Tag: yadda ake

  • Tarihin Dr. Magaji Ahmad Gaya (PhD)

    Tarihin Dr. Magaji Ahmad Gaya (PhD)

    An haifi Magaji Ahmad Gaya a garin Gaya da ke cikin jihar Kano 17 watan Janairu a sherarar 1974. Ya yi karatun addinin Musulunci a makarantar gidansu, wato makarantar Alaramma Malam Shehu da kuma wasu makarantu a unguwar Matamawa da ke garin Gaya, a makaranta Malam Isah, sannan kuma da makarantar Malam Shu’aibu Zai da ke a ƙaramar hukumar Dutse ta jihar Jigawa.

    Ya yi karatun Firamare a makarantar Dagara Firamare da ke garin Gaya, haka kuma ya yi karatu a makarantar horar da Malamai da ke dutse sannan ya kammala a makarantar horon Malamai ta Wudil a Shekarar 1990, inda ya kammala da takardar shedar malanta ta ɗaya (Grade II).

    Da ga nan kuma, ya halarci kwalejin ilimi ta Kumbotso wadda aka fi sani da (Sa’adatu Rimi college of Education Kumbotso) a shekarar 1995 inda ya sami takardar shedar malanta ta ƙasa (NCE). Ya ci gaba da karatu a jami’ar Bayero, inda ya yi digirinsa na farko wato (B.A. Hausa Special) a shekarar 2004.

    Ya sake komawa Jami’ar Bayero Kano inda ya yi karatun (PGD Hausa Studies) a shekarar 2008. Sannan ya koma Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sokoto ya yi karatun digirinsa na biyu (M.A. Hausa Ɓangaren Nazarin Al’adu) a shekarar 2018.

    Bayan nan ya ci gaba da karatun digirinsa na uku (PhD Hausa Ɓangaren Nazarin Al’adu) a Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’adua da ke garin Katsina, ya kammala a shekarar 2024. Haka kuma ya yi aikin koyarwa a wasu makarantun firamare da sakandare da kuma Kwalejin Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kumbotso.

    A halin yanzu yana koyarwa a Jami’ar Northwest, Kano Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya. Ya wallafa littattafai da maƙalu masu ɗimbin yawa. Yana da aure da ‘ya’ya masu albarka. Alhamdulillah.

    Karanta Sakamakon Bincike A Kan Wasan Ƙunshi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wasu Laƙanin Sunayen Hausawa A Al’adun Gargajiya 2

    Wasu Laƙanin Sunayen Hausawa A Al’adun Gargajiya 2

    51.Illo (Ilolo, Iro)
    52.Ilah
    53.Iro
    54.Inuwa
    55.Jumah,

    56. Jummai,
    57. Jimmah,
    58. Jumale (55, 56, 57, 58 duk ma’anarsu ɗaya)
    59.Dela, Delu, Dudu (56, 57, 58, 59 duk ma’anarsu ɗaya)
    60.Korau

    61. Magaji (korau)
    62. Kilishi (namiji/ mace)
    63.Kallah (Musa)
    64.Kawu
    65.Kulu (Hauwa’u)

    66.Kadarko (bayan Gambo)
    67.Lami
    68 Laminde (Lami)
    69.Ladi. Ladidi
    70.Laraba

    71.Larba
    72. Balaraba (Larba, Laraba)
    73. Lado
    74. Marka
    75. Maje

    76. Mati
    77. Mato
    78. Tanko (Mati, Mato)
    79. Mijinyawa
    80. Mantau (Tunau)

    81. Tunau
    82. Maiwada (Yalwa)
    83. Yalwa ( namiji/mace
    84. MaiDaura
    85. Maikaita

    86. Maikano
    87. Mowa
    88. Nadabo (Yusuf)
    89. Roro (Ci-wake)
    90. Rahwani

    91. Ramadan
    92. Shekarau
    93. Sha rubutu
    94. Sallau
    95. Bisallah (Sallau)

    96. Sambo
    97. Tabari (Sambo)
    98. Tari
    99. Tani
    100.Attine
    101.Tanungo (99, 100, 101 duk ma’anarsu ɗaya)

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Wasu Laƙanin Sunayen Hausawa A Al’adun Gargajiya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wasu Laƙanin Sunayen Hausawa A Al’adun Gargajiya

    Wasu Laƙanin Sunayen Hausawa A Al’adun Gargajiya

    1.Audi (namiji/mace)
    2.Auta (namiji/mace)
    3.Abba. Abbati. Abbe
    4.Abanbu

    5.Aruwa
    6.Asabe (Assibi, Gude)
    7.Alhaji
    8.Azumi

    9.Arzika. Arziki
    10.Bature
    11.Balarabe
    12.Balaraba

    13.Barau
    14.Bawa,
    15.Barmo,
    16.Bora

    17.Barmani
    18.Baiwa
    19.Bayi
    (17, 18, 19 duk ma’anarsu ɗaya)
    20.Baffa (Abba, Abbati, Babangida)

    21.Babangida
    22.Baturiya
    23. Ci wake
    24. Cibau

    25. Cindo
    26. Ɗanladi
    27. Ɗanlami
    28. ƊanTani

    29. Ɗanjuma
    30. Ɗan Assibi, Dan Asabe
    31. Ɗan Azumi
    32. Ɗari

    33. Dikko
    34. Delu
    35. Dudu
    36. Dela

    37. Kande
    (34, 35, 36, 37 duk ma’anarsu ɗaya)
    38.Bayi ( Ayashe, Bayye)
    39.Bute
    40.Yalwa

    41.Goshi
    (39, 40, 41 duk ma,anarsu daya)
    42.Damina
    43.Dago
    44.Gambo ( namiji/mace)

    45.Gwanda
    46.Gwamma
    47.Goshi
    48.Harande

    49.Hajiya
    50.Indo (kyabtin)

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Sunayen Abinci Ko Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 4

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin

    Ba ƙaramin mamaki Hajia da Alhaji suka yi ba da Mustapha ya gaya musu ya saki Khadeeja. Shi kaɗai ya shiga da yaran don ita Naja ma cewa ya yi ta zauna a mota saboda kada taɓbata musu lokaci. Suna shiga yaran suka wuce cikin gida shi da Hajia da Alhaji suka tsaya a parlor yana musu bayanin abinda ya faru.

    Alhaji yace ‘To kai wane irin rashin hankali ne wannan? Ai don mace tace a sake ta ba a sakin nata. Zuciya ce ta kwashe ta kuma sai daga baya za ta zo tana nadama. Da ka sani ka ba rta da aurenta idan ma tafiyar za ta yi ta tafi idan ka dawo ƙalau za ka ga ta dawo.’

