Tag: yadda ake

  • Abincin Hausawa Kashi Na 1

    Abincin Hausawa Kashi Na 1

    1.Alkaki
    2.Algaragis
    3.Alkubus
    4.Akuri
    5.Alala

    6.Alallagira
    7.Alewa
    8.Awara
    9.Acca
    10.Amaro

    11.Bado
    12.Balagade
    13.Burabusko
    14.Cuɗe
    15.Cuku

    16.Cin-cin
    17.Dambu (gero,dawa,masara)
    18.Dambu (nama, kifi)
    19.Dabuwa
    20.Dashishi

    21.Ɗan-narogo
    22.Ɗanwake
    23.Dage
    24.Daƙashi
    25.Dubulan

    26.Dankali
    27.Daƙuwa
    28.Daddawa
    29.Ɗan- bagalaji
    30.Ɗan-ta-matsitsi

    31.Dawo
    32.Dambun Da’u
    33.Fate
    34.Fura
    35.Fankasu

    FASIHIN KAITA

    Karanta Yadda Wasu Kayan Da Hausawa Ke amfani Da Su Ga Doki Suke

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Takwas

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Takwas

    Kwanci tashi sai da Khadeeja ta kwashe shekaru biyu tana aiki a gidan rediyon nan a matakin internship sannan aka sami gurbi aka ɗauke ta cikakken aiki, aka saka mata albashinta Naira dubu saba’in.

    Ba ƙaramin daɗi ta ji ba da samun wannan ci gaban domin tun da ta fara service ya zama wasu hidimomin nata ita take yi wa kanta kamar kayan shafe-shafe, turare wani lokacin ma har da sutura. Ba ta sani ba ko haka yake yi wa Najan ma tunda ita ma tana da albashi ko kuma ita kaɗai yake yi wa hakan.

    Sai dai ba ta da lokacin da za ta bincika ko kuma ta tambaya don haka take rayuwarta yanda ta ga za ta iya. Afaf ta shiga Jami’ar Bayero ta Kano inda take karantar Computer Science yayin da Habib yake SS3 yayin da Nasreen take JSS3 ita kuma Shukra tana primary 5.

    Zuwa yanzu duk baƙon da ya yi kwana ɗaya a gidan zai gane cewa gidan ya kasu kashi biyu; Shukra da Halifa waɗanda su ‘yan ɗakin Khadeeja ne da kuma Afaf da Nasreen waɗanda su ‘yan ɗakin Naja ne. Ko a wajen tarbiyya ‘ya’yan ɗakin Khadeeja sun fita daban da ‘yayan ɗakin Naja.

    Domin ita Khadeeja tarbiyyar take ba su da kulawa saboda Allah kamar yanda take yi wa Hammad, ita kuma Naja hankalinta yana kan yanda za ta ƙwace gida ta mallake maigidan don haka duk abinda zai saka shi farin ciki shi da yaransa shi take yi; ko da kuwa abun ba daidai ba ne.

    Lokuta da dama idan ta je wajen malamanta tana samu ta fara juya Mustapha, sai dai abun bai fiya daɗewa ba. Da zarar ta fara samun yanda take so sai kuma ta sake rasa kan maigidan nata. Ta yi iya bakin ƙoƙarinta ganin ta inda za ta samu ta haɗa shi faɗa da Afaf amma ta gagara; saboda son da yake yi wa Afaf ba kaɗan ba ne. Kuma kusan duk wani abu da zai yi to da Afaf yake shawara.

    Haka aka yi a farkon shekarar nan da zai canza mota; da kansa yake faɗa Afaf ce ta zaɓar masa motar bayan ita ba ta ma san zai canza motar ba sai da aka kawo motar gidan. Haka kuma aka yi da zai canza fentin gidan; Afaf ce ta zaɓi wanda take so aka yi, sai daga baya matan gidan suka ji labari.

    Lokuta da dama Naja ta so su haɗe kai da Khadeeja ko da su samu su ƙwaci Mustapha daga hannun ‘yayan ne, amma ba ta sami haɗin kai ba. Domin har yanzu zaman nasu dai babu yabo babu fallasa. Shi yasa ma Najan take wa Khadeeja kallon ba ta san me take yi ba saboda yanda ta bari yara suke controlling miji.

    Ita kuwa Khadeeja ba ta taɓa ɗaukan alaƙarsa da yaransa a matsayin matsalarta ba, matsalarta ɗaya da shi rashin adalcin da yake nuna mata tsakaninta da Naja. Idan dai abun a nuna kulawa ne da ƙauna to Naja yake nunawa, amma idan abu ne wanda za a yi masa hidima shi da yaransa to sai yace a kai wa Khadeeja.

    Duk wani ƙoƙari da za ta yi ta ga ya nuna mata so da ƙauna ta yi amma abun ya ci tura; har ta gaji ta zuba masa ido. Lokuta da dama idan ta yi magana sai dai ya dinga ƙoƙarin nuna mata cewa ya fi sonta kuma ya fi trusting ɗinta shi yasa yake saka ta hidimarsa da ta yaransa. Ta gaji da jin wannan tatsuniyar shi yasa ma ta haƙura ta daina ƙorafi; kawai dai duk abinda za ta yi za ta yi, abinda ba za ta yi ba kuma haka za ta zuba masa ido ya ƙaraci barazanarsa amma ba ta yi.

    Haka rayuwarsu ta cigaba.——–

    Tun kafin ta yaye Hammad al’adarta ta dawo, don haka kai tsaye ta tafi asibiti ta karɓo ƙwayoyin family planning; ko Mustaphan ma ba ta gayawa ba sai da ta karɓo. Ba wai haihuwar ce bata so ba, kawai dai ba ta da tabbas ɗin zaman auren.

    Kullum Mustapha nuna mata yake ita ce jakar gida yayin da Naja ita ce matar gida; don haka duk da yana kula da yaransa sosai kuma yana son su amma ba ta jin za ta iya tara masa wasu yaran balle ma a zo inda za ta yi magana a ce ta yi haƙuri ta zauna don yaranta.

    Tunda ta karɓi ƙwayar nan ba ta taɓa yin fashi ba kamar yanda likita ya sanar da ita, ko da kuwa ba ita ce da kwana ba haka take shan ƙwayarta. Amma a ‘yan kwanakin nan gaba ɗaya ta rasa gane kan jikin nata; wasu abubuwa take ji kamar na mai laulayi.

    A hanyarta ta dawowa daga office ta tsaya a chemist ta siyo pregnacy test strip, har ta zo gida tana fargaba saboda duk wasu alamu na ciki sun gama bayyana a tare da ita. Sai da ta bari ta yi baccin dare sannan ta ɗauki fitsarinta na sassafe ta gwada da shi; kafin sakamakon ya bayyana a jikin ‘yar takardar gaba ɗaya ta gama ruɗewa.

    Ko da ta ga layukan guda biyu sun bayyana ba tare da wata matsala ba sai da zuciyarta ta kusan bugawa, ta muttsike ido ta sake kalla amma har yanzu layukan suna nan guda biyu. Haka ta haƙura ta miƙe ta ɗauro alwala sannan ta fito daga banɗakin ta tayar da sallar asuba.

    Bayan ta idar da sallar ta zauna a kan daddumar ta yi shiru; ta daga hannu za ta yi addu’a amma ta rasa ta inda za ta soma. Gaba ɗaya ma ba ta san me take ji ba. ‘Alhamdulillah. Ta faɗa a fili kamar me yin raɗa. Haka ta ƙarasa azkar ɗinta sannan ta miƙe ta shiga hidimarta.

    Dole ta haƙura ta daina shan ƙwayar family planning ɗin da take sha saboda kada ta je ta cutar da abinda yake cikinta. Sai bayan kwana biyu ta ɗan sami natsuwa sannan ta je asibiti aka sake yi mata gwajin, aka tabbatar mata tana ɗauke da ciki na sati shida. Bayan ta dawo daga asibitin sannan ta sanar da Mustaphan.

    Wannan gwajin da ta yi kuma sai ya zama kamar ta kunno laulayin gaba ɗaya. Babu inda yake mata ciwo amma tana fama da kasala sosai sannan kuma ga rashin son cin abinci. Haka dai ta cigaba da lallaɓawa.

    Ranar kwananta ne don haka Mustapha a ɗakinta zai kwana. Yaran duk sun kwanta a ɗakinsu yayin da Hammad da Shukra suke kwance a ɗakin baƙinta wajen Hafsa. Yana zaune a gaban mudubinta yana aiki a computer ɗinsa yayinda ita kuma take kwance a kan gado tana game a waya. Ya bar aikin ya juyo yana kallonta ya kirawo sunanta, ta bar game ɗin ta mayar da hankalinta kanshi sannan ta amsa.

    Yace ‘Umm! Ina so dama na sanar da ke bana za mu je aikin Hajji da Naja. Da da ke za mu je amma kin ga ke laulayi ya saka ki a gaba don haka na cire sunanki na saka nata sunan. Ta ɗan yi shiru saboda yanda maganar ta zo mata a ba-zata; idan dai ba wai ba ta ga dai-dai ba ma kamar dai ganin da ta yi wa Najan shekaran jiya ta ga kamar ita ma tana ɗauke da yaron ciki; ko da bai fito ba dai amma ita Khadeejan ta ga wasu alamu.

    Domin a lokacin har ta ji kunya tana fatan Allah ya sa ba ganewa Najan ta yi ita tana ɗauke da ciki ba ta je ita ma ta yi. Kallon da ya kafe ta da shi ya sa ta yi firgigit ta dawo hayyacinta tana cewa ‘Masha Allahu, Allah ya nuna mana. Amma ai ana zuwa da masu ciki kuma zan iya; in dai an yi niyyar kai ni to a ba ni kujerata zan je.’

    Ya yi dariya ‘Haba aikin hajin fa ba wasa ba ne kuma ba a kwance ake yi ba, ko so kike mu je wahala ta sa ki sami miscarriage? Kuma ya za a yi na ɗauke ku mu tafi saudiyya gaba ɗayanmu? Mu bar yaran a wajen wa? Kin san Hajia yanzu ba lafiya ce da ita ba.’ ‘Haka ne, to ai sai Najan ta zauna ni na je tunda ni ka fara yin niyyar biyawa.’

