Tag: yadda ake

  • Wasu Kayan Aikin Sassaƙa

    Wasu Kayan Aikin Sassaƙa

    1. Gizago
    2. Ƙurfi
    3. Kibiya
    4. Matani
    5. Matankwari
    6. Tunga
    7. Kalaba

    FASIHIN KAITA

    Karanta Wasu Kayan Busar Hausawa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Matsayar Ɗanbala

    Matsayar Ɗanbala

    Lokacin da muke da manya,
    Lau muke ba a kashe wa.

    Zamanin da muke da manya,
    Babu bandits kaf Arewa.

    Sa’ilin da muke da manya,
    Babu kinafas Arewa.

    Lokacin da akwai su Baba,
    Duk da tarbiyya Arewa.

    Zamanin Ulama’u na nan,
    Babu mai kafurta babba.

    Lokacin da muke da manya,
    Ba mu yin rigima Arewa.

    Lokacin da su Inna na nan,
    Kanmu ɗai yake ba rabe wa.

    Lokacin Malamai su na nan,
    Ƙanƙana na bin na gabba.

    Lokacin su Waziri na nan,
    Malamai ba su fanɗare ba.

    Lokacin da muke da manya,
    Ba mu san Boko Haram ba.

    Zamanin da akwai mazaje,
    Ilimi namu bai zube ba.

    Lokacin da su Kawu na nan,
    Tsintsiya muke ba kawai ba.

    Yanzu da yake babu manya,
    Ba mu san asalin gabas ba.

    Yanzu da yake mun rasa su,
    Sai kashe mu ake Arewa.

    Yanzu da yake babu babba,
    Ƙanƙana ke zage babba.

    Tun da mun yi rashin su Inna,
    Dole mui ta ganin mu baibai.

    Kuma da yake ba magaji,
    Shi ya sa mu muke ta ɓarba.

    Babu babba a yau Arewa,
    In akwai sunansa kama.

    Na faɗa maka babu babba,
    In akwai ka kira shi yanzu.

    Da a ce ko muna da manya,
    Da ba mui ta ganin hakan ba.

    Da a ce da akwai su Baba,
    Ƙanƙana ba su zagi babba.

    Da da wanda muke jin tsoro,
    Da ba mu raba al’umma ba.

    Shehu Khalidu babu babba,
    Yanzu kaf a cikin Arewa.

    Wanga ita ce fahimta ta,
    Ko a gobe ina faɗa ma.

    Da da babba a yau Arewa,
    Da ba zan yi musun hakan ba.

    Ɗanbala daga Borno ne ni,
    Mai yabon a wurin Masoyi.

    Ɗan Amina abin nufina,
    Na riƙe shi ba zan shika ba.

    Ahlihi nasa na riƙe su,
    Ba riƙon igiya na yo ba.

    Da Sahabu ina biyan su,
    Ban da masu kiran gumaka.

    ©
    Mohammed Bala Garba
    6:39pm
    30 November, 2025.

    Karanta Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin

    Ranar ɗaurin aure tun da sassafe baƙi suka fara zuwa gidan, zuwan nasu ma sai ya fi mata sauƙi tunda ya ba ta dama ta baro Mustapha a sama ta taho wajen baƙin. Ba za ta iya tsayawa a inda yake ba yana ta faman walwala yana kai wa da kawowa yana kwalliya, sai ta ga kamar yana yi ne don ya ba ta haushi.

    Don haka ta ji daɗi sosai da aka ce mata Yaya Jidda ta zo da mutane. Nan ta sauko suka gaisa, ta buɗe musu ɗakin baki tunda dama a ɗaya parlor din suka sauka wanda ba na amarya ba. Sosai Yaya Jiddan ta so su hau sama amma sam Khadeeja ta ƙi ba da fuska, don haka suka haƙura suka baje zugarsu a nan ƙasan.

    Duk wani abu da suke buƙata na cefanensu sun taho da shi da manyan tukwanensu, shi kansa Mustaphan bai san a nan za su yi girkin ba da ya biya an girka musu don ba ya son a ɓata gidan nan. Amma haka yana ji yana gani kafin ma ya sauko an sauke kayan aiki an hau ƙoƙarin hura wuta; a cewar Yaya Jidda sun bayar a yi musu tuwon shinkafa da masa da shinkafa amma masu yi miyarsu ba ta daɗi don haka su za su girka tasu miyar.

    Nan da nan ya ja motarsa ya fice daga gidan suka tafi ɗaurin aure. Tunda Mustapha ya fita ta ɗauki Hammad ta haye sama, suka zauna da Nabila wadda dama ba ta sauko ba ma balle ta ga kalarsu. Hafsa mai aikinta dai ita dole ta zauna ana komai da ita, sannan ga su Afaf waɗanda tuni suka shiga cikin dangi ana ta rawar kai.

    Can kusan la’asar su Yaya Mama suka zo ita da cousins ɗinsu mutum biyu da kuma ƙannen Mommy su biyu. Bayan sun gaisa da Yaya Jidda a parlor ɗin ƙasa kai tsaye suka haye sama. Ba su daɗe da hayewa ba kuma Hajia mahaifiyar Mustaphan ta iso da tata zugar, nan da nan gida ya cika ana ta kai wa da kawowa.

    Bayan an gaggaisa Hajia ta dubi Yaya Jidda tace ‘Ina Khadeejan ne? Ban ganta ba. Inna Ramla ta yi sauri ta amsa kafin Yaya Jidan tace wani abu ‘A a suna saman benen nan fa ita da ‘yanuwanta, benen da ‘yan gidan ma ban ga suna hawansa ba tunda duk ga su nan tare da mu.’

    Ta sake duban Yaya Jidda tace ‘Ban gane tana sama ba. Ta taɓe baki ‘Toh haka muka gani, tana saman ita da ‘yan uwanta. Kafin tace wani abu Khadeejan ta sauko parlor ɗin da sallama; Shukra ce ta hau ta gaya mata zuwan Hajia shi ne ta yi sauri ta sauko saboda kada ta yi laifi.

    Ta ratsa mutanen har gaban Hajia ta tsuguna ta gaishe ta cikin girmamawa sannan ta yi mata Allah ya sanya alkhairi. Ta dubi mutanen duk suka gaggaisa tana kama sunan waɗanda ta sani. Har ta miƙe Hajia tace ‘Ina Mommyn naki, ba ta zo ba? Tace ‘Eh, ba ta zo ba, su Yaya Mama ne kawai suka zo.’

    ‘To madalla.’Ta miƙe ta fice tsakar gidan suka gaggaisa da mutanen da ke zazzaune, ta kalli wajen da su Yaya Jidda suka yi aikinsu yanda ya yi kace-kace ta ɗauke kai. Har ta juya za ta koma ciki Habib ya turo gate ya shiga, daga inda yake ya kirawo sunanta ‘Anti.’ Ta tsaya ta juyo ‘Yaya Habib, ina ka shiga ne tun ɗazu Shukra take nemanka.’

    ‘Ina nan Anti, wajen abokina na je. Yanzu ma wallahi yunwa nake ji, abinci za ki ba mu. Tace ‘To ai Anti Jidda za ka yi wa magana ga abinci nan an dafa. Ya shafa kai yana cewa ‘Anti ai na gaya mata, tuwo ne fa da masa Anti don Allah ni dai ki ba ni abinci. Ta yi dariya don ta san tabbas Habib ba ya cin tuwo da masa da ma abincin gargajiya da yawa, tace ‘Kaje sama wajen Anti Nabeela ta zuba maka.’

    Har ya wuce yace ‘Ni da abokaina Anti? ‘Eh, ka gaya mata ko ku nawa ne. Bai jima da hayewa ba ita ma ta bi bayansa, kafin ta je ya ɗauko flask Nabeela ta zuba masa shinkafa da kaza ga coleslaw da sauce ɗin dankalin bature wanda duk a nan saman suka dafa shi tunda ba su da yawa. Ya ɗauko kwanukan ya sauko ya fice.

    Haka aka yi ta hada-hada ana kai wa da kawowa. Sai dai zuwan Hajia ya sa babu yanda Khadeeja za ta yi dole ta zauna a ƙasa a yi da ita, don haka Yaya Mama da kuma Anti Innani suka sauko suka gaida Hajia suma suka zauna don taya ta zama. Bin mutane kawai take yi da kallo zuciyarta tana ƙuna; ji take a ranta kamar da za a buɗe zuciyarta to da za a tarar tana turiri saboda zafin da take ji.

    Fuskokinsu take kallo ɗaya bayan ɗaya, musamman Hajia wadda ake ta yi mata Allah ya sanya alkhairi ana barka da arziƙi tana amsawa kamar wadda aka yi wa bushara da kujerar Makka. Haka tacigaba da zama a cikinsu tana jin kamar ta ruga da gudu; sai dai lokaci zuwa lokaci ta kan tashi kamar mai duba wani abu ta haye sama, idan ta ja numfashi ta share ƙwalla sai ta dawo.

    Haka suka yi ta yi har gefin magriba; abokan ango suka zo da motaci suka ɗebi yan ɗauko amarya sannan suka tafi ɗauko amarya. Har ta yi sallar magriba zuciyarta tana dukan uku-uku; ta rasa ma abinda yake ɓata mata ran. Tabbas tana kishi to amma ta fi tsoron rashin adalcin da take ji a jikinta Mustapha zai shimfiɗa; amma tana addu’a kuma ba za ta fasa ba don ta san tabbas Allah ne gatanta.

    Wajen 8:30pm aka shigo da amarya, nan da nan gida ya ɗau guda mata na ta shewa. A lokaci guda kuma bugun zuciyar Khadeeja ya ƙara gudu. Tana zaune a kan kafet kusa da Hajia; duk su Yaya Jidda suka miƙe suna tarbar amaya, aka buɗawa waɗanda suka riƙo amarya suka ƙarasa gaban Hajia wadda take hakimce a kan 3-seater. Aka zaunar da amarya a gaban Hajia, mata suka cigaba da zabga guɗa.