    A fusace yace ‘Alhaji yarinyar ce ta ƙure ni, ita kullum sai dai a yi mata yanda take so amma ita ba za ta yi yanda ake so ba? Ta je idan mutuwar aure daɗi ne ai ta samu sai ta ɗana ta fi shiga hankalinta. Hajiya tace ‘Ai shikenan tunda haka ta zaɓa. To yanzu ina Hammad ɗin da Rukayya? Ban gansu tare da ‘yan uwansu ba.’

    ‘Shi Hammad dama yana gidansu, ita kuma Rukayya gidansu ta kai ta. Ai shikenan, Allah ya sauwaƙe. Idan ka dawo a san yanda za a yi domin dai aure bai kamata ya mutu saboda kujerar hajji ba.’ Alhaji ya faɗa cike da nadama. Mustapha ya dubi Hajia yace ‘Mukullin gida yana hannun Habib in an jima Baba Sani abokina zai zo ya kai su shi da Afaf su ɗebo kayansu su rufo gidan.

    Idan sun dawo sai ya ba wa Alhaji mukullin gidan ya ajiye min. Akwai ATM card ɗina hannun Afaf idan ana buƙatar wani abu na kuɗi sai ta je ta ciro ta bayar. Ya yi musu sallama ya fice zuciyarsa cike da damuwa.

    Zuciyarta fayau ta fito daga gidan tana addu’ar Allah ya sa iyakar zamanta kenan da Mustapha tunda ta san saki ɗaya ya yi mata. Suna tsaye a bakin titi ita da Hafsa suna jiran mota ya zo ya wuce su a guje a tashi motar. Ta bi bayan motar da kallo tana murmushi; ta tuna lokutan da yake zuwa ya wuce ta a titi za ta tafi makaranta amma ba zai iya rage mata hanya ba.

    Ta yi murmushi ta kawar da kai. Jimawa kaɗan da wucewarsu ta sami mota, suka hau suka nufi gidan Mommy. Tana tura gate ɗin gidan Baffa ne a tsaye yake rufe motarsa, da alama dawowarsa kenan. Suna haɗa ido da shi hawayen da ta kasa fitarwa ya ƙwace, ta saki akwatin da take ja.

    Ahmad wanda yake tsaye a kusa da shi ya ƙarasa ya riƙe akwatin yayin da ita kuma ta ƙarasa ta faɗa jikin Baffa wanda yake bin ta da kallon mamaki. Ya rungume ta sannan ya dafa kanta wanda ta kwantar a ƙirjinsa yana cewa ‘Subhanallahi! Me ya faru da ku Khadeeja? Ta kasa magana sai kuka kawai take har da shessheƙa.

    Baffa ya fara shafa bayanta yana cewa ‘Ya isa haka, ya isa, ki gaya min me ya faru? ‘Ya sake ni.’ Ta faɗa a cikin shessheƙar kuka kamar mai raɗa. Take fuskar Baffa ta canza, ranshi ya yi matuƙar ɓaci. Yace ‘Mustaphan ya sake ki? Ta ɗaga masa kai. Ya sake shafa kanta cikin yanayi na lallashi yana cewa ‘To shikenan, ya isa haka.’

    Ya ja hannunta suka shige gidan; da yake Mommy tana ɗakinsa kai tsaye can ya wuce da Khadeeja. Mommy tana ƙoƙarin yi masa sannu da zuwa ta kula da Khadeeja, tace ‘A a, Baffa a ina ka samo wannan? Ya zaunar da ita a gefen gadonsa yace ‘Mustapha ya sake ta. ‘Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un! Saki kuma? A yau ɗin? Na ɗauka ce min kika yi yau jirginsu zai tashi?’

    Ta share ragowar hawayenta ta ajiye jakar hannunta sannan tace ‘Eh, kafin su tafi airport ɗin ne ya sake ni saki ɗaya. Lallai Mustapha, to me kika yi masa ya sake ki? Ko kuwa dai tsabar wulaƙanci ne ya ga gara ya sake ki kafin ya wuce ya yi ibada?’ Mommy ta tambaya tana daga tsaye.

    Ba ta yi tunanin wata amsa da za ta bayar idan an yi mata wannan tambayar ba, amma dai tana jin gara ta faɗi gaskiya don ma kada ya zo shi ya ba da amsa da ta bambanta da tata. Ta ɗaga fuskarta suka haɗa ido da Mommy sannan ta sunkuyar da kai. Murya kasa-kasa tace ‘Ni nace ya sake ni.’

    Saura kaɗan wayar da take hannun Mommy ta kufce ta faɗi, ta riƙe wayar sannan tace ‘Kika ce ya sake ki Khadeeja? Saboda rashin hankali ko saboda me? Baffa da yake tsaye a gaban wardrobe ɗinsa yana rataye babbar rigarsa ya zagayo ya zauna a kusa da ita yana kallonta yace ‘Dije me yasa kika ce mijinki ya sake ki?’

    Kafin ta yi magana Mommy tace ‘Saboda wulaƙanci mana, ko kuma saboda yace ba zai je da ita aikin Hajji ba sai ya je da amaryarsa. Kallonta kawai Baffa ya yi ta yi shiru, ta gyara tsayuwarta tana binsu da kallo. Ya dubi Khadeejan ya sake cewa ‘Deeje me yasa kika ce mijinki ya sake ki?’

    Ta kalle shi suka haɗa ido sannan ta sake sunkuyar da kai tace ‘Baffa na gaji, wallahi Baffa ba ka ga zaman da muke yi a gidan nan ba. Tun kafin ya auri matarsa Baffa dama haƙuri nake, matsayina a gidan da kaɗan ya wuce matsayin ‘yar aiki. Kuma bayan ya auro ta ma ya kara tabbatar min da hakan; duk wani abu na walwala da jin daɗi da ita ake yi amma wallahi idan aiki ne da wahala Baffa ni zai kawowa kuma dole na yi.

    Ita kanta matar tasa haka yake saka ni na yi mata aiki babu sannu bare na gode. Shi yasa kwanaki da nace ba zan yi ba ya zo ya kawo maka ƙarata. Wallahi Baffa a lokacin sai da na yi wata takwas ina mata aikin gida da girki da komai kuma kullum shi a wajenta yake kwana.’Ta sake sunkuyar da kai ‘Na gaji Baffa, ba ya sona, wulaƙancin da yake min suna da yawa, gara na haƙura kawai shi yasa nace ya sake ni.’

    Ya kama hannunta wanda take wasa da shi a kan cinyarta ya kalle ta suka haɗa ido yace ‘To ya isa, kuka ya isa haka. Ki je ki kai kayanki ɗaki ki huta ma yi magana wani lokacin.’ Ta gyaɗa kai ta miƙe ta fice daga ɗakin. A fusace Mommy ta bi bayanta, cikin sauri Baffa yace ‘Zo mana.’

