce, kuma kariya ce daga azabarsa, kuma hanya ce ta samun kusanci zuwa gare Shi.

    Kuma ku kiyayi sauyawar ni’imar Allah gare ku, kuma ku lizimci jama’arku, kuma kada ku kasance ƙungiya ƙungiya, kuma lallai mafi wayo cikin mutane shi ne wanda ya yi wa kansa hisabi, kuma ya yi aiki don abin da ke bayan mutuwa, kuma ya nemi hasken da zai haskaka duhun kabarinsa da shi daga hasken Allah.

    Kuma lallai bawa ya ji tsoron Allah Ya tashe shi makaho ranar ƙiyama alhali ya kasance yana gani a duniya. Kuma ku sani cewa lallai duk wanda Allah yake tare da shi, to ba zai ji tsoron komai ba; kuma duk wanda Allah baya tare da shi, to wa zai yi fatan samun kariya daga gare shi koma bayansa.

    Ya ku taron muminai maza da mata: Lallai daga cikin manyan ni’imomin Allah ga halittunsa akwai cewa Ya shiryar da su kuma ya nusar da su zuwa ga yin imani da Shi, kuma Ya bayyana musu falalar da Ya yi musu, Allah Maɗaukaki ya ce: ((Gori suke maka don sun musulunta?; to ka ce: “Kada ku yi min gorin musuluntarku; a’a, Allah ne ma zai yi muku gori don Ya shiryar da ku zuwa ga imani, idan kun kasance masu gaskiya”)).

    Kuma imani da Allah Maɗaukaki shi ne tabbataccen gaskatawa da ƙudurta cewa lallai Allah shi ne Ubangijin dukkan komai kuma Mamallakinsu, kuma Mahaliccinsu, kuma Mai gudanar da su; da kuma cewa lallai Shi kaɗai ne wanda ya cancanci bauta, kamar Salla da Azumi da addu’a da fata da tsoro da ƙasƙantar da kai da rusunawa, da kuma cewa lallai Shi ne wanda ya siffantu da dukkan siffofin kamala, Wanda Ya tsarkaka daga kowane aibu da tawaya.

    Kuma ku sani – Allah Ya ya muku rahama – cewa lallai imani ba wata magana ce mai daɗi da ake furtawa da baki kawai ba, ko wasu burace-burace ba tare da aiki ba, bari dai, shi ne abin da ya tabbata a cikin zuciya kuma ayyuka suka gaskata shi, kuma shi furuci ne da harshe, da gaskatawa da zuciya, da kuma aiki da gaɓɓai da sassan jiki, yana ƙaruwa da ayyukan ɗa’a kuma yana raguwa da ayyukan saɓo.

    Kuma imani da Allah Maɗaukakin sarki shi ne tushen dukkan rabauta, domin ba a saukar da littattafai ba, kuma ba a aika manzanni ba, face don tabbatar da shi, da kuma dasa shi a cikin zukata, domin shi ne tushe mafi girma kuma rukuni na farko daga cikin rukunan imani guda shida.

    Kuma shi imani kyauta ce daga Allah, kuma ni’ima ce mai girma a rayuwar musulmi, ni’ima ce wacce take tsarkake shekaru, kuma ta sanya albarka a cikin rayuwa, kuma ta bada lamunin samun rabauta a lahira, kuma ta ɗaga darajar ma’abocinta a duniya da lahira, domin a cikinta ne rayuwa ta gaskiya da farin cikin lahira suke.

    Kuma wannan ni’ima babu wanda ya san ta sai wanda ya ɗanɗana ta, kuma babu wanda zai ji daɗinta sai wanda ya rayu a cikinta, kuma shi imani haske ne mai shiryarwa mai haskakawa, Allah yana ba da shi ga wanda Yake so daga cikin bayinsa, kuma Yana hana ta ga wanda Ya ga dama.

    Allah Maɗaukaki Ya ce: ((Ka ce: “Lallai Allah Yana ɓatar da wanda Ya ga dama, Yana kuma shiryar da wanda ya koma gare Shi)), kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da alayensa ya ce: (Duk wanda ya yarda da Allah a matsayin Ubangiji, kuma ya yarda da Musulunci a matsayin addini, kuma ya yarda da Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da alayensa a matsayin Annabi, to lallai ya ɗanɗani daɗin imani). Muslim ne ya rawaito shi.

    Kuma imani na gaskiya wanda Allah yake so, shi ne tushen kowane alheri, kuma maɓuɓɓugar ɗaukaka, kuma asalin karama da daraja da jagoranci, ma’abocinsa yana rayuwa cikin ɗaukaka da farin ciki da ƙarfi da tabbata a kan hanyar gaskiya.