    Sai da hayaniya ta lafa sannan aka gaisa da masu kawo amarya, suka miƙa ta hannun Hajia. Hajia tace ‘Masha Allah, Allah ya sa wannan aure har aljannah. Wannan ai ‘yar uwarta za a ba wa ita ba ni ba, ina Khadeejan ne da fa tana nan zaune kusa da ni. Wadda take zaune kusa da Khadeejan tace ‘Gata nan fa.’

    Mutane ne suka zauna a gabanta suka kare ta da aka shigo da amaryar; nan da nan aka buɗa. Hajiya ta miƙa hannu yayin da Khadeejan ta matso tana cewa ‘Zo Khadeeja ga ƙanwarki an kawo miki. Ta sunkuyar da kanta tana duban cinyarta domin tana tsoron kada idanuwanta su ba da ita ta hanyar tunkuɗa hawaye a daidai wannan lokacin.

    Hajia ta kama hannunta sanna ta kamo hannun Naja ta ɗora ta haɗa ta riƙe tana kallon Khadeejan tana cewa ‘Ga amanar ƙanwarki nan, ki riƙe ta amana ku zauna lafiya ku samarwa da mijinku nutsuwa. Allah ya haɗa kayuwanku. Mata suka kaure da amshi ‘Amin. Amin.’

    Wata cikin iyayen amaryar ta karɓe ta cigaba ‘Eh gata nan amana, a yi haƙuri uwargida sarautar mata ku zauna cikin amincin Allah domin kayan Allah na annabi ne. Aka sake kaurewa da guda. So take ta zare hannunta amma Hajia ba ta ba su dama ba; bugun zucuyarta ƙara sauri yake yayin da take jin hanunta kamar ta riƙe wuta.

    ƘoƘari take ta dafe bakinta saboda kada abinda yake zuciyarta ya fito; Amana! Ita za a ba wa amanar matar Mustapha? Ina ruwanta da ita? Ko sun yi mantuwa ne? Shi da ya ga zai iya da amanar ai ya yi gammo ya ɗauko. Don me za su ce ita aka ba wa amana? Tabbas wanna amana ce da ba ta karɓa ba kuma ba za ta taɓa iya karɓa ba.

    Sai da aka gama addu’oi sannan Hajia ta saki hannuwansu, cikin dabara Khadeeja ta faki ido ta goge ƙwallar da ta taru a kwarmin idonta. Ba daɗewa kuma aka fara miƙewa aka kama hannun amarya aka nufi ɗakinta, a haka ne Khadeeja ta samu ta sulale ta haye sama, yayin da su kuma matan suka bi bayan amarya.

    Haka ta koma cikin su Yaya Mama ta cigaba da dagewa, su kuma suna ta ba ta baki da nasiha. Wajen 9pm gayya ta fara watsewa, aka kirawo ta ta yi sallama da Hajia, ba daɗewa kuma su Yaya Mama suma suka yi mata sallama suka bar ta ita da Nabeela. Tana zaune a gefen gadonta tana jiyo yara wajen 11pm suka hawo saman, gaba ɗayansu sai da suka leƙa ɗakinta suka yi mata sai da safe amma banda Afaf, suka wuce ɗakinsu inda suke kwana tare da Hafsa.

    Ba su daɗe ba kuma Nabila ta fito daga ɗakin baƙin da yake saman ta turo ƙofar ɗakin a hankali ta shiga, ta wuce Khadeejan a gefen gadon ta zagaya ta kwantar da Hammad a gafe ta lullube shi. Ta zagayo ta zauna a kusa da Khadeejan, ba ta motsa ba kamar ma ba ta san an zauna a kusa da ita ba. Ta mika hannu ta dafa nata hannun da yake kan cinyarta tana kallon fuskarta tana cewa ‘Yaya Khadeeja ga Hammad fa na kwantar miki da shi.’

    Ta kalle ta suka haɗa ido, ba tare da tace komai ba ta sake kawar da idonta saboda ta tokare hawayen da suke neman ƙwace mata. Nabila ta ɗan matsa hannunta tana cewa ‘Ya Khadeeja. Kafin tace wani abu hawayen ya fara bin idonta, gaba ɗaya ta sake su saboda yanda take faman riƙe su tana jin kamar an ɗora mata dakon wani kaya mai nauyi.

    Gaba ɗaya ta faɗa jikin Nabeela wadda ta rungume ta gaba ɗaya suka sa kuka. Ita Nabeela auren ma gaba ɗaya ya ƙara ba ta tsoro, kuma ta tabbatar ko da wanne lokaci za a iya ɗaura nata auren; tunda da ba don Ahmad ya tafi UK ƙaro karatu ba da tuni ta shekara a ɗaki. Ita kuma Khadeeja gaba ɗaya komai ma ya tsaya mata; tana dai fatan Allah ya sa Mustapha ya zama mai adalci.

    A hankali suka fara lafawa, Khadeeja ta zare jikinta ta kalli Nabeela. Suna haɗa ido suka tuntsire da dariya duk da hawayen da suke fuskokinsu. Suka riƙe hannun juna suna murmushi. Khadeeja ta dube ta tace ‘Sorry. Itama murmushin tayi mata tana cewa ‘Its’s ok, you will be fine in sha allah. Komai zai wuce kamar ba ayi ba.’

    Murmushi ta sake mayar mata sanna tace ‘Ki je ki kwanta, na san yanzu Abbansu zai shigo. Ta sake rungume ta sannan ta yi mata sallama ta fice ta rufe mata ƙofa. Ba tare da ɓata lokaci ba ta miƙe ta shiga banɗaki inda ta yiwo wanka sannan ta fito da alwala, ta shirya ta sa kayan baccinta sannan ta kabbara sallar isha’i.

    A nan ya shigo ya same ta tana zaune a kan dadduma tana gyangyaɗi; kallo ɗaya ta yi masa ta ji zuciyarta ta sake komawa cikin damuwa wadda ta fi ta da. Sai wani faman yage baki yake yana muzurai a lokaci guda; a sanin da ta yi masa ta san murna ce da ɗoki yake yi na amarya kuma yana ƙoƙarin tabbatarwa ita ɗin ba ta kawo masa cikas ba.

    Nan da nan ta danne duk wata damuwa da take ranta ta ƙaƙalo murmushi ta yi masa sannu da zuwa. A tsaye ya amsa ya yi mata bangajiyar biki sannan yace ‘Um ni bari na je, na ga ke ma bacci kike ji. In ya so da safe na shigo da ƙanwar taki ku gaisa. ‘To Allah ya kai mu. Ya juya ya fice ya rufo mata ƙofa.

    Ta ji daɗi sosai da ya sanar da ita ba zai shigo da matarsa a wannan daren ba, domin gaba ɗaya a gajiye take. Ba jikinta ba har ruhinta ma ji take ya gaji, fatanta kawai waɗannan kwanakin su wuce ko kuma ma ta farka ta ga mafarki take yi.

    Ta ga rayuwarsu ta dawo kamar yanda take a farkon aurensu; ko da yake a farkon auren ma babu wani abun kirki da za ta ɗorar; kamar dai gara ma tace rayuwarsu ta dawo yanda ake kafin aure. Sai da bacci ya fara ɗibanta sannan ta tashi ta kwanta a kan ganto ta kashe fitila.

    Edita@rumasau-kallamu

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Tara

     

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Tara

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Tara

    Duk yanda take cikin damuwa da zarar Mustapha yana waje to sai ta shiga walwalarta da yara, yayin da shi kuma duk wasu shirye-shiryensa na tarbar amarya ne. Har ta kai ba ya iya ɓoye murnarsa; shi da yara kullum hirarsu ta Anti Naja ce. Musamman Afaf wadda zuwa yanzu kusan gaisuwa ce kawai take haɗa ta da Khadeeja.

    Lafiya suka tare a sabon gida kuma kamar yanda ta zaɓi ɗakin sama haka ya haƙura ya ba ta ɗakin saman; duk da daga baya ya yi nadamar hakan. Domin da a ce ya san ta riga ta san da maganar aurensa to da tabbas zai gaya mata amarya zai saka a sama. Sai dai a lokacin tunaninsa ba ta san da maganar auren ba kuma ɓoye mata yake son ya cigaba da yi.

    Tsaf ta gyara ɗakinta da parlor, ɗakin su Afaf kuwa tunda ta ga ra’ayoyinta suna cin karo na da Afaf kuma tana nema ta yi mata rashin kunya sai ta haƙura. Sosai ɗakinta ya yi kyau, ta tsara musu komai nasu ita da Hammad, don Baffanta ma da Mommy sai da suka ƙara mata kuɗi ta yi sayayya.

    Sati yana zagayowa kuma aka shiga hidimar bikinsa. Babu yanda ba ta yi da Mustapha ba a kan ita ba ta so a yi mata taro amma ya ƙi amincewa; domin yace Hajia tace dangi ba su san sabon gida ba don haka za su zo su karɓi amarya sannan su ga gida.

    Tun dare ta sanar da shi cewa idan gari ya waye za ta bi ‘yan makaranta ta je gida wajen Mommy, kuma ba tare da wani musu ba ya amsa. Bayan ya kai ‘yan makaranta ya dawo suka zauna tare a parlor ɗin sama suna cin abinci yayin da Hammad yake hannun Rashida. Shiru suke cin abincin babu wanda yake magana, kamar ma dai ba sa cikin walwala.

    Ya ajiye cokalin da ke hannunsa yace ‘Kin ce babu wani abu da kuke buƙata saboda taryar baƙi ko? Ba tare da ta daina cin abincinta ba tace ‘Eh. Ni kam ma ai don dai ka hana ne da sai na yi tafiyata wajen Mommy idan aka kawo ta aka tafi sai na dawo da daddare ko ma da safe.’

