Tag: yadda ake

  • Juyin -Juya Hali A Rubuce-rubucen Littattafan Adabi

    Juyin -Juya Hali A Rubuce-rubucen Littattafan Adabi

    Duk da cewa maza su suka. fara rubuce tun 1933 Mukhtar (2004). Amma wacce ta fara Rubuta ƙagaggen Labari na Hausa ita ce Hafsatu Abdulwaheed, Abdalla Uba Adamu (2024). Mace ta farko ‘Yar Arewa da fara rubuce-rubuce a Hausa da Fulatanci ita ce Dadasare Abdullahi Uwargidan Dr. R M. East takan taimaka wa Maigidanta Jaumisare (R.M. East) da labaran da akan saka a Jaridar Gaskiya Ta fi Kwabo da kuma tace labaran. Dadasare (2019)

    Waɗannan su ne wasu daga cikin talife-talifen wannan marubuciya wacce babu shakka ta yi namijin ƙoƙari a wannan nau’i na Adabin na tailfin Hausa da Fultanci. Bayan sai ita Zuwaira Isa wacce ta rubuta ƙagaggen littafi a 1972 sannan tana ‘yar makaranta a Rikkos can jos amma ba a buga ba sai daga baya, mai suna Ɗaki Ba Ya Tashi Jinka Ya Zauna.

    Ya iso kasuwar ta Kano tun 1992, to sai bayan shekaru uku ne wato a 1995 littafin Bilkisu ya fara bayyana kamar yadda aka gani a jerin littattafan nata, a sama. Ita kuma Bilkisu it ace ta fara rubuta littafai masu na Hausa, kimanin guda ashirin cikin shekaru uku zuwa huɗu.

    Littattafan zuwaira Isa Danlami Jos sun haɗa har da:

    • Zuwaira Isa daki Ya Tashi Jinka Ta Zauna (1992) Gaskiya corporation Ltd.Zaria.
    • Zuwaira Isa Labarin So (1995) littafi na 1-3 City Publishers Jakara, Kano.
    • Zuwaira Isa Sants in Soyayya (1996) littafi na 1-3 city Business Centre Daneji, Kano.
    • Zuwaira Isa  kissar Mata (1996) City Publishers Goron Dutse Road Jakara,Kano.
    • Zuwaira Isa  Wahala Siraxin Masoya (1997) Sauqi Bookshop and Publishing Company Sabon Gari,Kano.
    • Zuwaira Isa  ‘Ya’ya Mata (1999) littafi na 1-3 M Square Telecomm,Zoo Road, Kano.

    Sauran littattafan wannan marubuciya da muka ji labarinsu amma ba su zo hannuna ba har lokacin da zan buga wannan littafi sun haɗa har da:-

    • Zuwaira Isa  A Lallaɓa Auren Zamani
    • Zuwaira Isa  Mowar Mata
    • Zuwaira Isa  Ƙwarya Ta Bi Ƙwarya
    • Zuwaira Isa  Kara Da Kiyashi
    • Zuwaira Isa  A Ci Duniya Da Tsinke
    • Zuwaira Isa  Duniya Labari, Ciwon ƙauna, ƙishirwar Bege (d.s.)

    Bayan waɗannan, mata marubuta, daga cikin maza kuma waɗanda suka fi fice kamar yadda wallafe-wallafe ya nuna akwai Nazir Adam Salih da kuma Ado Ahmad Gidan Dabino. Wasu daga cikin littattafan Nazir Adam Salih sun haɗa da:-

    • Nazir Adam Salih  Me Ya Fi Kuxi? Kamnas Publishers, Kano.
    • Nazir Adam Salih  Kibiyar Ajali littafi na 1-2 (1996) City Business Centre Daneji, Kano.
    • Nazir Adam Salih  Naira Da Kwabo littafi na 1-2 (1998) Jet Age Publishers Kano.
    • Nazir Adam Salih Birnin Sarauniya (1998) Qamnas Publishers Kano.
    • Nazir Adam Salih Ta Leƙo Ta Koma (b. kw.) Qamnas Publishers Kano.
    • Nazir Adam Salih Mutuwar Kasko (1999) Layeet Printers Kano.
    • Nazir Adam Salih  Aljani Ya Taka Wuta (2000) Jet Age Printers Kano.
    • Nazir Adam Salih A Ci Bulus (b. kw.)
    • Nazir Adam Salih  Kudi Da Maciji (b. kw.)
    • Nazir Adam Salih  Damisar Takarda (2000) Jet age Printers Kano.

    Amma shi Ado Ahmed Gidan Dabino shi ma ya taka muhimmiyar rawa a cikin wannan nau’in adabi inda littattafansa suka fito kamar haka:-

    • In Da So Da Ƙauna (1991) Gidan Dabino Ado Ahmed  Publishers, Kano.
    • Masoyin Zamani I (1993) Gidan Dabino Publishers, Kano.
    • Wani Hanin Ga Allah (1994) Gidan Dabino Publishers, Kano.
    • Kaico! (1996) Gidan Dabino Publishers, Kano.
    • Duniya Sai Sannu (1997) Gidan Dabino Publishers, Kano. Mukhtar (2004)

    Adabin Kasuwar Kano

    To amma a cikin shekarar 1984 wata al’adar rubuce-rubuce ta ƙagaggun littattafai ta kunno kai wadda aka sa wa suna Adabin Kasuwar Kano, a Turance “Kano Market Literature”. An sami wani jigo na soyayya inda ya yi tasiri sosai da sosai a cikin wannan adabin. Daga cikin waɗanda suka share fage akwai irin su littafin;

    • Rabin Raina littafi na ɗaya(1984) na Talatu Wada Ahmed
    • Soyayya Gamon Jini (1986) na Ibrahim Hamza Abdullahi
    • In Da Rai (1987) na Idris Imam
    • Budurwar Zuciya (1987) na Balaraba Ramat Yakubu
    • Kogin Soyayya (1988) na A.M. Zahraddeen
    •  Idan So Cuta Ne (1989) na Yusuf M. Adamu.

    (Duba muƙalar Yusuf M. Adamu 1996).

    Bayan wannan an sami mace a karon farko wacce ta yi fice a cikin rubutun adabi na Hausa inda ta rubuta ƙagaggun littattafai a ƙalla sama da guda ashirin (20) a cikin shekaru huɗu rak. Wannan kuwa ita ce uwargida Bilkisu Salisu Ahmed Funtuwa, wadda kafin ta yi aure ake kira Bilkisu Ibrahim. Nabature Funtuwa.

    Ita dai wannan marubuciya ta yi fice a kan waɗannan rubuce-rubuce ba ma kawai tsakanin mata ba, hatta cikin mazan ma na wannan nau’in adabin babu wanda ya kamo ta. Binciken da muka yi, ya nuna cewa. Makaranta littattafan wannan nau’in adabin har bincikawa sukan yi ko sabon littafinta ya fito su yi maza su karanta don kada wani ya ba su labarinsa. Kaɗan daga cikin irin waɗannan rubuce-rubuce nata sun haɗa har da:-

    • Bilkisu S.A.F Allura Cikin Ruwa, (1995) Gidan Dabino Publishers Kano, Nijeriya.
    • Bilkisu S.A.F Sirrin Ɓoye littafi na 1-2 (1996) City Publishers Jakara Kano, Nigeria
    • Bilkisu S.A.F Wa Ya San Gobe littafi na 1-3 (1996) City Pulishers Jakara Kano, Nijeriya.
    • Bilkisu S.A.F Ƙarya Fure Take, littafi na 1-2 (1996) Nabila Surayya Bookshop.
    • Bilkisu S.A.F Gaskiya Na Mafaɗinta littafi na 1-2 (1997) Printed
    • Bilkisu S.A.F Kyan Ɗan Maciji littafi na 1-2 (1997) Printed
    • Bilkisu S.A.F In Da kwaɗayi littafi na 1-2 (1998).
    • Bilkisu S.A.F Ki Yarda Da Ni (b. kw) littafi na 1-2
    • Bilkisu S.A.F Sa’adatu Sa’ar Mata (b. kw)
    • Bilkisu S.A.F Maryamu (1999) littafi na 1-2
    • Bilkisu S.A.F Mugun Zama (1999) littafi na 1-2 Anti Bilki Bookshop Kano
    • Bilkisu S.A.F Kowa Ya Raina Tsaiwar Wata (1999) littafi nal-2 Anti Bilki Bookshop Kano.

    Kammalawa

    A taƙaice, takardar wata tafarki ce a fagen adabin Hausa, musamman ta fuskar rubuce-rubucen da suka shafi tarbiyya da gyaran halaye. Saboda haka Littattafan ƙagaggun Labari ba wai labaran soyayya kawai suke ba, har ila yau suna nuna irin rawar da adabi ke takawa wajen sauya tunani da ɗabi’a.

    A matsayin shawara, akwai buƙatar a ci gaba da nazarin irin waɗannan marubuta domin fahimtar tasirin rubuce-rubucen Hausa wajen gina tarbiyyar matasa da inganta al’ummar Hausawa gaba ɗaya. Duk waɗannan suna jan kunne ne da a tarbiyyantar da mutune su yi aiki da tarbiyya a cikin mu’amalarsu da mutane.

    Ana cusa tarbiyya wajen horar da mutane ko ilimantar da su, ko ta hanyar rubutu, domin a gano kaifin hankalin mai karatu idan da buƙatar gyara a gyara maka ko a cusa musu labarai na ban tausayi ko na jin ƙai ko ta hanyar yi musu tarbiyyar ta ta hanyar gargajiya misali Karin Magana da Tatsuniya ko kuma ta hanyar gaya musu wani labari mai daɗi na baka ko a rubutaccen ƙagaggen labari wanda kuma shi ne muka yi magana kai.

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga muƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

    Danna nan don karanta Samuwar Rubutun Ajami

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ƙarshe

    Mijin Marigayiya Babi Na Ƙarshe

    EPILOGUE

    Bayan shekaru 3. An yi auren Afaf an kai ta gidanta, yaron da ta aura ƙanin abokin Abbanta ne, da kanta ta je ta kai wa Khadeeja katin bikin nata wanda ta karɓa cike da girmamawa. Ta yi mata magiya a kan ta je amma duk da haka ba ta je ba, domin ba ta son abinda zai haɗa ta da Naja da dangin Mustapha a cikin taro.

    Kuma duk yanda Mustapha ya so ya saka ta a cikin shawarar bikin Afaf ɗin da inda zai sayi furniture haka ta zame da wayo da dabara har ya gaji ya rabu da ita. Yana nan dai yana bibiya da kuma addu’ar ta yarda su mayar da aurensu. Yana zaune a ɗakinsa a kan dadduma yana hutawa bayan sallar la’asar kwana biyu bayan auren Afaf haka kawai ya ɗauki waya ya kirawo Khadeeja.

    Ya gyara zama ya jingina da bangon da ƙofar ɗakin take jiki ta yanda idan aka buɗo kofar aka shigo zai zama yana bayan ƙofar kenan. Bayan ta amsa suka gaisa suka shiga hirarrakinsu, tana tambayarsa labarin biki. A haka har yace ‘Kin ga da kin yarda ai da tare da namu za a ɗaura.’

    Ta yi dariya tace ‘Kai kuwa ka ƙi ka bar maganar nan. ‘Ba zan bari ba Khadija, har sai kin amince. Ko na tsufa ma sai na dawo da ke ko da takaba ne kya yi min sai mu haɗu a aljannah. Dariya kawai ta yi don ba ta da amsar da za ta ba shi. Suka yi shiru na ɗan lokaci sannan yace ‘Duk wani condition da kike so Khadeeja ki saka na yi miki alƙawarin zan cika in dai za ki zama mata ta.

    Just one more chance Khadeeja, ki daina wahalar da zuciyata haka. Ta yi murmushi mai sauti ba tare da ta ce masa komai ba; tabbas yana nema ya gamsar da ita ta sake amincewa da aurensa, amma a halin yanzu ba ta san amsar da za ta ba shi ba. Ya gaji da shirun kuma yana ji a jikinsa cewa kalamansa sun fara yi mata tasiri.

    Ya katse shirun yace ‘Gobe da safe zan shigo, ok? ‘Ok, Allah ya kai mu. Amma ina da programme da safe so ka bari sai bayan azahar. ‘Ok, I will take you out to lunch then. No execuses. Ta yi dariya ‘Ka dai san ba zan je ba ko? Kada ma ka fara wata rigimar daban.’ ‘In dai rigima ce ai a wajenki na koya. I will see you tomorrow at lunch.’ Ya ajiye wayar ba tare da ya bari tace wani abu ba.

    Ko da ba za ta yarda ya fita da ita lunch ɗin ba ya fi so ta bar shi ya kwana da murnan zai fita da Khadeeja gobe, in ya so idan ya je office ɗin su yi faɗan da suka saba. Tana tsaye a jikin ƙofar ɗakin tana jinsa, duk abinda ya faɗa tana ji. Sai da ya ajiye wayar sannan ta banka ɗakin ta shiga a fusace.

    Firgigit ya juyo ya kalli ƙofar da aka mako, yace ‘Ya haka kamar za ki fizge ƙofar? Me ya faru ne? Ko wani abun ya biyo ki? Ta tsaya tana masa kallon raini tana jijjiga, sai da gaji da kallon nasa sannan a fusace tace ‘Mustapha na gaji da wulaƙancin da kake mina a kan matar nan, shekara huɗu ana abu ɗaya saboda tsohon naci. Wallahi babu ruwan Allah da kun taɓa aure alaƙarku haramtacciya ce.

    Kuma idan ma zina kuke Allah zai kama ku. Faɗan nata bai harzuƙa shi don ya saba ji, idan ma ba ta ji yana waya da Khadeejan ba kullum cikin duba masa waya take. Ba sa magana ta whatsapp don haka kullum cikin duba calls take, da zarar ta ga call ɗin Khadeeja to sai ta yi wannan masifar. Ya miƙee ya naɗe daddumar yana cewa ‘Kada ki kuskura ki jefi khadeeja da wannan kalmar yanzu ranki zai ɓaci, kuma kin sani.’

