Tag: yadda ake

  • Labari Mai Taken Tsatsar Zuciya

    Labari Mai Taken Tsatsar Zuciya

    Ko wane ɗa ba shi da burin da ya wuce ya samu iyaye masu ba shi kulawa, kama daga tarbiya, ilimi, ci da sha ke har ma da tarairaya da ɗaukar dukkan wata ɗawainiyya tasu, har zuwa lokacin da za su girma suma su zama wasu su taimaki iyayen su har ma da sauran Al’umma, amma ni ban samu wannan damar ba Khadija, sabo da….

    Dai dai wannan lokacin ne malam Hadi ya shigo cikin fushi daret ɗaki ya nufa kasancewa dama wasu lokutan bai fiye yin sallama ba musamman in yana cikin fushi.

    “Barira! Barira!!” “Na am baba”

    Wace kalar shashasha ce ke ina ta kira amma kamar banza yana magana iyeeh? “Ka yi haƙuri baba wallahi ban ji ba ne amma insha Allah ba za a kuma ba. ” Barira ta faɗa cikin ladabi. Wani irin kallo ya yi mata tare da faɗin

    “ina babar taki ?” “Ta je tayo awo ne saboda garin mu ya ƙare” “Ta dai tafi gantalinta ta ne kawai” Ba tare da sake ce masa komai ba Barira ta yi zugum tana kallon sa zuciyarta kuwa kawai tafasa take tare da karanta mata munanan wasiƙu.

    Washe gari da safe Bashir ya shirya da nufin tafiya makaranta ya yi sallama da Lami wadda ta kasance mahaifiya a gunsu, kafin ya nufi ɗakin mahaifin tuni kunnuwan sa suka cika da kiran sunan sa da mahaifin ke ƙwalawa, tuni ya nufi ɗakin yana isa ya tsaya a bakin ƙofa tare da yin sallama.

    “Fitowa kake son na yi dan uwaka? Rasa kunya ɓeran tanka..” Cikin fushi Bashir ya shiga ɗakin tare da faɗin “ga ni” Malam? Hadi ya ɗaga kai tare da faɗin “ina za ka ka ratayo jaka kamar wani wanzami..? Malam je ka ka cire kayan nan mu tafi kasuwa yau ina da aiki sosai a kasuwa”

    Bashir ya miƙe cikin fushi ya yi waje yana faɗar ƙananan maganganu. Minti goma Malam Hadi ya fito yana neman Bashir, Barira da ke tankaɗen gari ta yi saurin risinawa tare da faɗin “baba ai Bashir ya tafi makaranta..”

    “Makarantar banza da ta wofi, wato gani bawanku ko? In je in nemo muku ku ci ko? To wallahi yau in bai zo kasuwa ba sai na saɓa masa kuma ko sisi ba zan ba ku ba, yaran banza marasa albarka”

    Kallon sa kawai Barira ta yi domin wannan baƙin cikin ya daɗe da yin tsatsa a cikin zuciyarta, baba Lami kuwa fitowa ta yi cikin fushi domin ita kanta abun ya kai ta maƙura, suna haɗa ido ya yi wani tsaki tare da wurgi da robar da ke kusa da shi ɗauke da busashshen ƙanzo.

    “Malam gaskiya na gaji da tambaɗar mun da ‘ya’ya da kake yi, a ce kullum maƙota sai sun ji mu,” “To su ji mana ko rashin kunya za ki yi mun” “Babu rashin kunya amma dai ka sani duk mutumin da bai san haƙƙin iyalinsa a kansa ba to ya shiga matsala, duk yaran mu babu mai ilimi babu wanda ka sa a makaranta, sai wanda maƙota suka dubi Allah suka dubi Annabi suka saka su, ba ka damu da cinsu ba, shansu, sittira, zama da su ka ji damuwarsu, babu kuɗin sabulu babu na kitso babu kalaman kwantar da hankali, cefane ma sai ka yi gorin sa.

    To ka sani wannan haƙƙin ka ne da Allah ya ɗora maka, amma duk mijin da ke zagin matarsa ko aibata ta a gaban ‘ya’yan ta to bai nemi haɗa zuriya ɗayyiba ba haka ita ma matar, amma kullum kai ne Allah ya isa, lalatattu, marasa ilimi, Malam ta ya yaro zai ji ƙanka har ma ya taimake ka, ko wasu yara suna bukatar kulawar iyaye da ƙwarin gwiwa musamman yara mata amma malam…”

    “Ya isa lami kin gama rashin kunyar taki da kika koyawa ‘ya’yan ki ?” Malam Hadi ya yi tsaki tare da ficewa waje, Barira kuwa tuni hawaye sun wanke fuskarta. “Allah ka shiga lamuran gidan mu ka chanza halin dukkan wani miji mai irin halin baba Hadi…

    Wannan bayani an ciro shi ne daga maƙala mai taken TSATSAR ZUCIYA wadda Ismail Usman Abubakar  @Dr. Hisham ya wallafa, wadda aka gabatar a Taron Ranar Marubuta Ta Duniya na ranar (31/12/2025) a Dutsen Jihar Jigawa.

    Danna nan don karanta Yadda Manufar Rayuwarka Take

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waƙa Mai Taken Abokin Tafiya

    Waƙa Mai Taken Abokin Tafiya

    1. Rabbi ban hikima basira,

    Baituka zan so na tsara,

    Kyauta aiki kan mu lura,

    Don mu ɗau hanya ta tsira,

    Duniya har ran tsayawa.

    2. Zan rubutun baituka ne,

    Kan Hadisin Musɗafa ne,

    Don misali ya saɓa ne,

    kan gudanmu a duniya ne,

    In ajal gu nai ya zowa.