    ‘No, don Allah ki bar wannan maganar. Ai ya kamata dai a ce a samu a karɓi baƙin nan cikin mutunci. ‘Um. Suka cigaba da cin abincinsu, jimawa kaɗan yace ‘Hajia ma tace a nan za su zo su yi biki ranar Lahadin, in ya so sai su tsaya su karɓi amarya sannan su tafi.’

    Ta kalle shi suka haɗa ido sannan ta kawar da kanta, wani malolo ya zo ya tokare mata maƙogoro; su Hajia za su yi biki a nan? Saboda suna murna za a yi mata kishiya ko me?Ta ɗauki kofin shayinta mai zafi ta kurɓa da fatan zafin shayin zai tafiyar mata da abinda ya tokare mata maƙogoro amma hakan bai samu ba.

    Ta kalle shi a jigace tace ‘Ka ga shikenan sai na tafi gidan Mommy ko? Tunda ka ga masu karɓar amarya za su zo.’Ya ɗan zaro ido yana cewa ‘Haba dai! Hakan kuma ai bai yi tsari ba, kina matar gida kuma a zo biki gidan ba kya nan. Ko ba haka ba ma kin san Hajia za ta ga kamar kin raina ta ne shi yasa za ki tafi ki bar su su kaɗai su yi bikin. Please ki yi haƙuri kawai saboda kada abun ya zama wata fitina kuma. Kin ji?’

    Ta ɗaga kai tana cewa ‘Uh. Yauwa, please ki yi haƙuri a gama taron nan ba tare da wata matsala ba. Ta yi gajeran murmushi tace ‘In sha Allah. Ya ture kwanon bayan ya kurɓe ɗan ragowar shayinsa sannan yace ‘Zan saka miki kuɗi a account ɗinki saboda na san za ki iya buƙatar wani abun ko don baƙi.

    Akwai ruwa da lemo wanda zan kawo, abincin kuma dama tunda kika ce ba za ki yi a nan ba na bayar da kuɗin don haka su Hajia za su taho da shi. ‘Ok. ‘Idan kuma da buƙata za ki iya yin wani abincin a nan ko da kaɗan ne. ‘Ok, babu damuwa. Ya miƙe ya shige ɗakin domin ya ƙarasa shiryawa.

    Nan take ita ma ta ture kwanon indomie ɗin ta miƙe ta haye sama. Kuka take son ta yi ko za ta ji sanyi a ranta, amma ba ta so ta ɓata lokaci musamman da yake yana jiranta kuma tare za su fita. Haka ta yi sauri ta shirya suka sauko tare, ta karɓi Hammad a wajen Anti Binta suka fice suka bar Anti Binta da Hafsu wadda ƙanwar Rashida ce aka kawo mata bayan an yi auren Rashidan tun kafin ta haifi Hammad.

    Haka suka zauna a mota babu wanda yake magana da ɗan uwansa; ya riga ya kula da yanda take nema ta tayar masa da fitina a wajen bikin nan amma ba zai bar ta ba. Sosai ya ji daɗi da Hajia tace za su zo nan su yi biki don ba ya so ta bayar da matsala idan an kawo amarya, amma ya san tunda Hajia tana nan babu wata matsala da za ta ba su. Haka ya je ya ajiye ta a gidansu sannan ya wuce.

    Tana shiga gidan ta sami Ahmad a parlor yana shan shayi; nan da nan ya miƙe ya karɓi Hammad daga hannunta. ‘Ina Mommy?’ ta tambaya bayan ta amsa gaisuwar da yake mata. ‘Tana ɗakin Baffa. Ba tare da ta ba shi amsa ba ta bar masa Hammad ta wuce ta nufi ɗakin.

    A zaune ta hango Mommy a kan dadduma ta miƙe ƙafa da waya a hannunta, ta jefar da mayafinta ta ƙarasa gaba daya ta faɗa jikin Mommy ta rushe da kuka. ‘Inna lillahi wa Inna ilaihi raji’un! Khadeeja me ya faru? Ina Hammad ɗin?’ Mommy ta tambaya cikin tashin hankali.Da ƙyar ta buɗe baki tace ‘Yana hannun Ahmad.’

    Ita kanta sai da ta ji ajiyar zuciyar da Mommy ɗin ta yi, sanna ta cigaba ‘To me ya faru kike wannan kukan haka? Ko Mustaphan sakinki ya yi ne? Ta jijjiga kai alamar a a ba tare da ta ɗago ba, ta cigaba da kukanta. Kawai sai Mommy ta haƙura da tambayar ta zuba mata ido, a hankali ta ɗaga hannunta tana shafa kanta; ta dai san da maganar saura kwana uku a ɗaurawa Mustapha aure don haka wataƙila wani abun ya yi mata wanda ya sosa mata rai shi ne ta taho nan tazo tana wannan kukan.

    Sai da ta ɗauki loakci tana wannan kukan sannan ta ɗan numfasa ta ɗago ta kalli Mommy, suna haɗa ido kuma sai ta sake fashewa da kuka. Cikin sheshekar kuka tace ‘Mommy ba zan iya ba, ba zan iya ba Mommy. Ta ɗago fuskarta tana share mata hawayen tace ‘Menene ba za ki iya ba Khadeeja?’

    Ta tsagaita da kukan sai dai hawayenta ya kasa daina fita; ta sa bayan hannunta ta goge hawayen ta kalli Mommy suka haɗa ido na ɗan lokaci. Ta kawar da kanta tace ‘Mommy ban san me Mustapha yake so da ni ba. Bayan ya gama raina min hankali lokacin da yana neman aure yanzu kuma duk da ban ba shi matsala ba amma ba zai bar ni na zauna lafiya ba.

    Ta share mata hawaye tana cewa ‘Me ya yi miki kuma? Mommy nace masa ina so ranar da za a kawo amarya na taho nan idan sun gama kai ta sai na koma ya hana ni, na haƙura nace zan zauna amma ba zan yi taro ba; su kawo amaryarsu kawai su tafi. Da farko har ya yarda amma yau yake gaya min wai babarsa tace za ta zo a nan gidan namu za ta yi biki, kuma yace ba zan tafi na bar su ba.

    Mommy so suke baƙin ciki ya kashe ni? Ɗansu zai yi min kishiya kuma su zo suna celabrating a gaba na? Da mamaki Mommy tace ‘Ikon Allah, ita mahaifiyar tasa ce za ta yi biki saboda zai ƙara aure? Ta sa hannu ta goge ragowar hawayen da yake kan fuskarta sannan tace ‘Eh Mommy, wai za su zo suyi biki. Kin ga kenan na ce ba zan karɓi amarya ba amma za su yi min dole.’

    Mommy ta kama hannunta ta kalle ta sannan tace ‘Ki yi haƙuri kin ji, za ki iya. Kishiya ba ta kashe kowa ba in sha Allahu ke ma ba za ta kashe ki ba. Ki bi su a hankali, dare ɗaya ne a yi ya wuce. Da an kwana biyu ita ma za ta zama kamar ke kuma yanda ya yi miki haka zai yi mata.

    Ta jijjiga kai tana murmushi mai ɗauke da ma’anoni tana cewa ‘Hmm! Mommy ba zai taɓa yi mana adalci ba. Kina ganin yanda tun kafin ta shigo shi da yaransa da ‘yanuwansa suka karkata wajenta. Gaskiya ban saka rai Mustapha zai iya yi min adalci ni da matarsa ba, sai dai kawai nace Allah ya ba ni haƙuri ko kuma ya kawo min mafita mafi alkhairi.’

    ‘Kada ki damu, ai ba shi ya yi kansa ba, in sha Allahu Allah ba zai bari ya cutar da ke ba daga shi har ‘yanuwan nasa gaba ɗaya.’‘Hmmm!’ ta sunkuyar da kai tana kallon yatsunta da take wasa da su. Jimawa kaɗan tace ‘Mommy ba na son a yi min biki a gida, bana son a kawo min amaryarsa a ce za a ba ni amanarta ko a yi mana faɗa tare. Amma kinga duk sun shirya hakan za su yi.’

    Mommy ta sake kamo hannuwanta duka biyun ta kalle ta suka haɗa ido sannan tace ‘Kada ki damu, kamar yanda na gaya miki na ranar ne kawai. Kuma ke ma ‘yan uwanki za su zo, duk da kin ce kada a zo da yawa toh yayarki za su zo da kamar mutum huɗu haka. Nabila kuma tace gobe za ta taho ta taya ki kwana zuwa lokacin da za su gama bikin. Kada ki damu in sha Allahu komai zai wuce.’

    Haka suka zauna Mommy ta yi ta ba ta baki har zuwa yamma. Ta samu zuciyarta ta yi sanyi amma dai ba ta da tabbacin ko za ta iya ɗauka, ta dai haƙura ta ga yanda za ta kaya kamar yanda Mommy tace. Sai da yamma sanna ta shirya ta koma gidan zuciyarta cike da wasi-wasi.

    Washegari ‘yan uwan amarya suka zo suka yi kafi. Ba su ja fitina ba don haka lafiya aka rabu, ta sa Hafsa ta miƙa musu kuloloin abincin da ta bayar aka dafa musu; don ita tunda suka shigo gidan ta haye sama kuma har suka gama ba ta sauko sun haɗu ba. Sun tura Hafsa ta je ta kirawo ta sau ba iyaka amma haka Hafsan take dawowa tace musu saman a rufe yake.

    Haka suka gama kafinsu suna ta rangaɗa guda, ga turare da suka baɗe gidan da shi. Sai da suka kusan gamawa sannan yara suka dawo daga makaranta, nan da nan suka shige cikinsu da yake sun saba da ƙannenta saboda yawan zuwa gidansu da suke yi.

    Dawowarsu daga gidan kafi ya yi daidai da dawowarta daga wajen lalle, a zaune ta same su a farfajiyar gidan ana ta hirarraki. Ta dubi yayarta Ummi tace ‘Yaya har kun dawo daga kafin? Ta taɓe baki tace ‘Hmmm! Mun dawo. Ta ɗan kalle ta da alamar tambaya tace ‘Ya na ga kina yatsina fuska? Komai dai ya tafi dai-dai ko?’