    Ta juyo a daidai lokacin da Khadeejan ta rufe ƙofa, ya nuna mata inda Khadeejan ta tashi ta zauna. Sai da ya ɗauki lokaci yana kallonta sannan yace ‘Ki bi ta a hankali tunda dai kin ji bayaninta. Ni da na ba shi aurenta ai ba ‘yar aiki na ba shi ba ko? In ya dawo ya zo ya yi bayani in ya so sai a san matakin da za a ɗauka.

    Shi a zaman aure ma wani lokacin hutu kawai mutum yake buƙata; kada ki je ki ɗaga mata hankali. Ki barta ta huta ƙarshenta in ya dawo sai dai ki ji da kanta tana gaya miki ya mayar da ita za ta koma. Da-Allah kada ki ɗaga mata hankali tunda dai ita ta kawo mutumin nan tace tana so ai ba laifi ba ne idan ta dawo tace bata son shi.

    Ki ba ta lokaci ta sami nutsuwa tukunna. Ta sauke numfashi sannan tace ‘To. Ta tashi ta fice ta bar shi a ɗakin. A nan gidan Hajia ya ajiye motarsa ya samar musu taxi wadda za ta kai su airport, ya shiga gaban mota ita kuma ta shiga baya. Suna kama hanya ta zaro wayarta ta lalubo lambar Anti Wiyya ta tura mata sako ta wahtsapp tana sanar da ita an saki Khadeeja.

    Bayan sun gama hirarrakinsu na murna da nuna jin daɗi Anti Wiyya ta turo mata saƙo kamar haka “Kije ki yi ta addu’a Allah ya sa kada kuna dawowa ya dawo da ita. Nan ma in sha Allah akwai wani malami da zan kai wa abin sadaka ya yi miki aikin da ba za ta taɓa dawowa gidan ba, kin ga kin ci gida se yanda kika yi.”

    Ta turo mata emoji na dariya ta rufe wayar, ta mayar da hankalinta kan hanya zuciyarta fes cike da fatan Allah ya sa kada ya dawo da Khadeeja tunda ya ce saki ɗaya ne; in ya so sai ta ji da yaran kawai. A hankali Khadeeja ta ba je kayanta a gida; ta sanar da Baffa ko da ya dawo ma ba za ta koma ba domin ko ya mayar da aurenta to kotu za ta kai shi ya sake ta.

    A haka dai aka bar maganar domin shi Baffa gani yake kamar idan aka ba ta lokaci ta huce za su yi wa kansu sulhu ita da shi. Tun Baffa yana sa rai zai ji kira daga wajen iyayen Mustapha sun biyo sawu har ya fitar da rai. Saura kwana biyu babbar sallah suna zaune a parlor shi da Mommy suna hira yace ‘Mutanen nan dai shiru, babu wanda ya biyo sawun Dije.

    Na san dai babu yanda za a yi su ce ba su san ya sake ta ba tunda ai za su ga ba ita ya barwa yaransa ko? ‘Uhm, ni abun har ya ishe ni ma wallahi. To amma ko tuntuɓarsu za ka yi ka ji, tunda ai ba za mu taru mu zama ɗaya ba ko?’ Mommy ta ba shi amsa. Ya yi ‘yar dariya yace ‘Babu wanda zan tuntuɓa tunda ai da zan ba su aurenta ba ni na tuntuɓe su ba su suka zo har gida suka tuntuɓe ni.

    Idan na tuntuɓe su haƙuri zan ba su ko me? Ni aka yi wa wulaƙanci aka saki ‘yata ko ma don wanne dalili ne amma kuma ni ake jira na yi magana? To su cigaba da zamansu kada ma su zo inda nake. A haka suka bar zance domin Mommy ta san in dai Baffa ne yanda ya kafe ba zai yi magana ba to tabbas ba zai yin ba.

    Su ma daga can gidansu Mustapha a tunaninsu Baffan Khadeeja ne ya kamata ya neme su don ya kamata idan ta je gida a bincika a ji, sai dai har aka shiga hidimar bikin sallah babu wanda ya neme su. Sai suka bar maganar kawai suna jiran Mustaphan ya dawo su ji ko shi ya yi magana da iyayen nata.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Tara

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yanayin Littattafan Ƙagaggun Labarai Da Suke Koyar Da Tarbiyya

    Yanayin Littattafan Ƙagaggun Labarai Da Suke Koyar Da Tarbiyya

    Akasari akan sami:

    a. Koyar da Darussa na Rayuwa

    Littattafan ƙagaggun labaran sukan koyar da ɗabi’u irin su gaskiya, haƙuri, da tsoron Allah. Galibi sukan nuna yadda mugunta ke kai mutum ga halaka, abin da ke zama darasi ga masu karatu.

    b. Ƙarfafa Tunani da Basira (Tarbiyya ta musulunci)

    Suna motsa tunanin matasa su zama masu hangen nesa da ƙirƙire-ƙirƙire wajen magance matsalolin rayuwa. Inda ake gane tarbiyya

    c. Ƙarfafa Soyayya da Haɗin Kai

    Labaran na nuna muhimmancin taimakon juna da zaman lafiya a cikin al’umma.

    d. Hana Mugunta da Laifi

    Ta hanyar nuna sakamakon laifuffuka kamar sata, ƙarya da cin hanci, matasa suna fahimtar illar yin haka.

    e. Ƙarfafa Sha’awar Ilimi

    Jarumai masu ilimi a cikin labarai sukan zama abin koyi ga matasa wajen neman ilimi.

    f. Adana Al’adu da Harshe

    Kagaggun labaran suna adana harshen Hausa da al’adunta ta hanyar karin magana da hikima.

    Bilkisu Ahmad Funtuwa

    Bilkisu Ahmad Funtuwa tana daga cikin fitattun marubatan Hausa mata da suka taka rawar gani wajen gina tunani da tarbiyya ta hanyar adabi. Rubuce-rubucenta suna ɗauke da darussa na addini, zamantakewa, aure, da rayuwar mata. Ta yi amfani da labarai domin koyar da ɗabi’a, adalci, da darajar mace a cikin al’umma.

    Takaitaccen Tarihin Bilkisu Ahmad Funtuwa

    An haifi Bilkisu Ahmad Funtuwa a Funtua, jihar Katsina, kuma ta shahara a fagen rubutun littattafan soyayya, zamantakewa da ilimi. Marubuciya ce mai kishin addini da al’adun Hausa, wacce ke amfani da rubuce-rubucenta wajen gyaran halayen matasa da mata.

    Daga cikin shahararrun littattafanta akwai:

    – Wa Ya San Gobe

    – Allura Cikin Ruwa

    – Wa Ya San Jiki

    – Rabon Juna

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga muƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

    Danna nan don karanta Adabin Kasuwa A Ƙasar Hausa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Sakamakon Bincike A Kan Wasan Ƙunshi

    Sakamakon Bincike A Kan Wasan Ƙunshi

    Wannan bincike wanda aka gudanar, an yi amfani da hira da ziyar gani da ido da shiga cikin masu aiwatar da wasan inda ya binciko wasu bayanai masu matuƙar muhimmanci wajen gudumowar da suka bayar game da adana da bunƙasa tarihi da al’adun gargajiya na Hausawa musamman na Arewacin Nijeriya.