    Ta riƙe ƙugu tana dan zare ido tana cewa ‘Ohh! Yanzu kai ka fi son Khadeeja kenan dan kanka, kai na jefe ka da koma menene amm kada na jefi Khadeeja ko? To wallahi da kai da ita baku isa ba…. ‘Ke kika sani.’ Ya faɗa tun kafin ta ƙarasa faɗin abinda take faɗa, ya ajiye daddumar ya kewayeta ya fice daga ɗakin.

    Ta juyo ta bi bayansa da kallo cike da takaici sannan ta wuce ta zauna a gefen gado ta zuba fuskarta a tafukan hannunta ta fashe da kuka. Wannan wane irin wulaƙanci ne, tana murna ya saki kishiyarta amma kullum suna tare, ita kuma tana nan ya kulle ta a gida. Wannan wace irin musiba ce? So take ta ware rana ta je ta sami Khadeejan a office ɗin nata ta tara mata mutane amma dai tana tsoron kada Mustapha ya sake ta a kan hakan; don yanzu ta ga kamar ma ba a haiyacinsa yake ba.

    To yanzu babu aure a tsakaninsu yana mata wannan tsohon nacin idan kuma ta dawo ya za a yi? Ita menene makomarta ya dawo da rabin ransa me ƙaunar ‘yayansa. Ta ɗora hannu a ka ta sake rushewa da kuka.

    END

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu

    Dole tana ji tana gani ya kafa mata doka idan dai har zai ci abinci to parlor ɗin kasa zai ci. Babu yanda ba ta yi da shi ba yaran su dinga hawowa sama amma yace ba za su hau ba tunda ita saman take so a bar mata, haka ta haƙura ta saka masa ido saboda abun yana nema ya zama matsala a tsakaninsu.

    Duk wani taimako da aiki da malamai za su yi mata tana kan yi sai dai abun ya ƙi yi, idan ya yi kamar zai kama sai kuma ya sake botsare mata. Idan dai tana son ganin walwalarsa to ta yi wa yaran nan yanda suke so kuma ba tare da ta yi masa wani ƙorafi ba. Burinta ɗaya yanzu a aurar da Afaf domin haka ne kawai take ganin za ta sami natsuwa a gidan nan.

    Don a halin da ake ciki komai zai yi da Afaf yake shawara, wasu lokutan ko ta ba shi list ɗin cefanen gidan sai ya tambayi Afaf abinda take buƙata ita da kannenta ya siyo musu. Idan kuma ya kawo kayan sai ya tsaya a ƙasa Afaf ɗin ta ware nasu kayan sannan ya hau mata sama da sauran. Haka dai take haƙuri, musamman da yake ya iya lallaɓa ta ya tsara ta kawai dai ya nuna mata yaran nan nasa ba za su taɓu ba.

    Haka rayuwarsu ta cigaba.

    Duk yanda yake jin zai samu Khadeeja ta saurare shi ya gagara, ga shi kuma sai a yanzu Allah ya jarrabe shi da ƙaunarta. Kusan kullum sai ya yi mata waya, idan ta ga dama ta ɗauka idan kuma ba ta ga dama ba ta ƙi ɗauka. Ya mayarwa kansa duk Juma’a da yamma sai ya je gidan duba Hammad, sai dai hakan bai ba shi damar ganinta ba.

    Domin idan ya je ko da ya yi mata waya haka za ta saka a buɗe masa parlor ɗin baƙi ta turo masa Hammad, har ya gama hirarsa da Hammad ya tafi ba za ta fito ba. Don haka wasu lokutan sai kawai ya rutsa ta a office inda dole ta zauna su gaisa har su ɗan yi hira. Abu ɗaya ne yake hana shi zaƙewa a kan maganarta saboda har yanzu yana jin kunyar Baffanta, bai san da wane bakin zai je yace masa ya sake ba shi auren Khadeeja ba.

    Shi yasa ya dage yake ƙoƙarin ganin ya gamsar da Khadeejan ta je wa Baffan da maganar da kanta. Kwanci tashi har shekara ta zagayo. Tun da ya gama haɗa takardun yake cike da farin ciki, haka ya kwana cike da zaƙuwa sabodan yanda yake son gari ya waye ya je ya sami Khadeeja ya yi mata albishir.

    Yana fita office ɗinta ya fara tsayawa, ya yi sa’a kuwa ta riga ta zo. Kamar yanda ya saba a cikin office ɗin ya same ta tana zaune tana editing script ɗin da za ta yi amfani da shi wajen gabatar da show ɗinta. Yana shiga ya tura ƙofar sannan ya yi wa kansa mazauni a kujerar gabanta cike da walwala. Bayan sun gaisa yace ‘Kina jin daɗinki fa, kin ga yanda kike sheƙi kuwa.

    Ta yi dariya tace ‘Don Allah ka bari, haba. Ko waya ma ba ka yi min ba kace min za ka zo to da ka zo na riga na shiga studio fa? Shi ma dariyar ya yi yace ‘Sai na jira ki mana. Ai idan kina son na daina zuwa wajen nan to ki yarda mu mayar da auren mu mu huta, in ba haka ba dole kullum na zo nan na yi attendance don duk masu shirin yi min shigar sauri su ganni su san ina nan ba fashi.’

    Ta sunkuyar da kai don ba ta san me zata ce masa ba, amma dai yawan zuwan nashi office ɗin ya fara gundurarta. Ba wai don ba ta so a gan shi ba ne kuma ba wai tana jin ya isa ya hana ta kula wanda take son kulawa ba; kawai dai tana so ya ɗan ba ta space tunda ita dai ta gama magana a kan lallai ba za ta koma gidansa ba kuma har yanzu hakane a ranta.

    Muryarsa ce ta katse mata tunanin da ya kirawo sunanta, ta ɗago ta kalle shi suka haɗa ido sannan ta kawar da kai. Yace ‘Ki sauwaƙe mana wahala ki yarda mu mayar da aurenmu, duk wani abu da ya ɓata miki rai a baya na yi miki alƙawarin ba za ki sake gamuwa da shi ba a zamanmu.’

    Ta jijjiga kai ‘Na fahimce ka Mustapha, amma dai ka yi haƙuri. Ba wai kai ne ba zan aura ba, auren ne gaba ɗaya ba zan yi ba. Don Allah ka daina wannan maganar, ka mayar da hankali wajen kula da iyalinka. Ka ga yanzu ni babu aurenka a kaina, idan ta ji kana zuwa wajena zaku iya samun matsala. Ka zo kai ba ka sami natsuwa da ta gidan ba kuma ni ba aurenka zan sake yi ba.’

    Ya jijjiga kai don ba ya son wannan maganar, shi yana ji a jikinsa Khadeeja matarsa ce shi kaɗai don haka duk tsawon lokacin da za ta ɗauka tana yi masa yanda zai jure. Ya zaro envelope daga aljihunsa ya ɗora a kan tebur ɗin ya tura mata gabanta yana murmushi yana cewa ‘Wannan na zo kawo miki daman. Ta ɗauko tana dubawa tana cewa ‘Me na samu?’

    Ta zaro takardun daga envelop ta fara dubawa; kujerar Hajji Mustapha ya ba ta. Tana dubawa tana murmushi saboda yanda tunanin za ta je Hajji ya faranta mata zuciya. Ta ninke takardu ta fara mayarwa cikin envelop ɗin a daidai lokacin da murmushinta ya ragu. Ta tura masa gabansa tace ‘Na ji daɗi Abban Hammad, na gode Allah ya ƙara arziki da rufin asiri.

    Amma ka yi haƙuri ba zan iya karɓa ba, ba wai don na raina ba ko wani abu. Na gaya maka ba zan sake aurenka ba so ka ga babu wani dalili da zai sa na karɓar maka kujerar Hajji. Kuma ko na karɓa ma Baffa ba zai taɓa barina na je ba sai dai a ɗaura mana aure kafin na tafi; kuma wannan ba zai yiwu ba. Please ka yi haƙuri! Amma na gode sosai.’

    Kafin ta gama bayanin fuskarsa ta canza gaba ɗaya, ba tare da ya ɗauki takardun ba yace ‘To ki karɓa mana Khadeeja ki bari a ɗaura mana auren, please ki daina guduna haka. Ta sunkuyar da kanta cikin damuwa tace ‘Ba gudunka nake ba, amma dai ba zan iya ƙara aure ba.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci. Jimawa kaɗan yace ‘To yanzu ya kike so a yi? Ni da sunanki na biya wannan kujera. Ka yi hakuri ba zan iya karɓa ba. Suka sake yin shiru na ɗan lokaci. Kafin su yi magana aka ƙwanƙwasa ƙofar, ta amsa ta ba da izini aka shiga. Wata mace ce abokiyar aikinta ta ɗan leƙo tace ‘Anti Khadeeja yallaɓai yace ke ake jira a studio za a fara.’

    ‘Yanzu zan shigo.’ Ta faɗa tana shirin miƙewa. Ta dubu Mustapha tace ‘Bari na je kada ka sa a kore ni aiki. Ya yi dariya shi ma ya miƙe, sai dai tana kula da shi bai ɗauki takardun ba. Ta miƙa hannu ta ɗauka sannan ta zagayo ta tsaya a gabanshi, ta miƙa masa takardun tana murmushi tana cewa ‘Ka yi haƙuri ka tafi da wannan, wallahi ba zan iya karɓa ba.

    Idan na karɓa ba zan iya da rigimar Baffa ba tunda na san ba zan aure ka ba. Ka yi haƙuri please. Ya miƙa hannu ya karɓi takardun yana tsare ta da ido kamar mai binciken wani abun a idonta, har sai da ta kawar da nata idon. Ta wuce ya biyo ta a baya suka fito daga office ɗin, suka jero har zuwa reception sannan ta yi masa sallama ya fice ita kuma ta miƙe ta nufi studio ɗin.

    Tana fatan Allah ya sa dai kada ta kwafsa saboda yanda Mustapha ya jagula mata lissafi; me za ta yi da kujerar makansa? Wato ma shi har yanzu tunani yake saboda kujerar Makka yasa ta ƙi komawa gidansa? Bai ma san wacece ita ba kenan, zaman da suka yi tare bai sa ya fahimce ta ba.

    Ba ta buƙatar kujerarsa kuma ta san tabbas idan ba aurensa ta kuma yi ba ko kashi ta kai gida tace shi ya ba ta sai sun yi rigima da Baffa, kuma ba ta shirya ƙarya ba saboda Mustapha wanda take so ya rabu da ita ya daina damun rayuwarta.

    Tana tashi daga waje aiki ta wuce gidan Yaya Mama, ta yi sa’a yaran duk sun tafi islamiyya don haka ta sami Yaya Mama ita kaɗai. Bayan sun gaisa Yaya Mama tace ‘Bari na samo miki ruwa ko lemo. Ta dafe cinyarta tace ‘Bar shi kawai sai da na tsaya na ci abinci sannan na ƙaraso.’

    Ba tare da ɓata lokaci ba ta fara ba ta labarin kujerar Makkan da Mustapha ya kawo mata ɗazu. Sai da ta gama ba ta labarin suka sheƙe da dariya a lokaci guda sannan tace ‘Wai ni zai saya da kujerar Makka ɗan rainin hankali. Yaya Mama tace ‘Ai kuwa ɗan rainin hankali lamba ɗaya, wato tunda kin ce ya sake ki saboda kujerar Makka bari ya biya ki sai ki yarda ya mayar da aurenku.’

    ‘Ashe kin gane. Suka cigaba da hira suna tuna abubuwan da Mustaphan ya yi a baya. Sai da Magriba ta fara kawo jiki sannan Khadeeja ta fara shirin tafiya. Bari na wuce kada magriba ta yi min a nan. ’Yaya Mama ta dafa hannunta tace ‘Khadeeja, idan fa za ki koma gidan Mustapha kin san babu wanda zai hana ki ko? Don ni ina ganin ma gara ki koma can ɗin tunda kin ga ko babu komai ga Hammad.

    Kuma na ga har yanzu ba ki da wani manemin; duk da ma duk wanda za ki aura mijn wata ne don haka kin ga dole ki zauna da kishiya. Ni ina ga gara gidan Mustaphan tunda dai ya yi nadama har yana ƙoƙarin ya faranta miki. Nan take ta ɓata rai, ta zare hannunta ta ɗan matsa daga kusa da ita sannan tace ‘Ba zan taɓa komawa gidan Mustapha ba, aure kuma ba ya gabana balle na fara damuwa da rashin manemi.

    Idan Allah ya saka ina da rabon aure a gaba to duk wanda Allah ya sa shi ne mijina zan aura amma fa in sha Allahu ba zan sake auren Mustapha ba. Mutumin da ya ɗauke ni ne kawai a matsayin solution to his problem. Ko yanzun ma da yake ta ƙoƙarin na koma gani ya yi ƙiriƙiri matar tasa ta kasa kula masa da gidan da yara kamar yanda na yi.

    Shi yasa ya lallaɓo ya mayar da ni cikin wahalar da Allah ya raba ni da ita. Ba zan koma na, can su ƙarata. Ta miƙe ta ɗauki jakarta, don haka ita ma Yaya Maman ta miƙe. Ta san idan ta fiya takurawa da maganar yanzu za su yi faɗa don haka sai ta ƙyale ta suka yi sallama ta kama hanya.

    Wunin ranar gaba ɗaya bai yi masa daɗi ba. Ko da dai bai sa ran Khadeeja za ta karɓi kujerar ba tare da an kai ruwa rana ba amma kuma bai sa ran za ta ƙi karɓa haka gaba ɗaya ba ba tare da wata ƙofa ta sulhu ba. Haka ya wuni a office ɗin babu walwala. Sai da yamma ta yi sannan ya kwashi kayansa ya koma gida.

    Yana shiga ɗakinsa ya ajiye takardun hannunsa a kan mudubi; takardar kujerar da ya ba wa Khadeeja ce a sama tare da wasu takardun na office. Tunda ya je sallar magriba masallaci ya dawo ya yi zamansa a ƙasa shi da yara. Da farko ta ɗan zauna a wajensu ana hira gaba ɗaya, daga baya kuma sai ta tashi ta haye sama ta bar su.