    Salma wadda cousin ɗinta ce tace ‘Um babu laifi. Amma fa mu a ƙasa Mustaphan ya nuna mana ɗaki guda biyu da parlor yace nan ne naki kuma a nan muka yi kafi. Saman gidan nan ma dai ‘yar mulkin uwargidan taki ba ta ko bari mun hau ba ta ja ƙofa ta rufe don ba mu ko isa ta sauko mu gaisa ba ta aiko mana da kulolin abinci kamar wasu mayunwata.’

    Ta zumɓuri baki ‘Ban gane a ƙasa ya ba ku ɗaki ba? Ai ni sama muka yi da shi kuma ya amsa min a kan haka. ‘To ai kuwa dai bai isa ba don Hajia Babba ta haye sama, ba ta ko saukowa idan ba ta ba wa baƙo mahimmanci ba. Nan da nan idonta ya kawo ƙwalla, ta miƙe ta ɗaga waya ta nufi cikin gidan. Ba tare da ɓata lokaci ba Yaya Ummi ta miƙe ta bi bayanta.

    A ɗaki ta same ta har ta lalubo lambar Mustapha za ta buga. Ta dafe wayar tace ‘Ba sai kin kirawo shi ba domin ƙarya kawai zai yi miki ya sake ɓata miki rai, alamu dai sun nuna ita ce mai gidan. Kada ma ki ɗaga hankalinki a kan wannan maganar balle ki hana ku morar satin amarcinku, don in kika hana muku wannan kwanakin to kin yi mata alfarma ne don ita za ta so haka.

    Ko da ma kun yi magana da shi ɗin ki nuna masa babu komai. Ta kalle ta tana zumɓura baki tace ‘Yaya babu komai fa kika ce? Ai ba haka muka yi da shi ba. Tun lokacin da ya sayi gidan fa muka je da shi nace sama nake so kuma ya amince, shi ne zai je kuma ya canja magana.’

    Ta yi murmushi tace ‘Kika san me aka yi masa ya canza? Wannan mata duk da ban ganta ba amma na san a shirye take, idan ba mu dage ba zuwa za ki yi ki zama ‘yar kallo don da alama tana shimfiɗa mulki yanda ranta yake so. ‘To yanzu ya za a yi?’

    Ta yi murmushi ‘Kada ki damu zan yi magana da Inna, dama kin ga tunda aka fara maganar bikin nan take faman nemar miki taimako. Kin ga yanzu sai a mayar da hankali a yi aikin da za ki haɗa kan gidan ki mallake a sauke miki ita daga benen kuma a cire ta daga zuciyarsa gaba ɗaya.’

    ‘Anti dama fa ba ta zuciyarsa gaskiya, don gaskiya haƙuri kawai yake yi da ita ba tun yau ba. Da bakinsa ya gaya min babu ragowar ƙaunarta a zuciyarsa…..’ ‘Ke rabu da shi, namiji ai munafiki ne. Za dai mu yi maganinsa tunda mun ga kamun ludayinta.’ Ta katse ta tana yarfe hannuwa.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Takwas

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wasu Kayan Busar Hausawa

    Wasu Kayan Busar Hausawa

    1.Algaita
    2.Farai
    3.Ƙaho
    4.Siriki/kusumburwa
    5.Kakaki
    6.Sarewa
    7.Shantu

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Yadda Sunayen Wasu Hulunan Hausawa Suke

    Edita@rumasau-kallamu

  • Sunayen Wasu Wanduna Da Takalman Hausawa

    Sunayen Wasu Wanduna Da Takalman Hausawa

    WASU WANDUNAN HAUSAWA

    1.Buje
    2.Feto (Kaliso)
    3.Tsala
    4.Tsaitsaye
    5.Tumazagi
    6.Zinah
    7.Zabuni
    8.Tarangama

    WASU TAKALMAN HAUSAWA

    1.Balka
    2.Ɗangarfai
    3.Fadde
    4.Markuɓi
    5.Sambatsai
    6.Wufi
    7.Asho

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Wasu Kayan Kiɗan Hausawa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wasu Kayan Kiɗan Hausawa

    Wasu Kayan Kiɗan Hausawa

    1.Banga
    2.Dundufa
    3.Ganga
    4.Goge
    5.Gurumi

    6.Garaya
    7.Gadangama
    8.Jauje
    9.Jinjintu
    10.Kalangu

    11.Kazagi
    12.Kukuma
    13.Kuntigi
    14.Kurkutu
    14.Kotso
    15.Kuge

    16.Kwamsa
    17.Kurya
    18.Molo
    19.Shantu
    20.Talle

    21.Tandu
    22.Turu
    23.Zari
    24.Duman girke

    FASIHIN KAITA

    Karanta Yadda Sunayen Wasu Hulunan Hausawa Suke

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Takwas

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Takwas

    Duk yanda take cikin damuwa da yanda take so ta yi wa Mustapha tijara game da yanda ya ɓoye mata maganar aurensa da Naja haka ta haƙura ta danne zuciyarta. Domin ita kanta ta kasa ganin maslahar yi masa maganar; tunda dai ita ce ba ya so ta sani gara ta rabu da shi ta gani ko za a ɗauro auren ne a kai amarya sama jannati saboda kada ta sani.

    Cikin da take ɗauke da shi ma kasa gaya masa ta yi, domin ba ta ga alamar yana farin cikin kasancewarta matarsa ba. Gaba ɗaya ma cikin ya zo mata a wani lokaci ne da take jin cewa da ba ta same shi ba za ta iya haƙura da haihuwa a gidan Mustapha har sai ta fahimci inda auren nasu ya sa gaba.

    Ko da yake dai ta san ana cewa idan namiji zai ƙara aure matarsa da take gidan sai ta yi matuƙar haƙuri; to tabbasa ta ji a jikinta cewa lokacin nata haƙurin ne ya kama yanzun. Da kansa ya kula da yanda take mu’amalarta kwana biyu cikin kasala ga shi ba ta ma son magana, don haka ya tasa ta a gaba ya kai ta asibiti.

    A nan aka tabbatar masa da cewa tana ɗauke da ciki sati shida. Suna zaune a mota yana tuƙo su a hanyarsu ta dawowa ya dube ta yace ‘Kin gani ko, kin sami cikin a kwanciyar hankali ba tare da kin je nemansa a asibiti ba ko? Allah ya sa dai ba mai wahala ba ne? Ta ɗan yi gajeran murmushi tace ‘Amin ya Allah.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, ya dube ta yace ‘Wai ya na ga duk kin yi wani shiru ne? kamar ba abin nema ne ya samu ba? Ta kawar da kai tana murmushin yaƙe tace ‘Bana jin daɗi ne, bacci ma nake ji. Ta kwantar da kanta a jikin kujerar motar ta rufe ido, don haka shi ma ya ƙyale ta ya mayar da hankali a wajen tuƙinsa.

    A haka Khadeeja ta dage ta cigaba da mu’amalarta tana yin duk wata hidima da ta saba. Ko a wanne yanayi ta tashi haka take daurewa ta yi duk wata hidimarta don ba ta shirya drama da Mustapha ba. Ta riga ta san idan dai tana numfashi a gidan nan to duk wata hidima da matar gida take yi ba yafe mata zai yi ba; don haka ta daure ta cigaba da dagewa tana yi.

    Musamman da yake duk wani aiki da ta saba yi a gidan ta riga ta koyawa Rashida kuma ta iya sosai, ga shi yarinyar ba ta da ƙyashi ko ɗaya, don haka abubuwa suka zo mata da sauƙi sosai. Sai dai fargabarta ɗaya iyayen Rashida suna maganar ko da wane lokaci za a iya zuwa a ɗauki Rashida saboda aurenta ya kusa; duk da dai an ce za a kawo mata ƙanwarta to amma ta san akwai aiki.

    Haka ta cigaba da rayuwarta tana goyon cikinta. A hankali ta fahimci lokutan da yake zuwa zance wajen Naja, kuma da yake shi yake kai ta makaranta da ta shiga motar take gane Naja ta fita a motar ko kuma sun fita tare. Daidai lokacin da za su fara jarrabawar ƙarshe a lokacin cikinta ya shiga wata na takwas; ga hidimar gida, ga karatu kuma ga shi tana ƙoƙarin haɗa project ɗinta.

    A dai-dai lokacin ne kuma Mustapha ya gama gyara gidansa wanda yake fatan da zarar sun koma za a yi bikinsa da Naja. Sau biyu yana kai su gidan ita da yara, kuma duka zuwa biyun sai ta tambaye shi ko aure zai yi ne yake yin gidan kamar da zubin mata biyu. Amma duk lokacin da ta tambaya sai yace mata ko da zai yi auren to ba yanzu ba; ta rasa gane dalilin da yasa yake son ɓoye mata aurensa da Naja.

    Don haka ma ta daina tambayarsa gaba ɗaya. Ranar Asabar ce kuma tun dare ya sanar da ita da safe yara su shirya zai fita da su, don haka tun wajen tara na safe bayan da suka ci abinci ta sallame su ta koma ta kwanta. Ya dai ce mata gidan Hajia za su je kuma su ma yaran haka suka gaya mata; amma a ‘yan kwanakin nan yana yawan fita da yaran ranar da babu aiki yace wajen Hajia zai kai su.

    Ta riga ta gane wajen Naja yake kai su, sai dai ba ta ga dalilin da zai sa ta yi masa magana ba tunda ‘yayansa ne sannan kuma gaya musu da yake su ce mata gidan Hajia suka je su yake cutarwa ta hanyar koya musu ƙarya. Gaba ɗayansu suka fice banda Habib, wanda dama ya riga ya saba duk lokacin da za su yi wannan fitar shi baya bin su.

