Tag: yadda ake

  • Tatsuniyar ‎Gizo Da Namun Daji

    Tatsuniyar ‎Gizo Da Namun Daji

    ‎Ga ta nan ga ta nan ku.

    ‎Gizo ne dai yana son ya ci nama, amma ba shi da shi. Ya rasa yadda zai yi. Sai ya ce a ransa, ‘Bari dai in yi wata dabara. Sai ya sayo goro ya rarraba wa namun daji da tsuntsayen gida.

    ‎Sai ya fara kai wa kaza, ya ce, ‘Ga shi. Goron wasa ne wanda za a yi a cikin daji. Naki ne wannan. ‎Sai kaza ta ce, ‘To. Amma fa kada ka kai wa muzuru. Sai ya ce, ‘Haba, me zai sa in kai masa?’

    ‎Da gizo ya fita, sai ya shiga gidan muzuru, ya kai masa goro. Sai shi ma muzurun ya ce, ‘To, amma kada ka kai wa kare. ‎Sai gizo ya ce, ‘Haba me zai sa in kai masa? ‎Da dai gizo ya fita, sai ya shiga gidan kare ya ba shi nasa goron. Kare ya ce, ‘To, amma fa kada ka kai wa kura.’ Gizo ya ce, ‘Haba me zai sa in kai mata?’

    ‎Da ya fita, sai ya kai wa kura nata goron. Kura ta ce, ‘To, amma fa‎ kada ka kai wa Zaki.’ Ya ce, ‘Haba kura, me zai sa in kai wa Zaki? ‎Shi ke nan, sai ya kai wa Zaki nasa goron, ya ce, ‘Ranka ya daɗe. Wani ɗan wasa za a yi na kawo maka goro.’

    ‎Da Zaki ya karɓa, sai ya ce, ‘To Allah ya kai mu. ‎Shi ke nan. Da ya fita, sai ya shiga ya kai wa damisa. Damisa ta ce, ‘In ce ko dai ba ka kai wa Sarki Zaki ba? Sai Gizo ya ce, ‘Haba, haba. Wane ni da gayyatar Sarki? Sai damisa ta ce, ‘To, Allah ya kai mu.’

    ‎Da ya fito sai kuma ya shiga gidan giwa ya kai mata nata goron. Sai giwa ta ce, ‘To, in ce ko ba ka kai wa manyan dawa ba? ‎Ya ce, ‘Mhm. Yaya zan kai? Ko kai masa ne ma ai ke zan bai wa ki kai masa.’

    ‎Shi ke nan. Ana nan ana nan, sai ranar wasa ta zo. Gizo ya bayyana musu wurin da za su haɗu a yi wasan. Ya ce musu, ‘To, ku tafi zan same ku. Ni daga baya zan taho tare da makaɗa. Shi ke nan. Sai kaza ta fara tafiya. Ashe ba su sani ba, gizo ya riga su isa can. Sai kaza ta isa can. Gizo ya yi mata maraba. Ya ce, ‘To shiga wannan bukkar kafin su zo.’

    ‎Shi ke nan. Kaza ta shiga, ta zauna. Daga can sai ga muzuru ya taho. Sai Gizo ya gaya wa muzuru cikin raɗa, ‘Maraba. Shiga tana nan a ciki. Shi ke nan sai muzuru ya shiga ya tasar wa kaza zai cinye ta. Ya cinye ta.

    ‎Can kuma sai ga kare ya taho. Shi ma dai Gizo ya gaya masa kamar yadda ya gaya wa muzuru. Sai shi ma karen ya cinye muzuru. Daga nan kuma sai ga kura. Ita ma ya gaya mata kamar yadda ya‎ gaya wa kare da muzuru. Sai kura ta shiga ta cinye kare.

    ‎Kura kuma tana zaune a cikin rumfa. Sai ga Zaki ya taho. Shi ma Gizo ya gaya masa haka. Ya shiga ya cinye kura. ‎Daga nan sai ga giwa da damisa sun jero sun taho. Sai Gizo ya ce, ‘To. Ku shiga nan bukkar mana.’

    ‎Daga shigarsu, sai suka kaure da faɗa. Suka yi ta faɗa tun daga cikin rumfa har suka yiwo waje. Idonsu duk ya rufe, suna ta faɗa. Sai Gizo ya samo ganga, ya soma kiɗa yana waƙa:

    ‎Zaki bari, damisa bari.

    ‎Giwa bari.

    ‎Faɗanku na manya,

    ‎Wa yake shiga?

    ‎Sai wawa, sai mahaukaci.

    ‎Sai ko ni da ba ni da hankali.