    Sakamakon binciken takardar ta gano cewa, wasan ƙunshi wasa ne da yake ƙara haɗa kan matasa musamman samari da ‘yan mata na kusa da na nesa, wanda hakan yana samar da soyayya ta ƙullu har a samu zamantakewar aure a tsakani.

    Sannan takardar ta gano cewa, wasa ne da ake aiwatarwa sau ɗaya a shekara, wannan ya haifar da son kowa lokacin ya zo domin aiwatar da shi tare da kashe kwarkwatar idanunsa.

    Haka kuma, takardar ta gano ce har zuwa wannan lokaci ana aiwatar da shi, duk kasancewar akwai tasirin zamani kamar karatun addini musamman zuwa makaranta allo da islamiya sannan kuma da makarantar boko, wanda waɗannan suna taimaka wajen dusashewar wasan ba kamar yadda ake gudanar da shi a baya ba.

    Sannan takardar ta nazarci yadda wasan yake ƙara ƙulla zumunta da son juna Samar da zumunci a tsakanin al’umma da ƙara danƙon zumunta a tsakanin al’umma da ilimantar da jama’a kan zamantakewa da raya al’adun Hausawa na gargajiya da bunƙasa tattalin arziƙin a tsakanin al’umma.

    Takarda ta gano masu aiwatar da wasan sukan yaɗa tare da watsa wasan kai tsaye ta amfani da hanyoyi isar da saƙo na zamani ciki da wajen ƙasar nan. Wanda yin hakan ya taimaka gaya wajen sanin wasan da kuma masu bibiyarsa. Haka waɗanda ba su sami damar halarta ba bisa wasu dalilai su ma ba a bar su a baya ba.

    Daga ƙarshe binciken ya gano cewa, wasa ne na gargajiya da ake aiwatar da shi tsawon lokaci mai nisan domin babu wanda zai ce ga lokacin da aka fara shi, sai dai a bisa hasashe.

    Kammalawa

    A cikin wannan takarda da aka aiwatar, an yi taƙaitaccen bayanin game da ma’anar wasa da kuma wasannin gargajiya a ƙasar Gaya, sai kuma aka yi bayani a kan wasan ƙunshi da yadda ake aiwatar da shi da masu gudanar da wasan da rana haɗi da lokacin da ake gudanar da shi a ƙasar Gaya, da ke Jihar Kano.

    Har wayau, takardar ta fito wasu hanyoyi da ake bi wajen sanarwa da sadarwa haɗi da shirye-shirye gudanar da tanade-tanade wasan, an kuma yi bayanin masu aiwatar da shi, da kuma bayanin yadda ake gudanar da wasan a jiya. Haka kuma ta fito tare da bayani yadda ake aiwatar da wasan a yau tare da kawo yadda zamani ya yi tasiri a cikinsa. Kazalika takarda ta fito da muhimmmanci wasan yake ɗauke da shi, wasa ne da ya ke bunƙasa zumunci da tattalin arziƙi da kuma adana tarihi.

    Manazarta

    Alhassan, H. da Wasu, (1982). Zaman Hausawa. Bugu na Biyu. Zaria: Institute of Education, Ahmadu Bello University.

    Bunza, A.M. (2006) Gadon Feɗe Al’ada. Lagos: Tiwal Nigeria Limited.

    Bunza, D.B. (2016) “Taubashi Bahaushe: Wani Mashigi Na tantance Asalinsa Da Zuriyarsa”. Kaduna: A Cikin The Hausa People, Language And History Past, and Present and Future. Department of Nigerian Languages and Linguistics. Faculty of Arts, Kaduna State University. Garkuwa Publishing Ltd.

    Ɗangambo, A. (2008) Rabe-Raben Adabin Hausa. Kano: (Sabon Tsari) Amana Publishers Ltd, No. 1166 Sabon Gari Market.

    Ibrahim, M.S. (1982). “Dangantakar Al’ada da Addini: Tasirin Musulunci Kan Rayuwar Hausawa.” Kundin Digiri na Biyu. Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

    Gaya, M.A. (2018). “Keɓaɓɓun Wasannin Hausawa na Gargajiya a Ƙasar Gaya.” Kundin Digiri na Biyu, Sakkwato: Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo.

    Magaji, A. (2002). “Wasu Al’adun Hausawa Yanaye-Yanayensu a Ƙasar Katsina.” Kundin Digiri Na Uku, Kano: Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

    Sa’id, B. da Wasu (2006). Ƙamusun Hausa. Kano: Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Zaria: Ahmadu Bello University Press.

    Wanan bayanin an ciro shi ne daga maƙala mai taken Nazarin Wasan Ƙunshi Jiya Da Yau A Ƙasar Gaya wadda Magaji Ahmad Gaya Ph.D Sashen koyar da Hausa Jami’ar Northwest, Kano ya wallafa.

    Emai: magaya@nwu.edu.ng

    08066009039

    Danna nan don karanta Wasan Ƙunshi A Yau

    Edita@rumasau-kallamu

  • Sunayen Abinci Ko Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 4

    Sunayen Abinci Ko Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 4

    111.Ɗan gauta
    112.Daskasmi
    123.Ɗan gajera
    124.Ɗan sululu
    125.Ɗan bidis

    126.Ɗan boris
    127.Dubulan
    128.Gyaɗa kuriga
    129.Gurbiya
    130.Gyaɗa Amaro

    131.Hanjin Ligidi
    132.Kuɓewa
    133.Kanya
    134.Lubiya
    135.Loga

    136.Maɗi
    137.Muruci
    138.Miyar kuka
    139.Kafi kaza
    140.Shash-shaka

    141.Wake (fari)
    142.Wake (Ja)
    143.Waken Soya
    144.Kwakwameti
    145.Yalon Bello

    146.Goro
    147.Ƙosai (Are)
    148.Yaddo
    149.’Yar fako
    150 Tamatsitsi
    Da sauran su.