    A gida yake zama tare da Khadeejan da Rashida. Sai wajen ƙarfe biyar na yamma sannan suka dawo, lokacin ta riga ta gama abincin dare ta zuba a flask tana kwance a ɗaki. A ɗakinta yaran suka same ta tana kwance tana hutawa, suka sanar da ita sun dawo. Shukra kuwa sai ta wuce ta haye gadon ta kwanta kusa da ita tana cewa ‘Bacci kike yi Anti?’

    Tace ‘A a, hutawa nake yi. Ta ɗan matsa jikinta tana gyara kwanciya, Khadeejan ta ɗan gyara kwanciyarta tana kawar da Shukran daga cikinta. Ta yi dariya tana cewa ‘Na matsa ko Anti, kada na lotsewa ƙanina hanci. Ta yi dariya saboda ita ce ta saba gaya mata hakan a duk lokacin da take son kwanciya a jikinta tunda cikin ya fara girma; domin Shukra yarinya ce mai son jikin tsiya kuma ta samu Khadeejan ba ta ture ta.

    Tace ‘Yauwa, ashe dai kin gane. Kada a dinga ce miki yayar mai lotsattsen hanci. Suka yi dariya gaba ɗaya; Shukra ta ci gaba da wasa da hannun Khadeejan guda ɗaya yayin da Khadeejan take riƙe da waya a ɗaya hannun tana chatting. Jimawa kaɗan cike da damuwa tace ‘Anti.’

    ‘Umm.’ Ta amsa ba tare da ta bar abinda take yi ba. Tace ‘Gaskiya ni ba zan koma wajen Anti Naja ba, a wajenki zan zauna ko? Ta ajiye wayar tace ‘To wa yace za ki koma wajen Anti Naja kuma? Ai muna nan tare, ko ba gamu ba a gidanmu. Cike da damuwa tace ‘Ai ita ma tace auro ta Abbanmu zai yi ta dawo gidanmu. Amma sai mun koma sabon gida.

    Shi ne yau da muka je wajenta take cewa Yaya Afaf idan ta tare duk wajenta za mu koma. Gaskiya ni dai ba zan koma ba ko? Ta ɗan yi shiru tunani yana nema ya birkita ƙwaƙwalwarta; duk da bai gaya mata ba ta san yana kai yaransa wajen Naja, amma maganganun da Najan take gayawa yaran ba sa kama da maganganun da ya dace a gaya musu a daidai wannan lokacin.

    Sai dai ta san babu yanda za ta yi tunda shi ya ba ta dama. ‘Anti.’ Muryar Shukra ta katse ta tana kiran sunanta. Bayan ta amsa Shukran ta cigaba cikin damuwa ‘Tace saura wata biyu ta tare, gaskiya idan ta zo ki gaya mata ni a wajenki zan zauna ba a wajenta ba. Kuma ma na ji tana gayawa Yaya Afaf idan an koma sabon gida sama take so ke ce a ƙasa, na gayawa Yaya Afaf mu ne a sama mu da ke tace min wai da Allah can.

    Gaskiya ki gaya musu mu ne a sama. ‘Hmm! Zan faɗa musu Shukra, ai mu ne a sama kada ki damu. Ta cigaba da surututa tana ba wa Khadeeja labarin irin abubuwan da suke yi idan suka je gidan Naja. Duk da Khadeeja ba ta yi mamakin jin cewa Naja ta san da sabon gida ba amma ta yi mamaki da ta ji cewa har Naja ta zaɓi part ɗin da take so yayin da ita kuma har yanzu bai ma gaya mata ita da wata matar za su zauna a gidan ba.

    Ta kasa gane dabarar da Mustapha yake jin ya yi da ya ƙi gaya mata zai yi aure; amma dai za ta cigaba da binsa ta ga ƙarshen wulaƙancinsa. Ko da yake a ‘yan kwanakin nan ma yanda yake ƙara tubure mata ta tabbatar da tana biye masa da kullum sai sun yi faɗa.

    To sai dai ba ta da wannan lokacin tunda ga project ɗinta wanda take so ta gama kafin su fara jarrabawa wanda tana fatan Allah ya sa kada haihuwa ta zo mata har sai tayi final paper. Haka ta ajiye wannan ma a ranta tana jiran ranar da za ta titsiye Mustapha tunda haka ya zaɓa.

    Tun kafin su fara jarabawa ya sanar da ita idan ta haihu aka yi suna aka gama zuwa barka za su koma sabon gida, saboda ba ya so a je a ɓata masa gida. Ita ma tsarin ya yi mata don haka ba tare da wata matsala ba ta amsa. Kuma kamar yanda ya ba ta umarni ta fara haɗa kayanta da za ta tafi da su duk da cewa ya gaya mata ya saka sabbin furniture a gidan.

    Ranar da za ta yi jarrabawar ƙarshe ya kama yara suna hutun makaranta, kuma sai 2pm za su shiga paper. Don haka yace idan babu matsala yana so ta shirya da wuri su tsaya a sabon gida ta ga furniture ɗin da ya siyo in ya so sai ya ajiye ta a makaranta shi da yara su wuce wajen Hajia. Ta riga ta gama karatunta don haka tun wajen sha ɗaya ta shirya suka shiga mota gaba dayansu suka kama hanya.

    Saman gidan yana ɗauke da parlor guda biyu ƙarami da babba da kuma ɗakuna guda uku sannan da kitchen, ɗaki daya da parlor suna tare da juna wanda dama ya sanar da ita nan ne nashi part ɗin. Ƙasan kuma parlor ne guda daya me haɗe da ɗakuna biyu da kicin kamar na saman, sai wani babban parlor ɗin kuma da ɗakuna guda biyu waɗanda suke kusa da juna.

    Parlor ɗin ƙasan duk a nan aka sauke furniture ɗin; duk da kusan kowanne yana cikin kwalinsa. Suna shiga suka ɗan yayyage kwalin ita da yara suka gani. Ya dube ta yana nuna ɗakunan ƙasan yana cewa ‘Sai ki zaɓi a wane dakin za a saka miki gadon, in ya so ɗaya dakin kuma sai a ɗauko gadonki na tsohon gida a saka.’

    Ta kama hanyar sama tana cewa ‘Eh hakan ma ya yi; ɗakin wanda yake jikin nakan sai saka min sabon gadon a nan in ya so na kusa da shi sai a gyarawa ‘yan mata na ko? Shi kuma Yaya Habib sai a ba shi ɗaya daga cikin wannan na ƙasan. Shukra ce kawai ta biyo ta shi yana tsaye a inda yake. Ta dan juyo tana cewa ‘To ka zo mu je mana ka gani.’Ya yi ‘yar dariya yace ‘Na zata za ki fi son waɗannan ɗakunan na ƙasa ai, kin ga sun fi girma.

    Kuma ai ina ga zai fi min privacy a ce ɗakin ki yana nan ƙasa a madadin yana kusa da nawa idan kin yi baƙi ina jiyo ku. Ta yi dariya tace ‘Haba dai, kuma don ni ce duk faɗin gidan nan sai na rasa wajen sauke baƙi sai bedroom? Ai dama sama ba wajen saukan baƙi ba ne tunda nan ƙasan ma da parlor.

    Amma dai can ne ɗakina, in ya so idan ma ba ka so yaran su hau sama za a iya barinsu a ƙasa. Shukra tace ‘Gaskiya Abba mu ne a sama mu da Anti, in ya so ita Anti N…’ Kafin ta ƙarasa Afaf ta katse ta cikin ɗaga murya tana cewa ‘To ba ki ji me Abban yace ba, ƙasan ya fi girma ne da space. Khadeeja tace ‘To mu dai ba ma son ƙasa, muna sama abin mu.’

    Ta ja hannun Shukra suka haye saman. Habib wanda yake tsaye a kusa da Abban nasu ya dube shi yace ‘Haba Abba, dama ai sama na Anti Khadija ne.’ Kallon da Abban ya yi masa ya sa ya kawar da idonsa da sauri ya waske yana cewa ‘Bari na je na taya su zaɓen ɗakin. Haka ya haƙura shi ma ya bi su saman inda khadeeja ta nuna masa ɗakin da yake jikin nasa tace shi take so, ɗayan kuma wanda yake gefe ɗaya sai a bar wa yara.

    Ba shi da wata hujja da zai ba ta a kan hana ta ɗaukan ɗakin sama, kuma har yanzu ba ya jin ya shirya gaya mata cewa zai ƙara aure, ya fi so sai ta haihu tukunna saboda kada ma ya ji tausayinta idan tace za ta tayar masa da hankali. Haka suka gama zagayensu a cikin gidan sannan suka shiga mota suka nufi BUK don su kai ta.

    Har suka isa makarantar ba ta daina mamakin Mustapha ba; ta kasa gane sai yaushe zai daina yi mata wannan ƙaryar. Kuma ta kasa gane dalilin da yasa yake fifita buƙatar Naja da son zuciyarta a kan tata, amma dai haka za ta cigaba da biye masa ta ga gudun ruwansa.

    Kwanansu biyu da gama jarrabawa Khadeeja ta haifi yaronta, don haka ko kwana ba ta yi a asibiti ba aka wuce da ita gidanta. Sai daga baya aka kawo mata Anti Binta wadda kanwa ce a wajen Mommy. Tun a asibiti Mustapha ya sanar da su ya sakawa yaro suna Muhammad; sunan Baffan Khadeeja. Daga baya Nabila ta yi masa laƙabi da Hammad.

    Nan da nan aka shiga hada-hadar shirya bikin suna; kuma a lokacin Mustapha ya sanar da ita idan an yi suna da sati biyu za su koma sabon gida. Ranar kwana biyu da haihuwa Mustapha ya sameta a dakinta da daddare, tana zaune a gefen gado da baby a cinyarta tana kallonsa tana murmushi. Ya ajiye shopping bag ɗin da ke hannunsa sannan ya zauna a kusa da ita ya shafa kan baby yace ‘Shikenan kuma kin mayar min da yaro abun kallo kamar wata TV ko?’