    3. Ga mutum ga ‘yan uwansa,

    Su Uku da suke a gunsa,

    Zai tafi gun khaliƙinsa,

    Yai biɗar ɗaukinsu gunsa,

    Don su ne ya ƙyale kowa.

     

    4. Sai ya dubi gudansu yac ce,

    “Wane loto ya yi fauce,

    Me gare ni za ka zam ce,

    Taimaka min don na dace,

    Ban da kai ban nemi kowa.”

     

    5. Sai ya ce “Zan jinyatar ka,

    Zan tsaya nai hiddimar ka,

    In ko rai ya kau gare ka,

    Za na yo sutura gare ka,

    Zan biye ka zuwa kushewa.

     

    6. “Har da ni za ai saka ka,

    Ƙabbari a zamo rufe ka,

    Addu’a zan yo gare ka,

    San da duk an ambace ka,

    Zan tuna ka ina yabawa.”

     

    7. Wanga shi ne dangi nasa,

    Duk iyali har ɗiyansa,

    Za su ɗauke shi su kai sa,

    Sai su dawo can su bar sa,

    Fin haka ba sa iyawa.

     

    8. Ɗan uwa na biyu gare shi,

    Za ya nemi garai kira shi,

    Sai ya ce mar “Wane ga shi,

    Lokacina ya tuƙe shi,

    Zan tafi ba dawayowa.

     

    9. “Kanka nai duk rayuwata,

    Don biɗar ka na yo mutunta,

    Don na samu abin bajinta,

    Me kake amfanuwa ta,

    Yau na samu abin riƙewa?”

     

    10. Sai ya ce “Ai ni gare ka,

    Lokacin ruhi gare ka,

    Garkuwa kuma irli naka,

    Duk  buƙatu zan biya ka,

    Har ka zam ka zarta kowa.

     

    11. “In ko rai ya kau gare ka,

    Mun rabon hanya da ni ka,

    Za ka tai gun khaliƙinka,

    Ni ko ‘yan gado gare ka,

    Za su ɗau ni su zam rabawa.

     

    12. Wanga shi ne dukiyarsa,

    Wadda ya ba rayuwarsa,

    Duk wahalta ya yi don sa,

    Sun rabu bai ba shi fansa,

    Ko gare shi ya taimakawa.

     

    13. Ɗan uwa na Uku ya nema,

    Yac cane mar “Wane kai ma,

    Kai sani yau babu dama,

    Dawwamar ruhi jiki ma,

    Za na amsa kiran da anwa.

     

    14. “Me kake amfanatarwa,

    Don na zamto ƙetarewa,

    Zanguna da suke tahowa,

    Kwai haɗar da rikirkicewa,

    Zan buƙaci ka agazawa?”

     

    15. Sai ya ce “Duk inda za ka,

    Dukka zango ban barin ka,

    Tun kushewa ƙabbarinka,

    Zan cire kewa gare ka,

    Ran zuwan ‘yan tambayawa.

     

    16. “Ran tsayo gun khaliƙinka,

    In ka tashi ina biyar ka,

    Zan yiwo rana gare ka,

    Can a mizanin awonka,

    Zan shiga yai nauyayawa.”

     

    17. Wanga shi ne nasa aiki,

    Wanda ya yo shi na kirki,

    Kyautatar bauta ga Sarki,

    Kyauta niyya babu surki,

    Shi yake yin dawwamewa.

     

    18. Ko fa aiki bai yi kyau ba,

    Ya ƙazanta bai fari ba,

    Zai lazimci mutum a turba,

    Ƙabbari ba zai bari ba,

    Dole shi za yai riƙewa.

     

    19. Babu amfaninsa zai ci,

    Zai zamo babban kumurci,

    Yai ta saran sa yana ci,

    Hakka zai wanzu a ƙunci,

    Har zuwa ranar tsayawa.

     

    20. Gun awo muni na aikin,

    Sai ya rinjayi na kirkin,

    Rabbi tserar mu tafarkin,

    Muna aiki wanda kaidin,

    Shaiɗana ke shiryatarwa.

     

    21. ‘Yan uwa lallai mu farka,

    Tanadin aiki mu ɗauka,

    Wanda zai bi mu ya haska,

    Ƙabbarinmu har mu farka,

    Don fita ranar tsayawa.

     

    22. Ran da tarin dukiyarmu,

    Kaddarori dangi namu,

    Ba su amfani gare mu,

    Sai fa mai kyau ayyukanmu,

    Ba riya ba goratawa.

     

    23. Kar mu ruɗu yawan mutane,

    In a kan hanyar ɓata ne,

    Gwamma mun ɗau mai mutane,

    ‘Yan kaɗan in shiryata ne,

    Don mu samu abin riƙawa.

     

    24. Mun yi roƙo Jalla Sarki,

    Sa mu dace wajje ɗaki,

    Mui kulawar kyauta aiki,

    Don mu dawwama kan tafarki,

    Wanda ba zai karkacewa.

     

    25. Nasiru G. Ahmadu ne,

    Kowashe almajiri ne,

    Mai biɗar ƙarin sani ne,

    Shi ya saƙo baitukan ne,

    Ayyuka mui kyautatawa.

    Alhamdu lillahi.
    Wannan waƙa an ciro ta ne daga littafi mai suna TASKIRA wanda Nasiru G. Ahmad ya wallafa.
    Edita@rumasau-kallamu
  • Yadda Aka Yi Bautar Kurmin Jakara A Kano

    Yadda Aka Yi Bautar Kurmin Jakara A Kano

    BAUTAR JAKARA

    Ga abinda ya zo a littafin Tarihin Kano game da Bautar Kurmin Baƙin ruwa ko a ce kurmin Jakara.