    FASIHIN KAITA

    Karanta Sunayen Abinci Da Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 3

    Edita@rumasau-kallamu

  • Sunayen Abinci Da Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 3

    Sunayen Abinci Da Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 3

    71.Kantun nome
    72.Nono
    73.Rabeh
    74.Rummace
    75.Ramah

    76.Soɓo
    77.Sabulun salo
    78.Tabso
    79.Taka- yaga
    80.Tabshe/Taushe

    81.Taura
    82.Tubani.
    83.Tukuɗi
    84.Tumu
    85.Tsaba

    86.Tuwo (gero, dawa, acca, masara, shinkafa)
    87.Talunguba
    88.Tuwon ruwa.
    89.Ungududu
    90.Wake

    91.Waina (gero, masara, shinkafa)
    92.Yaɗiya
    93.Yalo
    94.Yakuwa
    95.’Yar kumbu

    96.Kwalshi, kwalo, tantalibo
    97.Aya
    98.Gudun kurna
    99.Ɗorowa
    100.Zure

    101.Zogale
    102.Zumah
    103. Gwanda
    104.Gwaba
    105.Faru

    106.Fara
    107.Tabar Malan
    108 (ƙuli-ƙuli, guru, buriji)
    109.Aduwa
    110.Tsaba-da-wake

    FASIHIN KAITA

    Karanta Sunayen Abinci Da Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 2

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Tara

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Tara

    Shirye-shiryen tafiya aikin Hajji sun kankama domin ana maganar saura sati uku alhazai su fara tashi. Duk wani abu da suke buƙata na kula da gida Mustapha ya tanada ya kawo musu, kuma ya yi mata bayanin abokinsa wanda dama ta san shi; shi ne zai kawo musu raguna kuma ya tsaya a yanka.

    Yanzu kullum sai yamma ta yi sai ya ɗauki Najan a mota su fice wai sun tafi bita, haka ta zuba musu ido tana ta ba wa kanta haƙuri. Gaba ɗaya maganar tafiyar ta fita daga ran Khadeeja, kuma Mustaphan ma gaba ɗaya ya fice mata daga rai; ji take yi kamar matsayinta a wajensa bai wuce na mai aiki ba.

    Zuwa yanzu ta san wanda ma bai san halin da suke ciki ba ya san Naja tana da ciki domin tara yawunta ya ƙaru kuma ta yi fari tas irin na masu ciki. Sai dai har yanzu ita Khadeejan ba ta sanar da Mustapha cewa ta san Najan tana da ciki ba. Sai shirye-shiryensa yake yi yana zuwa sallama da mutane domin Hajia ta gama gayawa kaf dangi Mustapha zai tafi Hajji da matarsa.

    Danginsa da na Naja sai zuwa suke sallama, duk wanda ya zo sai ya cewa Khadeeja Allah ya kirawo ‘yan baya. Wannan kalmar ba ƙaramin ɓata mata rai take yi ba, amma haka ta share ta kawar da kai. Tun jiya ba ta jin daɗi sai dai ba ta gane me yake damunta ba, haka take ta fama. Da yake ba ita ce da aiki ba kuma Hammad baya nan haka ta wuni a kwance.

    Daf da magriba ta fara gane abinda yake damunta; mararta ce take ciwo ga wani amai da yake taso mata amma ya ƙi fitowa. Haka ta sha panadol ta shige ɗakinta ta kwanta. Wajen 9pm Mustaphan ya shigo ɗakin domin sanar da ita ya dawo kamar yanda ya saba. Har ya juya zai fita ya ɗan tsaya yace ‘Wai ya na ganki a kwance ne? kamar ba ki da lafiya.’

    ‘Uhm, mara tace take ɗan ciwo.’ Ta amsa a gajiye. ‘Ok, Allah ya sauwaƙe. Ko kina buƙatar wani abu? Tace ‘No ina jin zai daina don na ma sha panadol. Ya sake yi mata sannu sannan ya juya ya fice. Can wajen 10:30pm ciwon ya matsa mata, tun tana daurewa har ta kasa. Ta lalubi wayarta ta kirawo shi, ba tare da ɓata lokaci ba ya shigo ɗakin nata.

    Kafin ya shigo ma ta riga ta shige banɗaki saboda yanda take jin kamar za ta yi kashi, kafin ta ƙarasa toilet ɗin abinda yake shirin fitowa daga jikinta ya riga ya fito sai jini da ya biyo baya gaba ɗaya da aman da ya tokare mata ƙirji. A tsugune ya same ta a banɗakin, ya ƙarasa da sauri ya duba halin da take ciki. Ya kama ta ta miƙe sannan ta ƙarasa ta zauna a kan toilet.

    Tace ya jira ta ta wanke jikinta sai su je asibiti. Nan da nan ta wanke jiki ta gyara sannan ta tattare zanin nata da bainda ya fita daga cikin nata gaba ɗaya ta saka a leda sannan ta fito ta shirya suka kama hanyar asibiti. Babu wanda ya yi magana sai shi da yake mata sannu lokaci zuwa lokaci; a haka har suka isa asibitin.

    Ba tare da ɓata lokaci ba likita ya duba ta kuma ya tabbatar da cewa cikin jikinta ya fice gaba ɗaya, don ko wankin ciki ma ba sai an yi mata saboda komai ya fice. Aka rubuta mata magunguna aka sallame su. Tun a mota ta gane Mustapha bai ji daɗin zubewar cikin ba, duk da ita ta fi shishiga damuwa da zubewar cikin; amma dai ta kula ba haka ya yi ba wancan lokacin da ta yi ɓari.

    Har yanzu tana jin ciwon mara don haka ba za ta iya surutu ba. Bayan sun dawo gida ta haye samanta ta sake yin wanka sannan ta sha magungunanta ta saka Hafsa ta haɗa mata indomie da shayi mai kauri ta zauna ta ci. Sai da ta ci ta ƙoshi sannan ta kirawo Mommy da Yaya Mama ta sanar da su.

    A daren Momy ta so zuwa sai da Khadeejan ta hana ta ta sanar da ita cewa ta sami lafiya su bari da safe sa zo; don haka suka haƙura. Can wajen ɗaya saura ya same ta a ɗakin; tana kwance a gefen gado tana shirin yin bacci. Ya zauna a gefenta yace ‘Sannu. ‘Yauwa. Ta amsa tana daga kwance.

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, ta san da zance a bakinsa don haka ta yi kasaƙe tana jiran ta ji me zai ce. Jimawa kaɗan ya gyara zama kamar wani mara gaskiya yace ‘Um wai ni me ya faru ne? Me ya kawo wannan miscarriage ɗin? Ko wani abun kika sha ne? Ta yi ‘yar dariya tace ‘Babu abinda na sha, Allah ne dai ya kawo kamar yanda ya kawo wancan.’

    Ya ɗan yi jim yace ‘Allah ya sauwaƙe. Ya sake yi mata sannu sannan bayan ya tabbatar babu abinda take buƙata sannan ya fice ya bar ta. Washe gari tun da safe Mommy da Yaya Mama suka zo, nan suka zauna suka zube mata kayan dubiyar da Baffa ya aiko mata. Mommy ta ji daɗi yanda ta ganta ta riga ta miƙe kamar ma ba daren jiya ta yi ɓari ba, sai kai wa da kawowarta take yi ana hira da ita.