    Ɗakinsa ta shiga don ta samu ta huta domin nan ne kawai idan ta rufo ƙofar Rukayya ba za ta so ta buga ta tashe ta ba. Har ta wuce mudubin sai kuma ta koma da baya, ta sa hannu ta ɗauki envelope ɗin da ta ja hankalinta. A buɗe take don haka sai kawai ta zaro takardun ta fara karantawa.

    Nan da nan kanta ya kulle; tabbas wannan sunan Khadeeja ne. To me hakan yake nufi?Suna tare kenan yanzu ta zama bazawararsa ko me? Tunda idan ba wata alaƙa ce tsakaninsu ba me zai saka har ya biya mata kujerar Makka? Kenan ma ita Mustapha zai rainawa hankali, ya saki matar sannan ya koma yana bin ta? Gaskiya ba za ta yarda ba.

    Ta ɗaga kanta ta hango wayarsa tana chaji a kan bedside durowa; nan da nan ta ajiye takardun ta ƙarasa ta ɗauki wayar. Ta riga ta san PIN ɗin don haka kai tsaye ta buɗe ta fara duba whatsapp; sai dai har ta gama dubawa ba ta ga sunan Khadeeja ba. Tana duba calls ta ga sunan ‘Sweetheart’ shi ne sunan da ya yi saving lambarta tun yana zuwa zance kuma bai taɓa canzawa ba.

    Bayan rabuwarsu Najan ta goge ta saka maman Hammad amma ba ta san yanda aka yi ya mayar ba. Ta mayar da wayar ta ajiye cike da damuwa da takaici. Ta tashi ta dawo ɗaya gefen gadon ta zauna ta zuba tagumi; tabbas za su yi rigima da Mustapha don ba zai yiwu ba ya dinga zagayawa wajen tsohuwar matarsa suna raina mata hankali.

    Sai wajen ƙarfe tara na dare ya hawo saman, lokacin ya je sallar isha’i ya dawo kuma sun gama cin abinci da yara. Zuwa lokacin ita ma ta gama duk abinda take yi ta kwantar da yara tana kwance a kan gadon ɗakinsa sanye da rigar bacci ta miƙe kafa tana kallo a waya ya shiga ɗaki. Bayan ta amsa sallamarsa ta mayar da hankali kan wayar hannunta.

    Kai tsaye ya wuce ciki ya canza kayansa sannan ya zauna a kan carpet ɗin da ke gaban gadon ya miƙe ƙafa ya janyo computer ɗinsa ya kunna ya kama aiki. Yawanci idan dai har yana da aiki to ya kan kai dare sosai a zaune yana aikin, ita kuma ba za ta iya jira ba. Don haka ta miƙe ta zauna ta ajiye wayar da take hannunta ta yi gyaran murya sannan tace ‘Uhm, na ga wata takarda, wai Maman Hammad ka biyawa Makka?’

    Bai yi mamakin jin tambayar daga gareta ba duk da bai sa rai da ita ba, amma dai ya san ya manta ya ajiye takardun a kan mudubinsa. Ba tare da ya bar aikinsa ba yace ‘Eh ita na biyawa, akwai matsala ne. Cike da neman rigima tace ‘To kuma a yanzu meye tsakaninka da ita tunda na ga dai babu aure. Ko kuma kun mayar da auren ne ni ce ban sani ba.’

    Har yanzu hankalinsa yana kan aikin yace ‘Ba mu mayar ba muna dai kan hanya. To shi ne kuma ka biya mata Hajji. Ya ɗago ya dube ta yace ‘Eh, akwai matsala ne? ‘Gani dai na yi bai dace ba tunda babu aure a tsakaninku. ‘Wannan ra’ayinki kenan. Ta kula so yake ya yi mata wulaƙanci don haka ta miƙe ta zauna sosai tace ‘Ina fatan dai ka san yanzu ita ɗin ba muharramarka ba ce.

    Kuma ina fatan ka san ba zai yiwu ina nan gida ina maka biyayya wai ni matar aure ba ka dinga zagayewa wajen tsohuwar matarka wadda ka saka da hannunka, ba zan ɗauka ba gaskiya.’

    Ya ɗago ya kalle ta rai a ɓace yace ‘Sai ki ɗau mataki a kai. Ta kula kamar haushinta yake ji sai dai ba ta san dalili ba, don lafiya ƙalau suka rabu da safe ya ajiye ta a office sannan ya fice; to meye ya harzuƙoshi hakan daga yin magana? Kada fa ka gaya min magana daga tambaya, na dai gaya maka ba zai yiwu ba ina nan ka kulle ni a gidanka a dinga ganinka a gari kana yawo da wata matar banzan.

    Ta faɗa tana miƙewa tsaye. A fusace yace ‘Khadeejan kike cewa matar banza saboda wulaƙanci? Sai dai kafin ya rufe bakinsa ta fice daga ɗakin ta rufe masa ƙofar; wanda wannan ɗabi’arta ce idan dai ya ɓata mata rai sai ta gaya masa magana mai zafi sannan take fita daga inda yake. Ya yi tsaki ya cigaba da aikinsa don so yake ya gama aikin kafin ya kwanta.

    Haka rayuwarsu ta cigaba. Khadeeja ta ƙi yarda a mayar da aurensu sannan shi kuma ya kasa tunkarar Baffanta da maganar don ya san ba za a yi mata auren dole ba. Amma kuma ya ƙi ya daina bibiyarta; har ta kai ba ya iya sati bai neme ta yaganta ba. Idan ya je gidansu wajen Hammad ta ƙi fitowa to tabbas zai same ta a office. Waya kuwa daman ba ta yankewa don idan ma ta ƙi ɗauka haka zai yi ta kiranta har sai ta gaji ta ɗauka.

    Duk wata kalma da zai yi amfani da ita wajen ganar da ita ta yarda su mayar da aurensu ya yi amma ta sanar da shi ba za ta iya komawa ba. Duk lokacin da ta ji kamar za ta haƙura su koma idan ta tuna yanda yake banzatar da ita a gidan kuma ta tuna yanzun ma sai da ya rasa yanda zai yi da gidan sannan ya fara nemanta sai kawai ta ji ta fasa.

    Tana sane da duk wata rigima da ta faru a gidan tunda kusan duk Asabar a wajenta Habib yake wuni, duk abinda ya dame shi sai ya je ya same ta ya gaya mata. Lokaci zuwa lokaci tana samun masu nuna sha’awar aurenta sai dai auren gaba ɗaya ya fice mata daga rai; don haka yawancinsu ba ta ma bari su zo gidansu.

    Kuma duk inda ta je idan dai ba an santa a wajen ba to tana gabatar da kanta ne a matsayin matar aure don ma kada wani ya zo mata da wata magana; don haka mutanen da suka santa sai suka kasu kashi biyu, wasu suna ganin tana da aure wasu kuma suna ganin ba ta da aure. Amma kuma yawancin mutane kasa tambayarta suke yi.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Uku

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Uku

    Kansa a cike yake saboda rashin bacci ga damuwa, don haka yana shiga office ɗin ya rufo ƙofar ya kwanta a kan 3-seater ɗin da take wajen. Yana rufe ido ya fara nadama; ya aka yi ya saki Khadeeja? Ya aka yi ya bari har ta gama idda bai mayar da ita ba? Tunda dai ai da ya mayar da ita ya san ba ta da wani zaɓi dole ta zauna da shi tunda ba za ta saki kanta ba.

    Tunda yake da Khadeeja bai taɓa ganin wata damuwa game da yaransa ba, ga shi wata takwas kacal da ta bar su gidan yana neman ya gagare shi. A da ya yi zaton Naja za ta fi ta kulawa da su musamman yanda ya ga tana nuna ƙauna garesu kafin ya aureta.

    To me ya canza mata ra’ayi har aka kai inda ba su da damar da za su ci abinda suke so a gidan ubansu? Lallai dole ya ɗau mataki. Haka ya wuni a office ɗin cikin rashin sukuni; yana tunani halin da yaransa suke ciki a gida sannan kuma ga shi zuciyarsa taƙki ta ƙyale shi da tunanin Khadeeja.

    Tabbas da Khadeeja tana nan da babu yanda za a yi ya wuni a office yana tunanin halin da yaran suke ciki. Domin ya tabbatar duk halin da suke ciki to ita ma tana cikin wannan halin a tare da su. Ya tuno lokacin da tace ba za ta yi musu girki ba yanda suka gaya masa gari suka sha kuma garin ma tare da ita suka sha.

    Ya yi dariya a fili; tabbas Khadeeja tana da rigima amma ta iya rigimarta. Ya tabbatar babu yanda za a yi ta ci kaza ta bar yara da baƙin shayi. Haka ya zauna yana aiki yana tuno rigimarsu da Khadeeja yana murmushi shi kaɗai. Bai taɓa zaton zai yi kewar rigimar Khadeeja ba amma yanzu tabbas kewar rigimar tata yake yi.

    Ƙarfe ɗaya da rabi daidai suka idar da sallah a farfajiyar office ɗin su. Yana shiga office ɗinsa ya zauna a kan kujerarsa ya tura ta baya kaɗan yana juyawa ya ɗauki wayarsa wadda take kan tebur ɗin ya lalubo lambarta ya dannan mata kira, ya kara a kunnensa bayan da ta amsa yace ‘Hello.’

    Bayan sun gama gaisawa yace ‘Kina ina ne? Da mamaki a muryarta tace ‘Ina office mana, akwai wata matsala ne? Murya a sanyaye yace ‘No, babu matsala kawai dai ina son ganinki. Zan iya zuwa office ɗin yanzu? ‘Umm! Akwai matsala ne? Ta sake tambaya. Ya yi ‘yar dariya ‘Babu matasala fa, akwai dai maganar da nake so mu yi. Zan iya zuwa, minti talatin kawai ya isa. ‘Ok, ina jiranka duk da dai na kusa tashi.’

    Ya ajiye wayar ya miƙe ya ɗauki mukullan motarsa ya kama hanya. Yana sane ya ƙi ya kirawo ta da ya isa don so yake ya shiga ya same ta a office ɗin nata, don haka bayan ya ajiye motarsa sai ya fito ya shiga gidan talabijin ya tambaya. Ba tare da ɓata lokaci ba aka nuna masa office ɗin nata.

    A hankali ya ƙwanƙwasa ƙofar, daga ciki muryarta ta ba shi amsa ‘Shigo a buɗe ƙofar take. Ya tura ƙofar ya shiga da sallama. Tana zaune a kan kujerar zaman mutum ɗaya wadda take gefe guda, da jakarta a gefenta tana ta danna waya; da alama ta gama shirin tafiya gida. Bayan ta amsa sallamarsa ya mayar da ƙofar ya rufe sannan ya ƙarasa ya yi wa kansa mazauni a kujerar da take kusa da wadda take zaune a kai.

    Bai san dalilin da yasa ganinta ya saka shi jin daɗi ba amma dai ya san ya ji daɗin ganinta. Cikin girmamawa ta gaishe shi kamar babu wata damuwa a tsakaninsu. Bayan ya amsa tace ‘Allah ya sa dai ba wata matsala don tunda kace za ka zo nake ta tunani.’ Ya yi murmushi yace ‘Babu wata matsala, kawai dai ina son ganinki ne.’

    Ta ɗan yi gajeren murmushi tace ‘Uhm, to gani. Ya yi dariya yace ‘Kamar dai kina kora ta. Ba korarka nake ba, kawai dai ina son na tafi gida don wallahi na gaji. Ya gyara zama; ya rasa ma ta inda zai fara domin ganinta ya goge masa duk zantukan da ya tsaro zai zo ya gaya mata. ‘Yara suna kewarki.’ Ya faɗa bayan ya gama nazarin ta inda zai fara.

    Nan da nan murmushinta ya ƙara faɗi, tace ‘Allah sarki ni da Hammad ma muna kewarsu. Don ma Yaya Habib yana zuwa gidan Mommy yana gaishe mu. Ya girgiza kai domin Habib bai taɓa gaya masa yana zuwa wajen Khadeeja ba, bai ma taɓa yi masa maganar Khadeejan ba tun bayan da suka rabu.

    ‘Ya Hammad? Ba ya kukan makaranta?’ Ya tambaya. ‘Baya yi, ka san ya haɗa wayon yayyinsa gaba ɗaya.’ Ta faɗa tana dariya. Suka yi shiru na ɗan lokaci; ita duk ta ƙosa domin so take ta tafi gida yayin da shi kuma ya gyara zama yana kwaso hira. Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan yace ‘Khadeeja. ‘Na’am.’ Ta amsa tana kallonshi.

    ‘Wai me yasa kika ce na sake ki? Ya tambaya yana tsare ta da ido. Ta sunkuyar da kai tana murmushi, ta ɗago ta kalle shi suka haɗa ido sannan ta sake yi masa wannan murmushin nata wanda yake ɗauke da ma’anoni daban daban tace ‘Right question at the wrong time; amma dai zan ba ka amsa.’

    Ta sunkuyar da kai a daidai lokacin da murmushin fuskarta ya gushe, ta ɗago suka sake haɗa ido sannan ta gyara zama tace ‘Gajiya na yi Musatapha. Ka san idan mutum wanda bai iya swimming ba ya faɗa ruwa to zai yi ta ƙoƙarin ganin ya fita da rai ko, amma duk daɗewa zai gaji. To haka ce ta faru da ni.

    Soyayya ce ta saka na aure ka, amma idan dai ba na manta lissafin ba tun a shekarar farko na rasa soyayyarka. Haka na dinga kokawar janyo attention ɗinka ko za ka fahimce ni amma ba ka ko kalli inda nake ba; kai dai abinda kake so kawai shi kake so. Na haƙura ina zama da kai a haka saboda I was ok with just sleeping beside you every night; sai kuma ka ɗauko aure.