    Kuma haƙiƙa Allah Maɗaukaki ya yi wa masu imani da kuma ɗa’a alkawarin samun nasara da kafuwa a doron ƙasa a cikin bayani mai daraja inda Ya ce: ((Wannan bayani ne don mutane, kuma shiriya ce da kuma wa’azi ga masu taƙawa. Kuma kada ku yi rauni, kada kuma ku yi baƙin ciki, kuma ku ne mafiya ɗaukaka in dai har kun kasance muminai Idan ma wani miki ne ya same ku a jiki, to haƙiƙa miki irinsa ya samu mutanen Makka.

    Kuma waɗannan kwanaki ne da muke jujjuya su tsakanin mutane domin Allah Ya bayyanar da waɗanda suka yi imani, kuma Ya riƙi shahidai a cikinku. Allah kuwa ba Ya son azzalumai Kuma don Allah Ya tace waɗanda suka yi imani, kuma don Ya halakar da kafirai.))

    Kuma masu imani suna farin ciki da jiɓantar Allah Maɗaukaki a gare su, kuma suna ni’imtuwa da daddaɗar rayuwa, kuma Allah yana son su, kuma muminai ma suna son su, kuma Allah Maɗaukakin sarki yana basu kariya, kuma suna da albishir a rayuwar duniya da lahira, kuma imani na daga cikin mafi girman abababen da ke sanyaya musu zuciya yayin masifu, Allah Maɗaukaki ya ce: ((Ba wata musiba da za ta samu sai da izinin Allah. Duk kuwa wanda ya yi imani da Allah zai shiryi zuciyarsa. Allah kuma Masanin komai ne)).

    Kuma su ne ma’abota tsaro da kwanciyar hankali, kuma suna gaggawar zuwa ga imaninsu, kuma suna samun ƙarfi da shi cikin duk abin da ya same su na alheri ko na sharri, na ɗa’a ko na saɓo, na sauƙi ko na wahala. Kuma suna amfana da wa’azi da tunatarwa, kuma suna cikin kulawar Allah Maɗaukaki.

    Kuma imaninsu yana kare su daga faɗawa cikin alfasha, kuma da hasken imaninsu suke bambance tsakanin gaskiya da ƙarya, da shiriya da ɓata, da kuma bidi’a da sunna.
    Kuma haƙiƙa Allah Maɗaukaki ya yi musu alkawarin samun nasara da kafuwa, kuma su ne ma’abota buwaya da ɗaukaka, Allah Maɗaukaki Ya ce: ((kuma taimakon muminai ya zama haƙƙi ne a kanmu)).

    Kuma Mala’ikun da suke ɗauke da Al’arshin Allah Mai rahama suna nema musu gafara, kuma Allah Maɗaukaki yana shiryar da su da imaninsu zuwa hanya madaidaiciya.
    Kuma Allah Maɗaukaki yana musu albishir da samun aminci da farin ciki a duniya da lahira, da kuma dawwamammiyar ni’ima a lahira.

    Allah Maɗaukaki Ya ce: ((Lalle waɗanda suka ce: “Allah ne Ubangijinmu”, sannan suka tabbata, to mala’iku za su sauko musu lokacin mutuwa suna cewa: “Kada ku tsorata, kuma kada ku yi baƙin ciki, kuma ku yi farin ciki da Aljanna wadda kuka kasance ana yi muku alƙawarinta “Mu masoyanku ne a rayuwar duniya da kuma ta lahira; kuma a cikinta za ku samu duk abin da rayukanku suke marmari, za kuma ku samu duk abin da kuke nema a cikinta“Liyafa ce daga Allah Mai gafara, Mai jin ƙai”)).

    Bayan haka, ya ku muminai: Haƙiƙa hikimar Allah Maɗaukaki ta hukunta cewa Ya sanya wannan al’umma ta zamo mafi alherin ul’umma wacce aka fitar ga mutane, tana umarni da kyakkyawan aiki, kuma tana hana mummuna, kuma tana imani da Allah.
    Kuma Allah tsarki ya tabbata a gare Shi Ya umurce su da yin ayyuka nagari inda Ya ce: ((Kuma ku aikata ayyuka nagari, lallai Ni Masanina abin da kuke aikatawa ne)).

    ma’abocinsa dukkan alheri a duniya da lahira, kuma shi garkuwa ne da bawa yake kare kanshi daga sha’awace-sha’awace da shubuhohi da manyan fitintinu da shi, kuma shi waraka ne ga zukata.