    Ma’abotan wannan ƙasa (Kano) waɗanda Bagauda ya same su a cikinta suna mulkin garinsu, ba su bin kowa sai Tsumburbura da duhuwa tasa JAKARA. Ana ambatonta (duhuwar) da KURMIN BAƘIN RUWA, domin shi ruwa ne baƙi, duhuwa ta kewaye shi, ana kiyaye dukan musiba da ita da gunkinsu.

    Mafarinta kuwa daga Gurgumasa har zuwa Dausara. Kiraranta da zartakenta ba su motsi sai idan musiba ta gabato wannan gari ta yi kuruwa sau uku, hayaƙi ya riƙa fitowa daga cikin Tsumburbura, wanda ke cikin tsakiyar ruwa. Sai su nemi baƙin kare su yanka a ƙarƙashin Tsumburbura, kuma su yanka baƙin bunsuru a cikin duhuwar.

    Idan hayaƙi da kururuwan sun daɗu, to babu makawa sai musibar ta sadu da su. Idan kuwa ba su daɗu ba, babu masiba. Sunan duhuwan nan kuwa MADAMA. Kuma sunan Tsumburbura RANDAYA’.

    Ƙarin Bayani game da KURMIN JAKARA

    Ita Jakara ana kiranta da suna KURMIN-BAƘIN-RUWA saboda ruwan tafkin baƙi ne, kuma kewaye take da bishiyoyi masu yawa. A cikin bishiyoyin ne akwai guda ɗaya da aljani yake kanta, wadda suke yin tsafinsu a kanta, kuma wadda take yin hayaƙi idan musiba ta tunkaro Kano.

    Ita wannan bishiyar a tsakiyar ruwan take. Wannan daji mai yawan bishiyu sunansa MATSAMA, Bishiyar tsafin kuma ita ce RANDAYA. Ɗaukacin wajen shi ne Jakara har zuwa inda Kasuwar Kurmi take a yanzu.

    Daga Littafin KANO TA DABO TUMBIN GIWA na Alhaji Ahmad Bahago

    Danna nan don karanta Asalin Kafuwar Jihar Katsina

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waƙa Mai Taken Ladubban Tsuguno

    Waƙa Mai Taken Ladubban Tsuguno

    1. Da sunan Rabbi mai baiwa gare mu,

                       Da nau’o’in ni’imta ba musawa.

    2. Salati da sallama ga Rasulu Ɗaha,

                       Da ya ceto mu bin hanyar ɓacewa.

    3. Cikin ni’imar da Rabbi ka yi gare mu,

                       Fitar najasa ga mu don tsarkakewa.

     

    4. In ban da haka jiki za tai zamanta,

    Guba ce wallah za tai illatarwa.

    5. A don haka gode Allah ya wajabta,

    Bisa ni’imar ga kullum mui ta yowa.

    6. Musulmi an buqƙaci ya yo ladubba,

    Ya bambanta da gayyar kafirawa.

    7. Idan ya buƙatu banɗaki ya zaga,

    Da Bismillah ake son yai shigewa.

    8. Ya sanya ƙafar hagu yayin shigarsa,

    Ya zam addu’ar tsari daga jinnatawa.

     

    9. Idan ba ka ambaci Allah shigarka,

    Al’aurarka sukan riƙa kallatawa.

    10. Hijabi naka Basmala du’a’i,

    Idan ka yi ba su duba ko tsayawa.

    11. Kada ka shiga da sunan Rabbi Allah,

    Jikin zobe waninsa an hanawa.

    12. Idan sarari ka je don tsuggunawa,

    Cikin dajin Ilahu ka zam kulawa.

    13. Ba a tsuguno a kan hanyar mutane,

    Da inwoyi na amfani ga kowa.

     

    14. Ƙasan bishiya da ‘ya’ya ta yi ban da,

    Da gefanni na gulbi mai wucewa.

    15. Da ramukka tana yiwuwa da jinnu,

    Da yin bawali ruwa mai dawwamewa.

    16. Ka nesaci duk idanu kar su gan ka,

    Ko sauti mai fita wari jiyowa.

    17. A nemi wuri da babu ruwa bisansa,

    Bai zam shi faƙo ƙasa mai taurarewa.

    18. A zancen Hausa ma an ce Mugunta,

    Fitsari kan faƙo zai fallatsowa.

     

    19. Ba a cire riguna ko janye wando,

                       Sai an yi kusan isa ƙasa za a yowa.

    20. Ba a fuskantuwar Qibla a yayin,

                       Da an tsuguna a fili mui kulawa.

    21. Hakan nan ba ta baya an hana shi,

                       In ba sutura ko banɗaki ginewa.

    22. A yayin ko fitar najasa ana so,

                       Qafar hagu za a ƙarfafa dogarewa.

    23. Ba a magana a yayin tsuggunawa,

                       Abin karhantuwa an tsawatarwa.

    24. Tsarkin bawali akan fara gabanin,

    Muhallin gayaɗi sai mui kulawa.

    25. Idan najasar ta ƙare fita a tashi,

    Kada a jima yawan nishi anaiwa.

    26. Ba a tsarki da hannun dama yayin,

    Wanke najasa hagun za ai sakawa.

    27. Ko da da Tishu ya zamto za a goge,

    A yo da hagu kafin da ruwa biyewa.

    28. Hakan ne ma bin so in ya samu,

    Gudun hannu taɓar najasa ya yowa.

     

    29. Ba a sanya ƙashi don goge najsa,

    Ko ko tutu na dabba an hanawa.

    30. Kaza da dukansa dangogin abinci,

    Da duk abu mai darajja ba a yowa.