    Har sun fara shirin tafiya suna zaune Yaya Mama tace ‘Kin ga idan dai ciki ne zai sa a fasa tafiya da ke ai yanzu sai a ba ki kujerarki ko. Ta yi dariya tace ‘Dama kujera ba tawa ba ce, babu ruwan ciki niyyar ba ni ne ba a yi ba. Mommy ta dafa ta tana ɗan zare ido tace ‘Khadeeja in ce ko dai ba wani abu kika sha kika fitar da cikin nan ba saboda kujerar Makka.’

    Ta ɗan zaro ido ta kalle ta suka haɗa ido tace ‘Mommy! Me ya yi min zafi? Wallahi babu abinda na sha, sai kace wata marar hankali? Ai na gaya miki fa ba ciki ne ya sa ba zai ba ni kujerar ba kawai haka ya yi niyya, yanzu kuma ɓarewar cikin ba za ta sa ya fasa tafiya da ita ba. Ni ce kawai ba za shi da ni ba. Yaya Mama tace ‘Haba Mommy, a kan wata kujera za ta ɓarar da ciki?

    Ta gyara zama ‘To ai abun naku ne sai a hankali. Suka ƙarasa hirarrakinsu suka yi mata sallama suka kama hanya. Ta zauna tana tunanin dalilin da yasa Momy za ta yi wannan tunanin; to ko tunanin da Mustapha ma ya yi kenan yake tambayarta me ya faru bayan sun dawo daga asibiti? Allah ya gani babu abinda ta sha, cikin nan ma ba ta taɓa kawo masa zubewa ba kuma ko da wasa ba ta so hakan ba.

    Kawai dai Allah ya yi ikonsa ne kamar yanda ya yi a wancan karon, kuma ta san shi ne zai fitar da ita daga duk wani zargi da zai iya tasowa. Kujerar Makka ma idan dai Mustapha ne zai ba ta kam ba ta so ta san Allah zai hore mata ta je tunda ita ma tana kan neman kudinta.

    Can da yamma su Hajia suka shigo ita da Yaya Jidda da ‘yan matanta. Ba ta san da Hajia suka shigo ba don haka ta yi banza da su tunda ta jiyo su a wajen Naja. Jimawa kaɗan suka hawo saman gaba ɗaya; ta sauke su a nan parlor ɗinta ta kawo musu ruwa da lemo, suka zauna suka yi mata dubiya da jaje. Suna cikin hirarrakinsu Mustaphan shi ma ya shigo ya zauna aka cigaba da hirar yana sa musu baki lokaci zuwa lokaci.

    Yaya Jidda ta dube ta tace ‘Alhazai dai sun kusa tashi balle ma a ce za a canza a ba ki kujera tunda cikin da ya hana ya fice, ko ka canza ne Mustapha? Ya kalle ta sannan ya kalli Khadeejan yace ‘A a ai an gama wannan maganar, ita za ta zauna da yara idan Allah ya kai mu shekara mai zuwa sai a je da ita. Hajia tace ‘E ai an gama wannan maganar.

    Allah ya ba ki lafiya ya kawo wasu yaran masu albarka. Ita Najan sai su je kamar yanda aka tsara. Ita dai tana zaune a tsakiyarsu amma ba ta iya ce musu komai ba; to kenan su ma zarginta suke yi da zubar da cikin ko me? To me Mustaphan ya gaya musu har suke mata wannan zargin? Sai da suka gama hirarrakinsu sannan suka yi mata sallama suka tashi suka fice.

    Bayan sallar Magriba Mustaphan ya same ta a ɗakinta tana zaune a gefen gado, bayan ta amsa sallamarsa ya karasa ya zauna a gefenta. Ta yi masa sannu da zuwa ya amsa suka zauna suka ɗan yi shiru, jimawa kaɗan ya kirawo sunanta. Bayan ta amsa ya kakkafe ta da ido sannan yace ‘Wai ni me kika yi ne cikin nan ya zube, ko wani abun kika sha saboda ya zube mu tafi da ke aikin Hajji.’

    Ta yi ‘yar dariyar takaici sannan tace ‘Mustapha ban zubar da ciki ba, domin kujerarka ta maka ba ta isa ta saka ni na zubar da ciki ba. Kamar yanda Allah ya kawo wancan cikin ya zube ba tare da na yi wani abu ba wannan ɗinma hakan ce ta kasance. Yace ‘To ai kin ce wancan wahala ce da aiyuka suka yi miki yawa ya sa ya zube, ko ba haka kika ce ba? Wanna kuma na ga babu wannan ko?

    Ta gyara zama ita ma ta kakkafe shi da ido tace cikin zafin rai tace ‘Mustapha wai ba ka ji me nace ba; ban zubar da ciki ba kuma kujerar Makka ba ta isa ta sa ni na aikata hakan ba. Na riga na san ba ka yi niyyar zuwa da ni Hajj ba domin lokacin da kake cewa ina da ciki ba za ka je da ni ba ita ma Najan cikin ne da ita. Ka dai zaɓi matarka wadda kake so ka tafi da ita ni kuma ‘yar aikin gidanka ka bar ni na kular maka da gida da yara kamar yanda ka saba.

    Idan ma kai ne ka gayawa ‘yan uwanka wannan maganar har suke yar min da magana to ka koma ka gaya musu ƙarya ne. Ya miƙe a fusace ‘Daga an tambaye ki kuma shi ne za ki yi min rashi kunya kamar yanda kika saba saboda ke ba a gaya miki gaskiya ko? Wannene rashin kunyar a ciki; ganewa da na yi cewa ka yi rashin adalci wajen zaɓar matar da za ka je da ita hajji ko kuwa gaskiyar da na gaya maka?’

    ‘Mtsewwwww!’ Ya ja dogon tsaki ya miƙe a fusace ya fice daga ɗakin. Ta zuba fuskarta a tafukan hannayenta, so take hawayenta ya fita ko za ta samu ta ji sanyi a ranta amma hawayen ya bushe ƙyamas. Ƙirjinta har zafi yake saboda yanda zuciyarta take turiri; Mommy ce ta fara yi mata wannan zargin ga shi yanzu Mustaphan ma da shi da ‘yanuwansa suna zargin ta zubar da cikin ne don ya je da ita Hajji.

    Tabbas Allah sai ya bi mata haƙƙinta. Haka ta kwanta zuciyarta na mata zafi saboda takaici; ta so ta kirawo Mommy ta gaya mata ko za ta sami salama a ranta, to amma hakan ba zai yi mata wani amfani ba. Tunda Mommy ɗin ce ta fara yi mata wannan zargin. Ta sake fashewa da kukan takaici ta gyara kwanciyarta; yau ita ce da kwana amma ta san yanda Mustapha ya fice daga ɗakin nan wataƙila sai dai idan ya dawo daga aikin hajji sannan ya waiwaye ta.