    Wanda duk lokacin da mutum ya gafala daga barin shi saboda kwaɗayin wani abin duniya mai ƙarewa, sai rayuwarshi ta ƙuntata, kuma zuciyarshi ta kamu da jinya, kuma lallai idan ka dubi dayawa daga cikin koke-koke da damuwowi da baƙin ciki da tsoro da taɓarɓarewar al’amura a rayuwar mutane, za ka ga alamomin nisantar imani da Allah Mai girma da ɗaukaka da bijire wa addininsa da shari’arsa a cikinsu.

    A’uzu billahi minash-shaiɗanir-rajim, Bismillahir Rahmanir Rahim: ((Waɗanda suka yi aiki nagari, na miji ne ko mace, alhalin suna muminai, to tabbas za mu raya su rayuwa mai daɗi, kuma tabbas za mu saka musu ladansu da mafi kyawun abin da suka kasance suna aikatawa)).

    Allah Ya amfanar da mu da Alƙur’ani mai girma, da shiriyar shugaban Manzanni, ina faɗi abin da kuka saurara, kuma ina nema mana gafar Allah, da sauran musulmi daga kowane zunubi, don haka ku nemi gafarsa, lallai shi Mai yawan gafara ne Mai jin ƙai.

    Huɗuba ta biyu:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah bisa kyautarsa da kyautatawarsa, kuma godiya ta tabbata gare shi bisa falalarsa da ni’imominsa, kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai Yake ba Shi da abokin tarayya, kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa, ya Allah Ka yi daɗin tsira da aminci ga bawanka kuma Manzonka Muhammadu da alayensa da sahabbansa.

    Bayan haka:

    Ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah, kuma ku tabbatar da imaninku da Ubangijinku, kuma ku sani cewa lallai Imani da Allah Mai girma da ɗaukaka yana sanya yarda da Allah Mai grima da ɗaukaka a zuciyar mumini a kowane hali, kuma yardar bawa ga Mahaliccinsa shi ne farkon sababi daga cikin sabuban natsuwar zuciya, wacce ita ce asalin rabauta, domin da yardar mutum da kansa da abin da Allah Ya ƙaddara masa ne zai samu natsuwa a kan hali da yake ciki yanzu, da kuma yaƙininsa da lahira da sakamako na adalci ne zai samu natsuwa game da gobenshi.

    Ma’anar haka, shi ne cewa lallai mumini ba ya cizon yatsa a kan abin da ya shuɗe ta hanyar kuka ko baƙin ciki, kuma ba ya rayuwa cikin baƙin ciki a kan yanayi da yake ciki, kuma ba ya fuskantar gobe da tsoro, saboda a cikin addininsa akwai makamai da zai yi dogaro da su wurin dogewa a kan gwagwarmayar rayuwa, kuma ya fuskanci masifunta da raɗaɗinta da bala’o’inta da su.

    Saboda haka, ahir ɗinka kuma ahir ɗinka da rabuwa da yarda da Ubangijinka ko da daidai da ƙiftawar ido ne, sai darajarka ta faɗi a wurinsa, saboda akwai ƙarfin rai da yarda da shi, da natsuwar zuciya a cikin ƙulla alaƙa da Allah, Allah Maɗaukaki Yana faɗi a cikin littafinsa mai girma: ((Ya ku waɗanda kuka yi imani ku nemi taimako ta hanyar haƙuri da salla. Lallai Allah Yana tare da masu haƙuri)).

    Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan wani abu ya tsananta a gare shi, sai ya garzaya zuwa ga salla, kuma sallarsa ba ta kasance wani abu na al’ada ne kawai da yake yi ba, bari dai, ta kasance kaiwa maƙura ne wurin ganawa da Allah, har ma ya kasance idan lokacinta ya yi sai ya ce wa sahabinsa Bilal Allah Ya ƙara masa yarda: (Ka hutar da mu da salla), wato ita wannan salla ya ku muminai tana ɗauke da makullan rayuwa da wani sashi na hanyoyin rayuwa cikin nutsuwa, don haka, ku dogara da ita saboda ku rabauta.

    Ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah, kuma ku kiyaye shi, kuma ku ɗau izina daga waɗanda suka shuɗe gabaninku, kuma ku sani cewa lallai babu makawa sai kun haɗu da Ubangijinku kuma zai muku sakamako a kan ayyukanku ƙananansu da manyansu sai dai abin da Allah Ya gafarta shi, lallai Shi Mai gafara ne Mai jin ƙai, saboda haka, ku kula da kawunanku, ku kula da kawunanku, kuma ku nemi taimakon Allah, kuma ba mu da wata dabara ko ƙarfi face da Allah.