    ‎Suna ta faɗa, can da giwa ta ga abin ba dama, sai ta fito ta yi‎ tafiyarta gida, ta bar zaki da damisa suna karawa. Sai Gizo ya ci gaba da yi musu waƙa. Ya yi ta yi, su kuma suna ta faɗa. Ashe Gizo da ma ya zo da yaji a ƙunshe. Sai ya ɗauko yajin nan ya barbada musu a idanunsu. Sai fa faɗa ya rincabe, idanunsu suka rufe ruf.

    ‎Daga can sai Gizo ya ɗauko wuƙa ya ce, ” ‘Yan banza. Ana so a ci nama an rasa yadda za a yi.” Sai ya kama yankan naman jikinsu yana tarawa, har ya kashe su duka. Sai ya jide naman ya kai gida aka soya masa, ya ci ya  ƙoshi, ya ajiye sauran, yana ci lokaci-lokaci.

    ‎Shi ke nan. Ƙurunƙus.

    ‎Wannan rubutu an ciro shi ne daga littafi mai suna TATSUNIYOYI DA WASANNI wanda Ibrahim Yaro Yahaya ya wallafa.

    Danna nan don karanta Ga Tsoro Ga Ban Tsoro

    Edita@rumasau-kallamu

  • ‎Tatsuniyar Yarinya Da Dodanni

    ‎Tatsuniyar Yarinya Da Dodanni

    ‎Ga ta nan ga ta nan ku.

    ‎Wata yarinya ce dai mai tsananin kyau, duk garinsu babu mai kyanta, ta ce ba ta son kowa sai maras tabo. Sai dodanni suka ji labari. Sai suka yi wanka a gidan tururuwa. Sai suka zama samari kyawawa da su.

    ‎Da ta gan su, sai ta ce ta sami mazan aure. Sai duk ta dube jikinsu, sai ta ga jikin wannan da ɗan tabo ɗan mitsitsi, sai ta ce ba ta son sa. Da ta duba jikin ɗayan ta gan shi‎ sumul ba ko ɗigon tabo a jikinsa, sai ta ce shi ta ke so.

    ‎Shi kenan, sai aka shirya aka yi biki. Sai suka ce za su tafi da ita garinsu, su ba mazauna ba ne, Sai aka ce to za a ba ta ƙanwarta ta taya ta zaman ɗaki. Sai ta ce ita ba ta so, ta zauna ita kaɗai. Shi kenan, aka yi aka yi su tafi da ƙanwarta ta ƙi. Sai ƙanwar ta zama ƙuda ta maƙale mata.

    ‎Shi ke nan, da suka je gidan dodanni, sai dare ya yi suka shiga ɗaka suka rufe ƙofa. Sai ta ga ƙanwarta, sai ta rufe ta da faɗa, ta ce, ‘Ke wa ya kawo ki nan? ‎Ita kuwa ƙanwar sai ta yi shiru. ‎Shi ke nan sai yar ta ƙyale ta.

    ‎Ita yar kamar sokuwa ta ke. In dare ya yi, sai ta yi ta shirga barci. Ita kuwa ƙanwar sai ta zauna tangar har gari ya waye. Sai uwar mijinta ta zo da tsakar dare ta ce:

    ‎Sarma-sarma duf-duf.

    ‎Sai ƙanwar ta ce:

    ‎Wane ne nan ya ke mana Sarma-sarma duf-duf?

    ‎Sai uwar mijin ta ce:

    ‎Uwar miji ce ta ke mu ku Sarma-sarma duf-duf.

    Sai yarinya ta ce:

    Me ki ke so ki ke mu ku Sarma-sarma duf-duf?

    Sai ta ce:

    Wuta na ke so na ke muku Sarma-sarma duf-duf.

    Sai yarinya ta ce: Iya ga wuta nan.

    ‎Ki bar mana Sarma-sarma duf-duf.

    ‎Sai yarinya ta watso mata wutar. Tsohuwa ta je ta kashe wutar ta kuma dawo musu. Nan kuwa ashe ba wuta ta ke so ba. So ta ke yi ta cinye su idan ta tarar sun yi barci. Kullum haka, kullum haka. Duk sa’ad da yarinyar ta gaya wa yarta game da uwar mijin mai zuwa ɗiban wuta da daddare, sai yar ta ce ƙarya ta ke yi.

    ‎Ana nan a haka sak, ran nan yarinya ta ce da yarta, ‘To, yau dai ki zauna kada ki yi barci don ki ji yadda mu ke yi da tsohuwar da kunnenki. Shi ke nan, ya ta zauna. ‎Sai ita uwar mijin ta zo ta yi musu irin yadda ta ke yi kullum. ‎Shi ke nan, sai ya ta ji da kunnenta.