    ‘To ai na gaya miki ke ga ciki, da a ce ba ki sami ciki yanzun ba da ke za mu je amma ki yi haƙuri sai shekara mai zuwa in Allah ya nuna mana. Ta tashi zaune ta ƙara marairaicewa tace ‘Idan na mutu a haihuwa fa? Ya harare ta yace ‘Ka faɗi alkhairi ko ka yi shuru.’

    Ta sunkuyar da kai tana murmushin yaƙe; yayin da ya juya ya cigaba da aikinsa. Ta zame ta koma ta kwanta; tabbas ba kuskure ta yi ba ciki ne da Naja, ko da kuwa bai kai sati shida ba. Kuma tabbas ta san ba ita Mustapha ya yi niyyar biya wa Hajji ba, Najan ya so biyawa. Kawai dai cikin ya zo masa ne a matsayin uzuri da kariya. Ya wanke kansa daga zargi.

    A hankali ta zame ta gyara kwanciyarta ta janyo abun rufa ta rufe jikinta sannan ta rufe idonta kamar mai bacci; haka ta kwana zuciyarta tana ƙuna. Me Mustapha ya mayar da ita ne; shikenan idan dai abun ƙaruwa ne ba zai iya sakata a ciki ba sai bayan ya saka Naja amma idan dai wahala ce ita ce a kan gaba? Yanzu yana nufin yace da matarsa zai tafi aikin Hajji; wadda ita ma cikin ne da ita sannan ita kuma ya barta ta kular masa da yara da gida duk da ita ma cikin ne da ita.

    Za ta iya wahalar kula da gida amma ba za ta iya wahalar ibada ba kenan? Sai yau ta gane girman rainin da Mustapha ya yi mata da kuma yanda ya ɗauke ta. Tun ranar da Mustapha ya sanar da ita zai tafi Saudiyya da Naja ta so ta je gida wajen Mommy, amma saboda kada abun ya yi kama da za ta yi reporting ɗinsa sai ta haƙura.

    Tun dare ta sanar da shi za ta je gida kuma ya ba ta izini, don haka gari yana wayewa da yake ba ita ce da girki ba ta shirya. Hafsa ta kama hannun Hammad suka sauko, suka fice tsakar gida suna jiranta yayin da ita kuma take rufo part ɗinta. Ta saba duk lokacin da za ta fita idan Naja tana nan sai ta leƙa ta sanar da ita ta fita, don haka yau ɗin ma tana saukowa ta shige parlor ɗin Naja.

    Tun kafin ta hango fuskokinsu ta ɗauki muryar Yaya Jidda, ba ta yi mamaki ba tunda yanzu sun saba zuwa gidan su wuni a wajen Naja idan ba ta sauko ba babu mai hawa nemanta kuma ko yara ba za a tura a ce ta zo ba. Ta ƙarasa ta zauna a kan hannun kujera ta gaida Yaya Jidda cike da girmamawa sannan suka gaisa da Naja.

    Har ta miƙe za ta fice Yaya Jidda ce ‘Sai muka ji abun arziki kuma, Mustapha yace da shi da Naja za su je aikin Hajji. Ta ɗan koma ta zauna tana murmushi tace ‘Eh, haka yace. To Allah ya sa su je a sa’a, muma ‘yan baya Allah ya kirawo mu. ‘Amin ya Allah.’ Ta amsa sannan ta miƙe ta yi musu sallama ta fice.

    Har ta je gida abun yana yi mata ciwo a rai; wato har ma ya gayawa ‘yan uwansa da Naja zai tafi Hajji kenan an fara zuwar mata murna ta kuma ana yi mata Allah ya kawo na ‘yan baya. Kuma wannan ganin da ta yi wa Naja ya ƙara tabbatar mata da cewa Najan tana dauke da ciki domin yawu ne a bakinta irin wanda masu ciki suke tarawa.

    Tun da ta shiga gidan Mommy ta san da matsala, amma dai ba ta tambaye ta ba saboda bata son ganin kukanta. Ta san yanzu da ta tambaye ta damuwarta sai ta yi kuka mai isarta sannan za ta gaya mata damuwar. Suna zaune a parlor ɗin Mommy bayan sun gama cin abincin rana suna hira yayin da Hammad yake ta kai wa da kawowarsa, Mommy ta dube ta tace ‘Ki bar min Hammad a nan ya kwana biyu ki samu ki ɗan huta, na ga duk kin yi wani zuru-zuru.’

    Ta yi gajeran murmushi tace ‘Ga shi nan Mommy an bar miki, idan na shirya sai Ahmad ya mayar da ni gida ya karɓo masa kayansa. Ta yi dariya ‘Dama neman kai ake da shi.’ Jimawa kaɗan tace ‘Momy wai Abbansu ne zai tafi Hajji shi da Naja. Nan da nan fara’arta ta ƙaru, tace ‘Kai ma sha Allahu, Allah ya amsa ibada.’ Ta kalli Khadijan suka haɗu kuma kamar wadda aka tunawa wani abu tace ‘Ah, to ke me yasa ba za a haɗa da ke ba ko kuma a fara kai ki, ko kin yi halin naki ne ya ɓata miki rai kin ce ba kya son kujerar?

    Ta sa yatsanta ta goge ƙwallar da ta faɗo a kwarmin idonta, ta kawar da kai sannan tace ‘Haka ya zaɓa ya fara tafiya da ita. Da mamaki ta zaro ido tana tambaya ‘To ke me kika yi masa, tunda dai ai kece babba ke ya kamata ya fara tafiya da ke ko kuma ya tafi da ku dukanku a lokaci guda.’

    ‘Yace wai ciki ne da ni don haka ba zai tafi da ni ba sai dai ko wata shekarar zuwa lokacin na haihu. Ta kalli cikinta sannan ta kalli fuskarta ‘Ciki? To ai ƙarami ne kuma na ga har yanzu ana zuwa da masu ciki sai dai idan basu da lafiya. Ni ban ma san kina da cikin ba ai. ‘Ni ma bai fi last week na gane ba, ban ma sa rai da shi ba kawai na gan shi.’

    Mommy ta dafa hannunta tace ‘To ai shikenan tunda ya zo sai mu ce Allah ya raya, amma dai masu ciki suna zuwa aikin Hajji har yanzu. Ana ta dai cewa za a hana amma ba a hana ɗin ba tukunna. Kawai da yace bai so zuwa da ke ba. Ta sake share ƙwalla tace ‘Tabbas Mommy bai so ba, don ita ma Najan ai ciki ne da ita.

    Kawai dai ya zata ban san tana da cikin ba ne shi yasa yake so ya raina min hankali kamar yanda ya saba. Ikon Allah. ’Suka yi shiru na ɗan lokaci; ita ma Mommy abun ya ɗaure mata kai. Duk gidajen da ta sani na mata biyu ko sama to idan irin wannan damar ta samu babba ake fara kai wa. Tabbas abun ya sosa mata rai to amma babu yanda za ta yi.

    Ta dafa hannun Khadeejan wadda ita ma ta yi nisa a nata tunanin tace ‘Kuma ba ki gaya masa Najan ma ciki ne da ita ba? Ban gaya masa ba Mommy, kuma ba zan gaya masa ba. Yana sane da abinda yake yi Mommy, tsaf ya san tana da ciki. Ita da take tara yawu idan tana laulayi, kuma ko yau ma da na shiga wajenta da yawun a bakinta.

    Kawai dai da ita ya yi niyyar zuwa, ko na gaya masa kuma ba canzawa zai yi ba sai dai kawai ya yi ta kawo hujjoji. ‘Uhm, to ai shikenan. Kin ga dama shi Hajji kiran Allah ne, ke ma in sha Allahu Allah zai kirawo ki nan ba da daɗewa ba ta hanyar da ya so. Kada ki sa wata damuwa a ranki balle ki illata ɗan da yake cikinki.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan ta gyara zama tace ‘Wallahi ni Mommy na ma gaji da auren nasa gaba ɗaya. Tabbas ko shekara nawa zan yi da Mustapha ba zai taɓa canzawa ba, ba zai iya yi min adalci ba. Wataƙila ya daina so na, wataƙila kuma iya son da yake min kenan. Amma dai gaskiya na gaji Mommy.’

    Ta dafa hannunta cike da kulawa tace ‘To ai haƙuri za ki yi, dama shi aure ya gaji haka kuma ribar aure ta me haƙuri ce. Ba ki sani ba ko ita abokiyar zaman naki wani abun take yi na biye-biyen malamai, ai duka ana yi. Ta yi murmushin yaƙe tace ‘Ai wallahi babu wani biye-biye Mommy, a hayyacinsa yake yi.

    Kawai dai idan hidima za a yi masa to ya fi so ni ya saka ni aiki, idan kuma morewa zai yi da harkar soyayya to wannan ita ta iya. Amma babu wani asiri haka ya tsarawa kansa. Ta sake kama hannunta ta riƙe tana kallon fuskarta tace ‘Ki dai yi haƙurin, in sha Allahu za ki ga ribarsa. Kuma idan dai Hajji ne da izinin Allah ke ma zai kirawo ki.’

    ‘Uhm.’ Nan suka ɗauki lokaci Mommy tana ba ta baki. Can zuwa yamma ta shirya Ahmad ya mayar da ita gida ta ba rwa Mommy Hammad.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Bakwai

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wasan Ƙunshi A Yau

    Wasan Ƙunshi A Yau

    Zamani ya yi matuƙar tasiri a wasan ƙunshi. Idan muka dubi shi kansa wannan wasa, za mu ga a ɓangaren da ake amfani da Tufafin da suke amfani da su a lokacin wasan akwai; atamfofi da shaddodi da leshe-leshe da boyal-boyal da wagambari da (material) da yaduka kala-kala da dogayen riguna da hijabai da niƙabai da mayafai da kayan ƙyale-ƙyale.

    Ana yin ɗinkuna iri daban-daban, waɗanda masu aiwatar da wasan ƙunshi suke amfani da su a lokacin aiwatar da  wasan. Masu aiwatar da wasan ƙunshi, a yau sukan yi ado da kwalliya a ranakun wasan, ba kamar yadda ake gudanar da shi a baya ba, tun daga ranar farko har zuwa ranar ƙarshe, daga kan sarƙoƙi da ‘yankunnaye da roses da awarwaraye da zobuna da barima, da agogo da ribas da jakankuna, har ma da tabarau.