    ((Lallai Allah da Mala’ikunsa suna salati ga Annabi. Ya ku waɗanda kuka yi imani ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)). Ya Allah Ka yi salati ga Annabi Muhammadu da alayen Annabi Muhammadu, kamar yadda Ka yi salati ga Annabi Ibarahim da alayen Annabi Ibrahim, Lallai Kai Sha yabo ne Mai girma, kuma Ka yi albarka ga Annabi Muhammadu da alayen Annabi Muhammadu, kamar yadda Ka yi albarka ga Annabi Ibrahim da alayen Annabi Ibrahim, lallai Kai Sha yabo ne Mai girma.

    Ya ku bayin Allah, ku Yawaita salati da sallama ga mafakar halittu a matsaya mai girma ranar alƙiyama, Annabinmu kuma mai cetonmu Annabi Muhammadu tsira da maincin Allah su tabbata a gare shi, kuma Ka masa sallama mai yawa.

    Kuma ya Allah Ka ƙara yarda da halifofi huɗu shiryayyu da sauran sahabbai gaba ɗaya, da tabi’ai, da waɗanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako, ya Allah Ka amfanar da mu da son da muke musu, kuma ya Allah Ka tashe mu a cikin tawagarsu, kuma kada Ka kautar da mu daga bin sunnarsu da tafarkinsu, ya Mafi karamcin masu karamci.

    Ya Allah Ka ƙarfafi Musulunci da musulmai, kuma Ka ɗaukaka kalmar gaskiya da addini da falalarka, ya Allah Ka taimaki shugabanmu kuma majiɓincin lamuranmu hadimin Masallatai biyu masu alfarma da gaskiya da dace da daidai, kuma Ka datar da shi ga abin da Kake so kuma Ka yarda da shi, kuma Ka yi riƙo da hannunsa zuwa ga ayyukan nagarta da taƙawa.

    Ka azurta shi da mashawarta nagartattu, Ka ɗaukaka addininka da kalmarka da shi, kuma ka sanya shi ya taimaki musulunci da musulmai, kuma ka haɗa kan musulmai bisa gaskiya da shiriya ta dalilinsa ya Ubangijin talikai, ya Allah Ka datar da shi da magajinshi da ‘yan’uwansa da mataimakansa zuwa ga gaskiya da shiriya, da dukkan abin da gyara ne ga bayi da ƙasa.

    Ya Allah Ka datar da shugabannin musulmai zuwa ga aiki da littafinka da sunnar Annabinka Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, Ka sanya su su zama rahama ga bayinka muminai, kuma ya Allah Ka haɗa kawunansu a kan gaskiya ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah Ka ƙarfafa kariyarka ga ƙasarmu da dukkan ƙasashen musulmi, kuma ya Allah Ka datar da jami’an tsaronmu da masu dako a kan fagage da iyakoki, kuma Ka zama Mai taimako da kawo ɗauki da agazawa da ba da nasarar a gare su.

    Ya Allah lallai muna tawassuli da yardarka, Ka tsare mu daga fushinka, kuma muna tawassuli da amincinka, Ka tsare mu daga azabarka, kuma muna neman tsarinka daga damƙarka, ba za mu iya ƙididdige yabo a gare Ka ba, Kana nan kamar yadda Ka yabi kanka.

    Ya Allah kada Ka mana uƙuba da munanan ayyukanmu, kuma kada Ka kama mu da abin da wawayen cikinmu suka aikata, kuma Ka isar mana a kan dukkan wani lamari da yake damun mu, kuma Ka zama mai taimako da ba da nasarar gare mu. Ya Allah Ka taimaki addininka, da littafinka, da sunnar Annabinka tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, a kowane waje, ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah lallai muna neman gafararka, lallai Kai Ka kasance Mai yawan gafara ne, Ka sauko mana da ruwan sama mai yawa, ya Allah Ka saukar mana da ruwa, ya Allah Ka saukar mana da ruwa, ya Allah Ka saukar mana da ruwa, ya Allah lallai mu halittu ne daga cikin halittunka, kada Ka hana mana falalarka saboda zunubanmu.

    Ya Allah Ka gafarta mana, da iyayenmu, da dukkan musulmai maza da mata, da muminai maza da mata, rayayyu daga cikinsu da mamata. Ya Allah Ka karɓa daga gare mu, lallai Kai Mai ji ne kuma Masani, kuma Ka karɓi tubanmu, lallai Kai Mai yawan karɓar tuba ne Mai jin ƙai.

    Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin buwaya daga abin da suke siffanta shi da shi, kuma aminci ya tabbata ga Manzanni, kuma dukkan yabo ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai.

    Karanta Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 31st Octoba 2025

    Edita@rumasau-kallamu

  • Kira A Kan Haɗin Kai

    Kira A Kan Haɗin Kai

    ‘Yan Najeriya muna cikin wani muhimmi lokaci. Wata mummunar fahimta tana shiga cikin al’ummarmu, tyana canza yadda muke kallon ‘yan-uwanmu da kuma rage darajar kanmu da ƙaunar ‘ƴan’uwanta da ta kasance tana bayyana mu.

    Dole mu dakata mu yi wa kanmu wata muhimmiyar tambaya: a cikin rayuwarmu ta yau da kullum don neman abinci da ci gaba, shin mun taɓa tunanin addinin manomi wanda ya noma shinkafar da muke ci? Shin muna tambayar addinin likitan da ya rubuta maganin da ya ceci rayuwarmu? Idan muka buɗe famfo, shin muna tunanin ko injiniyan da ya tsara tsarin ruwan yana da aƙidarmu?

    Amsar ba ta da shakku, ’A a’. Ba mu yi haka ba. Muna saye, muna ci, kuma muna rayuwa, muna dogaro ga juna a cikin hanyar da ba a iya rabuwa. Rayuwarmu ta yau da kullum shaida ce mai ƙarfi game da haɗin kanmu.

    To, me yasa, a wasu fannonin rayuwa, muka ƙyale a raba mu? Me yasa muke tallata bambance-bambancen addini alhali kuwa tarihinmu na gaba ɗaya ya faɗi wani labari daban?

    Mun yi yaƙi don ‘yancin kanmu tare, a matsayin mutane ɗaya tare da manufa guda. Mun zauna tare a cikin ajujuwa, muna koyo daga malamai ɗaya, muna mafarkin makoma guda ga Najeriya. Muna ciniki tare, muna murna tare, muna makoki tare.

    Wannan rarrabuwa ba hanya ba ce ta Najeriya. Guba ce da ke raunana mu da kuma hana mu ci gaba. Duk gidan da ya rabu da kansa ba zai iya tsayawa ba, balle ya ci nasara a rayuwa.

    Hanyar Ci Gaba: Komawa ga Ƙimar Mu Na Gaba ɗaya

    Don maido da girmanmu, dole ne mu zaɓi haɗin kai da juna. Ga yadda za mu iya farawa:

    1.  Yi Bikin Asalin Mu Guda: Ganin kanmu a matsayin ‘yan Najeriya—’yan’uwa maza da mata na al’umma ɗaya. Imaminmu wani ɓangare ne na asalinmu, ba makami da za a yi amfani da shi a kan maƙwabci ba.

    2.  Ƙarfafa Tattaunawa: Ƙarfafa tattaunawar addini a cikin al’ummominmu. Bari shugabannin mu na addini su yi wa’azin soyayya da haƙuri. Lokacin da muka yi hira, muna rushe ganuwar tsoro da rashin fahimta.

    3.  Mai da hankali kan Manufofi Guda: Talauci, jahilci, da rashin ingantaccen tsaro wannan ba sa bambanta tsakanin Musulmi da Kirista. Waɗannan su ne abokan gabanmu. Kamata ya yi mu karkatar da ƙoƙarinmu don yaƙar waɗannan, maimakon yaƙi da juna. Ci gabanmu gaba ɗaya ya dogara da ƙoƙarinmu gaba ɗaya.

    4.  Maido da Maganar Mu: Dole ne mu ƙi maganganun da ke neman raba mu. A shafukan sada zumunta da kuma a cikin al’ummominmu, mu zama jakadun zaman lafiya, muna raba labarun haɗin kai da abota waɗanda suka fi yawan labarun rikici.

    Najeriya ƙasa ce mai girma, mai albarka da ɗimbin albarkatun ɗan adam da na halitta. Ƙarfinmu yana cikin hadin kai. Kada mu ƙyale rashin fahimta ya canza mana tunani. Muna buƙatar juna don rayuwa da ci gaba.

    Mu zaɓi hanyar ‘yan-uwanta. Mu zaɓi hanyar haɗin kai. Mu zaɓi hanyar Najeriya ɗaya.
    A Haɗe Muke Da Ƙarfi, A Rabe Muke Da Rauni.

    Karanta Yaushe Ne Kwanakin Layya Suke Ƙarewa?

    Edita@rumasau-kallamu