    Ranar Laraba aka kirawo su Mustapha, jirginsu zai tashi ƙarfe biyar na yamma don haka aka ba su shawara su kasance a cikin airport ɗin tun kafin azahar. Sun gama haɗa kayansu shi da Najan kuma ya riga ya sanar da Khadeeja, ya danƙa mata duk wani abu da take buƙata don kula da gidan. Wajen ƙarfe sha ɗaya yana zaune a parlor ɗinsa shi da yara Khadeeja ta fito daga ɗakinta ta shige kitcen don ɗora abincin rana.

    Ya tsallake yaran ya bi bayanta ya tsaya daga ƙofar kitchen ɗin ya rungume hannuwansa a ƙirji sannan yace ‘Kada fa ki dafa abincin da ni yanzu za mu wuce airport, ki dafa ke da yara kawai. ‘To.’ Ta amsa murya ƙasa-ƙasa. Ya kula tunda suka yi maganar zubewar cikinta take son ta-da masa fitina shi kuma ba zai saurare ta ba, fata yake kawai Naja ta gama haɗa kayanta su fice su bar mata gidan kafin ta takalo rigima. Don haka ya juya ya koma cikin yara ya zauna.

    Har ta ɗauko tukunya za ta ɗora shinkafa sai kuma ta fasa, ta ajiye tukunyar ta fito daga kitchen ɗin ta koma ɗakinta. Tana shiga ta wuce gaban mudubi ta ja kujerar ta zauna; ba ta san me ya sa ta fasa ɗora girkin ta zo ta zauna ba. Kamar dai tana buƙatar wani wanda za su yi magana ne amma ta rasa wanda za ta gayawa damuwarta ya fahimce ta.

    Ta ɗaga fuskarta ta kalli kanta a cikin mudubin, ta yi wa kanta murmushi sannan ta sake sunkuyar da idanuwanta. Yanzu haka za ta cigaba da rayuwa a gidan nan a matsayin ‘yar aiki? Tunda matsayinta bai wuce hakan ba, duk wasu alamu sun nuna. Mustapha ya tabbatar mata ba zai taɓa iya yi mata adalci ba tun ma tana ita kaɗai matarsa balle yanzu da ya haɗata da wadda yake ƙauna.

    Ta sake daga ido ta kalli kanta a mudubin; to wai zaman me take a gidan Mustapha ne? Shi dai ya gama nuna mata ba zai taɓa canzawaba; duk wani abu da yake yi mata a halin yanzu za ta iya yi wa kanta. Buƙatar aure ce kawai wadda dama sai ya gama dama yake zuwa wajenta tunda ta daina bin shi ɗakinsa. Ta yanke ƙauna daga samun adalci a wajen Mustapha komai yawan ƙaunar da za ta nuna masa da kulawarta ga ‘yayansa.

    Ta tabbatar shi ba zai iya nuna mata ƙauna da kulawa ba; wataƙila sai dai idan ana ƙwatan soyayya ta ƙwata ta ƙarfin tsiya daga wajen Mustapha; to idan sai an ƙwata kuma ya koma ba so ba. Ta ja gwauron numfashi, ta zuba fuskarta a tafukan hannayenta, ɗumin hawayenta ne ya sa ta ɗaga fuskar tata ta kalli hawayen da ya ɗiga a hannuwanta.

    Ta jijjiga kai tana murmushi a lokacin da hawaye yake gangarewa a kumatunta; ta gaji, ba za ta iya ba, ta gaji da wannan kokawar, ta gaji da kokawar ƙwatowa kanta mutunci da so a wajen Mustapha, ta gaji ba za ta iya cigaba ba. Ta miƙe kamar wadda aka tsikara ta nufi gaban wardrobe, ta sauke akwati ta fara zuba kayanta. Ba za ta iya cigaba da wannan rayuwar ba, gara kawai a yi ta ta ƙare.

    A hankali ya turo ƙofar ɗakin ya shigo da sallama, fuskarta fayau kamar ma farinciki take. Ta dube shi ta amsa sallamarsa ta cigaba da jera kayanta a cikin akwatin. Ya dube ta da mamaki yace ‘Ya na ga kina haɗa kaya, ko wardrobe ɗin kike gyarawa? Ta ɗan tsaya da zuba kayan ta kalle shi tace ‘No ba gyarawa zan yi ba, gidan mu zan tafi.’

    Mamakinsa ya ƙaru, ya kasa matsawa kusa da ita ‘Ban gane gidanku za ki tafi ba bayan yanzu za mu tafi, shigowa ma na yi na gaya miki ki fito ku yi sallama da Naja za mu wuce. Ta rufe akwatin ta zuge sannan ta juya cikin wardrobe ɗin ta ɗauko jakarta ta sake ajiyewa a kan gadon. Ta kalle shi tace ‘Ka ba ni minti biyar na ƙarasa haɗa kayana na fita sai ka rufe gidan gaba ɗaya don ni ma gidanmu zan tafi.’

    Ya ɗan fara fusata ya matsa ya sha gabanta yana cewa ‘Ba na son wulaƙanci Khadeeja, wai ke me yasa ne duk lokacin da mutum yake cikin uzuri yake so ki yi masa wani abu sai kin yi fitina ne? An gama magana da ke amma yanzu saboda kina so ki sa mu yi missing flight za ki fara maganar za ki tafi gida. Ta yi murmushi ta ɗaga kai ta kalle shi tana cewa ‘In sha Allahu wannan ita ce fitina ta ƙarshe da zan yi maka Mustapha, daga ita ba zan sake ba.

    Gidanmu zan tafi Mustapha saboda na gaji da aurenka, kuma na gama aurenka daga yau. Za ka iya sakina yanzu ko kuma duk lokacin da ka sami natsuwa ka rubuta min takardar sakin ka aiko gida; amma ba zan sake zama a matsayin matarka ba. Gaba ɗaya yawun bakinsa ƙafewa ya yi saboda bai taɓa zaton Khadeeja za ta iya faɗa masa haka ba.

    Ya sake ta! Kuma a wannan lokacin; ya kalle ta ya sunkuyar da kai, jimawa kaɗan ya sake kallonta sannan yace ‘Saboda kujerar Makka kike so ki kashe aurenki Khadeeja? Kujerar da na gaya miki next year da ke za a tafi. Tukunna ma kin san hukuncin matar da ta nemi saki a wajen maigidanta ba tare da wani dalili ba?

    Ta jijjiga kai tana murmushi a daidai lokacin da ƙwalla ta faɗo daga idonta, ta share ƙwallar sannan tace ‘Ko ɗaya, kujerarka ba ta kai ta ɗaga min hankali ba tunda dai ƙasar Makka ta Allah ce ba taka ba. Alhamdulillahi ma kace wadda ta nemi saki ba tare da dalili ba; don ni ina da dalili kuma Allan da ya halicce ni ya fi ni sanin dalilin. Amma tabbas yau zan bar gidanka da aurenka Mustapha.