    ‎Shi kuma mijin nata yana wani ɗaki suna kwance tare da abokansa. Idan an yi abinci na aikin gona an kai musu, sai su yi haka su bunne. Sai su yi ta cin kwaɗi. Ita kuwa ƙanwar, wadda ta kai musu abincin, sai ta ce da su:

    ‎Mijin yata, ci kwaɗi.

    Mijin yata, ci kwaɗi.

    Mazan-wazata, ci kwaɗi.

    Sha da kwaɗi, ci kwaɗi.

    Sha da kwaɗi, ci kwaɗi.

    Su kuma idan sun ji wannan waƙar, sai su yi ta rawa suna cin kwaɗi. Shi ke nan. Da sun ga ƙanwar ta dawo daga gida, sai su zama mutane su ce, ‘Ga kwanukanki nan.

    Ki ce muna yi mata sannu da aiki. Shi ke nan. Da sun ga ƙanwar ta dawo daga gida, sai su zama mutane su ce, ‘Ga kwanukanki nan. Ki ce muna yi mata sannu da aiki. Shi ke nan, sai yarinya ta ɗebi kwanuka ta tafi da su gida. Kullum haka, kullum haka.

    ‎Sai rannan yar ta yi shawara da ƙanwarta don su gudu gida. Sai suka yi ta haƙa rami, tun daga nan gidan har ya zuwa hanyar ƙofar garinsu. Suna ta bin rami da ita da ƙanwarta har suka je gida.

    ‎Iyayenta suka ce da ita, ‘Lafiya?’ Sai ta ce wa iyayenta, ‘Ashe dodanni ne? Ni ca na ke mutane ne.’ Shi ke nan. ƘurunƘus kan ɗan ɓera. Ba don ƙarya ƙarya ce ba, wa zai zuba  ruwa a jallo, jallo ya fashe kuma ruwan bai zube ba?

    ‎Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafi mai suna TATSUNIYOYI DA WASANNI wanda Ibrahim Yaro Yahaya ya wallafa.

    Danna nan don karanta Labarin Kalala Da Kalalatu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Hadisi Na Biyu A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    Hadisi Na Biyu A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Amr ɗan Asi (Radiyallahu Anhuma) haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Masu tausayi Allah mai rahama zai tausaya musu. Ku tausayawa na ƙasa da ku wanda yake sama da ku zai tausaya muku.

    Abu Dawud da Tirmizi ne suka rawaito shi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Hadisi Na Uku A kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Shugabanci A Musulunci (Hadisai Tamanin Da Biyu Akan Shugabanci) wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi domin karanta cikaken Littafin danna nan.

  • Falalar Salla A Masallacin Haramin Makka Da Madina

    Falalar Salla A Masallacin Haramin Makka Da Madina

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu anhu) ya ce: Haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) yace; “Salla a masallaci na ta fi salla a wani masallaci sau dubu ban da masallaci mai alfarma”(Bukhari 1190 Muslim 1394).

    An karɓo daga Abdullahi Ibn Zubair (Radiyallahu anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) yace: “Salla a masallaci na tafi salla dubu a sauran masallatai ban da masallacin harami, kuma salla a masallacin harami tafi salla dubu ɗari a wannan masallacin” (Ahmad, Ibn Khuzaimaha, Suhihul Jami’I 3841).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Zama A Madina Ya Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Sallar Idi danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Zikiri Kafin (Gabanin) Da Bayan An Gama Alwala

    Zikiri Kafin (Gabanin) Da Bayan An Gama Alwala

    Zikiri Kafin (Gabanin) Alwala

    “Bismillaahi”.

    {Da sunan Allah}.

    Zikiri Bayan An Gama Alwala

    “Ashhadu an laa ilaha illallahu wah dahu laa sharika lahu wa Ashhadu anna Muhammadu abduhu wa rasuluhu”.

    {Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaɗai, babu abokin tarayya a gare shi, kuma ina shaidawa cewa Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) bawansa ne kuma manzonsa ne}.

    “Allahumma ja’alnii minat-tauwaabina waj’alnii minal mutaɗahhiriina”.

    {Ya Allah! Ka sanya ni a cikin masu yawan tuba, kuma ka sanya ni a cikin masu tsarkaka}.

    “Subhanakal-laahumma wabi hamdika Ashhadu an laa ilaaha illaa anta wa astagfiruka wa atubu ilaika”.