    Duk wani abu da nake so daga wajenka a lokacin ka ɗauka ka ba ta ina kallo. Haka na cigaba da kokawar samun attention ɗinka, ina ƙoƙarin ganin ka yi mana adalci amma hakan bai samu ba. Na tuna tun ina ni kaɗai ma ka fara kasa yi min adalci to balle yanzu mun zama mu biyu; ni da rabin ranka. So I gave up, ba zan iya ba, na gaji da faɗan da ba shi da ranar ƙarewa don na gane bana ma gabanka.

    Shi yasa na nemi saki kuma Allah ya taimake ni ka ba ni kuma ka bar ni har na gama idda. Idanuwansa suna kan fuskarta har ta gama ta yi shiru, ya cije leɓe yace ‘Kuma ba ki gaya min ba Khadeeja? How did I not see all this? Ta yi dariya tace ‘Da wanne yaren zan gaya maka?’

    Suka sake yin shiru na ɗan lokaci. Ta danna wayarta ta kalli agogo sannan tace ‘Time yana tafiya, wallahi so nake na tafi gida don na gaji. ‘Oh, sorry Suka sake yin shiru na ɗan lokaci sannan yace ‘Khadeeja yi haƙuri mu mayar da aurenmu, in sha Allahu haka ba za ta sake faruwa ba.’

    Ta miƙe tsaye tana dariya tace ‘Ka yi haƙuri Mustapha amma aure ba zan sake yi da kai ba, babu wannan zance don Allah kada ka sake yinsa. Shekarun da muka yi Allah ya amfana su kuma Allah ya sa kaffara ne amma kada Allah ya maimaita mana. Ya dafe kansa da hannuwansa biyu na ɗan lokaci sannan ya sauke hannuwan ya miƙe tsaye.

    Ta buɗe ƙofar ya fice sannan ta biyo bayansa suka fito daga office ɗin. Suka jero suka fito harabar office ɗin. Nan suka tsaya yana ta faman lallaɓata ta bari ya kai ta gida amma ta ƙi; yana ji yana gani ta tare taxi ta hau. Sai da ya tabbatar ta zauna a bayan motar sannan ya zagaya ya ba wa direban taxi ɗin kuɗinta. Suka ja mota shi ma ya koma ya shiga motarsa ya kama hanya.

    Ya dai ji tace ba za ta taɓa sake aurensa ba amma tabbas bai yarda ba, yana ji a jikinsa in sha Allahu za ta yarda su mayar da aurensu. Yanda zai yi da baffa ne ma yafi damunsa domin ya san tabbas Baffa ba zai saurara masa ba. Haka har ya isa gida yana wannan tunanin, sai dai yana saka ƙafarsa cikin gidan ransa ya ƙara ɓaci. Bai san a yanda zai je ya sami yaran ba sannan kuma ita kanta Najan yana jin haushinta do ba zai taɓa ba ta dama ta wulaƙanta masa yara ba.

    Ana cikin kiran sallar magriba ya shiga gidan, don haka ko zama bai yi ba ya ɗaura alwala ya ja Habin suka wuce masallaci. Ko da aka idar da sallar a can ya tsaya wajen magidantan unguwar suna hira, har sai da suka yi sallar isha’i sannan suka tashi daga hirar kowa ya koma gida.

    A parlor ɗin kasa ya sami yaran suna harkokinsu, ya wuce ya haye sama. Tana zaune a parlor tana jiransa saboda ba ta son yanda tun da safe ya ƙi ya ko kalli inda take. Ita idan ana faɗa ta fi so a yi hayaniya kowa ya faɗi abinda yake ransa, amma ya ma ƙi ya tambaye ta me yasa ta yi wa yaran haka balle ta samu ta yi masa bayani.

    Ba ta jin ya amsa sannu da zuwan da ta yi masa, idan kuma har ya amsa to tabbas ita dai ba ta ji ba. Ba tare da ya kalli inda take ba ya shige ɗakinsa. A fusace ta miƙe ta bi bayanshi. Yana tsaye a gaban mudubi yana rufe durowa ta shiga ta turo ƙofar, ta tsaya a bayan ƙofar ta rungume hannu tace ‘Ga abinci can a dining table.’

    Ba tare da ya kalle ta ba yace ‘Ki sauka da shi ƙasa a can zan ci ni da yara. Ta sunkuyar da kai ‘To bari nace su hawo sai ku ci a nan, duk da su ma na zuba musu nasu abincin kuma duk tuwon ne dai. ‘Ba sai sun hawo ba ni zan sauka, ki ɗauka ki kai can.’ Ya faɗa sannan ya juya ya zauna a gefen gado.

    Ta ƙarasa ta zauna a kusa da shi, ta dafa gwiwarsa ta dan marairaice tace ‘Don Allah ka ba wa Hajia haƙuri, wallahi abinda ta gani ba haka ba ne. Kai ma ka san babu yanda za a yi na ci wani abu na hana yara. Hawowa ne ba su yi ba na ajiye musu nasu a kitchen kuma da ka shiga za ka gani.’

    Ya kalle ta sheƙeƙe yace ‘Ai ba yau kika fara ba, kuma ba yau na fara yi miki magana ba. Babu wani haƙuri da zan ba ta idan kin gyara halinki su yaran za su gaya mata ai. Mugun halin da kike nuna musu kuma ki cigaba kada ki fasa. Ya miƙe zai fita, ta kama hannunsa ita ma ta miƙe tana cewa ‘Don Allah ka yi hakuri, yaran da nake hidimarsu tun kafin na aure ka kuma yanzu ribar me zan ci idan na yi musu mugunta?’

    ‘Ni ma shi ne abinda nake mamaki, wataƙila daman ba don Allah kike yi ba ko kuma zuga ki aka yi kika canza hali ni ban sani ba. Abinda na sani kawai shi ne kusan tun da Khadeeja ta bar gidan nan kika dage sai kin raba rayuwarki da ta yaran nan, ina kula da yanda kike ƙoƙarin ganin ba su hawo benen nan ba saboda tsabar samun waje…’

    ‘Don Allah ka dai wannan maganar, wallahi kai ma ka san ba haka ba ne. Na ga dai ko gidan waye akwai part ɗin mai gida inda ba a bari yara su shiga, amma in sha Allahu ba zan sake hakan ba tunda na ga kai ba haka ne tsarinka ba.’ Ta katse shi cikin ƙosawa. Ya zare hannunsa da ta riƙe ya miƙe yana cewa ‘Ki kawo min abincin parlor ɗin ƙasa yanzu.’

    Ya fice ba tare da ya saurari amsarta ba. Haka ta gama zumɓura baki ta sauko ta kawo masa abincin nan parlor ɗin ƙasa inda ya zauna suka ci da yaran; duk da sun nuna masa su ma tuwo aka ba su irin nashi. Haka ya kafa mata dokar idan dai yana gidan to a parlor ɗin ƙasa zai dinga cin abinci wajen yara, babu roƙon da ba ta yi masa ba a kan ya bari yaran su dinga hawowa saman ana cin abincin tare amma ya ƙi ya saurare ta.

    Ya kula cewa ganin saman bene take kamar wani abu na musamman don haka ya yanke shawarar bar mata saman benen ita kaɗai. Ya yanke shawarar a ƙasa zai dinga zama hira kuma a nan zai dinga kallo yana cin abinci, in ya so idan zai yi bacci ya dinga hawa saman ya kwanta. Ta yi yanda take so da saman ita kaɗai.

    Yana sane ya ƙi zuwa gidan Hajia a ranan sai washegari; ya san idan ya je zancen nan bai huce ba Hajia da Alaji haɗuwa za su yi a kansa har sai ya rasa abinda yake masa daɗi. Don haka washegari yana tashi daga office ya wuce gidan Hajia. Bayan sun gaggaisa ya sami Alhaji a parlor, yana gama amsa gaisuwarsa yace ‘Mustapha me yake faruwa ne a gidan naka? Ban ji daɗin bayanan da na samu daga wajen Habib ba kuma sai ga Hajia ta je ta gani da idonta. Me yake faruwa ne?’

    Ya gyara zama ya shafa kansa sannan yace ‘Wallahi Alhaji ‘yar matsala ce aka samu kuma na ma yi mata magana in sha Allahu hakan ba za ta sake faruwa ba. Ya tashi daga kashingiɗar da yake yana cewa ‘Yar matsala? ‘Yar matsala fa kace Mustapha? An bar yara a ƙasa kamar masu zaman kansu amma kana cewa ‘yar matsala? Gidan naka har ya kai an raba tukunya, ta marayun yaranka daban ta matar gida daban.

    Anya kuwa Mustapha? Rashin uwa ai ba hauka ba ne da za ka wulaƙanta su saboda Allah ya ɗauki ran mahaifiyarsu. Ya sake shafa kansa ‘Wallahi Alhaji akasi aka samu kuma in sha Allahu hakan ba za ta sake faruwa ba. Ya kawar da kai cike da damuwa ya yi shiru, jimawa kaɗan ya cigaba ‘Ita Khadeeja ya wajen nata da Muhamadun? Kana zuwa dai?’

    Ya gyara zama yana murmushi ‘Eh, ina zuwa. Jiya ma na je. ‘To ya kamata dai ka san yanda za a yi ku daidaita tsakaninku tunda dai ka ga ita ba a taɓa samun wata matsala tsakaninta da yaran nan ba, haɗawa ta yi ta riƙe su tun kafin ma ta sami nata. Kuma da ta sami natan ma babu abinda ya canza. Ka ga ita ce ta zama uwa ta gari a wajensu tunda ga su ƙalau da tarbiyyarsu.’

    ‘Haka ne Alhaji, in sha Allahu za mu daidaita. ‘Ya kamata dai ka san abun yi tunda ka san dai yanzu a kasuwa take, idan ba ka maida hankali ba wani zai iya yi maka shigar sauri. Suka ƙarasa hirarrakinsu sannan ya yi musu sallama ya wuce office.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Rubuce-Rubucen Talatu Wada Ahmed A Kan Tarbiyya

    Rubuce-Rubucen Talatu Wada Ahmed A Kan Tarbiyya

    Gabatarwa

    A fagen adabin Hausa, musamman na zamani, marubutan mata sun taka muhimmiyar rawa wajen isar da saƙonnin da suka shafi rayuwa, tarbiyya, da matsayin mata a cikin al’umma. Ɗaya daga cikin fitattun marubutan nan ita ce Talatu Wada Ahmed, wadda rubuce-rubucenta suka yi tasiri matuƙa wajen gina tunanin matasa da wayar da kan al’umma game da darajar tarbiyya, ‘yanci, da ilimi.

    Wannan takarda na nazari ne kan yadda rubuce-rubucen Talatu Wada Ahmed suka ba da gudunmawa wajen inganta tarbiyya ta fuskar ilimi da halaye a tsakanin matasa, musamman mata.

    Tarihin Talatu Wada Ahmed

    Talatu Wada Ahmed an haife ta ne a shekara ta 1966 a ƙauyen Gaurawa da ke Jihar Katsina. Ta yi karatun farko da na sakandare a garuruwan Katsina kafin ta wuce zuwa Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), inda ta kammala digiri a fannin ilimi.

    Talatu Wada Ahmed tana daga cikin marubutan farko mata a arewacin Najeriya da suka fara rubuta littattafan soyayya da suka ɗauki jigogi masu ƙarfi na tarbiyya, ilimi da ‘yancin mata. Rubuce-rubucenta sun taimaka wajen kafa tubalin da marubutan mata suka bi, musamman a tsakanin shekarun 1980 zuwa 1990.

    Jigogin Rubuce-Rubucenta

    Rubuce-rubucen Talatu Wada Ahmed sun fi mayar da hankali ne kan batutuwan da suka shafi tarbiyya, soyayya, da matsalolin zamantakewa. Littafinta mafi shahara, ‘Rabin Raina’, ya nuna yadda mace ke da ikon yin zaɓi a cikin rayuwarta ta aure da soyayya.

    Wannan jigo yana nuni da tarbiyya ta zamantakewa da kuma buƙatar inganta fahimtar mace a cikin al’umma. Bugu da ƙari, rubuce-rubucenta suna da manufar ilmantarwa da inganta tunani, domin suna amfani da labarai wajen koyar da halaye nagari, gaskiya, da mutuntawa.

    Gudunmawar Rubuce-Rubucenta ga Tarbiyya

    Rubuce-rubucen Talatu Wada Ahmed sun taka muhimmiyar rawa wajen gina tarbiyyar matasa ta hanyoyi da dama.

    • Na farko, ta yi amfani da labarinta wajen nuna muhimmancin ilimi ga mace, ta yadda mace za ta fahimci darajar kanta da kuma rawar da take takawa a ci gaban al’umma.
    • Na biyu, ta ƙarfafa girmama iyaye da bin dokokin addini a cikin labaran nata.
    • Na uku, ta yi kira ga zaman lafiya, juriya, da fahimtar juna tsakanin ma’aurata da al’umma baki ɗaya.

    Waɗannan saƙonni suna nuni da cewa rubuce-rubucenta suna koyar da halaye na gaskiya, amana, da mutunci waɗanda su ne ginshiƙan tarbiyya.

    Littafin Ina Son Sa Haka ya nuna cewa tattaunawa kan soyayya, aure da rayuwar matasa ba kawai don nishaɗi ba ne, har ma don gina tarbiyya. Ta hanyar labaranta, Balaraba Ramat Yakubu ta zama malamar tarbiyya ta hanyar adabi – tana koyar da gaskiya, ilimi, da gyaran halaye cikin salo mai sauƙi da jan hankali a taƙaitaccen darasi.

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga maƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

    Danna nan don karanta Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Ado Ahmad Gidan Dabino

    Edita@rumasau-kallamu

  • Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Ado Ahmad Gidan Dabino

    Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Ado Ahmad Gidan Dabino

    Gabatarwa

    Ado Ahmad Gidan Dabino yana daga cikin fitattun marubutan Hausa na zamani, waɗanda suka ba da gudunmawa wajen ilmantarwa da tarbiyyar al’umma ta hanyar rubuce-rubuce. Ayyukansa suna ɗauke da saƙonni masu cike da darussa na rayuwa, da koyar da kyawawan ɗabi’u musamman ga matasa da mata.