    Ta yi ‘yar dariya tace ‘To ina laifi, ina yaba halittar Allah ne. Ya matsar da ledar kusa da ita yana cewa ‘Ga wannan ‘yan office ɗinmu ne suka bayar a kawowa Baby. Ta karɓa ta ɗan buɗa ta leƙa sannan ta mayar ta ajiye tana cewa ‘Mun gode, Allah ya saka da alkhairi. Ai dole Muhammad ya kawo tukuici tunda an yi masa takwara.’

    Ya yi dariya. ‘Wannan ma ba na Muhammad ba ne, sauran ma’aikatana ne dai. Shi yace sai gobe za su zo da matarsa. ‘Allah sarki mun gode, Allah ya bar zumunci. Suka ɗan taɓa hira sannan ya fita. Yana fita ta ɗauki ledar ta zazzage kayan; rigunan Baby ne masu kyau da tsada guda biyu, sai set ɗin kayan sanyi guda ɗaya, set ɗin huluna da kuma set ɗin kayan wasa.

    Ta taɓe baki ta mayar da kayan cikin ledar, jikinta ya ba ta wannan kayan Naja ce ta bayar don haka ko burge ta ba su yi ba. Rawar kan da yake yi da ya shigo da kayan kaɗai ta isa ta sa ta san cewa daga wajen Naja kayan suka fito. Ta tsani yarinyar gaba ɗaya ta tsani ta tuna ta, ba ta ko son jin sunanta. Haka ta ajiye kayan da niyyar da zarar an gaya mata haihuwa ita ma za ta yi barka da su.

    Lafiya ƙalau aka gama taron suna; musamman da yake Khadeeja ta kawar da kanta daga abubuwa da yawa. Domin hatta abincin sunan Yaya Jidda cewa ta yi ya ba su za su yiwo su zo da shi, shi kuma ya hau kai ya zauna. Tunda ta ga haka ta gayawa Mommy kada su yiwo gayya da yawa, sannan Baffa ya ba su kuɗi suka shirya nasu abincin wanda suka taho da shi.

    Ko da Yaya Jidda ta gansu da kulolin abincinsu sai ta soke duk wani wulaƙanci da ta shirya yi musu, haka aka gama taro kowa ya watse lafiya. Bayan kwana biyu tana kwance a ɗakinta tana hutawa da daddare wayar Mustapha ta shigo; ta riga ta san yana cikin gidan don haka ta san kiranta yake yi. Haka yake yi tunda Anti Binta ta zo; baya shiga ɗakinta sai dai ya yi mata waya ita ta same shi a ɗakinsa.

    Ba tare da ɓata lokaci ba ta miƙe ta nufi ɗakin. Ta ƙarasa ta zauna a gefen guda kusa da shi tace ‘Gani. To sannunki da zuwa.’ Ya faɗa yana bin idonta da kallo yana ƙoƙarin karanto yanayinta. Ta yi murmushi tace ‘Godiya nake, a ba ni abinda aka kawo min. Suka haɗa ido na dan lokaci, ya ɗauke nashi idon ya ɗan cije leɓe sannan yace ‘Ya shirin tashi, saura kwana biyar fa.’

    ‘Ai ni na gama shiri, maƙota ma duk na gama sallama da su. Sai mun tare zan yi musu kwatance su zo ganin gida. To da kyau. Suka yi shiru na ɗan lokaci; ita tana sauraronsa don ta kula da magana a bakinsa yayin da shi kuma yake ta sake tauna maganar bakin nasa yana tunanin ta inda zai fara. Ya kalle ta suka haɗa ido ya yi gajeran murmushi, ita ma ta mayar masa da murmushin. Cikin sanyin murya yace ‘Um ki yi haƙuri ki saurare ni kuma ki fahimci maganar da zan gaya miki.’

    Ta kalle shi na ɗan lokaci da mamaki a fuskarta tace ‘In sha Allah.’Ya sake gyaran murya sannan yace ‘Um Khadeeja aure zan yi, don maganar da nake miki ma saura sati biyu a ɗaura auren. Idan mun tare a sabon gida da sati ɗaya ita ma za ta tare. Suka haɗa ido, ta yi murmushi sosai sannan ta zare hannunta daga nashi tana cewa ‘Allah sarki, abun ya zo kenan. Toh Allah ya sanya alkhairi.’

    Buɗe baki ya yi yana kallonta saboda tsabar mamakin yanda ta nuna halin ko in kula da maganar tasa kamar dai wadda yake cewa gobe Litinin a ranar Lahadi. Ta miƙe za ta fice ya riƙe hannunta yana cewa ‘Um wani abun kike yi ne kike saurin tashi. Ta koma ta zauna tana cewa ‘A a, na zata ka gama maganar da za ka faɗa ɗin.’

    Ya ɗan sunkuyar da kai saboda gaba ɗaya ya kasa haɗa ido da ita, wannan halin ko in kula ɗin da ta nuna yasa duk ya firgice; gaba ɗaya ta goge masa haddar kalaman da ya tsaro don ya ba ta haƙuri. Cikin sanyin murya yace ‘Um baki ma tambayi wacece wadda zan aura ba. Ta ɗan yi dariya tace ‘Oh, Naja ce mana. Ko ka fasa auren nata ne?’

    A jigace ya amsa ‘Ita ce. Ta daga gira cikin halin ko in kula tana shirin miƙewa tace ‘Allah ya sanya alkhairi. ‘Um, wai dama kin san zan yi auren ne ko na ga kamar kin sani tun tuni. Ta yi ‘yar dariya ta koma ta zauna tace ‘Na sani mana, ko bai kamata na sani ba? Ya jiijiga kai ‘No, ina dai mamaki ne. Suka yi shiru na ɗan lokaci.

    ‘To don Allah wa ya gaya miki?’ Muryarsa ta katse mata tunani yana tambaya. Ta yi ‘yar dariya tace ‘Oh, ka san fa na ɗauka kai ka gaya min; ashe ba kai ba ne. Ina jin dai a cikin waɗanda ka gayawa ne kace kada su gaya min aka sami wani ya gaya min. Ya sunkuyar da kai domin ya kasa haɗa ido da ita; wato duk wannan tsawon lokacin ashe kallonshi kawai take yi duk abinda yake ɓoyewa ta sani.

    Ba ƙaramin mamaki ya yi ba. Kafin yace wani abu suka jiyo kukan Hammad daga cikin gidan, don haka ta dube shi tace ‘Ka ji yarona can yana kuka, bari na je na gani. Ta fice ba tare da ta saurari amsar shi ba. Tana fitowa daga ɗakin Mustaphan ta tarar da Anti Binta a parlor tana ta jijjiga Hammad, tun kafin ta ƙarasa wajensu tace ‘Yunwa yake ji, zo ki ba shi ya sha.’

    Ta karbe shi ta shige ɗakinta Anti Binta tana biye da ita. Haka ta daure ta haɗiye malolon da ya tokare mata maƙogoro har ta gama ba shi nono suna hira da Anti Binta. Sai da ya sha ya ƙoshi sannan ta miƙawa Anti Binta shi tana cewa ‘Ga shi Anti Binta, banɗaki nake son shiga. Ta karɓe shi ta miƙe tana cewa ‘To muna can ɗakin yara muna hira da mutuniyata.’

    Ta fice ta ja mata ƙofa sannan ta miƙe ta shige banɗakin don ta san idan dai tana cikin ɗakin nan wani sai ya zo nemanta, idan kuma ta rufe da mukulli za a yi ta faman tambaya. Tana shiga banɗakin ta turo ƙofar ta jingina a jikin kofar, take hawayen da take riƙewa suka ƙwace kamar an kunna famfo. Ta haɗa tafukan hannayenta ta rufe fuskarta tana jijjiga kai, saboda tsabar takurar da zuciyarta ta yi har wani ɗaci take ji a bakinta.

    Yaushe Mustapha ya raina ta haka? Wannan ma ya fi ƙarfin raini ya koma wulaƙanci. To me yasa ya yi mata haka? Daman can ba ya sonta ne ko kuwa son da yake mata ne ya ƙare? Ba ta taɓa tunanin za ta auri miji ta zauna ita kaɗai ba amma dai ta ɗauka idan ka auri mutum zai cigaba da girmama ka yana ganin mutuncinka har ƙarshen tarayyarku.

    A halin yanzu ta rasa wanne za ta yi; murna ta haihu ita ma ta sami yaro ko kuwa jaje za ta yi wa kanta tunda ko babu komai wannan yaron da ta haifa zai ƙarawa alaƙarta da Mustapha tsawon rai. Ba ta san tsawon lokacin da za ta iya ɗauka tana jure wulaƙanci irin wannan da Mustapha yake mata ba, amma dai ta san tabbas ba za ta iya jurewa har abada ba.

    Ga shi shi ba dukanta yake ko zagi ba, wani irin wulaƙanci ne yake mata yana nuna cewa komai normal ne, kuma a mafi yawancin lokuta ma idan ta yi magana sai a dinga nuna mata haka maza suke. Domin kowa ce mata kawai yake idan dai namiji ne ba ta ga komai ba. Ta bar wa Allah al’amarinta kuma za ta jira su tare ta ga yanda yanayin zaman zai kama; amma tabbas idan aka cigaba a haka ba ta jin za ta iya zama da Mustapha.

    Zuwa yanzu kuma duk wasu alamu sun nuna mata cewa ba zai taɓa yi mata adalci ba ita da Naja, kamar ma dai yanzu ne ya yi aure na soyayya wanda yake sa ran zai more rayuwarsa a ciki; tunda ta gama yi musu wahala ta raini yaransa lokacin da suke tsananin buƙatar uwa. Yanzu sun girma sun zama mutane don haka sai ya aure wadda yake so ta zo su more rayuwarsu ita kuma a mayar da ita saniyar ware.