    {Tsarki ya tabbata gare ka ya Allah tare da yabo gare ka. Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai kai, ina neman gafararka kuma ina tuba gareka}.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Zikiri Yayin Fita Daga Gida danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Ayyukan Gida Domin Taimako Juna danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Rasuwar Makaɗa, Sarkin Kiɗan Maradun Alhaji Musa (Ɗanƙwairo)

    Rasuwar Makaɗa, Sarkin Kiɗan Maradun Alhaji Musa (Ɗanƙwairo)

    Rasuwar Makaɗa, Sarkin Kiɗan Maradun Alhaji Musa (Ɗanƙwairo) Usman Ɗankwanagga a 1991.

    Sarkin Kiɗan Maradun, Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun, bayan wata gajeruwar rashin lafiya; Allahu cikin ikonsa ya karɓi rayinsa a ranar Juma’a 13 ga watan Satumba, 1991. Ya rasu a gidansa a Gidan Kano, Ƙaramar Hukumar Maradun, Jihar Zamfara.

    Allahu, karimun rahimun, ya daɗa haskaka makwancinsa, ya hore masa ni’imomi na Raudhatun min Riyadhil Jannah.

    Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo bawanka ne, ya sami shekaru talatin (30) izuwa ga jinƙanka; Allahu ka daɗa yafe kurakuransa, ka yi masa afuwa, ka kwantar da shi cikin Rahamarka, madauwamiya.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Takaiceccen Tarihin Rayuwar Dr. Yahaya Tanko danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatar Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Waƙa Mai Taken Gudumar Dukan Rashawa

    Waƙa Mai Taken Gudumar Dukan Rashawa

    1. Ya Allah sunanKa farko,

    Don aikina ya yi ƙarko,

    Har al’umma duk su farko,

    Mu kauce hanya mai duɗewa.

     

    2. Na yi salati gun sa Manzo,

    Wanda ya ce duk mu yi ƙwazo,

    Biɗar halal duk inda mun zo,

    Shi ne tafarki mai ɓulewa.

     

    3. Waƙa zan yi a kan halinmu,

    Wanda ya zam shi jiki gare mu,

    Tamkar umarnin khaliƙinmu,

    Mun ɗauke shi muna riƙewa.

     

    4. Yin rashawa ko toshe baki,

    Don kwaɗayin ai wani aiki,

    Wanda ya kauce wa tafarki,

    Albarkarmu yake ragewa.

     

    5. Guba ce wallah in ka karɓa,

    Ko ko ka bayar anka karɓa,

    Dokar Allah ce ka saɓa,

    Ƙin gaskiya hanyar ɓacewa.

     

    6. Mutunci farko zai zubewa,

    Aiki ya zam ba kyautatawa,

    Sai amaja da sukurkucewa,

    Al’amuranmu su dagulewa.

     

    7. Mai haƙƙi ne an hana shi,

    Wanda take mai kyau niyarshi,

    An ba mai bayar da toshi,

    Wanda niyarsa abar gujewa.

     

    8. Muddin an haka ba amana,

    Ba adalci sai hiyana,

    Sannan babu zaman lumana,

    Sai ɗar-ɗar sai firgicewa.

     

    9. Kwai rashawar daɗaɗa zance,

    Wata da aiki kan kasance,

    Wata jaka ce za a sunce,

    Ɗan hasafi a zamo yiwowa.

     

    10. Wata ko kyauta za a ba ka,

    Iyaye ko ko a ba wa ɗanka,

    Domin biɗar wani abu gun ka,

    Ka yarda ko ko ka zam ƙiyawa.

     

    11. Kowane nau’i ya haramta,

    Annabi ya tsine wa yin ta,

    Mai karɓa har wanda yai ta,

    Dai dai ne suke ba rabewa.

     

    12. Ga lamura yau sun ƙazanta,

    Harka duk an sassaka ta,

    An rufe duk munin sifarta,

    Sunanta an kyautatawa.

     

    13. Na yi tunanin me ya sa ne,

    Ba ƙyamar ta wurin mutane?

    Duk mai cin rashawa mu gane,

    Har mai ba shi abin gujewa.

     

    14. Rashin kishi ni a ganina,

    Shi ke sawa har a raina,

    Halali sai a ga wai kaɗan na,

    Sai an ɗora haram daɗawa.

     

    15. Duk mai kishi ga ƙasarsa,

    Mai kishin kuma al’umarsa,

    Ba ƙofar rashawa a gun sa,

    Siraɗi gobe yake wucewa.

     

    16. Son kai yai kanta a zuci,

    Tai tsatsa sassanta ya ci,

    Shi ke sa rashawa ake ci,

    Ba ƙyama sai ƙawatawa.