    31. Shi ma bawali a yo Istinjimari,

    Kafin tsarkin ruwa ya zamo biyewa.

    32. A zam addu’a idan za ai fitowa,

    Da banɗaki a bayan tsuggunawa.

    33. Mu zam gode wa Allah don raba mu,

    Da duk najasa da mun zam kasayewa.

     

    34. Kaza najasar ruwa da mukai bawalta,

    Aminta don gare mu yai daɗowa.

    35. A nan zan dakata ya ‘yan uwana,

    Kurenmu Tabaraka yai garafawa.

    36. Ya Rabbi daɗo salati babu haddi,

    Ga Manzo naka jikan Hashimawa.

    37. Idan an tambayi mai tsara waƙar,

    Nasir Ahmad iri na Bukar ya yowa.

    38. Baitoci Arba’in Biyu babu waƙar,

    Dubu Biyu sha Tara Maris na yowa.

    Alhamdu lillahi

    Wannan waƙa an ciro ta ne daga littafi mai suna TASKIRA wanda Nasiru G. Ahmad ya wallafa.

    Karanta Tarihin Marubuci Nasiru Garba Ahmad

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tarihin Marubuci Nasiru Garba Ahmad

    Tarihin Marubuci Nasiru Garba Ahmad

    Assalamu alaikum.

    Sunana Nasiru Ahmad Garba. A lokacin karatu sunan Ahmad ɗin ya koma karshe. An haife ni a unguwar ‘Yan awaki da ke cikin birnin Kano, ran Lahadi, 16 ga watan Safar, 1384, BH. (4 – 2 – 1964). Na yi karatun Alkur’ani a unguwar Ƙoki, kasancewar a can na taso, ina wurin yayata.

    Ban fara karatun zamani da wuri ba, domin sai a 1981 na gama makarantar Firamare Islamiyya ta ‘Yan awaki. Na yi makarantar nazarin addinin musulunci mai zurfi (School for higher Islamic Studies) ta Shahuchi (Aliya), daga 1981-1985.

    Sai makarantar nazarin shari’ar musulunci ta Aminu Kano (Legel), a 1986-1989, inda na sami Diploma a harsunan Hausa da Larabci da nazarin addinin musulunci. Daga 1993-1996, na je Jami’ar Usmanu Danfodiyo ta Sakkwato, inda na sami digirin farko a harshen Hausa.

    A 2009-2010 na yi karatun neman digiri na biyu kan adabin Hausa fannin rubutattun waƙoƙi, a Jami’ar Ahmadu Bello Zariya. A 1984, na yi karatun sarrafa keken rubutu (Typewriting) ƙarƙashin hukumar yaɗa ilimin manya ta Kano. A 1992, na halarci wani kwas da Jami’ar musulunci ta Madina ke shiryawa don horar da malaman harshen Larabci da addinin musulunci, a Jami’ar Bayero ta Kano.

    A 1999, na yi karatu ƙarƙashin “Sincere Writers Club,” inda na sami satifiket kan aikin jarida. Daga Janairu zuwa Disamban 2002, na yi karatu a “Alliance Francaise de Kano” inda na sami satifiket kan harshen Faransanci. Na yi nisa a karatun Diploma kan Faransancin, amma ban sami ƙarasawa ba.

    A 2006, na yi karatu ƙarƙashin kwalejin horar da ma’aikatan mulki ta ƙasa (Administrative Staff College Of Nigeria -ASCON). A 2008, na yi karatu a “I.H.D.I.T.” (Institute for Human Development & Information Technology) da ke Tarauni Kano, inda na sami satifiket, da kuma Diploma (a 2011) kan sarrafa kwamfuta.

    Na fara rubuta waƙa ran 15 ga Janairun 1983. A shekarar dai na rubuta wani littafin koyon ibada ga yara cikin rubutun Ajami, na kuma rubuta wani wasan kwaikwayo, wanda muka yi ni da abokaina, muka naɗa a rikoda, muna kwaikwayon wasan kwaikwayo na rediyo.

    A 1985 na shiga ƙungiyar marubuta da manazarta waƙoƙin Hausa ta Nijeriya, reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin marigayi Mal. Aƙilu Aliyu a lokacin. Bayan ita, na shiga ƙungiyar marubuta waƙoƙin Hausa ta “Hikima Club,” ƙarƙashin jagorancin marigayi Abdullahi Sani Makarantar Lungu. A 1992, na yi ƙungiyar wasan kwaikwayo ta matasan Ɗambatta, lokacin ina aiki a can.

    Yanzu haka ina cikin shugabannin ƙungiyar mawallafa ta kasa (ANA) reshen jihar Kano. Memba ne ni a ƙungiyar mawallafa littafan Hausa ta HAF Kano, da ƙungiyar marubutan Hausa ta Nijeriya (HAWAN), da ƙungiyar mawallafa ta Alƙalam Kaduna, da Tsangayar Adabin Hausa

    Ni malamin makaranta ne. Na yi aikin koyarwa a makarantu da dama na Firamare da Sakandare, tun daga 1984 zuwan yanzu.