    A hankali ta zame a jikin ƙofar ta zauna ta sake fashewa da kuka. Sai da ta yi mai isarta sannan ta ba wa kanta haƙuri ta wanko fuskarta ta fito daga banɗakin.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Bakwai

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Bakwai

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Bakwai

    A zaune yake a parlor ɗin Alhaji, yayin da Hajia take zaune a kusa da Alhajin. Zuwa ya yi musu da labarin auren yana son ya ƙara don har ma yana gaya musu sati me zuwa yake so a je a kai kuɗin aure.

    Cikin walwala Alhaji yace ‘Ai kwanaki da muka yi magana da kai da na ji ka shiru na zata ka fasa. Ya yi ‘yar dariya ‘Ba fasawa na yi ba Alhaji, na dai ɗan tsaya ne na ƙara shiryawa, na gaya maka zan sayi gida ai.

    To dama tsayawa na yi a samo gidan, kuma yanzu an samo, cinikin ne ma bai faɗa ba saboda ina so su ɗan yi min ragi. Amma in sha Allahu ina sa ran za mu daidaita shi yasa nake son yanzu a kai kuɗin auren.’

    Murmushin Alhaji ya ƙara faɗi, ya dubi Hajia sannan ya dubi Mustapha yace ‘To ma sha Allahu. Wannan ai sai dai mu sa albarka kawai. Ka je ka sami babanka Safiyanu ka yi masa bayanin ita yarinyar idan ya gama bincikensa ya tabbatar gidan mutunci ne ai sai su je su kai kuɗin. Allah ya sa albarka, Allah ya ƙara buɗi.’

    Suka haɗa baki shi da Hajia suka ce ‘Amin. Hajia tace ‘To ka gayawa Khadeejan ko? Me tace? Ya shafa kai yana murmushi ‘Ban gaya mata ba tukunna, amma in sha Allahu zan gaya mata. So nake sai an gama magana tukunna idan ya zama saura kamar sati uku ko huɗu sai na gaya mata ko don saboda gudun fitina.

    Kafin nan na siya gidan mun koma. Alhaji yace ‘Eh, to hakan ma ya yi. Sai dai kuma Allah ya sa kada mata su riga ka gaya mata. Hajia tace ‘A a babu wanda zai gaya mata, ka yi abinka a hankali idan ka shirya ka gaya mata. Nan suka ƙare hirarrakinsu daga baya ya yi musu sallama ya kama hanya.

    Abu ɗaya ne yake ci wa Khadeeja tuwo a ƙwarya rashin haihuwa, domin har yanzu tun bayan cikin da ta samu ya ɓare ba ta sake ko da ɓatan wata ba. Ga shi yanzu har sun shiga final year amma babu wani labari.

    Duk lokacin da ta yi yunƙurin zuwa asibiti Mustapha sai ya nuna halin ko in kula ko kuma yace lafiyarta ƙalau za ta je ta fara neman fitina, don haka ta tattara ta haƙura. Sai dai ta yankewa kanta hukuncin cewa da zarar ta gama final exam za ta je asibiti a duba ta a tabbatar mata da abinda ya hana ta samun ciki; ko babu komai ita ma tana so ta ga ta haifi dan cikinta.

    Tunda idan ta gama karatu ba ta san lokacin da za ta sami aiki ba. Haka ta haƙura ta mayar da hankali a kan karatunta tana addu’a. Zamanta da yaran Mustapha kaɗai ya isa ya sa ta ji tana son haihuwa; domin yanzu yaran sun girma tunda Shukra auta ma tana primary 1 yayin da Afaf take SS.

    Kusan gaba ɗaya yaran yanzu ba daɗinsu take ji ba, domin abinda suka ga dama suke yi. Habib ne ma kawai wanda ya damu da rayuwarta kuma yake neman shawara a wajenta kamar uwa, amma Afaf da Nasreen ma ba ta san wanene yake ba su shawara ba.

    Ta dai san duk wani abu na wulaƙanci da suke yi mata da sa hannun Yaya Jidda. Ga wani mahimmanci da Musttapha yake ba wa Afaf ta yanda ko da sun gama magana da Khadeejan Afaf tana iya saka shi ya canza. Duk abinda ya shafi yaran kuma ko da Khadeeja ce ta gaya masa to a ƙarshe da Afaf ɗin zai yi shawara.

    Hatta kitchen ɗin gidan ya zama kamar na mata biyu; domin a lokuta da damam sai ta gama girka abinda kowa zai ci ta fita daga kitchen ɗin sai Afaf ta shiga ita ma ta dafa abinda ta ga dama tace ba ta cin wanda Khadeejan ta dafa. Ta yi magana har ta gaji, tunda Mustaphan ya fara nuna tana so ta takurawa Afaf ne saboda ba ita ta haife ta ba.

    Tana kwance a ɗakinta tana jiyo hayaniyar yaran a parlor; Afaf ta shigo ta same ta ta miƙa mata waya tana cewa ‘Anti Abba ne yake waya yace yana kiran wayarki ba ta shiga. Ta tashi zaune ta karɓa ta ɗan kalli wayar ta ga whatsapp call ne, sannan ta kara a kunnenta.

    Yace ‘Ina kika shiga ne nake kiran wayarki ana ta cewa not reachable? Ta yi ‘yar dariya tace ‘Sai dai ko idan network ne don ga wayar ma a hannuna. ‘Kin san Ali Ahmed ko? Abokina da muke zuwa zance tare. ‘Eh na san shi mana.’

    ‘Yauwa da Allah shi ne ya shigo gari nan da kamar awa ɗaya za mu zo gidan, me za ki iya dafa masa sai mu yi dinner tare. Yana dai son tuwo ‘Ok, to sai a yi tuwon ai. Amma dai ka bari na duba freezer tukunna na ga yawan kazarmu yadda za a samu a yi muku peppersoup ma ko?’

    ‘Eh, ƙwarai kuwa da zobo ma please. Duba idan babu kazar sai na bayar a kawo miki yanzu, riƙe wayar ki duba ki ba ni amsa. Ta miƙe ta dubi Afaf da take tsaye tana jiran wayarta ta nufi kitchen.

    Suna fitowa parlor Afaf ɗin ta ga Nasreen ta canza channel ta mayar Disney Junior, da sauri ta yi kanta tana cewa ‘Wane mara kunyan ne ya canza min channel ban gama kallo ba. Anti idan kin gama wayar ina nan.’

    Ta shige kitchen ta bar su. Tana shiga ta ƙarasa ta buɗe freezer ta duba sannan ta ce masa ‘Za ta isa ma, amma dai idan za ka dawo sai ka siyo wata don gaba ɗaya zan kwashe na dafa muku yanzun. Suka yi sallama ta katse wayar.

    Sunan da ta gani a jerin chats ɗin kan wayar shi ya ja hankalinta ta fasa fitowa daga kitchen ɗin tana ƙarewa sunan kallo; Anti Naja aka rubuta da alamar zuciya ta emoji. Daga haka da take kallon hoton da yake kan sunan kuma tabbas Naja ce sakatariyar Abbansu.

    Ba tare da ta yi wani tunani ba ta danna kan sunan ya buɗe mata chats ɗin, har za ta yi sama sai kuma wani saƙo da yake cikin jerin saƙunan da ke ƙasa ya ja hankalinta. Afaf ce ta turawa Naja saƙon kamar haka “Congrats Anti, Abba ya ce min an kawo kuɗin auren ko?”

    “Eh my girl, sun kawo har da sadaki ma. Saura kawai ya gama gyaran sabon gidan mu shikenan. “I can’t wait to have you here with us Anti.”“Soon my girl. Amma dai ta daina ba ki matsala ko? “Ta daina, tunda ta ga babu riba. Yanzu ba sosai ma take kula ni ba dama ni haka nake so. Habib ne kawai sarkin rawar kai ya manne mata.”

    “Kada ki damu kwanan nan zan zo na gyara mata zama. Motsin da Khadeejan ta jiyo ne ya sa ta yi sauri ta rufe saƙonnin ta dire wayar a kan teburin da yake kusa da freezer ɗin ta kama murfin freezer ɗin ta ɗaga kamar a lokacin ta rufe. ‘Anti ina wayar?’ Afaf ta faɗa bayan da ta ƙarasa shigowa kitchen ɗin.

    ‘Kin ganta nan a kan tebur, ɗauki. Ta ƙarasa ta ɗauki wayarta ta fice ta koma parlor ɗin. Cikin sanyin jiki Khadeeja ta tsaya a ta jigina da freezer ɗin ta kafa tagumi. Kusan wata takwas da suka wuce Mustapha ya kalli tsabar idon Baffa da Mommy yace musu ba auren Naja zai yi ba, amma ga shi daga waɗannan chats ɗin da ta karanta yanzu har an kai kuɗin aure da sadaki.

    Wato ma Afaf ta san komai ita ce kawai ba ta san mijinta zai ƙara aure ba kenan; kuma kamar dai ba shi ma da niyyar gaya mata. To me ta yi wa Mustapha ne? Me yake tunanin za ta yi a a kan ƙara aurensa da yake ɓoye mata?

    Ita dama da ya kai ta gidan da ya siya yanda ta ga gidan ta san sai ya ƙara aure, kawai dai ba ta zata Naja zai auro ba don kwata-kwata ba ta sake ganin wata alama da take nuna yana tare da Naja ba tun bayan da suka je wajen Baffa.

    Wato dama da take zargin Yaya Jidda ce take hure mata kunnen yara ashe Naja ce, tunda ga shi nan ta gani har tana gayawa Afaf cewa za ta shigo ta gyara mata zama. Ta jijjiga kai, ta goge gumin da ya fara tsattsafowa daga goshinta sannan ta tuna ce mata fa ya yi nan da awa ɗaya za su zo.