    Bugu da ƙari, suna amfani da kayayyakin irin su; mayukan shafawa iri daban-daban, da turare, da jambaki, da hoda barbaɗa-kumatu, fiƙe-hanci, da ataciman da yin ƙunshi, na zamani wato fulawoyi, kala-kala, a hannu da ƙafa.

    Haka wasan ƙunshi a wannan lokaci ya tasirantu musamman masu aiwatar da wasan suna yin amfani kayan kaɗe-kaɗe da waƙoƙin na zamani, inda suke amfani da mp da bluetoot  da rikoda da sauransu, wajen sanya waƙoƙi iri daban da daban. Suna amfani da su ne musamman wajen ƙara armashin wasan haɗi da nishaɗantarwa.

    A yau, an samu wadatuwar wasu hanyoyin fasahar sadarwa na zamani, wasu daga cikin su sun haɗa da wayoyin tafi da gidanka ko kuma wasu suce wayoyin hannu da computer suna taimakawa matuƙa gaya wajen aiwatar da wasan, a na ɗaukar hotuna da turawa saƙonnin kar ta kwana ta amfani da fasahar sadarwa da suka haɗa da instgram da facebook da tiktok da sauransu.

    Ana tura yadda wasan ke gudanar wasu kai tsaye ga ‘yan uwa da abokanan arziƙi zuwa ga waɗanda basu sami damar halartar wasan ba,ta hanyar tura musu saƙonnin ciki da wajen ƙasar nan, kamar Ghana da Kamaru da Saudi Arabiya da Mali da sauran sassan ƙasahen duniya. Sannan kuma sukan ɗauki yadda ake gudanar da wasan kai tsaye tare da yin jawabi wasan yake kasancewa tamkar kamar yadda ake aiwatar a nan take.

    Haƙiƙa a yau, an samu sauye-sauye, musamman a ɓangaren addini a domin yaran da ba sa cika azumi ko kuma basa yin sa, da yin sallah a lokacin da ya dace da sauran abubuwan da suka shafi addini. A yau abin ba haka yake ba. Masu aiwatar da wasan suna tafiyar da harkokin addinisu kamar yadda shari’ar musulunci ta sharaɗanta kamar yin azuminsu ba tare da ƙin yi ba ko kuma karya shi, haka ma suna aiwatar da sallah a lokacin da ake gudanar da ita, da sauran abubuwan da suka shafi addini. Sai dai idan da (akwai dalili na rashin yin hakan musamman mai lalura (‘yan mata).

    Sannan kuma wasan a yau, yana kan hanyar dusashewa, saboda sauye-sauyen zamani, kamar ta fuskar addinin musulunci, karatun boko da sauransu. Wasu a waɗannan ranaku suna zuwa dai ranar da ake karatun makarantar allo da makarantar islamiya da kuma makarantar boko, wanda sun taimaka wajen rage kaifin aiwatar da wasan kamar yadda ake aiwatarwa a baya.

    Sannan kuma a sakamakon a yau babu wadatattun filayen wasanni, wannan shi ma ya taimaka gaya wajen koma bayan aiwatar da wasan ƙunshi. A yau filaye sun yi ƙaranci babu wadatattu wasu an yi gine ginen gidaje, yayin da wasu kuma gwamnati ta yi wasu abubuwan na ci gaban al’umma.

    Haka nan, ta fuskar tsaro a wannan lokaci ba iya samun damar wasan ya kai wani lokaci mai tsaho ana gudanarwa kamar a baya, wannan yana faruwa a ‘yan shekarun nan sakamakon rashin wadataccen tsaro, wanda a yau ƙasar Hausa a wannan lokaci take fuskanta. Wannan ya taimaka a yau iyayen yara basa barin ‘ya’yansu sukai wani dogon lokaci suna aiwatar da wasan kamar yadda ya kamata.

    Wanan bayanin an ciro shine daga maƙala mai taken Nazarin Wasan Ƙunshi Jiya Da Yau A Ƙasar Gaya wadda Magaji Ahmad Gaya Ph.D Sashen koyar da Hausa Jami’ar Northwest, Kano ya wallafa.

    Emai: magaya@nwu.edu.ng

    08066009039

    Danna nan don karanta Yadda ake Gudanar da Wasan Ƙunshi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda ake Gudanar da Wasan Ƙunshi

    Yadda ake Gudanar da Wasan Ƙunshi

    Da zarar watan azumin ya kama, watan (Ramadan), ‘yan mata su ne masu ko suke gudanar da wannan wasa a ƙarƙashin tallafin ‘yan uwa da abokan arziƙi na danginsu da ma na dangin surukai, har ma da abokan ‘ya’yansu, da samarinsu da abokan samarin, da duk waɗanda suka sani suna da alaƙa da su.

    Wannan alaƙa ta ‘yan uwantaka ko kuma ta zaman tare, a ɓangaren cinikayya ko kuma a zaman unguwa ɗaya, mutun ya kan bayar da tallafinsa na gudanar da wannan wasa da zarar watan ya kama na azumi daga dangi na kusa da na nesa.

    Yadda ake karɓar wannan tallafi shi ne yarinya za ta yi wanka ta ɗaura atamfa kyakkyawa kamar ranar Sallah, a wannan lokaci tana bin gidajen danginta, tana zuwa gaishe su, inda za ta faɗa musu ta zo karɓar hatsin ƙunshi. Nan take idan wurin da za a yi wasa da dariya ne, sannan a ɗebo abin da ya samu a ba ta.

    Waɗansu sukan bayar da gero, ko dawa ko maiwa ko shinkafa ko kaza ko zakara ko ɗan shila. Waɗansu na bayar da zabi waɗansu ƙwai waɗansu kuma sukan bayar da kuɗi da dai sauran abubuwan da mutum yake da halin da zai iya bayarwa. Idan ta haɗa waɗannan kayayyaki ta kammala karɓar tuwon ƙunshi na wannan shekara ke nan.

    Abu na gaba, za ta tafi ta ɗauki ‘yar ƙunshi. Ita ‘yar ƙunshi yarinya ce ‘yar ƙarama za ta samu ko ‘yar yayarta ko ‘yar ƙanwarta ko kuma ‘yar uwar ɗakinta, ko kuma ‘yar abokiyar wasanta, ko kuma wata daga cikin dangi. Wannan yarinya ita ce ‘yar ƙunshinta, sai ta sanar da mahaifan yarinya, yarinyar wacce ba ta wuce shekara shida zuwa shekara tara ba (6-9).

    Daga wannan lokaci su ma iyayen yarinya ta same su, domin kuwa su ma za su haɗa kayan abinci su ba uwar ɗakin ‘yarsu, daga wannan lokaci wannan yarinya da aka ɗauko wato (‘yar ƙunshi), shi ke nan duk wata ɗawainiyarta, ta koma kan uwar ɗakinta, (wato wannan budurwa).

    Wankanta da shanta da cinta, waɗansu ma idan suna da hali har ma tufafinta duk sun koma kan uwar ɗakinta. Wannan nauyi ya ɗoru har lokacin da za a yi auren wannan budurwa. Wannan yarinya ita ce za ta zama ‘yar zaman ɗaki kafin kwana arba’in (40).

    Za a saka tabarma ta kaba (turarriya) a yi mata ado mai kyau. Wannan tabarma za a ba wa ‘yar ƙunshi a ce mata ga tabarmarmu ta cin tuwon ƙunshi, saboda haka, wannan yarinya ita ce mai alhakin kula da ita, bayan an kammala waɗannan shirye-shirye. Ga waɗanda suke da hali suna yin sababbin ɗinkuna, waɗanda kuma ba su sami halin hakan ba, sukan sanya tufafinsu kyawawa.

    Ita wannan yarinyar za a yi mata ƙunshi tare da uwar ɗakinta kafin lokaci ya rage kwana ɗaya ko biyu. A ranar da ake azumi na ashirin da shida (26), a wannan rana kowace budurwa komai girmanta, ba za ta yi azumi ba, saboda rana ce ta wannan wasa na ƙunshi.

    Dangane da waɗancan kayayyakin abinci da kuɗaɗe waɗanda aka samu daga dangi da abokan arzuƙa. A ranar ashirin da shida (26) har zuwa ashirin da takwas ana girke-girke, na alfarma a duk gidan da budurwa take, idan an gama dafa abinci, su yara ƙanana-ƙanana suna shiga gida-gida suna cewa a ba su tuwon ƙunshi, kowanne da kwanonsa, za a karɓa a zuba musu.

    Da rana ta yi, za a tafi wani gida da aka ware ko dai gidan wata Amarya a unguwar ko kuma gidan wata mata wadda ta yi fice a wannan unguwa, inda ‘yanmatan suke wasanninsu tare hirarsu a gidan, sai su ce bana a gidan wance za a ci tuwon ƙunshi.

    Idan an kammala dafa abinci kowacce ‘yar ƙunshi da aka ɗauko za a ɗora mata wannan tabarma a saka ta a tafi wancan gida da aka ambata a can za a ci tuwon ƙunshi. Kowacce budurwa a nan gidan za ta ɗauko abincinta ta ci. Kuma kowacce zata zo da sabuwar tabarma da aka saƙa ta musamman.

    A wancan lokaci yara maza suna zagawa wurin waɗanda suka sani, suna cewa a ba su tuwon ƙunshi, kowanne da kwanonsa. A ɓangaren yarinyar ‘yar ƙunshi a ranar babu abin da za ta yi sai zama da kuma cin abinci wadda take so. Sannan a hannu guda kuma, ita wannan matar gida, ‘yanmata za su zuba abinci a kwano a kai mata.

    Haka abubuwan za su ta tafiya tare da kai wa-da-komowa wasu zau tafi dandali wasu kuma bayan gari ya danganta inda suka ga dama har bayan sallar la’asar ana guje-guje da tsalle-tsalle da wasannin gargajiya iri-iri da gata da waƙoƙi da sauran wasanni har zuwa almuru ko kuma faɗuwar rana, sai kuma a dawo wannan gida, kowacce ta rage kuma ta ajiye abincinta haɗi da tabarma ta za a ɗauko sauran abincin a ƙarashe shi, daga nan an gama cin tuwon ƙunshi na ranar farko.