    WALLAFE-WALLAFE

    NA ADDINI

    1. Sahabbai Goma da aka yi wa Bushara da Aljanna (Wallafa)
    2. Yaƙin Badar (Wallafa)
    3. Addu’a da yadda ake yin ta (Wallafa)
    4. Huɗubobin Annabi Goma (Wallafa)
    5. Fassarar Umdatul Ahkami (Fassara)
    6. Fassarar Risala (Fassara – Ba a buga ba)
    7. Mas’aloli 70 kan Azumi (Fassara)
    8. Fatawoyi 50 kan Azumi (Fassara)
    9. Salatin Annabi: Matsayinsa da Hukunce-hukuncensa (Fassara)

    NA LABARU

    1. Antar Ɗan Shaddadu 1-2 (Fassara)
    2. Abu Firaas 1-2 (Fassara)
    3. Ra’asul Guuli (Mai kan fatalwa) 1-4 (Fassara)
    4. Sha-Alwashi 1-2 (Fassara)
    5. Hikayoyin Marowata (Ba fassara ne kai-tsaye ba)
    6. Dare Dubu da Ɗaya (Sabuwar fassara) 1-5
    7. Garin Banza…. (Ƙirƙirarren labari ga hukumar A daidaita Sahu ta Kano)

    NA ILIMI

    1. Guzurin Marubucin Waƙa (Wallafa)
    2. Ƙa’idojin Rubutun Hausa a Sauƙaƙe (Wallafa)

    Akwai kimanin littafai goma da ba a buga ba

    Danna nan don karanta Waƙa Mai Taken Jakadan Allah

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tsokacin A Kan Littafin Garina Abin Alfaharina

    Tsokacin A Kan Littafin Garina Abin Alfaharina

    “Garina Abin Alfaharina.” Littafi ne da ya zamo tamkar madubin da ke haskaka zuciyar al’umma, domin a cikinsa an ɗaura labarin a kan gaskiya, haɗin kai, da sadaukarwa. Gari fitila ce, amma mutane su ne wutar da ke haskakata (kunna ta).

    Marubucin ya zubo bayanai cikin hikima, ya zana halaye da ɗabi’u a matsayin tubalin gina al’umma. Har ila yau, al’umma ba ta tashi da cigaba, sai da haɗin kai. A wannan littafin an nuna mana cewa “Gari na bunƙasa ne da mutanensa”, domin ba gine-gine ba ne kaɗai suka gina gari ba, hasalima zuciyar mutanenta ce.

    Ga Malam Yahaya Garba, Malam Mammaada, Malam Surajo Yunusa, Malam Aliyu Labaran, Malam Magaji Ƙofa, Malam Idi Ɗanlula da sauran malamai, waɗanda suka zama tamkar katanga ga iska, suna tsayawa a kan ilimi da tarbiyya.

    Haka kuma marubucin ya kawo wasu matasa masu kirki; Dakta Mujaheed da Salmanu Faris, Alhaji Abubakar Suleiman, Barrister Anas Lawal Audi, waɗanda suka yi tsayawan tsayin daka ga ‘ƴan siyasa, don ganin an samar da cigaba a garinsu.

    Kuma sun tabbatar da haka, domin sai da suka miƙa kundin buƙatun al’ummarsu ga duk ɗan siyasan da yake neman ƙuru’arsu kafin su zaɓe shi.

    Lafiya uwar jiki, babu mai fushi da ke in ji Ɗan Hausa, a cikin littafin an ga lokacin da Dakta Ado Zakari, Dakta Murtala Muhammad, Dakta Khalid Gambo da Hajiya Gude suka tsayin daka wajen warware wasu cututtuka a garin gami da sadaukar da ilimin su, don amfanuwar garin.

    Abin da ya fi jan hankali shi ne yadda marubucin ya sassaƙa turakun zaman lafiya tsakanin ƙungiyoyin addini, wato Tijjaniya, Izala da Shi’a. Kamar yadda ake cewa: “Idan ruwa ya yi yawa, sai ya zama teku.”, kuma ” Zaman lafiya ya fi zama ɗan Sarki.

    Saboda, gari yana samun cigaba ne a lokacin da aka samar da zaman lafiya (tsaro), ilimi, sana’a da kasuwanci da sauransu. An hango wasu harsunan mutane, waɗanda suka sadaukar da rayuwarsu don cigaban garin ta fuskar tsaro, an kuma zayyano wasu gwadabe na samar da tsaro da cigaban gari.

    Shi ya sa wannan littafin ya kasance tamkar gorar ruwan sanyi ne ga mai tafiya a cikin sahara.

    Danna nan don karanta Waƙa Ta 2 Ga Farfesa Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Asalin Kafuwar Jihar Katsina

    Asalin Kafuwar Jihar Katsina

    Ga abinda yazo daga littafin tarihin Katsina

    (Kitabu Taarikh Ummaratu Hazihil Qaryatu Al-mashhuratu bi- Katsina min binaaiha ila yaumina haza”

    Da sunan Allah Mai Rahama Mai  jinƙai, godiya ta tabbata ga Sarkin Sarakuna. Mun faɗa, Amma Allah ne mafi sani. Tabbas, wannan ne tarihin wannan shahararren birni Mai suna Katsina tun daga kafuwarsa kawo yanzu.

    Wasu masanan tarihin sun ruwaito cewa tsohon birnin ya gabaci Adaamus (an ce wani shahararren Sarki ne da aka taɓa yi a Ƙasar Hausa) da shekaru 4. Sannan masanan sun tafi a kan cewa BAGANI JARGO wanda ya Gina ganuwar birnin ya sarauci Katsina tare da zuriyarsa har tsawon shekaru dubu uku da hamsin kafin zuwan  SANAWU (Wanda a zamaninsa Musulunci ya shigo Katsina) wanda ya ɗauki gabarar sarautar birnin.

    To Amma, Sanawu, da Bagawu da Katsina, sun kasance shahararrun ‘ya’yan Bawo ne, Kuma sun wanzu a mulkin Katsina na tsawon lokaci. Sun yi mulki na tsawon shekaru ɗari Tara. Daga nan sai MUHAMMADU JANHAZO, da shi da zuriyarsa sun shimfiɗa mulki na tsawon shekaru ɗari biyu da ashirin.