     

    17. Ƙyashin samu ga waninmu,

    Da ci da zuci ke hana mu,

    Yin haƙuri bisa matsayinmu,

    Wanda Ilahu ya zam rabawa.

     

    18. Sai haɗama sa har da wannan,

    Son a fiye wancan da wannan,

    Su ke sa rashawa ƙasar nan,

    In mun bar su tana gushewa.

     

    19. Yaƙin halayen ga dole,

    Kishin ƙasa mu riƙe shi lalle,

    Sai lamuranmu su sake lale,

    Albarka ta isa ga kowa.

     

    20. Irin haka ne manyan ƙasashe,

    Da ke amo kowane sashe,

    Na duniya suka yi koyaushe,

    Al’umarsu take ta shewa.

     

    21. Ba su barin azzalumina,

    Sun taushe maciya amana,

    Ba sa ƙyashin ikhiwana,

    Cima gabansu suke biɗowa.

     

    22. Dubi yawan jama’a ta Caina,

    Sun haɗa kai babu hiyana,

    Sun aiki a dare da rana,

    Yau kayansu muke shigowa.

     

    23. Turawa haka sunka dage,

    Duk aiki nasu babu coge,

    Cin rashawa duk sunka toge,

    Ba sa yin sa suna ƙiyawa.

     

    24. Don haka ne duk al’umarsu,

    Tai bunƙasa arziƙinsu,

    Yai albarka kowanensu,

    Na fahari da abin da kewa.

     

    25. Mu ma dole mu ɗaura niyya,

    Yin aiki ja mui gamayya,

    Kowa ya zo yara da manya,

    Mu ɗau rashawa izuwa kushewa.

     

    26. Niyya ƙwaƙƙwara mu ɗaura,

    Don yaƙar duk asharara,

    Masu zagon ƙasa masu ƙera,

    Turakun ci bayan da kewa.

     

    27. Ba wasu ne maciya amana,

    Ga dukiya ta ƙasa su danna,

    Wasoso sun ƙi su daina,

    Ha’intar mu suna ta yowa.

     

    28. Ƙaunar ƙasa ta zamo gabanmu,

    Don bunƙasar arziƙinmu,

    Da ci gaban duk jama’armu,

    Alheri ya isar wa kowa.

     

    29. Lallai mu so wa ɗan uwanmu,

    Abin da muke ƙauna ga kanmu,

    Ko ma mu fifita shi kanmu,

    Babu ganin ƙyashi da rowa.

     

    30. Doka mai tsanani a yo ta,

    Kan rashawa duk masu yin ta,

    A kame don sun yo mugunta,

    A kai wa Yari ya zam tsarewa.

     

    31. A nusarshe da dukan mutane,

    Munin aikin don su gane,

    Su ƙyamaci mai yi ko wane ne,

    Don ba son mu yake yiwowa.

     

    32. Azzalumai ku mu yo rahoto,

    Zuwa hukuma don a ƙwato,

    Haƙƙoƙi kowane loto,

    Ba tsoro ko razanewa.

     

    33. Mutum ne zai tono masifa,

    Ba shi ɗai ne za ta shafa,

    Har kowa dole mu dafa,

    Ɓarnatai mu zamo hanawa.

     

    34. Cin rashawa ke sa talauci,

    Aikin ɓarna ya yi kauci,

    Duk lamura saura su ɓaci,

    Dole mu yaƙar ba gazawa.

     

    35. Aikin kowa ne da kowa,

    Hukumomi ku mu tallafa wa,

    Domin ƙasarmu ta zamowa,

    Abar fahari ba ha’inawa.

     

    36. Hukumomin jin ƙorafinmu,

    Sun tsaye domin taimakon mu,

    Yaƙar kaskar da ka cin mu,

    Cima gabanmu suna hanawa.

     

    37. Mu roƙi Allah taimakonsa,

    Kan yaƙi bisa ‘yan ta’asa,

    Masu ciye rashawa su ƙosa,

    Da ha’inai ‘yan handamewa.

     

    38. Allah ba mu yawan ƙana’a,

    Ƙaunar juna da muru’a,

    Cin rashawa mu yi mai bara’a,

    Don Manzo ɗan Hashimawa.

     

    39. Nasiru G. Ahmad ya yi ta,

    Don harkar rashawa mu bar ta,

    Mu soyi juna mu rabauta,

    Halinmu ya zamo yabawa.

     

    40. Goma huɗu baitinta jumla,

    Ce Arba’in na gode Allah,

    Allah tsare mu biye ralala,

    Amin sarki mai iyawa.