    Ado Ahmad Gidan Dabino a Taƙaice

    An haifi Ado Ahmad Gidan Dabino a Kano, kuma ya shahara wajen rubuta littattafan soyayya, zamantakewa da addini. Yana ɗaya daga cikin masu kafa “Soyayya Books” a cikin shekarun 1980s zuwa 1990s. Sannan kuma ya shugabanci ANA. Wato ƙungiyar Marubuta Nijeriya. Daga cikin sanannun littattafansa akwai:

    • In Da So Da Ƙauna
    • In Da Ruwan Zuma
    • Malam Zalimu

    Koyar da Tarbiyya a cikin Rubuce-rubucensa

    Tarbiyyar Addini

    A cikin littattafan Gidan Dabino, ana samun koyar da imanin Musulunci, ibada, da gujewa haramci.

    Misali:

    • A cikin Malam Zalimu, ya nuna muhimmancin amincin kasuwanci.
    • A wasu daga cikin rubuce rubucucensa, ya nuna sakamakon zinar aure da rashin kunya.

    Tarbiyyar lyali da Aure

    Ayyukansa suna koyar da yadda aure ya kamata ya kasance bisa so, fahimta, da mutunta juna.

    Littafin In Da So Da Kauna ya bayyana cewa so ba ya wuce gona da iri, dole ne a daidaita tsakanin soyayya da tarbiyya.

    Tarbiyyar Matasa

    Marubucin ya yi nuni da yadda matasa ke fuskantar ƙalubale na zamani, kamar shaye- shaye, bin duniya, da son hawa-hawa. Ya gargaɗi matasa cewa su mai da hankali kan ilimi da gaskiya.

    Tarbiyyar Zamantakewa

    Ado Gidan Dabino yana amfani da labaransa wajen koyar da al’umma muhimmancin:

    • Hakuri da juriya a rayuwa
    • Girmama manya
    • Girmama mata da iyaye
    • Guje wa zalunci da ƙeta da kuma amfanin haɗin kai

    Salon Koyarwarsa

    • Yana amfani da labarai masu jan hankali, amma a ƙarshe yana gargaɗi ne da nasiha.
    • Yana ɗora saƙon tarbiyya cikin maganganun jarumai a cikin labaransa.
    • Yana haɗa adabi da addini domin isar da saƙo cikin natsuwa.

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga maƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

    Danna nan don karanta Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Bilkisu Ahmad Funtuwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Koyar Da Tarbiyya A Cikin Littattafan Yusuf M. Adamu

    Koyar Da Tarbiyya A Cikin Littattafan Yusuf M. Adamu

    Gabatarwa

    Yusuf M. Adamu yana daga cikin manyan marubutan Hausa na zamani da suka yi fice wajen rubuce-rubucen adabin ilimi, tunani da tarbiyya. Rubuce-rubucensa suna ɗauke da saƙonni masu zurfi da suka shafi rayuwa, ilimi, addini, da halin ɗan Adam. Ya yi amfani da adabi a matsayin hanya ta gyaran halaye da tunani musamman ta fuskar tarbiyya.

    Taƙaitaccen Tarihin Yusuf M. Adamu

    An haifi Yusuf M. Adamu a Kano a shekarar 1968. Malami ne, marubuci, kuma masanin kimiyyar ɗan Adam da muhalli (Geography). Ya rubuta labarai, gajerun labarai, da waƙoƙi masu  dauke da darussa. Daga cikin sanannun littattafansa akwai:

    • Idan So Cuta ne
    • Ummul-Khairi

    Tarbiyyar Addini

    Ayyukan Yusuf Adamu sun nuna muhimmancin bin dokokin Allah da guje wa haramci. Misalai:

    • A cikin littafin Ummul-Khairi, ya bayyana irin goyon bayan da iyaye ke ba wa ‘ya’yansu a bin hanyar Allah.
    • A Idan So Cuta ne, ya nuna illolin son zuciya da rashin haƙuri, yana koyar da cewa komai nufi ne na Allah. Wato dogaro da Allah Jari, wato a taƙaice dai haƙuri.

    Tarbiyyar Zamantakewa

    Yusuf Adamu yana nuna muhimmancin girmama mutane, gaskiya, da adalci. Yana nuna cewa mutunci da amana su ne ginshiƙin zaman lafiya.

    Ya koyar da mu’amala mai kyau tsakanin maza da mata, manya da ƙanana.

    Tarbiyyar Iyali

    Yana ba da muhimmanci sosai ga dangantakar aure da tarbiyyar gida.

    • A Idan So Cuta ne, ya nuna cewa aure ba wasa ba ne, kuma ya kamata ya kasance bisa gaskiya da jituwa.
    • Ya gargadi matasa kan auren dole ko auren soyayya ba tare da an yi hankali ba,

    Tarbiyyar Ilimi Da Aiki

    Ayyukan Yusuf Adamu suna ƙarfafa:

    • Neman ilimi a matsayin hanya ta ceto al’umma daga jahilci.
    • Aiki tuƙuru da gaskiya, a maimakon neman riba ta hanyar yaudara.
    • Ya nuna cewa ilimi da tarbiyya su ne ginshiƙin ci gaban al’umma.

    Tarbiyyar Matasa

    A cikin labaransa, Yusuf Adamu yana jaddada cewa matasa su guji bin son rai, su zama masu hangen nesa, su kuma zama abin koyi ga al’umma.

    Yana sukar:

    • Shaye-shaye
    • Rashin biyayya
    • Rashin mutunci

    Sannan kuma yaba wa:

    • Neman ilimi
    • Girmama iyaye
    • Taimakon al’umma

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga maƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

    Danna nan don karanta Yanayin Littattafan Ƙagaggun Labarai Da Suke Koyar Da Tarbiyya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wasu Laƙanin Sunayen Hausawa A Al’adun Gargajiya 3

    Wasu Laƙanin Sunayen Hausawa A Al’adun Gargajiya 3

    102.Tatu
    103.Talatu
    104.Lanti
    105.Lantana
    (102, 103, 104, 105 duk ma’anarsu ɗaya)

    106.Tanko (Mati, Mato)
    107.Talle
    108.Tallafi (alle)
    109.Tasallah
    110.Tabari

    111.Taningo
    112.Turai
    113.Tambai (namiji/mace)
    114.Tambari
    115.Uwani

    116.Uwale
    117. Abambu (115,116,117 ɗaya ne)
    128.Goggo
    129.Inna
    130.Yalwa. Yalwati
    131. Yawale ko Mijinywa

    TSATSON HAIHUWA.

    1.Kaka
    2.Uba
    3.Ɗa
    4.Jika
    5.Tattaɓa- Kunne
    6.Taka-kusheyi
    7.Tankaɗen hannu
    8.Unhun!!!!!

    FASIHIN KAITA

    Karanta Wasu Laƙanin Sunayen Hausawa A Al’adun Gargajiya 2

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Biyu

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Biyu

    Ba a fi sati ɗaya da kwashe kayan Khadeeja ba Naja ta saka Mustapha a gaba sai da ya sake fentin saman aka gyara ta kwashe kayanta ta koma. Yaran kuma gaba ɗaya ta tattaro su ta dawo da su ƙasa tare da masu aikinta guda biyu. Ɗakinta da parlor ɗinta nan ta mayar ɗakinsu Afaf, suna ji suna gani babu yanda suka iya.

    Shi kanshi Mustapha abun bai yi masa daɗi ba amma ya kasa magana; yana matuƙar mamakin abinda yasa ba ya iya hana Naja abinda take so a ‘yan kwanakin nan. Cikinta yana cika wata tara ta sake haifar ‘yarta mace, haka ta dage ta shirya taron suna fiye ma da wanda ta shirya a haihuwar Rukayya. Aka sakawa yarinyar suna Maryam.

    Washegarin suna su Anti Wiyya da sauran dangi suka soye naman suna suka gyara komai, sannan suka tafi suka bar Anti Wiyya ita kaɗai wadda za ta ƙara kwana biyu saboda taya ta jego. Tana zaune a parlor ɗin sama Anti Wiyya ta shigo da sallama, bayan ta amsa ta ƙarasa ta zauna a kusa da ita sannan tace ‘Wannan mai wankin naki gaskiya ya iya wulaƙanci, sai da ya fuskanci ana taro sannan ya gudu.

    Ni dai wallahi ko kayan sakawa gobe ba ni da su duk sun yi datti, ga shi duk jikina ciwo yake balle na zage na wanke kuma ‘yar aikinki ma dai ta fi ni gajiya. ‘Ai mai wankin nan ya yi wa kansa, in sha Allahu gobe Abban Rukayya zai samo mana wani mai wankin kowa ya huta.’ Ta faɗa tana gyara zama.

    Anti Wiyya tace ‘Don ma dai ‘yayanki ba sa moruwa ne in banda haka ga Habib can a ƙasa yana wanki ai da ko kala ɗaya ne ya wanke min. Ta gyara zama ‘Au ai ban san ma yana gidan ba kwaso kayan duka bari na kirawo shi zai wanke miki yanzu. Ba tare da ɓata lokaci ba ta juya ta koma ƙasa inda ta kwaso kayan nata yayin da ita kuma Naja ta ƙwalawa Afaf kira ta saka ta ta turo Habib.

    Kusan a lokaci guda suka isa parlor ɗin, shi ya tsaya daga a bakin ƙofa yayin da ita kuma ta ƙarasa ta zube kayan a gaban Naja. Yana daga tsaye a bakin ƙofa yace ‘Anti ga ni.’ Tace ‘Mai wanki ya kwana biyu ba ya zuwa, ka kwashi kayan nan ka wankewa Anti. Ya kalli kayan ya kalle ta yanda take muzurai; ba wai ba ta saba yi masa hakan ba ne, ta riga ta saba musamman tun bayan da Khadeeja ta bar gidan.

    Kawai dai ya kan yi mata abinda zai iya wanda ba zai yi ba kuma ya bar mata kayanta. Ya sake kallon kayan yace ‘Ah ku bar shi dai yanzu zan fita sai na samo muku wanda zai wanke ku biya shi. Har ya juya ya fara tafiya tace ‘Kana nufin ba za ka wanke ba ko me.’ Ya dan dawo ya kalle ta ya kalli kayan, har ya buɗe baki zai yi magana kuma sai ya fasa, ya fice ya barta nan a zaune da kayan.

    A fusace ta miƙe tana huci, kafin ta yi magana Anti Wiyya tace ‘Ai na gaya miki waɗannan yaran ba sa moruwa. ‘Ni ka tafi ka bari ina magana ko Habib? Saboda ka ga ni ba uwarka ba ce kuma ba khadeeja ba ce ko? Saboda ba a isa a saka aiki ka yi ba ko? To wallahi bari Abban naku ya dawo, sai dai ko ni ko kai a gidan nan don idan dai ba zan more ka ba sai dai ka bar gidan wallahi.’

    Wiyya tace ‘Ah to, yaron da bana jin ya haura sha takwas ya dinga yi miki irin wannan rainin, wannan nan da ‘yan shekaru ai sai ya kai miki duka. ‘Wallahi bari ubanshi ya dawo, dole ya bar min gidan nan idan ba haka ba ni na bar masa gidan. Idan ma Khadeejan ce take zuga shi ta janyo masa. Haka Wiyya ta sakata a gaba ta ƙara zuge ta kafin ya dawo.

    Ana idar da sallar Magriba ya shiga gidan, Habib ne ya buɗe masa gate tare da Baba maigadi ya yi masa sannu da zuwa sai dai bai raka shi har cikin gidan ba. Kamar yanda ya saba a parlor ɗin ƙasa ya sami yaran suna zaune suna kallon TV, bayan ya amsa sannu da zuwansu ya wuce sama.

    Da da ne Nasreen da Shukra sai sun raka shi har ɗakinsa, sai dai yanzu saboda yanda Naja take yawan korarsu tana nuna musu su dinga tsayawa a ƙasa ya sa sun haƙura, haka ya haye shi kaɗai zuciyarsa babu daɗi; saboda shi ma yana kewar wannan rakiyar. A ɗakinsa ya same ta tana ta cika tana batsewa, domin ko sannu da zuwa haka ta yi masa tana ta faman zumɓura baki.

    Bayan ya amsa yace ‘Me ya faru ne naga kina ta wani ɓata rai? Ta sake haɗe rai sannan tace ‘Ya za a yi a gidan nan a ce ban isa na saka Habib aiki ya yi ba? A gaban kowa zan ce Habib ya yi aiki amma kai tsaye ya ce min ba zai yi ba? Ai ba haka yake yi wa Maman Hammad ba, ko da yake na ji suna cewa yana zuwa wajenta ban sani ba ko ita ce take zuga shi ya dinga yi min rashin kunya.’

    Ya ajiye jakarsa ya zauna a kan kujerar gaba mudubi ya fara cire takalmansa yana cewa ‘Kada ki saka Khadeeja a cikin wannan maganar, da za ta sa wani ya yi miki rashin kunya da tun tana nan za ta saka su. Habib ɗin me kika ce ya yi ya ƙi yi? ‘Wankin kayansa yake yi shi ne na kirawo shi na ba shi kayan Anti Wiyya kala ɗaya nace ya taimaka ya wanke mata amma yaron nan ya ƙi, kuma yana kallo mai wankin namu ya gudu.

    Ita ce ta ke ta fama kula da gidan kayanta duk sun yi datti amma a gabanta Habib ya ce ba zai wanke mata kala ɗaya ba don wulaƙanci don ya nuna mata ban isa ba. Ya miƙe ya cire kayansa yana cewa ‘Ki ɗauko kayan idan na fito zan ba shi ya wanke in ya so zan gayawa Baba Maigadi ya zagaya nan makarantar almajirai ya samo yaro a wajen malaminsu wanda zai dinga zuwa yana wankin.’

    Kafin tace wani abu ya shige banɗaki. Ta zumɓura baki ta ja tsaki don ba haka ta so ba, so take a yi masifa ta sami damar da za a ce Habib ya bar gidan. In ya so sai ta san yanda za ta yi da Afaf, tana gamawa da waɗannan biyun ta san gidan ya zama nata, musamman da yake Shukra ita matsoraciya ce duk yanda ma aka juya ta haka take yi.