    Har ila yau, an ruwaito cewa TSAGA RANA ya shafe shekaru hamsin da bakwai (Masani Dr Yusufu Bala Usman ya ambace shi a matsayin Sarki na bakwai, ya yi sarauta a wuraren 1767-68). Sa’annan ya bai wa babban ɗansa mulki, sunan sa WARI MAI-KYERAAYI, wanda ya shafe shekaru goma Sha uku Yana sarauta (ya mulki Katsina daga 1649-1660.

    (A zamanin mulkinsa ne ya yaƙi Kano, Abdullahi yana sarautarta. An ce sai da ya taɓa rarakar Kanawa har sai da ya tuƙe da su zuwa ƙofar Kansakali ta birnin Kano sannan ya juyo). Sannan ya miƙa mulki ga GIMA da ga Daƙaasariy, shi ma ya shafe shekaru talatin da biyar yana sarauta, daga Nan sai AGWARAGI ya karɓa wanda ya yi mulki tsawon shekaru arba’in da biyu.

    (An ce shi ne Sarkin Katsina na takwas, ya yi mulki a wajajen 1778-96. Tarihi ya KIYAYE cewa Agwaragi shahararren Sarki ne, a zamanin sa ne Katsina ta kwaci wata takobi daga hannun Sarkin Gobir a zamanin da ake karin battar yaƙi tsakanin Katsina da Gobir ɗin, sunan takobin Bee-bee.

    Har yanzu, nasarar Katsinawa a kan Gobirawa na ɗaya daga ababen alfaharin Katsinawa; a duba KATSINA: a historical document wanda Centre  Regional de Documentation Pour la Tradition Orale Niamey ta wallafa a 1970.)

    Daga shi sai GWOZO, maruwaitan tarihi sun ce ya shafe shekaru talatin da bakwai yana sarauta. Sauran shekaru sha ukun da suka rage, sarakuna irinsu MUHAMMADU AL-ZAAHID wanda bai jima kan sarautar ba, har manya nesanta kansa daga abubuwan duniya har ma daga ƙarshe ya yanke shawarar yin murabus daga sarauta, wataƙila shi ne silar laƙaba masa suna Al-Zaahid (Mai gudun duniya).

    Akwai da yawansu waɗanda muka manta sunayensu tare da lokutan da suka yi mulki kafin tukewarsu zuwa ga Mallam Umar (Ummarun Dallaje Wanda ya kafa tutar Shehu Usmanu a Katsina, kuma wanda aka wallafa littafin a zamanin sa 1807-1835). Ƙarshe! (Godiya ga SALISU BALA Wanda ya alkinta mana shi)

    Asalin Sunan Katsina

    Labari mafi inganci shi ne, sunan tsohon birnin Katsina ‘DURƁI TA KUSHEYI’. Sunan mutanenta Durɓawa. Wasu na cewa asalin Durɓawa maguzawa ne tsatson mutanen NOK da Kwatarkwashi duba da kaburburansu da aka samo masu tsayi kamar falwaya, amma waɗansu na cewa asalinsu Mallawa ne daga Mali suke.

    Da akwai mabambantan ra’ayoyi dangane da ASALIN inda aka samo Sunan  KATSINA

    1. Ra’ayi na farko na cewa, an samo sunan ne a zamanin Sarki MUHAMMADU Korao, a lokacin da ya sanya wani makusancinsa mai suna Katsina ya ringa duba yadda ake gina ganuwar birnin a madadinsa.

    2.  Ra’ayi na biyu: Aka ce sunan Katsina ya samo asali ne daga sunan wata mace mai suna matar sarki mai suna KATSI wadda ta fito daga Durbawa, mazaunan birnin na farko. An ce ta bar tsohon garin Katsina ne zuwa inda sabon birnin yake, a lokacin yana matsayin ƙaramin ƙauye, ba tare da an sani ba, da aka bazama nemanta sai aka riske ta, shi ne mazaunan garin suke cewa ‘Ai KATSI NA NAN’.

    3. Ra’ayi na uku na cewa sunan Katsina  ya samo ne daga wani Sarki da aka taɓa yi mai suna Katsina Ɗan Bawo. Amma marubuci Tijjani Lawal Ingawa yace Sarki Katsina ɗan Kumayo ne a wani rubutunsa.

    Daga Sadiq Tukur Gwarzo

    Danna nan don karanta Yadda Za Ka Tambayi Kanka Da Kanka

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waƙa Mai Taken Jakadan Allah

    Waƙa Mai Taken Jakadan Allah

     

    1. Allahu ba ni dubun basira mayyawa,

                                 In yi baitukan bege ga ɗan Adanani

    1. Ga munasaba ta watan Rabi’ul Lawwali,

                                 Wata na samun Sayyidul kaunaini.

    1. Kafin zuwansa duniyar ga baƙi ƙirin,

                                 Duk ta nutse a duhun ɓata tai muni.

    1. Tauhidi loton babu shi sai nadiran,

    Kaɗaita bautar Rabbu tai nuƙusani.

    1. Sai kame-kame ake cikin kogin ɓata,

    Bautar wanin Allah da bin shaiɗani.

    1. Sai zulmu ko a ina da danne haƙƙuna,

    An juya shar’un Rabbana Mannani.

    1. A wanga hali Ɗaha ya zo duniya,

    Don tsarkake ta ga dukkanin ɗuguyani.

    1. Ta tsatson ababen zaɓuwa gun Rabbana,

    Nasaba da halayen ƙwarai ihsani.

    1. Ya zo a tsarkake ba ƙazanta ko kaɗan,

    Ya girma kamamme ga duk buɗlani.