    Jikinta a sanyaye ta koma cikin gidan ta kirawo Rashida sannan suka fito suka kama aiki. Haka ta haɗiye duk wani ɓacin rai ta yi ta haba-haba da abokinsa, sai bayan sallar isha’i sannan ya yi musu sallama ya tafi.

    Ta san cewa ya kula da yanayinta yanda ya sauya, amma bai yi mata magana ba. Duk da dai ko da ya yi mata maganar ma za ta gaya masa gajiya ce kawai. Haka dai suka kwana shi yana baccinsa ita kuma Khadeeja duk lokacin da ta yi juyi sai ta kalle shi tana tambayar kanta wai me ta yi masa ne yake mata abubuwa kamar wata wadda aka aura ba don soyayya ba?

    Haka ta haƙura ta yi ta danne zuciyarta har gari ya waye. Sai ƙarfe biyu na rana take da lecture amma haka ta shirya da wuri lokacin da Mustapha ya shirya zai tafi office tace ya wuce da ita ya kai ta gidan Mommy, in ya so daga can sai ta wuce makarantar ta kuma dawo gida. Haka kuwa aka yi.

    Tunda ta shiga gidan Mommy ta karanta damuwa a fuskarta, ta dai kyale ta har Baffa da Nabila suka gama shirinsu suka fice. A nan parlor ɗin inda suka bar su Mommy ta zuba mata ido na ɗan lokaci, har ta ji a jikinta Mommy ɗin kallonta take. Tana juyowa kuwa suka haɗa ido; ta ɗan yi dariya tace ‘Mommyy.’

    Ita ma ta yi dariyar tace ‘Ya aka yi ne? Kamar dai kina da damuwa. Ko kuma ba kya jin daɗi ne? Ta jijjiga kai tace ‘Mommy Mustapha aure zai yi.’Ta ɗan zaro ido ‘Aure? Ikon Allah.’ Sai kuma ta saki fuskarta ta cigaba ‘Ko da yake wannan ba abin mamaki ba ne ai don haka kada ma ki saka wa kanki damuwa.’

    Ta sunkuyar da kai cikin damuwa tace ‘Mommy ni ma ba damuwa na yi ba, kawai dai yayanyin abun ne. Ban gane ba. Nan ta sanar da ita wadda zai aura sannan ta sanar da ita a inda ta ga labarin auren da kuma irin saƙonnin da Afaf take tura wa Najan da kuma yanda take fama da Afaf ɗin a ‘yan kwanakin nan.

    Duk da Mommy ba ta yi mamaki ba amma dai ta ji babu daɗi, musamman yanda Afaf ta zama ‘yar rahoton Naja. Tace ‘Ikon Allah, to shi me yasa yake ɓoye miki auren? Tace ‘Wallahi ban sani ba, ko da wasa bai taɓa gaya min ba kuma danginsa ma babu wanda ya gaya min.

    Amma kin ga yaran har sun sani, tunda ga shi har ana gaya musu za a zo a gyara min zama. Lallai mutum sai a bar shi. Dama na gaya miki Mommy tunda na ga gidan da ya saya nace miki gidan nan ba na mace ɗaya ba ne, kin ga maganata ta tabbata.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan Mommy tace ‘To da ce mata aka yi ba ki zauna daidai ba da take cewa za ta gyara miki zama ko me? Amma kafin ta gyara miki zama ke ce za ki bi dare ki gyara zama ta hanyar addu’a, idan gari ya waye kuma ki ɗora da sadaka.’

    Ta sunkuyar da kai tana ƙoƙarin ɓoye ƙwallar da ta gangaro a kwarmin idonta; wannan kalmar ta za a gyara mata zama ta tsaya mata a rai. Domin dai kalma ce da za ta iya ɗaukan kowacce ma’ana. Amma kamar yanda Mommy ta faɗa hakan za ta yi tunda ta san ba ta da gatan da ya wuce Allah.

    Haka suka cigaba da hira Mommy tana ta ba ta baki kuma tana yi mata alƙawarin daga nan ma za ta dinga yi mata addu’a kuma da sadaka, ta tabbatar mata ba za ta yi nasara a kanta ba.

    Da wuri Mommy ta sauke abinci saboda Khadija ta ci kafin ta tafi makaranta, tana daga kitchen ɗin ta ƙwalawa Khadeejan kira. Tana shiga kitchen ɗin ta fara gatsina fuska tana cewa ‘Mommy wannan wane irin kifi ne kika dafa me azabar ƙarni? Allah ya sa dai ba da shi kika yi abincin ba.’

    Mommy ta ƙare mata kallo na ɗan lokaci sannan tace ‘Wane kifi da aka dafa tun jiya da daddare aka cinye, ni shinkafa da wake ma na dafa. Nana da nan fara’arta ta ƙaru, ta ɗauki plate ta matsa tana miƙawa Mommy tana cewa ‘Yauwa Mommy zuba min na fice don wallahi kitchen ɗin nan ƙarni yake.’

    Ta karɓi plate ɗin tana cewa ‘Ciki ne da ke ko? Ta kalli Mommy da baki a buɗe, suka ɗan zuba wa juna ido sannan ta rufe bakin tace ‘Anya kuwa Mommy, tunda dai ni ban ji wani sauyi na a zo a gani ba.’Ta zuba mata abincin ta miƙa mata tana cewa ‘To ki dai bincika tukunna kafin ki yi saurin cewa a a, don tunda kika shigo nake kula da ke gaba ɗaya ma na dauka abinda ya kawo ki kenan.’

    ‘To ban sani ba gaskiya Mommy, amma zan duba yau ɗin nan kuwa. Bayan ta gama cin abincin ta yi sallah sanna ta fice ta kama hanyar makaranta. Sai da ta tsaya a chemist ta sayi abun pregnacy test sannan ta wuce. Ta riga ta san su Rahma suna jiranta a hostel don haka kai tsaye can ta wuce, tana ajiye jakarta a ɗakin ta fice ta faɗa toilet.

    Tana tsoma abin nan a fitsarinta ya nuna raɗau positive; wato tana ɗauke da ciki. Ta yi murmushi tana ji kamar ta daka tsalle saboda murna, nan da nan idonta suka ciko da ƙwalla saboda jin dadi. A take kuma jikinta ya yi sanyi da ta tuna cewa Mustapha ne ya yi mata ciki kuma shi ne yake shirin auro matar da ta ke ikirarin za ta shigo ta gyara mata zama.

    Ta sunkuyar da kai ta saki takardar a ƙasa sannan ta fito daga banɗakin cike da damuwa. Yanayin da ta shiga ɗakin ya tabbatar musu da akwai matsala, don haka tun kafin ta Zauna Farida ta miƙe ta tare ta tana cewa ‘Ya na ganki haka, lafiya dai ko?’

    Ta zauna a kan gado Rahma kamar wadda aka jefa, ta kalli Farida suka haɗa ido sannan ta saki murmushe wanda yake haɗe da takaici tace ‘I am pregnant Farida. Nan da nan su Rahma da Amina da ke zaune suka dako tsalle suka faɗa jikinta sun ihu.

    Sai da suka fahimci ita ba ta taya su ihun kamar yanda suka saba sannan suka tsaya suna kallonta. ‘Girl, wannan ai abun murna ne na ga kamar ke ba ki ji daɗi ba.’ Amina ta faɗa tana riƙe da hannun Khadeejan.

    Ta sunkuyar da kai ta zare hannunta ta goge ƙwallar da ta faɗo daga idanunta. Ta ba su labarin auren Mustapha da kuma abinda ta gani da ma yanda yake ɓoye mata. Tace ‘Ban ma san wanne zan yi ba; murna ko baƙin ciki? Ni da za a zo a gyarawa zama ina zan miƙe ƙafa na fara haihuwa; haihuwar da ni ban ma tabbatar zai yi murna da ita ba.

    A yanzu ma gaba daya kai na ya kulle. Mommy dai tace kada na kuskura na yi masa maganar ƙara aurensa, na bar shi har sai ya zo da kansa ya gaya min, a lokacin sai a yi duk wadda za a yi. Amma wallahi ban sani ba ko zan iya jurewa. Gaba ɗaya ma yanzu ban san matsayina a wajen Mustapha ba, kuma ga ciki.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci. Amina ce ta katse shirun nasu tana cewa ‘Gaskiya mutumin nan dan wulaƙanci ne, haba!’ Rahma tace ‘Amma gaskiya ina bayan Mommy, ki bar shi kawai kada ki yi masa magana in ya so idan ya zo zai gaya miki da kansa sai ki yi masa wankin bargo tunda dai babu abinda zai sa ya fasa wannan auren da yayi niyya.’

    Tace ‘Haka ne. Nan suka ɗauki lokaci suna ba ta baki, sannan daga baya Farida da Rahma suka fice suka tafi lecture ɗin suka bar su a ɗakin ita da Amina wadda ta tsaya ta taya ta zama don tace ba za ta iya zuwa lecture ɗin ba.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Shida

    Edita@rumasau-kallamu

  • Amfanin Rake Ga Lafiyar Ɗan Adam

    Amfanin Rake Ga Lafiyar Ɗan Adam

    Bincike ya tabbatar da Rake yana da matuƙar amfani ga jikin Ɗan Adam kamar haka:

    1- Rake yana taimaka wa HANTA.
    2- Shan rake yana maganin CIWON ƘODA.
    3- Shan rake yana saukar da ZAZZAƁI.
    4- Shan rake yana maganin matsananciyar MURA.
    5- Shan rake yana saukar da HAWAN JINI.
    6- Shan rake yana taimaka wa ƙwaƙwalwar Ɗan Adam.

    Domin Shi sukarin da yake cikin Rake yana ɗauke da sinadarin FOLIC ACID

    6- Yana da amfani ga namiji me matsalar zafin fitsari.
    7- Haka kuma yana da matuƙar muhimmanci ga mace mai juna biyu.

    Karanta Amfanin Kankana (Watermelon)

    Edita@rumasau-kallamu