    Jimawa kaɗan ya fito ya sake kaya sannan ya wuce ya zauna a dining table ya fara cin abinci. Yana cikin cin abincin ya ɗauki waya ya kirawo Habib, ba tare da ɓata lokaci ba ya hawo ya same shi. ‘Abba gani.’ Ya faɗa yana tsaye daga gefe. Ya ajiye cokalin da yake hannunsa sannan yace ‘Habib me yasa Antinka ta saka ka wanki ka ƙi yi?’

    Yace ‘Abba ba ƙin yi na yi ba, wankin ne da yawa kuma nace gobe zan samo musu yaro ya wanke a biya shi. ‘Kala ɗayan ne da yawa? Kayan ma da ba nawa ba ne.’ Ta faɗa tana wasu muzurai. Yace ‘Ni dai kayan da aka ba ni za su kai kamar kala biyar ko fiye, ban sani ba ko ba su aka nuna maka ba.’

    Abbansu yace ‘Ka ga Malam, ba na son wani ƙarin bayani. An ce kaya kala ɗaya ne kuma gobe ake so a yi amfani da su. Ka je a ba ka kayan ka wanke yanzu in ba so kake ranka ya ɓaci ba, kuma daga yau ba na son a saka ka aiki ka dinga ƙin yi. Ba zan ɗauki taurin kai da rashin kunya ba. Ya buɗe baki zai yi magana sai kuma ya fasa, ya juya ya fice.

    Ya dubi Najan yace ‘Ki je ki ce mata ta ba shi kayan ya wanke. Ta tashi ta fice. Yana zaune a tsakar gida wajen Baba maigadi Shukra ta je ta kirawo shi. Yana shigowa ya ci karo da wankin a zube a bakin ƙofa; tabbas wankin sun fi kala biyar. Yana shiga cikin parlor ɗin kafin ya yi magana Naja da take tsaye tace ‘Gasu nan ka je ka wanke, kuma wallahi idan ba su fita ba sakewa za ka yi har sai sun fita.’

    Ta juya ta haye sama ta bar su a nan shi da ƙannensa. Ya juya ya dawo ya tsaya a kan wankin yana ƙare musu kallo yana tunani; tabbas ba zai yi wankin nan ba, ko da kuwa kala ɗayan ta bayar kamar yanda tace. Kuma yanda ya ga a gaban Abban tace kala ɗaya ne kuma ta ɗauko kaya da yawa haka ta ba shi ya san ta shirya wata maƙarƙashiyar.

    Ya san ba lallai Abbanshi ya saurare shi ba saboda tana gabansa tana tsara masa zance, kuma ya san idan har ya yi wannan wankin to ta sami damar da za ta mayar da shi ɗan aikin gida kuma ba zai yi ba. Haka ya kewaye ya fice ya bar wankin a nan inda ta ajiye su. Suna sama ita da maigidan suna ta hirarsu cikin kwanciyar hankali, sai waje ƙarfe tara sannan Anti Wiyya ta fito daga ɗakin baƙi ta ga wankin.

    Ta yi matuƙar mamaki musamman da ta tambayi Afaf ta tabbatar mata Habib ɗin ya fice bai ɗauki wankin ba. Nan ta koma ɗaki ta kirawo Naja a waya wadda ta sauko, ta nuna mata wankin sannan ta yi mata bayanin cewa a nan ya fice ya bar su.Yaran suna kallo ta tsuguna ta tsince kayan ta bar kala ɗaya da hijab guda ɗaya sannan Anti Wiyyan ta koma ɗaki ita kuma ta haye sama.

    Jimawa kaɗan Mustapha ya sauko yana tambayar Afaf ina ƙaninta. ‘Abba ban ganshi ba, ficewa kawai ya yi ba tare da yace komai ba.’ Ta ba shi amsa. A fusace ya murɗa ƙofar ɗakin Habib ɗin ya shiga yana kiransa, sai dai ga mamakinsa Habib ɗin ba ya cikin ɗakin. Ya fice wajen Baba Maigadi inda ya tabbatar masa bai san inda Habib yake ba, ya ƙara da cewa ‘Bana jin ma fita ya yi, don tun da aka ce ya zo kana kiransa ban sake ganin gilmawarsa ba.

    Sai dai ko da ina sallah ne ya fice ban sani ba. Ya koma cikin gidan ba tare da yace komai ba. Yana shiga parlor ɗin ya dubi kayan yace ‘Nasreen zo ki kwashi kayan nan ki mayar mata, yayan naki zai zo ya same ni. Ya haye saman inda ya tarar da Naja a zaune a parlor ita da Rukayya, ya sami waje ya zauna sannan ya ɗauki wayarsa ya dannawa Habib kira.

    Ba ƙaramin mamaki ya yi ba da ya ji wayar Habib ɗin a kashe, sai dai ya yi tunanin kashe wayar Habib ɗin ya yi don ya san ba shi da gaskiya. Don haka sai kawai ya sauko ya sanar da Baba Maigadi cewa idan Habib ya shigo gidan ya yi masa waya. Tun yana sa ran shigowar Habib har abun ya fara ba shi tsoro; yaran duk sun tafi sun kwanta har sha biyun dare ta yi amma Habib bai shigo gidan ba, ga shi sai kiran wayarsa ake yi a kashe.

    Yana son ya kirawo Hajia ko Habib ɗin ya je can amma kuma ba ya son ya ɗaga musu hankali. To ina Habib zai shiga? A karo na babu iyaka motsin shigarsa ɗakin ne ya farkar da ita daga bacci, ta gyarawa Baby Maryam kwanciyarta sannan ta dube shi tace ‘Wai bai dawo ba. A jigace yace ‘Eh, wallahi har abun ya fara ba ni tsoro. To ina Habib zai tafi?

    Ina ma ya sani a garin nan shi da ba wani yawo yake ba? Tace ‘Ya za ka ce ina ya sani yaron da yake level 1, kuma yake tafiya makaranta da kansa. Ai yanzu ba kamar da ba ne, tsaf ya san ko ina. To ina zai tafi a wannan daren? Ga shi Baba Maigadi ma yace ko fitarsa bai gani ba kuma gidan nan babu inda ba mu duba ba baya nan.’

    Tace ‘To ka dai yi hakuri ka zo ka kwanta tunda ka ga yanzu ɗayan dare ta kusa, zuwa wayewar gari sai a nemo shi a ba shi haƙuri a gaya masa ya bar wankin. ‘Mtseww! Wai kin san me kike faɗa kuwa? Na zo na kwanta saboda ke kin kwanta ko? Ya sake jan tsaki sannan ya fice daga ɗakin ya rufe mata ƙofar da ƙarfi, rufe ƙofar da sai da ya farkar mata da Baby daga barci.

    Ta juya a fusace tana gunguni ta ɗauki yarinyarta ta saka mata nono. Yanda ya ga rana haka ya ga dare, yana zaune a parlor shi kaɗai. Sai dai idan bacci ya ɗauke shi ya yi firgigit ya farka, ya sake buga lambar Habib amma a kashe. Yana fara jin kiran sallar asuba ya kirawo Alhaji ya sanar da shi ba a ga Habib ba.

    A shirye ya fice masallaci, bayan an idar da sallar asuba ya sanar da su ɓacewar habib. Yana dawowa gidan ya ɗauki mukullin motarsa ya fice ya nufi gidan Hajia. Su ma a tsaye ya same su cikin tashin hankali, nan suka zauna suna jira gari ya ƙara wayewa su je police station su sanar. Suna zaune a parlor ɗin Alhaji cikin tashin hankali Hajia ta dubi Mustapha tace ‘Kuma ka tuntubi kakanninsa, can gidan su Ma’u da ma ita Khadeejan ko wajensu ya tafi?’

    Ya gyara zama yana cewa ‘Khadeeja dai na tambaye ta ita ma ba ta ganshi ba, amma gidan mama ma ni na manta da su. Bari na kirawo su na ji. Kafin ya gama laluben lambar suka jiyo bugun ƙofa, gaba ɗayansu suka nufi ƙofar saboda Alhaji ya ba da sanarwa a masallaci ya yi zaton ko an sami wani labari ne. Ga mamakinsu Kawu Auwal ne wato ƙanin Ma’u tare da Habib ɗin.

    Suna haɗa ido Mustapha ya kai masa duka yana cewa ‘Shi ne za ka fice ba tare da ka gayawa mutane ba saboda raini ko? Alhaji yace ‘Ka bar shi mana ya zauna ya yi bayani.’ Suka ƙarasa cikin gidan suka zauna a parlor ɗin Alhaji. Bayan sun gaggaisa Kawu Auwalu yace ‘Wallahi ni ma da asuba Mama ta kirawo ni tace na zo na dawo da shi, ita ma ta yi zaton an san yana gidan shi yasa ma ba ta nemi kowa ba.

    Sai ɗazu bayan sallar asuba Antinsa Khadeeja ta kirawo ta tana cigiyarsa. Shi ne ta kirawo ni tace na kawo shi nan na yi bayani. Alhaji ya yi masa godiya sannan ya dubu Habib yace ‘Mutumina ya haka kuma? Me suka yi maka a gidan da za ka bi dare ka gudu? Kuma madadin ka zo ka gaya min sai ka tafi ka ɗagawa Mama hankali.’

    A nan ne ya sami dama ya gayawa Alhaji abinda ya faru, sannan ya sanar da shi irin zaman da ake yi a gidan. Hajia tace ‘Dama Aminan Jidda ta faɗa, tace wancan zuwan da suka yi gidan ba su ma ga Najan ba. Kamar yaran suna ƙasa su da mai aiki suna rayuwarsu ita kuma tana sama ita da nata yaran, kuma yanda ya faɗa haka Aminan ta faɗa tace shi kanshi Mustaphan yaran ba sa ganinshi sai dai idan ya sauko.’

    Shi ma Auwalu ya tabbatar musu da cewa duk waɗannan maganganu yaran sun daɗe da yi wa Mama bayani, sai dai da yake ta ɗauka ba huruminta ba ne shi yasa ma ba ta ce komai ba. Amma dai gaskiya da akwai matsala, tunda ai da ba a taɓa samun matsala irin wannan ba. ‘Haka ne, in sha Allahu za a duba kuma a ɗauki mataki.’ Alhaji ya faɗa.

    Suka ƙarasa tattaunawa Auwalu ya yi musu sallama ya tafi. Shi ma Mustapha ya miƙe ya sa Habib a gaba don su tafi, sai dai shi Habib ɗin ya nuna ba zai koma don ya fi so ya zauna a nan wajen Hajia. Alhaji ne ya saka shi a gaba da nasiha yana nuna masa gara ya zauna saboda ƙannensa, kada ya tafi ya barsu su kuma bai san me zai faru da su ba.

    Sai wajen ƙarfe tara sannan Hajia ta shirya suka kama hanya tare da Habib ɗin da Mustapha suka koma gidan. A cikin tashin hankali suka sami yaran, Nasreen da Shukra suna sanye da uniform ɗinsu; don sai da suka fara shirin makaranta sannan Naja ta sauko ta sanar da su ba za su makaranta ba Habib ya ɓata Abbansu kuma ya tafi nemansa.

    Babu wanda ya ji shigowarsu gidan saboda Mustapha a waje ya ajiye motarsa saboda Hajia tace yanzu za ta fito ya mayar da ita. Da sallama suka shiga parlor ɗin, Nasreen ce da Shukra suna zaune a parlor ɗin da flask ɗin shayi a gabansu da ƙaton bread. Sai dai sun kasa shan shayin sun yi tsuru-tsuru. Da gudu suka miƙe, Shukra ta faɗa jikin Habib tana dariya yayin da Nasreen ta matsa kusa da Hajia. Suka ƙarasa ciki suka zauna.

    Hajia tace ‘Ina Afaf? Nasreen tace ‘Tana ɗakinmu. ‘Antin fa da Rukayya? Nasreen ce ta sake sunkuyar da kai tace ‘Ba su sauko ba. Hajia tace ‘To ki je ki kirawo min ita ki ce ta zo. Shukra tace ‘Yanzu fa ta leƙo kuma tace kada wanda ya hau mata sama ya dame ta, ko menene a jira sai ta sauko. Hajia ta jijjiga kai, ta kalli Mustapha.

    Ya ɗan diririce sannan yace ‘Hajia tasowa za ki yi mu je saman ai. Ba tare da wani musu ba ta miƙe ta tasa Nasreen da Shukra a gaba tana biye da su yayin da Mustapha da Habib suke biye da ita. Anti Wiyya ce a zaune a kan kafet da kwanuka a gabanta suna cin abinci ita da Rukayya, yayin da Naja take zaune a kan kujera tana cin nata abincin suna hira.

    Da yake kicin a buɗe yake ana hango mai aikinta da goyon baby tana goge-goge. Shukra ce ta fara shiga tana surutu don haka a fusace Anti Wiyya tace ‘To sarkin tsurku, ba cewa aka yi ku zauna a ƙasan ba shi ne kika shigo kina….’ A lokaci guda kuma Naja tace ‘Ai sai na yi maganin wannan yar… Sallamar Hajia ce ta katse musu zantukan, ta ƙarasa ciki yayin da Shukra ta zagaye ta koma bayan Abbanta.

    Suka ƙarasa ciki suka zauna yayin da Naja da Wiyya suka diririce. Naja ta yi wuf ta miƙe ta kwashi kwanukanta tana cewa ‘Bari na wanko hannu.’ Ta nufi kicin cikin sauri. Ita ma Wiyya ta kwashi nata kwanukan ta miƙe tana cewa ‘Sannu da zuwa Hajia, bari na kawo miki abinci. Rukayya tace ‘Anti ban ƙoshi da naman ba.’ Ba ta ko saurare ta ba ta wuce kichin yayin da ita kuma ta tashi ta bi bayanta da sauri.