    1. Mai gaskiya aka san shi fai har baɗini,

    Da riƙon amana sun kira shi Amini.

    1. Allahu ya zaɓe shi don manzantaka,

    Ta isar da Tauhidi ga dukkan kauni.

    1. Ya ba da dukkan rayuwarsa wajen isar,

    Saƙo na Tauhidi a san gufrani.

    1. An tsangwame shi a Makka har dangi nasa,

    Da dukan Sahabbai masu bin Rahmani.

    1. Yai shekara har Sha Uku a cikin matsi,

    Laifinsa Tauhidi da ƙin ausani.

    1. Ya bar garinsa na haihuwa a bisa haka,

    Haka ma Sahabbai nasa sun hijrani.

    1. A Madinatu Yasrib ya zauna har zuwa,

    Ƙarshe na rayuwarsa bisa ga amani.

    1. Qur’ani an saukar garai don shiriya,

    Bautar Ilahu da kyauta dukkan shani.

    1. Rayuwarsa ta zam bauta Rabbil izzati,

    Koyar da Qur’ani gami da bayani.

    1. Mai tausayi ga dukan halitta ya zamo,

    Mai kyauta hulɗa ne ga duk insani.

    1. Mai yafiya ga dukan kure ne Musɗafa,

    Mai tarbiyantarwa bisa ihsani.

    1. Mai tsai da adalci ga kowa Annabi,

    Mai ƙyamatar haƙƙin wani a yi danni.

    1. Mai koya shar’a aikace don ai biya,

    Bai bar a keta umarnukan Rabbani.

    1. Mai ƙas da kai ne babu girman kai ga shi,

    Mai girmamar babba da ma sibyani.

    1. Mai yin hidimtawar iyali nasa ne,

    Haka ma sahabbansa bila firƙani.

    1. Mai son lumana ba shi son ce-ce-ku-ce,

    Bai yaƙi kowa sai bisa burhani.

    1. Mai murmushi ne shi ga kowa Sayyadi,

    Kowa gare shi yana zuwa ya yi zauni.

    1. Mai yin du’a’in shiryuwar umma yake,

    Don sauƙaƙar tsayuwa gaban Rahmani.

    1. Kyawun halinsa ya ba Sahabbai kwaikwayi,

    Suka ɗabbaqa su a ko’ina ba zanni.

    1. Sun tarbiyantu gare shi baban Ƙasimu,

    Suka yaɗa Tauhidi a ƙauye birni.

    1. Sun keta dazukka Hamada sun isar,

    Sun ƙetare Kogi da dukkan Tsauni.

    1. Haka Tabi’ai suka bi a wannan hidima,

    Ta yaɗa saƙonnin farin addini.

    32.Matsayinsa gun Allahu mai girma yake,

    Tamkar ya shi babu cikon Manzanni.

    1. Duk Manzani izuwa mutanensu kaɗai,

    Ya taƙaita saƙon Rabbi kan imani.

    1. Shi ko Rasulullahi dukkan duniya,

    Allah ya ce ya isar da Alqur’ani.

    1. Haiwanu dabbobin tudu da na Maliya,

    Bayan dukannin ‘yan Adam wal Jinni.

    1. Ceto a ranar tsayuwa shi za a ba,

    Farko gabanin dukkanin Manzanni.

    1. An ba shi tafkin Kausara mai waraka,

    Ga dukan ƙishi Manzo jinin Adanani.

    1. Saƙon da an masa ya isar mun tabbata,

    Kamar da Rabbi ya ba shi ba nuƙusani.

    1. Musulunci ya ratsa dukannin duniya,

    Lungu da saƙo sai tilar Qur’ani.

    1. Ya Sayyadi baban Ruqayya da Ɗayyibu,

    Mun shaida ka yi isar da duk saƙonni.

    1. Ya mai yawan zikiri da bautar Rabbana,

    Mun yarda Allah ɗai yake Wahadani.

    1. Ya mai yawan jinƙai ga dukkan talikai,

    Ka ceci al’umma ga bin ausani.

    1. Ya Sahibas Siddiƙi Umar naka ne,

    Suruki wajen Usmanu Zun-Nuraini.

    1. Ya surukin Haidar Aliyu mazan ƙwarai,

    Kakan tagwaye Alhasan da Husaini.

    1. Ya wanda zai karɓi Luwa’ul Hamdi ran,

    Tsayuwa ga Allah Sahibat Tijjaani.

    1. Ya wanda zai ceci Musulmi na ƙwarai,

    Ranar hisabi da awon mizani.

    1. Ya Sayyadi Allah muke roƙo ya sa,

    Mu mutu bisa ga biyar Kitab was Sunni.

    1. Ya Abba Fatima Albatulu Habibuna,

    Allah ya ba mu zama da kai a Jinani.

    1. Allah muna yin hamdala munka zamo,

    A cikin Musulmi khiiratul adyani.

    1. Allah ka tsai da mu siraɗul mustaƙim,

    Izuwa macewa kar mu zam khusrani.

    1. Allah ka dumata zuciyarmu bisa biyar,

    Manzo naka da ka bai wa Alqur’ani.

    1. Allah muna a cikinsa ƙarshen zamani,

    Mai haɗari da yawan biye shaiɗani.

    1. Allah tsare mu da makarul a’adaa’i,

    Na son mu raunata har mu bar imani.

    1. Allah ka dawwama son Rasulu a zuciya,

    Ya zamo abin koyinmu dukka shu’uni.

    1. Begen masoyi ya halatta ga taliki,

    Balle Rasulu da Rabbi ya yi umarni.

    1. Yabon gwani ko wajibi haka anka ce,

    Manzo gwani na gwanaye ne ba zanni.