    A rana ta biyu (2) wato ranar ashirin da bakwai (27) da kuma ranar ashirin da takwas (28), duk waɗannan wasannin iri ɗaya ne, sai kawai hidimar wata rana tana fin ta wata rana, a nan ake samun bambanci. To idan an yi wannan abinci na ranar ashirin da takwas ga wata (28), wato ranaku uku (3) ke nan ana gudanar da wannan wasa, to shi ke nan an kammala cin tuwon wasan ƙunshi.

    Ita kuma ‘yar ƙunshi za a yi mata saye-saye daga gidan su uwar ɗakinta (wadda ta ɗauko ta), sannan ta ɗauke ta mayar da ita wurin iyayenta, shi ke nan wannan ‘yar ƙunshi ta yi uwar ɗaki, shi ke nan duk shekara ta zama ita ce ‘yar ƙunshinta ba wacce za ta ɗauki wannan yarinya sai ita.

    Yayin da wannan budurwa ta kawo munzalin ayi mata aure, ita mahaifiyar ‘yar ƙunshi sai ta taka rawar gani a al’amarin auren, idan an yi auren ‘yar ƙunshin da ita za a tafi gidan mijin, sannan a canza mata suna ta koma ‘yar burganci”, ma’ana mai yi wa amarya aikace-aikacen gida, da ayyukan da amaryar nan za ta yi. Wannan ‘yar burganci ita ce mai yi mata hidima kamar share-share da wanke-wanke da duk wani aiki da amarya za ta yi. A nan gidan take kwana take tashi, har kwana arba’in.

    Game da azumin da ba a yi ba wato suka sha ya tafi shi ke nan, sannan kuma sauran azumi guda biyu (2) ko ɗaya (1) ba kowace budurwa rama shi ba ko kuma take ƙara yinsa ba, da yawa ba sa ramawa, wasu kuma sukan ƙara har zuwa ashirin da tara ko talatin (30) ya danganta da yadda aka yi a wannan shekarar, ashirin da tara (29) ko talatin (30).

    Wanan bayanin an ciro shi ne daga maƙala mai taken Nazarin Wasan Ƙunshi Jiya Da Yau A Ƙasar Gaya wadda Magaji Ahmad Gaya Ph.D Sashen koyar da Hausa Jami’ar Northwest, Kano ya wallafa.

    Emai: magaya@nwu.edu.ng

    0806600903

    Danna nan don karanta Bukukuwa Da Wasanni Da Nishadi Na Bahaushe

    Edita@rumasau-kallamu

  • Menene Wasan Ƙunshi?

    Menene Wasan Ƙunshi?

    Wasan ƙunshi, yana daga cikin nau’o’in wasannin gargajiya wanda samari da ‘yan mata suke aiwatarwa shekara-shekara. Sannan yana ɗaya daga cikin wasanni na al’ada da ake aiwatar a watan cika ciki.

    Mafi tsufa daga cikin mutanen da aka gana da su sun bayyana cewa wannan wasan haka suka tashi suka ga ana gudanar da shi ba za su iya tabatar da lokacin da aka fara shi ba. Sun bayyana mana sunayen iyaye da kakanninsu da suka yi wannan wasa irin su: Uba maiwake da Hamza Kashi da Tokare da sauransu. (Hira da Shehu Maroɗo).

    Wasan ƙunshi wasa ne na Hausawa na gargajiya a ƙasar Gaya ya nuna al’ada ce daɗaɗɗiya “wasa ne da ake gudanar da shi domin nuna farin ciki musamman a cikin watan azumi.”(Hira da Ɗahiru Roka). “Wasa ne na gargajiya wanda ake haɗuwa samari da ‘yan mata da yara wajen nuna farin ciki da sanya nishaɗi.” (Hira da Rabi’u).

    Don haka,a taƙaice wasan ƙunshi wasa ne wadda ake gudanar da shi a tsakanin ‘yan mata da samari domin sanya nishaɗi tare da motsa jiki bisa tsarin gargajiya.

    Ranar Wasan Ƙunshi

    Babu wata rana da ake sanyawa domin a tsayar da lokaci ko wuri wajen aiwatar da wasan. Wannan ya samo tun asali tun farko farko samar da wasan, saboda haka kowa ya san watan da kuma ranar aiwatar da shi.

    Amma a wannan lokaci ko kuma a yanzu saboda tasirin zamani ana yin la’akari da ranakun da ba a yin aikin gwamnati, misalin Asabar ko Lahadi, domin ranaku ne da ba a zuwa makarantun boko, suna yin haka, saboda wasu daga cikin ‘yan matan da ake shirya wasan tare da su, suna a makarantun kwana.

    Hanyoyin Sanarwa da Sadarwa

    Kafin samun kafofin sadarwa na zamani da kuma hanyoyin isar da saƙo na karta kwana, babu wata hanya da ake amfani da ita wajen sanar da wasan sai ta hanyar gargajiya, ita ce wannan ya faɗawa wannan da dai sauran hanyoyin isar da saƙo na gargajiya.

    Amma a sakamakon juyawar zamani ana amfani da waɗancan kafafen yaɗa labarai da kuma wayoyin tafi da gidanka wajen faɗakar da al’umma, musamman samari da ‘yan mata.

    Masu Aiwatar da Wasan Ƙunshi

    Bisa al’ada yawancin wasannin gargajiya a ƙasar Hausawa, ya fi ta’alaƙa ga samari da ‘yan mata musamman wajen aiwatar da shi, domin su ne matasa manyan gobe. Haka abin yake a wasan ƙunshi, masu aiwatar da wannan wasa su ne samari da ‘yan mata sai kuma ƙananan yara waɗanda suke taimakawa wajen gudanar da shi, duk da kasancewar iyaye mata ba abar su a baya ba, domin suna bayar da gagarumar gudummawa tare da ruwa da tsaki wajen aiwatar da wasan.

    Lokacin Gudanar da Wasan Ƙunshi

    Wasan ƙunshi, wasa ne da ake gudanarwa shekara-shekara, ana gudanar da shi a cikin watan azumi (Ramadan). Watau ana fara wa daga ranar ashirin da shida (26) ga watan, zuwa ashirin da takwas (28) ga wannan wata, wato kwanaki uku (3) ake yi ana gudanar da shi

    Tanade-Tanaden Wasan

    Iyaye mata sukan tanadi wasu abubuwa waɗanda za su taimakawa ‘ya’yansu wajen alkinta kafin lokacin aiwatar da wasan, a wasu lokutan akan tanadi kayayyakin amfanin gona da aka samu daga roro ko kale ko ja-gindi ko tsinka da sauransu, wacce yarinyar ta samo domin adanawa sai lokacin ya zo, wadda da irin wannan ne ake sayarwa domin a yi mata sabon ɗinki da takalmi da a warwaro da sauran kayan ƙawa.

    Haka nan, Budurwa takan kai ziyar gidajen ‘yan uwa da abokan arzuƙa, da sauran dangi, bayan sun gaisa akan ba ta wasu abubuwa da suka haɗa da; sabulai da turare da kayayyakin abinci kamar hatsi da wake da gyaɗa da sauran nau’o’in kayan amfanin gona. Wasu kuma sukan bayar da kuɗi, dukkaninsu suna daga cikin tanade-tanaden gudanar da wasan ƙunshi.

    Sannan samari da ‘yammata sukan tanadi kuɗaɗe, idan ranar wasan ta kusanto sukan je kasuwa su sayo kayayyakin da suke da buƙata. ‘Yammata ne suke ɗaukar nauyin saye-sayen kayayyakin da ake da buƙata, domin samarinsu da iyayensu na samar masu da kuɗaɗen, domin su sami damar sayen kayayyakin da suke buƙata.

    Amma a yau abubuwa wasu sun sauya saboda sauyin zamani inda samarin da ‘yanmatan su ne suke tanadar waɗannan abubuwa da kansu da suka haɗa da; kayayyakin ciye-ciye wadda suka haɗar da; biredi da cincin da biskin da doya da kwai da arnaki da biri-biri. Sai kuma kayayyakin shaye-shaye, waɗanda suka haɗa da; kyayyakin tsotse-tsotse, misalin; alawar madara, da sauran alawoyi, iri daban-daban.

    Ana amfani da kayayyakin shaye-shaye na zamani, irin su lemukan roba da bobo da yagot da lemon kwalaba kamar fanta da kokakola da diyu da kuma lemukan gwangwani kamar maltina da fefsi da lakasera da mirinda da sifirayit, da lemukan kwali, misalin fayif alayif da kuma ruwa iri daban-daban.

    Daga cikin samari da ‘yan mata masu aiwatar da wannan wasa akan samu wasu daga cikinsu sukan ɗinka sababbin tufafi domin yin amfani da su, a lokacin wasan. Amma yin ɗunkuna ba wajibi ba ne. Saboda haka, ana samun wasu daga cikin samari da ‘yan mata waɗanda ba su yi sabon ɗinki ba a lokacin wasan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga maƙala mai taken Nazarin Wasan Ƙunshi Jiya Da Yau A Ƙasar Gaya wadda Magaji Ahmad Gaya Ph.D Sashen koyar da Hausa Jami’ar Northwest, Kano ya wallafa.

    Emai: magaya@nwu.edu.ng 08066009039

    Karanta Waiwaye A Kan Al’adun Gargajiya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Bakwai

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Bakwai

    Kamar yanda Khadeeja ta faɗa ba ta sake kula hidimar yaran a ranar da ba ita ce da kwana ba, sai dai ranar kwanata tana fitowa ta sallami kowa sanna ta cigaba da harkarta. Idan kuma dare ya yi ta shiga ɗakinta ta yi kwanciyarta don ta tabbatarwa Mustapha cewa ta ba shi kwanan.

    Ranar Asabar ce don haka yara babu makaranta duk suna gida, kamar yanda suka saba tunda Khadeeja ta ƙi hidimar yaran to duk ranar girkin Naja Anti Wiyya ce take abinci har yaran. Ita kuma Najan ita ce za ta tsaya a kansu su yi wanka su shirya, sai dai ranar da ba ta tashi ba dole haka Mustaphan yake tashi ya yi ta faman yi musu faɗa har ya samu su gama shiryawa a hankali.