    Sai dai duk saurinsu kowa ya riga ya ga abinda yake cikin kwanukan nasu; farfesun kaji ne wanda suke haɗawa da burodi da shayi suna ci. Bayan sun zauna Hajia ta dubi Mustapha sannan ta dubi Nasreen tace ‘Nas ku ina naku naman na ga kuna cin gayan burodin. Ta yi darya tace ‘Ba a bamu ba, dama kullum abincin sama daban da na ƙasa har gara ma idan Abban yana nan.’

    Hajia ta sake kallo shi tace ‘Allah ya sauwaƙe. Naja ce ta dawo parlor ɗin ta zauna a kan kafet ta gaida Hajia, bayan ta amsa ta dubi Nasreen tace ‘Je ki kicin ki taya Anti Wiyya ta ɗauko wa su Hajia abinci. Hajia ta ɗaga hannu tace ‘Ki ce ta bar shi, ku bar shi ma, abincin da na ga bai isa an raba da yara ba ai ba zai isa har a ba wa baƙo ba. Ni na ci abincina ku bar shi na ƙoshi.’

    ‘A a Hajia ai akwai, su ma hawowa ne ba su yi ba nake jira Jummai ta gama wanke-wanke ta miƙa musu. ‘To me za su shigo su yi, su da za ki yi maganinsu. Ai sai dai kawai a cigaba da addua kada a wayi gari kin koro su daga gidan kamar yanda kika koro ɗan uwansu cikin dare.’ Hajia ta ba ta amsa.

    ‘Wallahi Hajia babu wanda ya koro shi. ‘Allah ne kawai zai gane gaskiya, amma dai ke ki ji tsoron Allah. Kin ba ni kunya, wallahi kin ba ni kunya! Ban taɓa zaton haka daga gareki ba. Gaba ɗaya mun zata zuwanki gidan nan zai sa yaran nan su sami kulawa ta musamman ashe ba haka ba ne. Ke da ‘yauwarki da ‘yayanki kuna sama kuna cin kaji yaran suna ƙasa suna fama da burodi.

    Kuma ma har sharaɗi aka kafa musu cewa kada su hawo su dame ki. Kamar dai ba gidan ubansu ba. Suka yi shiru kamar ruwa ya cinye su. Hajia ce ta karya shirun ta dubi Mustapha tace ‘Kai dai ba ka kyauta ba, yanzu rayuwar da kuke yi kenan? Su waɗannan da uwarsu ta mutu kun bar su a ƙasa kuna sama kuna jin dadi. To ka ji tsoron Allah. Ke ma kuma ki ji tsoron Allah.

    Bana jin sun taɓa ganin haka a wajen Khadeeja, ashe dama jira kike ku kore ta daga gidan ki cuzgunawa marayun Allah. Ta sunkuyar da kai kamar wadda za ta dungura. Habib yace ‘Ai tunda suka dawo daga Saudiyya aka hana su hawowa nan, ɗakinsu ma da komai nasu ya koma ƙasa.’

    Hajia ta dubi Mustapha duba na takaici har sai da ya sunkuyar da kansa cike da kunya. Ta miƙe tana cewa ‘Ai shikenan, amma tabbas ba zan bar wannan zaluncin ba. Kuma ko da kin ga kamar kin yi nasara to Allah yana kallonku gaban ɗaya. Yaran su ma suka miƙe, Hajia ta dubi Mustapha wanda kunya ta hana shi miƙewa tace ‘Za ka samu ka mayar da ni gida ko sai ta ba ka izini?’

    Ya miƙe kamar wanda aka tsikara. Naja tace ‘Don Allah Hajia ki yi haƙuri. Wallahi ba haka abubuwan suke ba rashin fahimta kawai aka samu wallahi ana kula da su. Ta dube ta tace ‘Allah ya sa, ai ni ma haka nake so. Sai dai kowa yayi don Allah ai ya sani ko, Allah kuma yana sane. Ta wuce yaran da Mustapha suka bi ta a baya suka fice.

    Har suka isa gida tana faman caccakar Mustapha a kan yanayin da ta gani a gidansa kuma tana tuna masa girman haƙƙin yaran nan a wuyansa da shi da matarsa. Ba shi da abinda zai gaya mata sai haƙuri kawai yake ba ta; shi ma ba ya jin daɗin yanda gidan ya koma tun bayan rabuwarsa da Khadeeja. Ba da son ranshi ba ta mayar da yara ƙasa kuma wannan raba abincin ya sha yin magana a kai.

    Amma ta iya abun ganin ido ne kawai, idan yana nan sai ta yi kamar komai normal amma da zarar ya fita sai ta tsawatarwa yaran kowa ya shiga hankalinsa. Abinci kuwa dama idan dai ba a gidan zai ci ba tabbas abincin da ake dafawa a sama daban kuma abincin da take ba wa mai aiki ta dafawa yaran daban ne. Duk wani daɗi a sama suke ci ita da yaranta da ‘yan uwanta su kansu yaran har sun saba.

    Ga shi ta hana su kula ubansu sosai, domin in dai yana saman nan ba ta barinsu su ganshi. Har sun gaji da yanda take musu sun haƙura sun ma daina cewa suna son magana da shi. Haka ya ƙarasa gidan ya ajiye Hajia a bakin gate ya dawo saboda ba ya son ya shiga ciki saboda ya san ba zai ji da daɗi ba a wajen Alhaji.

    Suna fita Anti Wiyya ta fito daga kitchen jiki a sanyaye, ta zauna kusa da Naja ta kama haɓa tana cewa ‘Ikon Allah, kin ji mutane ko? Ko motsin shigowarsu ba mu ji ba sai kace shiri. Ta taɓe baki ‘Hmmn! Su suka sani. Dama tafiya ya yi ya kai rahoto shi yasa ya bi dare su kuma ba su yi tunanin su kirawo mutane su sanar cewa ya isa can ba saboda sun shirya tsiya. A kansu zata ƙare in sha Allahu.’

    Ta miƙe kamar an tsikare ta tana cewa ‘Bari ki gani na haɗa kayana na bar gidan nan kafin ya dawo ya kore ni da kansa. ‘Haba Anti, saura sati biyu dama fa ki tafi tunda kin ce ba za ki yi min arba’in ba. Ki yi zamanki babu abinda zai yi.’ Ta faɗa tana gyara zama. Wallahi tafiya zan yi, da wanne idon zan kalle shi ya riga ya gama raina ni. Ina nan ina yagar kaza na bar masa yara suna fama da gayan burodi.’

    Ta marairaice ‘Anti idan kika tafi ma in ya dawo ai sai yace ba ni da gaskiya. Ta nufo ƙasa don haɗa kayanta tana cewa ‘Ku kwashe ƙalau amma ni da mijinki ba za mu sake haɗuwa ba in sha Allahu, ko a kwararo balle ma a gidansa. Tana ji tana gani Anti Wiyya ta fice ta bar mata gidan. Ba ta daɗe da fita ba Mustapha ya dawo.

    Yana shiga parlor ɗin ƙasa ya tarar da Afaf ta fito tana shan baƙin shayi da burodi yayinda sauran yaran suke zaune suna kallon TV. Bayan ya amsa sannu da zuwansu ya ƙarasa ya zauna a kusa da Shukra, ya kalli kofin shayin Afaf wanda ta ajiye a kusa da ita tana ƙoƙarin sake yago burodi. Yace ‘Ya kike shan baƙin shayi Yaya?’

    Tace ‘Um, babu madara a nan dama idan na yi canjin kuɗin makaranta ne nake siyo mana kuma yanzu ka ga ina hutu shi yasa ba ni da kuɗi. Takaici ya cika shi, yanzu da ransa da lafiyarsa madarar shayi a ce sai Afaf ta tara kuɗin makarantar da yake ba ta ta siya sannan za su sha. To wai ina kansa ya shiga hakan take faruwa a gidansa? Tunda yake a rayuwarsa bai taɓa ganin Khadeeja ta hana yaranshi wani abu da ya siyo ba, sai dai ma ya san lokutan da take sayen abu da kuɗinta su ci ita da yaran.

    To wai yaushe ma Khadeeja ta bar gidan? Ba a fi wata takwas ba fa da rabuwarsa da Khadeeja amma gidan duk ya zama haka? Ita da take zama cin abinci a tsakiyar yaran balle a ce ta ɓoye wani abu ta hana su. Ya bi fuskar yaran da kallo gaba ɗayansu babu wadda take da cikakkiyar walwala, tabbas yanzu ne za su ji nauyin maraicinsu.

    Shi kanshi sai ya ji ƙwalla tana neman kwace masa, sai da ya yi da gaske sannan ya mayar da ƙwallar. Ya dubi Nasreen yace ‘Nas ɗauko min kofi ni ma na sha shayin.’ Ta tashi ta shiga nan kichin ɗin ƙasan ta ɗauko masa tsohon kofin tangaran ta kawo masa da sugar a ‘yar roba. Ya kalli kofin duk ya dafe ya dubi Nasreen ɗin da ta ajiye kofin yace ‘Ki je sama ki dauko min wani kofin mai kyau.’

    Tace ‘Abba Anti Naja fa tace kada mu hau kuma wallahi idan na hau zagina za ta yi in na yi magana tace na mata rashin kunya, sai dai ko yaya Afaf ta je ta ɗauko. Haka ya karɓi kofin ba don ya so ba ya haɗa banƙin shayi ya sha tare da ragowar burodin da suke ci. Sai da ya gama sannan ya tashi ya haye sama domin ya shiryo ya fita aiki.

    Ta ji dawowarsa tunda ya shigo da motarsa, sai dai da ta ji shiru ta saka rai ya tsaya a wajen yaransa don ya ƙara jin abubuwan da za su gaya masa a game da ita. Don haka a parlor ya same ta tana ta cika tana batsewa ita a dole kada ya yi mata faɗa. A gajiye yake sannan ba shi da karsashin hayaniya da ita, don haka ko inda take bai kalla ba ya shige ɗaki ya fara shirinsa.

    A shirye tsaf ya fito ɗauke da jakarsa, tana nan zaune a inda ya bar ta. Ya ɗauke kai ya nufi ƙofa bayan ya amsa a dawo lafiyar da Rukayya ta yi masa. Ta miƙe ta nufo shi fuska babu walwala tana cewa ‘Ga abincinka can za ka fita ba ka yi breakfast ɗin ba. Ya kalle ta a fusace ba tare da ya daina tafiya ba yace ‘Abincin da kike hana yarana? Ni na ƙoshi ki kirawo ragowar ‘yan uwanki ku cinye.’

    Ta buɗe baki za ta yi magana sai dai kafin ta ce wani abu ya ci rabin ƙafar benen, tana nan tsaye kamar za ta haɗiyi zuciya ta jiyo ficewar motarsa daga gidan. Dole ita ma ta shirya ta fice ta tafi wajen aiki domin a hakan ma ta san sai an harare ta tunda ta makara.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Ɗaya

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Ɗaya

    Suna daga cikin na farko-farkon dawowa a alhazai. Tun kafin su baro masaukinsu ta gama magana da shi a kan ba za a ɗauko yara ba sai ta yi kwana biyar tana hutawa, don Rukayya ma tace kada a dawo da ita sai bayan sati biyu. Abokinsa ne ya ɗauko su daga airport ya kai su har gida, da yake ya saka Habib ya buɗe gidan an gyara tsaf suka sami ko ina.

    Da safe suka sauka don haka kafin su shiga gidan sai da suka yi order ɗin abincin rana. Sai can da yamma bayan sun gama hutawa sannan ya shirya ya wuce gidan Hajia. Nan ya zauna suka yita hira a wajen Hajia. Duk da ya gaya musu ba yau zai tafi da su ba amma Shukra ta kafe a kan ita a ranar take son ta bi su, don haka yace su shirya tare da su zai tafi.

    Sai bayan sallar magriba sannan Alhaji ya dawo, bayan sun gaisa suka cigaba da hirarrakinsu. Alhaji yace ‘Yauwa, ya wajen Khadeeja kuwa? Kun yi magana ne? Yace ‘A a ni ban neme ta ba kuma ba zan neme ta ba Allhaji, ita ce fa tace na sake ta kuma na saketan, ta je ta ɗana zaman gidan.’

    Alhaji ya ɗan ɓata rai yace ‘Kai! Ba a yi wa mata haka, idan jira kake ta neme ka to ba lallai ta neme ka ba gara ma ka je idan da wani abu ka yi wa iyayenta bayani su yi mata faɗa ka mayar da aurenta. Ya jijjiga kai ‘Alhaji ni ba inda zan je, idan tana son auren nata za ta neme ni tunda ai da kanta ta nemi sakin.’

    Haka Alhaji ya saka shi a gaba ya yi ta yi masa nasiha, daga baya ya yi musu sallama ya kwashi yaransa suka wuce. Ba shi kaɗai ba hatta yaran ma sai da suka gane ba ta ji daɗin dawowarsu a ranar ba, haka dai suka gaggaisa suka yi mata sannu zuwa kowa ya shiga harkarsa. Inda Allah ya taimake ta ma shi ne ya siyo musu abincin dare.

    Ta riga shi kwanciya saboda gaba ɗaya ba ta ma jin daɗin jikinta, sai da suka gama hira shi da yaransa sanan ya rufe gidan kowa ya tafi ya kwanta. Motsin shigarsa ɗaki shi ya tashe ta daga bacci, sai da ta bari ya gama shirinsa ya kwanta sannan ta gyara kwanciya tace ‘Kai da muka yi da kai ka bar yara sai mun huta shi ne ka taho da su?

    Ya gyara kwanciyarsa yace ‘To sun ce za su taho, su ma fa ba daɗin zaman suke ji ba a wani wajen kin san kowanne yaro ya fi son gidansu. Ta kula idan dai a kan yaransa ne ba zai saurare ta ba don haka ba tare da ta ce komai ba ta juya masa baya ta cigaba da baccinta; amma dai ta san tabbas dole ta ɗauki mataki don babu yanda za a yi ta bari ya kori kishiyarta kuma ya mayar da yaransa kishiyarta.

    Dole ta ɗauki mataki. Sai da ta yi sati da dawowa sanna ta je gidansu ta taho da Rukayya, don ko ‘yan gidan nasu ma da za su zo musu sannu da zuwa cewa ta yi kada a zo da ita don idan ta zo ba za ta yadda ta koma ba. Bayan ta gama hirarta a gidan ta wuce gidan Anti Wiyya.