    1. Aikin da ya yi wa duniya tamkar ya shi,

    Ba a yo ba har yau in akwai wane ni?

    1. Kullum salati gare shi kar mu sake da yi,

    Guzuri gare mu manauyayin mizani.

    1. Sallaa alaikallahu ya khairal bashar,

    Wa ’Alika wa Sahabi wal ikhwani.

    1. Mai tsara waƙar Nasiru G. Ahmadu,

    Mai son Rasulu hasanarsa da rauni.

    Alhamdu lillahi.

    Wannan waƙa an ciro ta ne daga littafi mai suna TASKIRA wanda Nasiru G. Ahmad ya wallafa.

    Karanta Yadda Falalar Suratul Ƙulhuwallahu Ahad Take

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waƙa Ta 2 Ga Farfesa Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    Waƙa Ta 2 Ga Farfesa Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    Daga Salmanu Faris Kudan, Shugaban Ƙungiyar Marubutan Arewa ta Ƙasa Nijeriya

    1.

    A yau mun taru cikin alkunya,

    Domin girmama gwarzonmu mai dubayya,

    Haske ya sake yalwata cikin Hausaniya,

    Da samun Farfesa Mu’azu a mai kyan halayya.

    2.

    Ka jima kana hura wutar hikima,

    Kana tsarkake harshenmu ba taƙama,

    A makarantu sun ɗauki darusa ba gardama,

    Sun zame wa ɗalibai hasken tafarki mai tsunduma.

    3.

    Mu’azu Sa’adu, ginshiƙin Hausar mu ta dauri,

    Ka ɗaukaka harshen da kakanni suka bari.

    A yau an saka maka rawanin girma tuturi,

    Ka zama damina mai sanyaya shuka ba fari.

    4.

    Salmanu Faris Kudan na taya ka murna,

    Da wannan matsayi mai jan hankalina,

    A madadin marubutan Arewan zaurena,

    Muna yi maka fatan ƙarin nasarori da zayyana.

    5.

    Girmanka ya zama abin jingina ba wariya,

    Ƙwararrun marubuta suna sanya ka a zuciya.

    Ka zama tubalin da ya ƙara ɗaure ginin Hausaniya,

    Harshen da ke ɗaukaka Arewa da Nijeriya.

    6.

    Muna yi maka addu’ar fatan alheri,

    Rayuwa mai cike da ƙarin annuri.

    Allah Ya saka maka cikin mafi alheri,

    Ya ƙara nisan kwana bisa tsari.

    Karanta Waƙar Murnar Zama Farfesa Ga Mu’azu Sa’adu Muhammad

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waƙar Murnar Zama Farfesa Ga Mu’azu Sa’adu Muhammad

    Waƙar Murnar Zama Farfesa Ga Mu’azu Sa’adu Muhammad

    Daga Salmanu Faris Kudan, Shugaban Ƙungiyar Marubutan Arewa ta Ƙasa Nijeriya

    1. A yau Arewa ta wayi gari da annuri,

    An kunna fitilar da ta daɗe da alheri,

    Gwarzon ilimi Mu’azu Sa’adu mai annuri,

    Ya ɗaukaka harshe cikin nutsuwa bisa tsari.

     

    2. Ranar nan ta zamo alfahari ga dukkanmu,

    An ɗaga rawani a kan ƙashin kaifin basirarmu.

    Ka hau kujerar Farfesa cikin ladabinmu,

    A ɓangaren harshen Hausa mai cike da tarihinmu.

     

    3. Ka zama jagoran harsunan Nigerian Languages,

    A Jami’ar Sule Lamiɗo, Kafin Hausa mai darajas.

    Ka ɗauki nauyin harshe da ƙarfin halis,

    Kana koya wa duniya kima da martaban Hausas.

     

    4. Ka reni ɗalibai da armashi da hikima,

    Ka zuba ilimi kamar ruwan sama.

    Darussanka sun zama turakun hawa sama,

    Sun gina ƙarni masu zuwa tun kafin anjima.

     

    5. A fagen nazari ka zama tamkar tauraro,

    Kana haskakawa masana masu sauraro,

    Littattafanka sun zama ginshiƙai abin dogaro,

    Duk inda ake Hausa, za ku taho har ɗan goro .

     

    6. Ka zama madoga ga marubutan Arewa,

    Mai tsarkake harshen har da rera wa,

    Ka zama ginshiƙi da ba ya dusashewa,

    Wanda ya daidaita harshenmu cikin dubawa.

     

    7. Ni Salmanu Faris Kudan, mai buƙata,

    Na miƙa wannan waƙa a madadin marubuta,

    Mu na yi maka barka da wannan babban kyauta,

    Allah Ya ƙara maka lafiya ban da kunyata.

     

    8. Rayuwarka ta zama izina ga matasa,

    Ga waɗanda ke neman hasken don yai tasa,

    Ka nuna musu cewa aiki ne jawur ga matasa,

    Su ne hanyoyin da ake hawa don tasa.

     

    9. Duniyar Hausa ta yi murna da annushuwa,

    Ta ƙara jin ƙima da samun ɗaukakawa,

    Nasara irin taka ta zamo abin dubawa,

    Ga duk mai son zama abin koyi a rayuwa.

     

    10. Malam Mu’azu, Allah Ya yi maka albarka,

    Ya ƙara nisan kwana da nutsuwa a gare ka,

    Ya zuba hikima wacce ba ta yankewa gare ka,

    Ka ɗaukaka fiye da yadda kake yanzu da albarka.

    Danna nan don karanta Tsokaci A Kan Littafin Salmanu Da Salma

    Edita@rumasau-kallamu