    Afaf ce ita kaɗai a parlor ɗin Naja tana kallo saboda TV ɗin parlor ɗinsu Startimes ce ita kuma ta fi son DSTV wadda take parlor ɗin Naja; yayin da Anti Wiyya take ta kai wa da kawowa tana ƙoƙarin dora a bincin rana. Ta wuce Afaf a parlor ta shige ɗakin Naja inda ta same ta a kwance a gefen gado; bayan ta amsa sallamarta ta ƙarasa ta zauna a gefen kafarta kamar a fusace.

    Tace ‘Sannu Anti, kina ta hidima. Lallaɓa ta nake yi idan ta ƙoshi goya ta zan yi na fito na taya ki. Salaman ma ina jin yau ba za ta zo ba; ko wa take so ya yi mana wanke-wanke da sharar oho ga girki. Ta yi tsaki ta kawar da kai tace ‘Kin ganni a cike nake da haushinta, ga shi kamar ta shirya wulaƙanci tunda yau wanke-wanken ya fi na kullum yawa sannan ta ƙi zuwa.’

    ‘Hmm! Ai sai haƙuri masu aikin zuwa da dawowa ba su da kirki, ni ma da na gama jegon nan me kwanan zan ɗauka. Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan Anti Wiyya tace ‘Ita kuma wannan ‘yar taki wallahi ita ma ba ta da mutunci; yaushe za a ce budurwa kamarta ba za ta yi aiki ba komai ƙanƙantarsa?

    Sai dai ta dinga bin mutane da kallo suna mata aiki sai kace ubanta sayenmu ya yi. Gaskiya ku sake zama a gidan nan, haba! Idan banda ma rashin mutunci ya za a ce mace tana jego kuma a barta da kula da gida da yara bayan tana da kishiya? Ai kamata ya yi ta karɓar miki aikin. Ko da yake wannan ‘yar mulkin kishiyar taki na kula daga ke har maigidan tsoronta kuke yi.’

    Ta tashi zaune ta kwantar da Rukayya wadda ta riga ta yi bacci, ta kama haɓa ta dubi Antin tata tace ‘A a shi dai yake tsoron matarsa, duk abinda ta ga dama tace ba za ta yi ba haka zai yi ta kame-kame saboda ita ba a iya yi mata dole. Ta kalle ta sheƙeƙe tana cewa ‘Kece karkatacciyar kukarsa mai daɗin hawa ko? Shi yasa kina jego amma aka lafta miki aiki?

    Ita ko kunya ba ta ji? Sai ta sauko ta ishi mutane da gaishe-gaishe kamar wata musulmar ƙwarai. Cikin damuwa tace ‘Haka take fa, da an haɗu ta yi ta haba-haba da mutum amma mugun halinta yana nan fal cikinta sai mu da muke zaune da ita muka san halinta. Anti Wiyya ta ɗan yi ƙasa da muryarta tace ‘To gaskiya dai dole a yi aiki a kan wannan matar, yanda ta kama maigidan nan tana juya shi ai ba fin mu iyawa ta yi ba.

    Kema idan kika zo yawon arba’in da kaina zan kai ki inda za a taimaka miki a ƙwato miki daraja. Wannan kwarjinin da take da shi take yi wa kowa har maigidan ke ma a samo miki shi. Taimako ne da ayar Allah ina da malamina a hannu kuɗi kawai za ki bayar. Har yaran ma don ubansu ko su bi ki su zauna lafiya ko kuma su koma ‘yan kallo.’

    Tana ta jijjiga kai saboda gamsuwa tana cewa ‘Babu komai Anti, in sha Allahu za mu je. Don ni ma wallahi zaman haka ya ishe ni. Kuma dama Yaya ma tace za mu je ban san me ya ɗauki hankalinta ba. Nan suka zauna suka gama ƙulla yanda za a yi sannan suka fito suka kama hidimar gidan.

    Haka suka cigaba da yi har Naja ta yi arba’in; duk wata kalma da Mustapha zai yi amfani da ita ya sa Khadeeja ta karɓi hidimar nan ba ta yi amfani ba har ya gaji ya sakawa sarautar Allah ido. Sai da Naja ta yi arba’in sanna suka cigaba da rabon kwana. Idan Khadeeja ce da kwana sai Mustaphan ya je ɗakinta yayin da ita kuma Naja take zuwa ɗkinsa.

    Kwanci tashi har ya zama ta mayar da saman nasa kamar nata, ya zama kullum tana ciki ko parlor ɗinsa ko ɗakinsa. Ba ta daɗe da yin arba’in ɗin ba kuma Khadeeja ta gama bautar ƙasa; sai dai duk yanda ita da Baffanta suke ƙoƙarin samar mata aiki bai samu ba. Inda ta yi bautar ƙasar ma ta so su riƙe ta amma suka nuna mata ba sa buƙatar ma’aikata.

    Ba ta son zaman gidanta, domin ta san in dai ya zama Naja za ta tafi aiki ta barta a gidan da yara to dole Mustapha zai yi duk yanda zai yi ya tursasa ta ta dinga kula da yara. Ya zama shi da matarsa suna yawon neman kuɗi ita tana musu hidimar gida da ta yara. Don haka ta sanar da manager za ta dinga zuwa Litinin zuwa Juma’a tana yi musu aiki kyauta.

    Da ya ji haka sai ya sa aka ɗora ta a kan tsarin internship da suke da shi; inda duk wata za a dinga ba ta naira dubu goma sha biyar har zuwa lokacin da za a sami wani gurbi a gidan rediyon kawai sai a ɗauke ta. Sosai hakan ya yi mata daɗi, kuma ba tare da wata fargaba ba ta sanarwa Mustapha sun riƙe ta aiki, ta cigaba da zuwa.

    Kusan wata takwas kenan da haihuwar da Naja ta yi; kuma kamar yanda suka tsara an kai ta wajen malami. Bayan malamin ya ji bayaninsu ya ba ta wani abu mai kama da gishiri yace ta yi sati tana zuba musu a abnci duk gidan kowa ya ci har Khadeeja. Haka ta dage ta yi amfani da abun nan sai dai ba ta da tabbcin Khadeeja ta ci abun marmarin da take girkawa tana aika mata, shi ma Habib ba ta da tabbacin cinsa domin ya fi cin abinci a wajen Khadeeja.

    A hankali ta fara ganin sauyi, kamar dai duk yaran da Mustaphan suna saurararta; tunda wasu lokutan idan ta sa Afaf aiki haka za ta tashi ta yi ko ba ta so kuma Mustaphan ya daina hanata.

    Sun gama magana da ita a kan zai siya mata mota, amma ga shi lokaci yana ta ƙurewa yanzu ya ma ce mata shi ba alkawari ya yi mata ba; shi kawai ce mata ya yi zai yi tunani. Cikin damuwa suke waya ta sanar da Anti Wiyya halin da ake ciki; tace ‘Wallahi Anti nema yake ya canza maganar.

    Kuma dama na gaya miki aikin malamin nan ba kullum yake ci ba, tunda ko Mustaphan ya fara saurarar maganata da an kwana biyu sai ya sake komawa kamar da. Gani ma nake kamar duk lokacin da matarsa ta karɓi kwana sai ta warware min aiki, shi yasa nake ta fama da shi. Daga ɗaya ɓangaren Anti Wiyya tace ‘Au haka ne? To bar ni da su, ai ba mu za a yi wa bariki ba.

    Akwai wani malamin aikinsa yana da zafi sosai, in kin sami lokaci kiyi min waya sai mu je wajensa. Ke kanki sai kin yi mamakin aikinsa. Suka ƙarasa hirarrakinsu suka yi sallama. Ta jefa wayarta a kan gadonta cike da ƙwarin gwiwa; ta san Mustapha yana ƙoƙari wajen kyautata mata amma ita gani take kamar tsoron khadeeja yake yi. Kuma ma ita so take ya zama gaba ɗaya gidan sai abinda ta faɗa za a yi.

    Tana ganin yanda maza suke yi wa matansu kyauta ta burgewa, ita ma haka take so ya dinga yi mata, duk abinda ta nema ya ba ta kawai tunda ta san yana da kuɗin. Idan ma ta sami yanda take so to ko ganin Mustapha yaran ba su isa su yi ba sai da izininta, domin ta kula da yanda yake saurararsu yana bin ra’ayinsu kamar su suka haife shi.

    Sai an yi magana yace su marayu ne. Tabbas dole gidan nan gaba ɗaya ya dawo tafin ƙafarta don ta gaji da wannan mulkin da ake mata ana kasa mata hankalin miji tsakanin uwargidansa da yaransa.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Shida

    Edita@rumasau-kallamu

  • Samuwar Rubutun Ajami

    Samuwar Rubutun Ajami

    Bincike ya nuna cewa an fi samun rubuce-rubucen Ajami na zube a cikin hanyar rubutu Magaribi, wato ba a faye samun rubutun Ajami da yawa a cikin rubutu na sharƙiyya ba. Haka kuma bincike ya nuna cewa, an fi shekaru ɗari biyu (200) ana amfani da Ajami a ƙasar Hausa kafin shigowar rubutun boko wanda sai kuma ya faru ne a dalilin zuwan Turawa ƙasar Hausa.

    Dalilin cewa rubutun Ajami ya shekara 200 kafin na boko shi ne idan mutum ya yi la’akari da irin rubuce-rubucen da aka samu tun wajen ƙarni na 17 irin rubuce-rubucen Malam Abdullahi suka Kano da Wali Ɗanmasani a cikin Birnin Katsina da Malam Muhammadu na Birnin Gwari da dai sauransu.

    Amma dangane da ilimin Arabiya da samuwar Musulunci wannan tun wajen ƙarni na 9 ne, domin akwai alaƙa tsakanin ƙasashen Hausa da na Larabawa tun a wannan ƙarni inda a Jami’ar Al-azhar akwai wani sashen da ake kira Ruwaq- Al-Barno, inda mutanen Borno suke zama a cikin Jami’ar. Yahaya (1988)

    Har kwanan gobe Malaman zaure na ƙasar Hausa idan za su yi rubutu na zube a cikin rubutun Ajami suke ƙaddamar da shi. Haka kuma akwai jaridu da akan buga a cikin ajami kamar su Albishir da Alfijir. Haka kuma ba wai kawai a Hausa ba hatta a ƙasashen Afirka ta Gabas kamar su Tanzaniya da Uganda da Afirka ta kudu suna rubuta harshen Ki-swahili da Ajami.