     

    Danna nan don karanta Waƙa Mai Taken Masha-Jini

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waƙa Mai Taken Masha-Jini

    Waƙa Mai Taken Masha-Jini

    1. Allah ba ni buɗi in yi tsari na baituka,
    A kan ƙwaro wanda bai da tausai a duniya.

    2. Ƙwaron da yakan cutar da manya da ƙanƙana,
    Mai shanye jini na ɗan Adam ba shi tausaya.

    3. Gwanin zilliya yake da ɓoyo jikin tufa,
    Ko gashi na kai ya zam shi birni ya wataya.

    4. Gudun kar ku ƙosa Kwarkata ce nake nufi,
    Bai ƙyale baƙar fata fara ko ko rawaya.

    5. Abin da kan samar ta ƙazanta ce Lamba Wan,
    Haɗewar zufar jiki da dauɗa annakiya.

    6. Da wannan haɗi Allah kan samar da kwarkwata,
    Ta rayu tufar mutum gashin kansa kulliya.

    7. Tana sanya ƙwai ta ƙyanƙyashe shi da hanzari,
    Su zamto yawaita ɓamɓare ta akwai wuya.

    8. Abinci nasu jinin mutum za su yi ta sha,
    Ya kasa sukuni a dare ko ko safiya.

    9. Hanyar yaɗuwa tata kusantar jikin mutum,
    Da ya zam yana ɗauke da ta ko da sau ɗaya.

    10. Ko ko sanya rigarsa hula ko ko fattala,
    Hakan nan kwana da mai ita gun ɗaki ɗaya..

    11. Idan har ta samu sai a wanke dukan jiki,
    Da ruwa na kogi “Ma’ul Khalli” a gauraya.

    12. Mutum kan yi kwarkwata ba don ba shi tsaftace,
    Jikinsa sai Ibtila cire ta akwai wuya.

    13. Misali mutum Biyu cikin wanda anka wa,
    Busharar shiga Aljanna tun nan a duniya.

    14. Abdurrahamani Auf Sahabi attajiri,
    Zubairu ɗan Awwamu Sahabi abin biya.

    15. Allah ya jarabce su da ƙwaron ga kwarkwata,
    Tufarsu da gashin kai dare har da safiya.

    16. Har Manzo ya sauƙaƙa gare su halal yake,
    Rigar Alharini sunka sanya ta duniya.

    17. Hakan nan a Hajji ya halatta su aske kai,
    Su bayar da fiddiya ga nassin Ƙur’aniya.

    18. Dalili na Ukku nan ga samo na kwarkwata,
    Azaba ga kafirai su komo ga shiriya.

    19. Misali Fir’auna lokacin da ya kangare,
    Da shi da mutanensa ɓarna sun yi dulmiya.

    20. Aazabobin gargaɗi da anka saukar musu,
    Ciki har da kwarkwata jikinsu tufafiya.

    21. Har sai da sukai roƙon a janye ta za su bi,
    Musa Annabi ya roƙi Allah ta zam tsaya.

    22. Akwai wanda kwarkwata ba sa yin ta ko kaɗan,
    Luɗufi na Allah ne gare shi a duniya.

    23. Shi ne mai kuturta wanda ta ci yatsu nasa,
    Da ba yatsan kama ta gare shi ko da ɗaya.

    24. Ba a cin ta kwarkwata ƙwaro ne masha jini,
    Jini ko haramun ne umarnin kitabiya.

    25. Hakan nan abinci in ta faɗa ciki nasa,
    Ita da Kuɗin cizo barin cin sa lafiya.

    26. Jininta jikin tufar mai salla an sahhale,
    Ba ya ɓata salla ta dare ko ta safiya.

    27. Haka ma kashe ta nan a salla abin bari,
    Sai dai binne ta ka so ko ƙyale ta bai ɗaya.

    28. Ba a son a kamo ta a jefar abin ƙiya,
    Domin kar jikin wani ta hau tai ta wataya.

    29. Muna roƙon Allahu ya ƙare mu lafiya,
    Ya ije dukkan cuta gare mu baki ɗaya.

    30. Alfarmar Alƙur’ani da Sidi Muhammadu,
    Da an ba wa cetonmu a rana ta tambaya.

    31. A nan zan taƙaita ɗan bayanin da na shira,
    A kan kwarkwata masha jini babu tausaya.

    32. Sunana Muhammad Nasiru Garba Ahmadu,
    Almajir da ke biɗar sani kar ya sulmiya.

    33. Baitoci Talatin ne da Ukku ran Litinin,
    Alfaini da Isshirin Agusta yai gomiya.

    Alhamdu lillahi

    Karanta  Waƙa Mai Taken Nagartaccen Jagora

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waƙa Mai Taken Nagartaccen Jagora

    Waƙa Mai Taken Nagartaccen Jagora

    1. Da sunan Rabbana Karimi sarki guda,
    Da ke bayar da ɗaukaka daji ko gida,
    Da ya aiko wa duniya Ɗaha Muhammada,
    Da ya ɗora mu kan tafarki mara gargada.