    Nan suka zauna ta yi mata bayanin ayyukan da aka yi mata, sannan ta ba ta wasu layu guda biyu tace ‘Gasu nan hatimi ne aka rubuta da ayoyin Allah, ki sami waje ki ƙone su ƙurmus sai ki zuba masa tokar a miya. In dai ya sha miyar nan to ba zai sake yi miki musu ba. Wannan aikin bana haufinsa kamar yankan wuƙa ne sai dai idan ba ki aikata ba.

    Ta karɓa ta mayar cikin ledarsu ta kulle ta jefa a jaka tana cewa ‘Ai dai kin ce ayoyi ne ko? Tace ‘Wallahi ayoyi ne, ke malamin fa har almajirai gare shi suna karatun allo. Ai idan kin haihu za mu je ki gani da kanki idan har kina da wata matsala. ‘Hmm! Ai dole ma na yi Anti Wiyya, daga dawowarmu ya fara neman ya nuna min iyakata a kan yaransa, ga shi su baka isa ka saka su aikin komai ba sai dai kai ka ƙare a hidimarsu.

    Ai yau ɗin nan zan aikata wannan layun kowa ya shiga hankalinsa. Ko nan ma fa da zan taho shi so ya yi na taho da su wai saboda kada na bar su su kaɗai, ki ji don Allah sai kace wasu jarirai. ‘Ya zata ke ma Khadeejan ce. Suka yi dariya gaba ɗaya. Sai gefin magriba sannan ta ɗauko Rukayya suka dawo gidan. Tana zuwa ta ɗora abincin dare inda ta dafa tuwo miyar kuka.

    Tsaf ta haɗe tokar layun nan ta juye masa a miya ta juya komai ya shige, ta yi sa’a kuma ya sami tuwon nan ya yi masa cin ƙoshi. A hankali ta fara ganin kyawun aikin da Anti Wiyya ta yi mata. Cikin wata ɗaya da dawowarsu ta tattare kayanta ta koma sama part ɗinshi, ba ta son ta yi maganar part ɗin Khadeeja sai ta bari wata uku ya cika saboda kada ma ta tuna masa ya je ya dawo da ita.

    Yanzu ta samu idan suna sama shi da ita ta hana yaran hawa kuma ya kasa yi mata magana. Ta san bai ji daɗi ba don yana nuna mata a fuska amma wannan ba damuwarta ba ce, kuma idan shi ya zauna a ƙasan da zarar ta kirawo shi haka zai tashi ya bi bayanta su koma saman da shi da ita da Rukayya, sauran yaran suna ƙasa.

    Sai dare ya yi idan za su kwanta ne suke hawa saman da yake ɗakinsu yana can. Suna hawa sai ta kaɗa su su wuce ɗaki su kwanta. Tun ranar da ta koma gida take lissafi, duk da dai tana jini a lokacin amma dai sai da ta lissafa jini uku, kuma jiya ne ranar da ta fita daga jini na uku bayan rabuwarsu da Mustafa.

    Tana zaune a gefen ƙaramin gadonta wanda shi ne dai gadonta tun kafin ta auri Mustapha, ta rufe fuskarta da tafukan hannunta tana tunanin yanda rayuwarta za ta cigaba; tabbas ta ji daɗin rabuwa da Mustapha, ba ta yi nadama ba kuma ba za ta koma ba. Domin ko babu komai yanzu ne ta tabbatar tana cikin nutsuwa.

    Duk wani abu na kulawa da Hammad yake buƙata za ta iya yi masa don haka ba zama ta nemi Mustaphan da maganar Hammad ɗin ba saboda ma kada yace ta ba shi yaronsa. Fatan ta ɗaya Allah ya tabbatar mata da alkahiri a cikin rayuwarta ta nan gaba; duk da ba ta tunanin akwai namijin da za ta sake aure.

    Ba za ta yarda a sake yi mata yanda Mustapha yai mata ba kuma ba ta fatan ta zama dalilin da zai saka wani namijin ya mayar da matarsa kamar yanda Mustapha ya mayar da ita bayan ya ƙara aure. A hankali ta miƙe ta fito daga ɗakin. Ta ji daɗi da ta sami Baffa da Mommy a parlor suna zaune suna cin abinci. Bayan ta gaishe su ta dubi Baffa tace ‘Baffa ina so a debo min kayana na gidansu Hammad.’

    Ya ajiye cokalinsa yace ‘Ikon Allah, bai neme ki ba kenan? ‘Eh Baffa, duk da ma ko ya neme nin ba zan koma ba. Jiya ne na gama iddata ka ga auren ma ya ƙare kenan. ‘Haka ne, Allah ya sa haka ne ya fiye muku alkhairi gaba ɗayanku. Gobe sai ƙaninki ya shirya su je a kwaso miki kayan, ki yi masa bayanin abubuwan da za su kwaso. ‘To Baffa.’

    Mommy tace ‘To ya za a yi da Hammad? Ai dai ya kamata a yi magana da Mustaphan ya dinga turo abinda za a kula masa da yaron ko? Tace ‘Eh ba mu dai yi magana da shi ba, amma da bari na yi sai zai shiga makaranta tukunna. Baffa yace ‘A a tun yanzu zai ɗauki nauyin ɗan sa, ni zan neme shi in sha Allahu.’

    Mommy tace ‘Haka ne kam, ba sai daga baya ba a zo ana sa toka sa katsi. Suka ƙarasa hirarrakinsu sanna Khadeeja ta yi musu sallama ta tafi office. A mota suke tafe yana tuƙa su, zai sauke Naja a wajen aikinta sannan ya wuce. Wayarsa ce ta fara ringing, kusan a lokaci guda suka kalli screen ɗin wayar “Babe” shi ne sunan da ya yi saving lambar Khadeeja da shi tun kafin aurensu kuma rabuwarsu ma ba ta saka ya goge ba.

    To me ya mantar da shi Khadeeja ma da bai ko da kirawo ta a waya ba tun bayan dawowarsa daga aikin Hajji? Ko da yake ba mantawa ya yi ba jira yake ta kirawo shi ta ba shi hakuri idan ba haka ba ma ya ƙyale ta ta ɗanɗana zawarcin daga baya ya koma a sake ɗaura musu aure idan ta gane shayi ruwa ne. To menene take kiransa yanzun?

    Ko har zawarcin ya ishe ta ne? Wataƙila kuma ta ga tana daf da gama idda ne bai neme ta ba shi ne ita take nemansa ya zo a daidaita. Ya ɗauki wayar ya amsa sannan ya kara a kunnensa a daidai lokacin da ya kaucewa haɗa ido da Naja wadda take ta faman bin shi da kallo saboda ta san lambar wacece ya yi saving da sunan Babe.

    Babu wata alamar nadama ko kuma damuwa a muryarta, cike da walwalarta suka gaisa kamar babu wani abu na rashin daɗi da ya taɓa haɗa su. Bayan sun gaisa tace ‘Na gama idda jiya, so in sha Allahu idan babu damuwa gobe zan turo Ahmada za su zo su ɗebar min kaya na. kayan da suke bedroom ɗin kawai za a ɗauka tunda dama duk na sabon gida ne ka saka.

    Amma akwai food flasks ɗina a kitchen guda uku da kuma tea flask da za su haɗo min da su shikenan. Ina fatan babu wata damuwa. Sai da ya buɗe baki da niyyar ba ta amsa sannan ya gane yawun bakinsa ya riga ya ƙafe, ya kifta ido ya ɗan lalubo yawun bakin nasa sannan ya kalli Naja wadda take ta faman binsa da kallo kamar wata mayunwaciyar kura a yayin da ta hango nama yace ‘Ehhm, babu matsala. Um kin gama idda kenan?’

    ‘Eh, na gama jini uku a jiya. Idan ma an haɗa da jinin ɓarin da na yi jini huɗu kenan duka da shi kwana biyu ya yi ya ɗauke tun kafin sakin. ‘Oh haka ne, Allah ya kai mu, sai sun zo ɗin.’ Ya amsa. Da yake ranar aiki ce za su zo da wuri domin su same ka a gidan in sha Allahu.’ Ta faɗa sannan ta yi masa sallama ta ajiye wayarta.

    Ya mayar da tashi wayar ya ajiye a inda ya ɗauka ya mayar da hankalinsa ga hanya. Naja wadda take ta kallonsa tana jiran ya ba ta labarin abinda aka faɗa wayar ta gaji da kallonsa kuma bai yi alamar zai yi magana ba tace ‘Maman Hammad ce? A gajarce yace ‘Eh.’ Ba iya wannan amsar take son ji ba don haka tace ‘Wai menene?’

    Cikin yanayi na ƙosawa yace ‘Ta gama idda ne take so gobe da safe za a zo a kwasar mata kayanta. Ta gyara zama ta ɓata rai tana cewa ‘Ai na zata furnitures ɗin naka ne? A fusace yace ‘Eh, iya nata za a kwasar mata ai ko akwai naki a ciki ne kuma. Ta taɓe baki tace ‘A a, me ya yi zafi.’

    Daga haka har suka ƙarasa ya sauke ta babu wanda ya sake magana. Duk yanda ya so ya mayar da hankali a kan aikinsa hakan bai samu ba; zai iya cewa ba ya nadamar rabuwa da Khadeeja amma tabbas yau da ta gaya masa ta gama idda jikinsa ya yi sanyi. Zai yi kewarta, kuma ya ma ji a jikinsa kamar a gutsure wata tsoka daga jikinsa.

    Bai ma taɓa tunanin zai yi kewar Khadeeja haka ba amma ga shi kayanta kawai aka ce za a kwasa amma ya ji babu daɗi. Bai daɗe da shiga office ɗin ba ya lalubo wayarsa ya danna mata kira, kamar ɗazu yanzu ma muryarta cike take da walwala. Sosai ya kasa kunne yana ƙoƙarin ko gano wata alama ta damuwa a muryarta amma ji yake kamar ma an ƙarawa muryarta zaƙi.

    Bayan ta amsa sallamarsa tace ‘Um ka yi mantuwa ne? Kamar wanda aka farkar daga barci yace ‘No. Umm! Hammad fa? Ya kamata ya dawo cikin ‘yan uwanasa ai ko? A nutse tace ‘Eh haka ne, amma ka ga bai ƙarasa shekaru huɗu ba ma. Ina ganin nan da zuwa ya gama primary in sha Allahu sai ya dawo cikin ‘yan uwansa tunda tabbas ni na san kula da yaro akwai wahala, musamman da yake ka ga Antinsu ba zama take ba tana aikinta.

    Ina ganin ka bar min shi duk wani abu da yake buƙata in sha Allahu zan sanar maka, idan ya iya kula da kansa sai ya dawo gida. So yake ya ce mata hakan ba zai yiwu ba ko don ma ya ɓata mata rai, amma ya kasa. Tabbas yana son ganin yaronsa a kusa da shi cikin ‘yanuwansa amma kuma idan ya karɓe shi ba ya jin Naja za ta iya haɗawa da shi ta riƙe, don yanzun ma kullum cikin ƙorafi take a kan yara suna gajiyar da ita.

    Gara ma ya bari ta riƙe shi in Allah ya yi da ragowar zaman sa koma tare. ‘Um haka ne, to babu damuwa. Sai goben kenan. ‘Ok, Allah ya kai mu goben. Ba ta taɓa tsammanin Mustapha zai bar mata Hammad da sauƙi ba, don haka ma da ya yi saurin amincewa da maganarta sai ta ji wani daɗi marar misaltuwa; domin ta hango wahalar da zai sha idan ya koma gidan; zama zai yi kamar maraya.

    Tunda su Shukra su huɗu ne, Rukayya kuma uwarta tana gidan sai shi kaɗai wanda ba shi da uwa ba shi da ɗan uwa a gidan. A hankali ta mayar da wayar tata ta ajiye a kan teburinta. Ta sunkuyar da kanta ta share ƙwallar da ta taru a kwarmin idonta sannan ta zuba fuskarta a tafukan hannunta; ta tuno lokacin da suna soyayya da Mustapha kafin suyi aure. Wai ina soyayyar nan ta tafi ne?

    Ya barta ita kaɗai tana ta dakon soyayyarsa har tsawon shekaru takwas? Tabbas ta sha wahala a gidan Mustapha; ba wai wahalar jiki ba don wahalar jiki ta san abinda ta yi bai wuce abinda matar aure za ta yi ba. Sai dai wahalar zuciya da ta sha; kulawa da tausaya tare da ƙauna da zuciyarta take buƙata daga wajen Mustapha su ne ba ta samu ba.

    Ko su ɗin ma ta haƙra da su tana zama haka tunda ko babu komai tana kallonsa a matsayin mijinta kuma suna kwana tare. Amma daga lokacin da ya auro wata kuma ya ke ba ta kulawa da ƙauna wanda ita ya kasa ba ta daga lokacin ta yanke ƙauna daga zaman gidan Mustapha.

    Ba za ta ce ba ta jin zafin rabuwa da shi ba domin tabbas ta san ko babu ƙauna akwai sabo, amma tabbas ba za ta sake komawa gidan Mustapha ba. Domin ta yi sujjada ta roƙi Allah kada ya sake haɗa ta zaman aure da Mustapha. Da farko ta fara jin haushnsa amma daga baya sai ta ga jin haushin babu wani amfani; ko babu komai dole ta yi wa Hammad kara ta girmama mahaifinsa.

    Ta sake share ƙwallar da ta taru a kwarmin idonta, ta kalli ruwan hawayen da ta lakata a hannun nata; to kukan me take a halin yanzu? Ta zata ta gama kuka a kan Mustapha. Ta yi murmushi ta sake goge ƙwallarta; ta san ba za ta iya goge Mustapha daga cikin tarihin rayuwarta ba amma tabbas ba ta fatan sake rayuwa irin wadda ta yi a gidansa. Ta goge fuskarta ta fice ta nufi cikin studio inda za ta gabatar da labarai.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin

    Edita@rumasau-kallamu