    Amma a ƙasar Hausa Ajami bai sami cikakken gata ba sai a 1985 a Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo da ke Sakkwato ƙarƙashin shugabancin Shugaban Jami’ar na wannan lokaci, wato Farfesa Mahdi Adamu Ngaski inda ya sa aka kira taro na ƙasa domin kyautata rubutun Ajami inda aka kira manyan malamai daga ko ina a ƙasar Hausa, taro ya fara zama ranar 28 ga watan Janairu na 1985 inda aka yi kwana uku sai kuma a cikin 19 ga watan Agusta inda aka sake kiran taron aka yi kwana uku aka tattauna akan abubuwa kamar haka:

    a)A samar wa Ajami tsayayyiyar ƙa’idar rubutu
    b)A kyautata rubutun Ajami domin a sauƙaƙa wa mai karatu yadda zai ji daɗin karanta shi.

    Ka san an ce “Ajami gagara mai shi”, da aka kirawo taro, daga ƙarshe an samar da nagartacciyar hanyar rubuta Ajami, karɓaɓɓiya wadda wata hukuma ce ta gwamnati ta yi wannan hoɓɓasa . Kafin wannan lokaci masana sun kasafta hanyar rubuta Ajami zuwa gida uku:-

    1700-1950

    1950-1985

    1985/88 zuwa yau

    Daga 1700 inda aka sami rubuce-rubuce irin na su Wali Ɗanmasani babu wata ƙa’idar rubuta Ajami kowa yana rubutawa yadda yake so, sai a 1950 inda Alhaji Halliru Binji da Alhaji Na’ibi Sulaiman Wali suka rubuta wani littafi mai suna Mu Koyi Ajami Da Larabci (1950). Shi kuwa wannan yunƙuri ba na gwamnati ba ne, illa dai mutane kawai wanda ya karanta shi ke nan.

    To sai a 1985 inda Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo aka kira masana suka gabatar da shawarwari a kan ƙa’idar rubutun Ajami to amma rahoton binciken da masanan suka yi bai fito ba sai a 1988, wato bayan shekara uku, mai suna “Report On Hausa Ajami Writing” (1988). Shi wannan littafi a kan Ajami ya ƙunshi babi (13) amma babu 2-10 su ne suka ƙunshi zallar yadda ƙa’idar rubuta Ajami take.

    Idan aka ce rubutun zube ana nufin rubutun da ba waƙa ba, ba kuma wasan kwaikwayo ba. Zube ana nufin tsagwaron rubutu kai tsaye wanda aka yi shi cikin shafi ko shafuka da sakin layi daban-daban, a rubuce ko a maganance, wato ta hanyar magana.

    Rubutun zube na Hausa ya samo asali ne ta hanyoyi guda biyu. Hanya ta farko ita ce ta hanyar addini wato rubutun zube ta hanyar Ajami wato hanyar rubuta Hausa cikin haruffa na Larabci. Wannan hanya Hausawa ne suka ƙirƙiro abarsu tun asali ta hanyar rubuta sunaye na gargajiya a jikin fahami kamar misali; Malam Ɗantsoho, Malam Ɗantsamiya, da kuma ire-iren sunayen da akan haɗa laƙunƙuna da su kamar gaɓar kara, ɓawon yawa, da dai sauransu to ta irin wannan hanya kuma manya-manyan malamai da manyan sarakuna sukan rubuta wasiƙu a tsakaninsu. Mukhtar (2004)

    Samuwar Rubutun Boko

    Kafin a fara rubutu da Hausar boko a ƙasar Hausa, sai da aka daɗe ana amfani da ita a ƙasashen Turai. Amma mutumin da ake jin ya fara amfani da ita shi ne wani Baturen ƙasar Jamus mai suna James Frederick Schon wanda ya zo ƙasar Saliyo aikin Mishan a 1840. Schon shi ya yi tunani ya kuma ƙirƙiro cewa ya kamata ya yi amfani da haruffan Latiniyya ya rubuta lafazin Hausa:-

    “na riya waɗannan ƙa’idojin rubutu a raina ne, bayan na yi shakaru inda lura da abubuwa. Saboda haka na yi amanna da dacewarsu.” (Schon, 1862:X).

    Bayan da Schon ya yi niyyar amfani da haruffan Latiniyya ya rubuta Hausa, sai wani Bature mai suna Lepsius, ya ba shi shawarwari a kan yadda zai kyautata rubutun. Sauran Turawa waɗanda suka biyo irin wannan hanyar rubutu ta J.F. Schon sun haɗa har da Prietzer (1904), sai Mischlich a (1906) sannan Westermann a shekara ta (1911) da sauran waɗanda suka biyo baya.

    Wata hanyar rubutun zube cikin boko da aka fito da ita, ita ce wadda Robinson (1896) ya fito da ita, ko da yake Robinson shi ma Latinanci ya yi amfani da shi, sai dai shi ya ɗauki tsarin Ajami ne wajen sarrafu baƙaƙen da babu su a wasu harsuna. Misali v da q da x da sauransu a hanyar rubutu ta Robinson waɗannan haruffan ɗigo ake musu a ƙasa irin na Ajami maimakon lanƙwasa. Wato sai a rubuta su kamar haka:- b k d ba tare da lanƙwasa ba.

    A lokaci na farko da hukuma ta tsoma baki a kan rubutun zube shi ne lokacin mulkin mallaka a nan Nijeriya inda Hanns Vischer wanda ake kira Ɗan Hausa ya tsara ƙa’idojin yadda za a yi amfani da Hausar boko a (1910) sai dai shi ma ya yi amfani ne da Hanyar Robinson inda yake sa ɗigo a ƙarƙashin harafi mai alhamza.

    Wata hanyar rubutun zube kuma ita ce wadda Bargery (1934) ya yi amfani da ita; shi kuma waƙafi ya dinga sa wa hamzatattun haruffa maimakon ɗigo. Kamar haka:-

    ‘b k’ ‘d da kuma dai sauransu.

    Hukumar Fassara ta Jihar Arewa ita ce ta fara ba da shawara a (1938) cewa ya kamata duk hamzatattun baƙaƙe a dinga lanƙwasa su maimakon ɗigo ko waƙafi.

    Litattafan Ƙagaggun labarai da marubuta ke rubutawa sun kasu gida hudu:

    1.) Akwai masu gajeren zango wato (fiction) wadanda ba sa wuce shafuka arba’in (40) zuwa shafi 200 da kuma,

    2.) Masu dogon zango, wato (novels) masu shafuka 200 zuwa sama.

    3.) Akwai Litattafan Kagaggun labarai da aka yi su, domin Hausawa a cikin akwai garuruwan Hausawa da tattalin arziki irin na Hausawa tunani irin na Hausawa. Sai kuma

    4.) Litattafan Kagaggun labarai da aka rubuta su da Hausa, kawai domin a gabatar da saƙon da Hausa a matsayin harshen sadarwa amma labaran ba domin Hausawa aka gina su ba.

    Irin waɗannnan ba na gyaran hali ba ne, shi ya sa akan samu batsa a ciki, sannan Hausar ba ta inganta ba. Don haka waɗanda aka gina labaran don Hausawa akwai ilmantarwa, nishaɗantarwa da gyaran halin al’umma. Saboda haka Wannan tana da muhimmanci domin tunatar da malamai, iyaye da marubuta wajen fahimtar yadda ƙagaggun labarai ke tasiri wajen gina tarbiyyar matasa. Haka kuma za ta ƙarfafa wa matasa gwiwa domin su karanta littattafai masu ɗauke da darussa da koyarwar tarbiyya a cikinsu.

    Masana da dama sun tattauna a kan irin rawar da adabi yake takawa wajen gyaran halin Bil adama. Misali, Abubakar Imam cikin littafinsa Magana Jari Ce ya yi amfani da ƙananan labarai wajen koyar da gaskiya, haƙuri da adalci. Haka kuma Hafsat Abdulwaheed cikin So Aljannar Duniya ta nuna illolin soyayya marar tushe da muhimmancin kyawawan halaye a tsakanin matasa.

    Waɗannan misalan sun nuna cewa ƙagaggun labarai ba wai nishaɗi kawai suke sa wa ba, har ma suna zama kayan gyaran hali da watsar da munanan ɗabi’u da ba nagari ba a cikin al’umma. Saboda haka dai a wannan takarda an yi amfani da hanyar binciken ɗakin karatu (Library Research Method), inda aka tattara bayanai daga littattafan Hausa, mujallu da wallafe-wallafen ca suka shafi adabin Hausa da yake magana a kan tarbiyya.

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga muƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

    Danna nan don karanta Amfanin Ilimin Kwamfuta

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waiwaye A Kan Al’adun Gargajiya

    Waiwaye A Kan Al’adun Gargajiya

    Masana irin su Ibrahim (1982) da Bunza (2006) sun gabatar da bayanai dangane da asali da ma’anar kalmar al’ada. Don haka a taƙaice kalmar al’ada tana nufin dukkanin rayuwar ɗan Adam tun daga haihuwarsa har zuwa kabarinsa.

    Dangane da wannan fasali da ake magana a kai, al’adun gargajiya na nufin tsarin rayuwar Hausawa wadda ta shafi abinci da sutura da muhalli da zamantakewa da shugabanci da bukukuwa da wasanni da makamantansu.

    Ma’anar Wasa

    Sa’id, B. (2006) sun bayyana ma’anar wasa da cewa, “abu ne da akan yi don raha ko nishaɗi, ko motsa jiki.” A wata ma’anar kuwa Ɗangambo (2008) ya bayyana kalmar wasa da cewa, “shi ne motsa jiki don samun walwala.” Duba ga waɗannan bayanai da ma’anoni da suka gabata, za a iya cewa wasa shi ne sanya walwala da nishaɗi tare da nuna farin ciki, wanda a wasu lokutan har da motsa jiki.

    Wasannin Gargajiya A Ƙasar Gaya

    Al’umma kan tafiyar da rayuwarsu, da al’adunsu cikin gwagwarmaya don cimma wasu buƙatu na rayuwa. Wannan yakan jawo wa al’ummar ingantaccen tarihi mai cikakken asali da abubuwan alfahari. Haka kuma al’adun kan samar da annashuwa ba ya ga ilimantarwa.