    Ya ja baya ya sake ƙare mata kallo, yace ‘Kin san me kike faɗa kuwa Khadeeja? Please idan wasa kike ki bari kada ki saka mu yi missing flight. Ta yi ‘yar dariya yayin da ta ware hijabinta ta saka tana cewa ‘Ba wasa nake ba, amma dai kana da zaɓi. Ka sake ni yanzu ko kuma ka tafi idan ka dawo ka rubuta min takardar ka aiko min gida.’

    Ta kewaye shi ta ɗauko jakarta daga kan gadon ta nufi gaban mudubi. Yana tsaye mamaki ya hana shi magana. Yana ɗaga kai idonsa ya sauka a kan agogon bangon yake kafe a saman ɗakin; 12:52pm agogon ya nuna; shi da aka cewa su zama suna cikin airport kafin azahar. ‘Mtseww!’ ya ja ɗan gajeran tsaki sannan ya fesar da iska daga bakinsa.

    ‘Khadeeja yanzu ya kike so na yi da yaran bayan mun gama magana da ke? Kuma me na yi miki da har za ki riƙe a matsayin hujjar da ta saka za ki ce na sake ki? Yara kam ai yanzu ba matsalata ba ne, duk yanda ka yi da su daidai ne. Ni dai zan tafi, yanzu in sha Allah. Ta sauke akwatinta ta fara ja tana nufin ƙofar ɗakin. Ya bi bayanta da kallo; to me ya yi mata da har za ta ce ya sake ta a wannan lokacin?

    Anya kuwa ta san menene zawarci? Kawai saboda baƙin cikin ba da ita zai fara tafiya aikin Hajji ba? Ko ma me take nufi ya kamata ya cika mata burinta, wataƙila kafin ya dawo ta dawo hayyacinta kuma ta gane mahimmancin aure a rayuwarta. In ya so idan ya dawo da ita sai ta haƙura ta zauna tunda dai shi bai ga wani abu da ya yi mata ba.

    Tana daf da ƙarasawa bakin ƙofar yace ‘Khadeeja. Ta juyo ta ɗan tsaya ‘Ki je na sake ki saki ɗaya. Ta yi sauri ta juya fuskarta saboda kaucewa haɗa ido da shi; duk da ita nema kuma da yaƙinin zai aikata haka amma sai da fitar kalmar ta yi mata ciwo. Ta sake juyowa cikin murya ƙasa-ƙasa tace ‘Nagode.’

    ‘Za ki yi nadamar rabuwa da ni Khadeeja.’ Ya faɗa a gajarce. Ta kalle shi ta yi murmushi sannan ta kawar da kanta ta faki idonsa ta goge ƙwallar da ta taru a kwarmin idonta. Bugun ƙofa ne ya katse su da Shukra tana cewa ‘Abba Anti tace za ku makara fa. ‘Um, gani nan zuwa.’ Ya amsa daga cikin ɗakin.

    Ya wuce Khadeejan ya buɗe ƙofar ya fice. Ta bi bayansa janye da akwatinta. Shukra ta tsaya a gefenta tace ‘Anti ke ma har da ke za a tafi? Ta kama hannunta tace ‘A a ni gidanmu zan tafi ba da ni za a tafi ba. Gidan Mommy? To da mu za ki tafi? Ta tambaya da mamaki.‘Eh, gidan Mommy zan tafi amma ba da ku zan tafi ba. Abbanku zai gaya muku wadda zata zauna da ku.’

    Gaba ɗaya yaran suka zuba mata ido suna ƙoƙarin gane me take faɗa. Ta ƙwalawa Hafsa kira ta ba ta umarni ta haɗa kayanta su tafi gida. Ba tare da ɓata lokaci ba ta juya. Ta dubi Naja wadda take zaune tana binsu da kallon mamaki tace ‘Maman Rukayya sai kun dawo, Allah ya amsa ibada Alah ya maimaita mana. ‘Amin.’ Ta amsa a gajarce sannan ta dubi Mustapha tace ‘Ban fa gane ba, me yake faruwa ne?’

    Kafin ya ba ta amsa tuni Khadeeja ta ja akwatinta ta fice daga parlor ɗin. Shukra wadda ta ƙarasa ta faɗa jikin Abbanta ta rushe da kuka; saboda ta kasa fahimtar me yake faruwa su da aka ce za a yi tafiya har Abbansu a bar su da Anti kuma Antin ta fara tafiya. Ya dubi Naja yace ‘Cewa ta yi na sake ta kuma na sake ta, tunda ita ta nema.’

    Ta ɗan firgita ta dafe ƙirji, ba ta san lokacin da yawun da yake bakinta ya wuce ba tace Saboda me? Kai kuma ka biye mata? Saboda baƙin cikin zan tafi dake Hajji ban tafi da ita ba.’ Ya faɗa cike da ɗacin rai. Ya ƙarasa ya zauna a kan kujera a jigace kamar wanda aka tura. Sukayi cirko cirko suna kallon shi. Habib ya shigo a guje ko sallama bai yi ba, yana cewa ‘Abba na ga Anti tafi. Me yake faruwa ne? Waye zai zauna da mu?’

    Ya miƙe a jigace yana cewa ‘Maza kowa ya ɗebo kaya ko kala ɗaya ne mu wuce, sai na ajiyeku gidan Hajia. In ya so ko gobe sai ku dawo da Yaya Jidda ku ɗebi kaya. Antin ta tafi. Ya fice ba tare da ya saurare su ba Naja ta rufa masa baya. Nasreen ta kalli Habib ta kare gefen bakinta kamar me raɗa tace ‘Ya sake ta. Ya zaro ido zai yi magana suka jiyo muryar Abbansu daga ƙafar bene yana cewa ‘Maza fa ku sauko. Suka miƙe gaba ɗaya suka shirya suka fice.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Takwas

    Edita@rumasau-kallamu

  • Sunayen Abinci Da Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 2

    Sunayen Abinci Da Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 2

    36.Ganda
    37.Gauta
    38.Gaskami
    39.Gawasa
    40.Giginya

    41.Gindi- kwalo
    42.Gumba
    43.Gurasa
    44.Goriba
    45.Halawa

    46.Jimɓiri
    47.Kifi
    48.Kamu
    49.Ƙato-da-lage
    50.Koko

    51.Kunu (zaki, kanwa, fari, tsamiya)
    52.Ƙwai
    53 Kantun Gana
    54.Ƙosai
    55.Kwaikwaye

    56.Kulele
    57.Kwarbebe
    58.Kilishi
    59.Kurna
    60.Kauci

    61.Lula
    62.Lulaye
    63.Makani (gwaza)
    64.Mandaƙo
    65.Masara

    66.Magarya
    67.Mai (gyada, shanu)
    68.Mangwaro
    69.Nama
    70.Nakiya

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Abincin Hausawa Kashi Na 1

    Edita@rumasau-kallamu