    2. Baitoci ne nake nufin yi don shugaba,
    Babban masani kama tai ba a yi shi ba,
    Bai yarda a bar talakka halin ni-‘yasu ba,
    Bai mallaki duniya da ya bar bayansa ba.

    3. Shi ne ya zamo mujahidi rai ya ba da shi,
    Shi yat tari duk aradu ta faɗa kai nashi,
    Shi yai tsayuwar talakka komai a yiwo da shi,
    Shi yaj ja rundunar adalci a tsayar da shi.

    4. Ya samu amintatar dukan ‘yan Nijeriya
    Ya zam sane duk ƙasa Kudunta da Shimaliya,
    Ya zam jigo ƙasa da shi ne aka fariya,
    Ya rungumi duk talakka bai yarda da wariya.

    5. Na san wasu sun zaƙu shin waye a faɗa mana,
    Nagartaccen mutum nufina ba tsokana,
    Najeriya shi yake da siffar da na bayyana,
    Nasara garai suna da shayi har razana.

    6. Aminu Kano nake nufi ya san shari’a,
    Aikin da ya yi kawar da zaluntar jama’a,
    A neman ‘yantuwar ƙasa ya yi mubaya’a,
    A mulkin mallakar da Turai suka ɗabba’a.

    7. Mulkin mulaka’u sunka yaƙa da akai mamu,
    Mulkin kai sunka tabbatar ya samu ga mu,
    Mulki ya zamo ga ‘yan ƙasa don hidima wa mu,
    Mulki na Nasara ya tafi sai murna ga mu.

    8. Malam burinsa adalanci ba taƙama,
    Mai son a kawar da ɓangaranci ba haɗɗama,
    Mai son talaka ya tsira cuta bisa haƙƙuna,
    Maza mata lallai mu waye ba riggima.

    9. Ba za a yiwo batun siyasa ba a sa shi ba,
    Batun ‘yancin talakka malam na kan gaba,
    Ba za a faɗi gwagwarmayar haƙƙu a bar shi ba,
    Bangon talaka na jingina ban ga kamar sa ba.

    10. Bisa haka NEPU sun kafa haƙƙi don a bi,
    Biɗar talaka ya walwala babu tararrabi,
    Bisa haka sun wahaltu ɗauri kuwa bi da bi,
    Bi hamdillahi sun nasartu bisa martabi.

    11. Jamhuriya fari sun tsayu an ja sunka ja,
    Jan aiki ne sukai na sai da rayi ba amaja,
    Jari nasu lafiya da kutsen dukkan luja,
    Jama’a sun samu horuwa daga duk a ja.

    12. Karo na biyun jamhuriya an san ɗaukaka,
    Kafon P.R.P. jam’iya an tsayuwar daka,
    Karantarwar Aminu ta ratsa dawa ɗaka,
    Kano da Kaduna sun shiga tutar talaka.

    13. Haraji anka soke karɓar sa a nan jiha,
    Hakan nan jangali ka soke shi ba raha,
    Haƙiƙa talakanmu ya ‘yantu ya farraha,
    Harkoki sun yi kyautuwa don an sarraha.

    14. Malam ya kutsa takara an yi arangama,
    Matakin shugaban ƙasa yab biɗi yaz zama,
    Mai ba da abin Ilahu bai so bisa hikkima,
    Masoya nasa ya kafa manya sun zama.

    15, Fa mulkin lokacin Gawan soja da an kafa,
    Fahimtar daraja ta Malam mai falsafa,
    Fa an zaɓar Minista aiki ya yi kaifafa,
    Farar aniyarsa ta fito ta shiga duk kafa.

    16. Sanin haƙƙin nisa’u mata ɗan “ب” ya sa,
    Sahun farko biɗa ga haƙƙinsu shi ka sa,
    Samun ‘yanci na walwalarsu Malam ya sa,
    Saka su a gwamnati da saurran aikin ƙasa.

    17. Gogaggen malamin siyasa bai zam rago,
    Goran ƙarfe fagen sani maliya bai shigo,
    Goni a kitabu har da sunna kan ɓuɓɓugo,
    Goman fanni dubunsa Malam ba ya tago.