    A ƙasar Gaya akwai wasannin gargajiya waɗanda al’ummar suke gudanar da su, wasu daga cikin wasannin sun haɗa da: wasan Mage da wasan Ƙunshi da wasan Jemau da wasan Taushen fage da wasan Dagajirau (saran-kai) da sauran wasanni waɗanda sun sha bamban da al’ummar ƙasar Hausa.

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga maƙala mai taken Nazarin Wasan Ƙunshi Jiya Da Yau A Ƙasar Gaya wadda Magaji Ahmad Gaya Ph.D Sashen koyar da Hausa Jami’ar Northwest, Kano ya wallafa.

    Emai: magaya@nwu.edu.ng

    08066009039

    Danna nan don karanta Nason Al’adun Baƙi Maƙwabta Na Kusa A Wanzancin Hausawa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Wasu Kayan Da Hausawa Ke amfani Da Su Ga Doki Suke

    Yadda Wasu Kayan Da Hausawa Ke amfani Da Su Ga Doki Suke

    1. Bante
    2. Bawaji (majanyi)
    3. Bulala (kurhu)
    4. Dabaibayi.
    5. Ɗangaba

    6. Ɗangamba
    7. Ɗangoshi
    8. Ɗan wuya
    9. Ɗan kai
    10. Caraskiya

    11. Gindi/Tarnaƙi
    12. Ilgami
    13. Ja-kuturi.
    14. Jikka
    15. Jalala

    16. Kwacciyar sirdi
    17. Kwarno
    18. Kubuttai
    19. Ƙaimi
    20. Kalmazuru

    21. Likkafa (karama)
    22. Likkafa (Wangami)
    23. Linzami
    24. Mashinfiɗi
    25. Maɗauri (sarka/igiya)

    26. Ragama
    27. Talala
    28. Turke
    29. Turmi/Baho/Diram.
    30. Tumbas

    31. Kitso
    32. Zabba
    33. Zabukka
    34. Sirdi (Hausa/Turawa/Azbin)
    Da sauran su.

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Wasu Kayan Aikin Rini

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Shida

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Shida

    Tun wajen 12pm ta nemi izini a wajen aikin nata ta fice, kai tsaye gidansu ta nufa. Ta ci sa’a ta sami Mommy da Yaya Mama suna zaune a parlor suna hirarrakinsu. Bayan sun gaisa Khadeeja ta dubi Yaya Mama tace ‘A nan kika kwana Yaya. Ta yi dariya tace ‘Ga jakata a kusa da ni kina kallo amma kike min wannan tambayar, to ni yanzu ma zan tashi saboda 2pm zan ɗauko yara a makaranta sannan mu wuce gidan.’

    Ita ma ta yi dariyar, ta umurci Hafsa da ta shiga ɗakin Nabila ko ta je kitchen wajen masu aikin gidan ta zauna. Tun kafin tace wani abu Mommy ta dube ta tace ‘Lafiya dai na ganki kamar a fusace, sarkin rigima. Ta zumɓura baki ta sunkyar da kai tana kallon hannunta kamar me ƙunƙuni, sai da ta gama zumɓura bakin sannan cike da takaici tana ƙoƙarin danne hawayen da ya taso mata tace ‘Mommy ni Mustapha zai mayar ‘yar aiki, kuma Baffa ya goya masa baya.’

    Mommy ta gyara zama ta fuskance ta sosai tana kallon fuskarta da mamaki sannan tace ‘Ban gane ba, kuma me kawo Baffanki a cikin mayar da ke ‘yar aiki? Shi Mustaphan me ya yi miki? Tana buɗe baki za ta yi magana hawaye ya ƙwace mata, ta sa bayan hannunta ta goge sannan ta labartawa Mommy abinda ya faru.

    Zuwa lokacin hawayenta ya gama ƙwacewa yana zuba kamar ana zubar da ruwan famfo, Mommy ce ma take ƙoƙarin goge mata. Tace ‘Mommy yanzu shikenan haka zan yi wata tara ina mata hidimar gida tana kwana da miji, bayan ni haka na yi nawa laulayin ko tausayina ba ya ji. Ko haihuwar Hammad fa ana gama suna dole na miƙe na koma hidimar gidan saboda ban ma ga fuskar cewa ba zan iya ba.

    Amma yanzu saboda ya auro ‘yar gwal shi ne zan karɓar mata aiki ita kuma ta yi laulayi. Yaya Mama tace ‘Ni fa gaba ɗaya ban gane ba. To ke me yasa ba kya zuwa ɗakin kike barinta ta je, ai da sai ki je ki yi kwanciyarki a can ki ga ta inda marasa kunya za su kwana tare.’

    Kafin ta yi magana Mommy tace ‘Gaskiya ni ma dai ban gane dabarar yin hakan ba, ai ɗakin ya kamata ki gyara ki tare har sai kin gama kwananki. Ta sa bayan hannunta ta goge hawayenta sannan tace ‘Mommy ba zan iya ba, ya kwana da wata matar a kan gadon sannan ni ma ya kwana da ni a kan wannan gadon.

    Wataƙila ma da ya yi aurensa ba tare da ya ci min mutunci ba abubuwa da dama za su zo min da sauƙi, amma gaskiya ba zan iya ba. Tunda ko bayan ta tare ranar da zan karɓi girki bayan da ta gama kwana takwas ɗinta na shirya tsaf zan shiga ɗakin, amma har magriba ba ta fito daga ciki ba. Lokacin shi kuma ya riga ya fita.

    Don haka na ƙyale ta na shirya masa abincin dare tunda na gama kintsawa. Amma yana dawowa ko kallon abincin bai yi ba ya same ni wai tunda ina jego na ba shi kwanakin ya kai wa amaryarsa in ya so idan na yi arba’in sai a fara rabon kwanan. Kin ga kenan ita ta riga ta san ba zai ba ni kwanan ba shi yasa ta ƙi fita ma daga ɗakinsa.

    Daga wannan lokacin ɗakin da me ɗakin suka ƙarasa fice min daga rai gaskiya. Idan yana buƙata ta ya same ni a ɗakina, kuma yana zuwa ɗin. ’Mommy wadda take binta da kallo tana jijjiga kai tace ‘Lallai Mustapha, ni na rasa ma me zan ce. Ni fa mamakin da nake Baffanki ko gaya min bai yi zai je ba balle da ya dawo ya gaya min, wataƙila jiya bayan ya fita da magriba Mustaphan ya yi sa’a ya same shi a gate suka gama magana.’

    Yaya Mama tace ‘Hmm! Ai komai daɗinki da miji idan dai wata macen ta gifta to sai abinda kika gani. Watan haƙurinki ne ya kama har ya gama yayinta. Mommy tace ‘To yanzu ya za a yi? Kin ga Baffanki ya riga ya sa baki a maganar ba tare da kin gaya masa ainahin abinda yake faruwa ba.

    ‘To Mommy ya za ayi na yi masa duk wannan bayanin ya gane, ai ban ga alamar zai ma gane ba tunda ko a lokacin ma yace amfanin mata biyu kenan ɗaya ta taimakawa ɗaya. Kuma ya za a yi na zauna ina gaya masa Mustapha yana satar min kwana saboda na ƙi zuwa ɗakinsa? Umm, haka ne kuma. To Allah ya kyauta.

    Yanzu kam sai dai ki yi haƙuri a ga abinda hali zai yi tunda dai babu wanda zai je ya kwance maganar Baffanki. Ina ga kula da yaran wanda kika yi a baya bai kashe ki ba ba na jin na wata tara nan gaba zai dame ki. Haka suka zauna suka yi ta ba ta hakuri; sai daga ƙarshe Yaya Mama tace ‘Kuma ke ma idan kin gaji kawai ki yi pretending ki kwanta masa, wallahi da kaina zan zo na taho da ke na kawowa Mommy ta yi jinyarki idan kin huta kya koma.’

    Mommy ta kai mata duka tana cewa ‘Allah ya shirye ki yayar kwabo. Suna nan zaune wajen 1:30pm Baffa ya shigo gidan da sallama, bayan ya amsa gaisuwarsu da sannu da zuwa ya dubi Mommy tana zaune a tsakiyar su Khadeeja yace ‘Gulmar wa kuke yi suka saka ki a tsakiya haka. Ita ma dariyar ta yi tace ‘Ba dai gulmarka muke yi ba.’

    Yaya Mama ta yi musu sallama ta fice yayin da Khadeeja ta miƙe ta nufi ɗakin Mommy ba tare da tace komai ba. Baffa ya bi bayanta da kallo sannan ya yi dariya ya dubi Mommy yace ‘Wannan iya rigimar ƙarata ta kawo ko? Ta harare shi tace ‘Ashe ka san ka yi mata laifi? Ya yi dariya yace ‘Rabu da ita da-Allah, ya za a yi a ce mutum yana da mata biyu a ce ɗaya ba za ta karɓi ɗaya aiki ba idan ba ta da lafiya? Ai ita ma ba ta so a zauna lafiya ba.’

    Nan ta ƙara yi masa bayanin yanda zaman nasu yake, sai dai ta kasa gaya masa cewa Mustaphan yana ba wa Naja kwanan Khadeeja saboda Khadeejan ba ta yarda ta je ɗakinsa. Yanda ta san shi ta san tabbas ba zai ɗauki wanna ba, tunda shi ma tashi uwar har ta koma ga Allah turaka take zuwa ranar kwananta.

    Haka dole Khadeeja ta haƙura ta cigaba da hidimar gida da ta yara. Shi ma Mustapha da ya gama zagaye-zagayen haka ya same ta a ɗakinta yana nuna mata jin daɗinsa ganin yanda take kula da yaran sai dai baya jin daɗin yanda idan ta jera abinci take komawa ɗaki ta bar su shi da ‘yayansa.

    Duk yanda ya so ta ba shi haɗin kai su tattauna maganar ta ƙi, da ya dame ta da zance ma sai tace ‘Don Allah ka bari! Kai dai ba so kake na cigaba da hidimar gidanka da yaranka ba amaryarka tana hutawa? To ai ina yi ko? Ina ga duk a inda na zauna na ci abinci ma wannan bai kamata ya zama damuwa ba tunda dai ku kun ci naku.’

    Kafin ya ba ta amsa ta fice ta bar masa ɗakin. Dole ya haƙura ya zuba mata ido tunda dai tana yin abinda yake so kuma duk ranar da ya kai mata kwananta ba ta hana shi buƙatarsa.

    Da fari lokacin da Mustapha ya ƙara aure Khadeeja ta ga ‘yan uwansa ba sa wani damunta ta yi zaton tunda an mata kishiya sun fita harkarta. Sai dai tunda suka ji labarin Naja tana da ciki sai suka kama zarya gidan; babu yanda za a yi Yaya Jidda ta yi sati ba ta zo gidan ba. Haka za ta taho da girki a flask wai Hajia ce tace a kawo wa Naja saboda kwaɗayin mai ciki.

    Ga shi idan ta zo a wajen Najan za ta sauka, sai dai idan Khadeejan tana nan ta shiga su gaisa sai ta koma wajen Najan. Sai kuma ta yi ta aiko yara; a ba ta abinci. Idan ta cinye kuma tace a ba ta wani ɗan abun taɓawa. Ranar da ba ta zo ba kuma sai a turo yaranta da abincin; haka za su zo ta wuni surutu da hidima da su ba ta taɓa jin wani yace Hajia tana gaisheta ba.

    Kuma shi ma Mustaphan yana kallo ana yi amma bai taɓa cewa komai ba; sai dai yawan godiya da za ta ji shi yana yi wa mutan gidan nasu. Haka ta kawar da kai ta cigaba da duk wannan hidimar tana ganin rawar kai kala-kala. Haka ta cigaba da dagewa har Allah ya sauki Naja lafiya, aka sami yarinya mace wadda tun ranar da aka haihu Mustapha ya yi mata huɗuba da suna Rukayya.

    Ba su tsara za ta tafi gida ba don haka sai aka kawo ƙanwar mahaifiyarta Alawiyya wadda suke kira da Anti Wiyya ta zo yi mata zaman daɓaro. Tun Khadeeja tana saka ran za ta ji Mustapha yace zai haɗe mata kwanan saboda Naja tana jego har dai ta fitar da rai. Ranar da aka kwana takwas da haihuwa ranar ta kama kwanan khadeeja ne sai dai a daren ranar za ta fita daga girki.

    Da yake a ɗakinta suka kwana a nan yake shirin fita office; musamman tunda banɗakin ɗakinsa ya kwana biyu rabon da a wanke saboda Naja ba za ta iya wanke wa ba kuma Khadeeja ta ƙi ma shiga ɗakin; ga shi kuma yana ƙyashin ya saka Afaf ta wanke tunda ba ya son damuwarta. Yana zaune a gaban mudubinta yana shafa mai ta fito daga wanka, ta ɗauki kayan shafawarta ta koma gefen gado, suna yi suna taɓa hira.

    Jimawa kaɗan tace ‘Yauwa, tazarce za mu yi ko? Sai na haɗe kwanakin tunda Naja tana jego har zuwa ta yi arba’in ko? Ya ɗan yi dum, alamar maganar ta shammace shi; tun ranar da Naja ta haihu ta gaya masa ba za ta bayar da kwananta ba saboda ko ba za ta iya biya masa buƙatarsa ba tana so ya kwana da su ita da Baby, in ya so kwana biyu sai su haƙura.

    Ya riga ya amsa mata hakan domin shi ma hakan ya yi masa; duk da dai shi ba mutum ne mai son jarirai ba domin ko ɗaukan yaro ba ya son yi har sai yaro ya iya zama sosai. To amma dai tunda ta nuna tana so shi ma sai ya ji hakan ya yi masa ko hira ce sa yi, musamman da yake bai taɓa tsammanin Khadeeja za ta nemi wani ƙarin kwana ba duk da ita ta ba da nata kwanan an ba wa Najan.

    ‘Um, no ina ga ba haka za a yi ba. Na riga na yi magana da ita amma ba ta ba da kwanan nata ba, tunda kin ga ke ma tambayarki na yi kika bayar ba tare da na yi miki dole ba. To ita ba ta bayar ba, don haka sai a cigaba da kwana bibbiyun kawai.’ Ya faɗa cikin in-ina yana satar kallon Khadeejan ta cikin mudubi.

    Sai da ta yi da gaske sannan ta haɗiya malolon da ya tokare mata maƙogoro; duk da dama hakan ta sa rai zai faɗa amma sai da abun ya yi mata ciwo. Ita ba ta ma yarda Naja ce ba za ta ba da kwananta ba, ta fi yarda shi ne dai ba zai iya ba ta kwana arba’in ba ba tare da ya ji ɗumin rabin ransa ba.

    Ta daure ta yi murmushin yaƙe sannan tace ‘Allah sarki haka ne kam, to babu damuwa Allah ya raya mana Rukayya ita kuma mai jego Allah ya ƙara mata lafiya. Shikenan ai tunda ta haihu lafiya idan ta karɓi kwana yau to ta haɗa da sauran hidimar gida da yara da nake yi ni ma na samu na huta.

    Ya yi shiru da bakinsa a buɗe yana kallon Khadeejan ta cikin mudubi; to a gaban Antin tata zai sakar mata aikin gida da na yara bayan ga ɗanyen jego sannan kuma ga Khadeejan tana kallo? Kuma a ce ita ce za ta tashi ta shirya masa yara, duk da dai kusan sun iya shirya kansu amma dai idan ba a tsaya a kansu ba haka za su yi ta shiririta har su makara.

    Ga shi Afaf ta shiga SS 3 yanzu tun 7:15 am ake tare su makara. Ya san idan dai ba a tsaya a kansu ba to kullum sai dai ya dawo da Afaf. Ya rasa ma me zai ce mata, domin ya san kusan ko me yace tana da amsar ba shi kuma ya tabbatar fitinar da ba ta yi ba ce a lokacin da Baffanta yace ta dinga taya Naja aiki take shirin biyan bashinta yanzu. Ta miƙe ta kwashi mayukanta da ta gama shafawa ta ƙarasa gaban mudubin ta ajiye.

    Ta ɗan tsaya daga gefensa tana kallonshi fuskarta cike da walwala kamar ba yanzu ta haɗiye ɓacin rai ba, tace ‘Kuma ni na yafe nawa kwanan ka haɗa mata, idan kuka yi arba’in sai mu cigaba da rabon. Ka ga ita da Baby suna buƙatar lokacinka da kulawarka sosai a waɗannan kwanakin. Ta wuce ta nufi gaban wardrobe domin saka kaya.

    Yana nan zaune a gaban mudubin ta shirya ta fice ta bar shi a ɗakin; nan da nan ta haɗa masa breakfast ta jera a kan table sannan ta dawo ɗakin ta same shi ya riga ya gama saka kaya. Tana tsaye daga bakin ƙofa tace ‘Na yi serving breakfast. ‘Ok.’ Ya amsa. Ta juya ta fice ya biyo bayanta. Suka zauna tare suna cin abincin. Har suka ci kusan rabin abincin babu wanda yace wani abu; kowa da abinda yake ransa.

    Ya ajiye kofin shayinsa bayan da ya kurɓa sannan ya ɗauki fork ɗinsa ya tsikari dankalin baturen da yake gabansa, ya ɗan ajiye fork ɗin ya kirawo sunanta a hankali kamar ma ba ya so ta ji kiran. Ta ɗaga kanta daga kallon kwanon abincinta ta amsa tana kallonsa. Ya yi gyaran murya sannan yace ‘Um, da-Allah ki yi haƙuri ki cigaba da girki a ƙalla har zuwa lokacin da Antin Naja zata gama yi mata wanka ta tafi.

    Tunda kin ga ga Hafsa nan tana taimaka miki kuma na san Afaf ɗin ma yanzu duk abinda kika gwada mata za ta iya taya ki da shi. Saura kaɗan dariya ta ƙwace mata; wato yanzu Afaf ta kai ta taimaka wajen girki kenan tunda ya auro matar so? Ashe ma ya san kunya tunda ga shi ba ya so ya ji kunyar iyayen Naja.

    Ta ajiye cokalinta ta kurɓi shayinta sannan tace ‘Don Allah Abban Afaf mu bar wannan maganar, hidimar gidannan ta wata takwas na karɓar mata. Ai na yi ko? Yanzu sai ta cigaba daga inda ta tsaya. Kwanan kuma da nace na ba ta da gaske nake, ku je ku yi jegonku na masoya kwana arba’in; wataƙila dai a kwankin da suka kama nawa ne na yi aikin gidan idan ina nan in ya so ita sai ta kwana da angonta.’

    Cike da jin zafin abinda ta faɗa yace ‘Khadeeja ni kike gayawa wannan maganar? A cikin abinda ta faɗa ba ta san menene ya ɓata masa rai haka ba tunda ita dai a iya saninta ba rashin kunya ta yi masa ba, amma ta ga ya fusata yana faman yi mata muzurai. Ita da ya kamata a ce ita ce ranta ya ɓaci haka saboda nauye-nauyen da yake nema ya ɗora mata waɗanda ƙarara suke nuna rashin adalci.

    Ta kalle shi ta kawar da kai tace ‘Allah ya ba ka haƙuri. Ta kurɓe ragowar shayinta ta miƙe da kofin da kwanonta ta wuce kitchen. Tana ajiye kwanukan ta fito ta wuce ɗakinta, tana turo ƙofar ɗakin hawayen da take riƙewa suka ƙwace mata, ta ƙarasa ta zauna a kan kujerar gaban mudubi. Ta zubawa mudubin ido tana kallon yanda hawaye suke fita daga idanuwanta suna gangarewa ta kan kumatunta.

    Wai me Mustapha ya ɗauke ta ne? Mai aikin Naja? To da me yasa ya aure ta ne? ko dama haka ake soyayya? Ba ta sami amsar tambayoyinta ba ƙarar fitar motarsa daga gidan ta katse mata tunani, ta tuna ita ma aiki za ta tafi. Don haka ta miƙe ta wanke fuskarta ta ƙarasa shiryawa ta fice daga gidan zuciyarta cike da damuwa.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Biyar

    Edita@rumasau-kallamu