    18. Sun ɗaukaka ɗaliban da ya zam koyar da su,
    Sukul fannin siyasa sun zamto ba ya su,
    Su ne hulafa’u nasa har gobe muna da su,
    Sunansu ba zan kira al’umma ta san da su.

    19. Aminu Kano mutum da bai ƙyamar jama’a,
    Abin hannunsa bai bari sai ya wazza’a,
    Abin koyi tawali’u ga shi da ƙanna’a,
    Allahu Gwani ka tausasa mar mun addu’a.

    20. Lamarin harkar siyasa yau an sa ƙin kula,
    Lallai shiriyar Aminu in mun bi a hankala,
    Lagon matsalar da ke ciki har duka mushkila,
    Labari zai zamo gaba sai yin hamdala.

    21. Allahu ka kyautata makwancin mai jama’a,
    Aminu Kano garai rahama taka wassa’a,
    Aljanna ka sa ta zam gare shi ran Waƙi’a,
    Albarkar  Musɗafa ka tashe shi da fara’a.

    22. Nasir Ahmad ya yi ba a san ni ba ko’ina,
    Na dai zam mai biɗar sani ilmu na shinshina,
    Na gaishe da dukka kowa nai jinjina,
    Nai roƙo ga Rabbana ba mu yawan shina.

    Alhamdu lillahi.

    Danna nan don karanta Waƙa Mai Taken Kowa Ya Bar Gida…
    Edita@rumasau-kallamu

     

     

  • Waƙa Mai Taken Kowa Ya Bar Gida…

    Waƙa Mai Taken Kowa Ya Bar Gida…

    1. Suna na Allah farawa,

    Baiwarsa mun yo godewa,

    Yawan salati ƙarawa,

    Wajen Rasulu abin kewa,

    Gare mu ba ma fasawa.

    2. Batu nake son saƙawa,

    Kan duniyarmu ta Hausawa,

    Da ba shi kyautu mu mantawa,

    Tadarmu mai kyau da daɗewa,

    Da ayyukanmu na kyautawa.

    3. Sunanmu ya tafi nesawa,

    Da kyan halinmu na yabawa,

    Aikin fasaha da ƙwarewa,

    Abin amana mu tsarewa,

    Da gaskiya ba sauyawa.

    4. Tsarin shigarmu gwanin ƙawa,

    Da kwarjini ba kushewa,

    Kowa ya gan mu yana shawa,

    Duk duniya tai shaidawa,

    Kyawun ɗabi’un Hausawa.

     

    5. Tsarin sarautun mulkawa,

    Mun yi fice mun tserewa,

    Mun gaji wannan da daɗewa,

    Har yau muna ta kiyayewa,

    Don kar su zam salwancewa.

    6. Zumuntaka mai ɗorewa,

    Haƙƙin zumunci sadawa,

    Ƙauna ga juna aikawa,

    Kullum muna sabuntawa,

    Da ƙin zumunci yankewa.

     

    7. Mun yi fice gun kyauta wa,

    Dukkan maƙwabta ba rowa,

    ‘Ya’yanmu duk babu rabewa,

    Tare muke tarbiyyarwa,

    Sashensu ba fifitawa.

    8. Kowa yana da abin yowa,

    Yara ga tarbiyyantarwa,

    Ba ware Bora ko Mowa,

    Babu batun wannan nawa,

    Don me ka bi shi ka mar tsawa?

     

    9. Kowa sana’a ka riƙewa,

    Don al’uma amfanawa,

    Mu ke saƙa tufar sawa,

    Mu zam rina ta ta yi ƙawa,

    Kafin mu kai ta ga ɗinkawa.

    10. Mu jeme fata tsafcewa,

    Mu yo jaka takalmawa,

    Taiki Kube da Zabirawa,

    Har da su Banten ɗaurawa,

    Domin mu kare tsiraicewa.

     

    11. Abinci mu ke nomawa,

    Mu taskace mai saidawa,

    Kowa ya ƙoshi ba yunwa,

    Nama muna kiwantawa,

    Muna fita mu farautowa.

    12. Ba mai zama haka Hausawa,

    Kowa sana’a tai kewa,

    Zama na banza ba maiwa,

    Wanda ya ɗau sangarcewa,

    Ba zai yi matar aurawa.!

     

    13. Zaman iyalinmu da ƙawa,

    Kwai disfilin adaltawa,

    Yara ba a bambancewa,

    Ɗan kishiya ma ka riƙewa,

    Tamkar uwar da ta haifawa.

    14. Akwai haɗin kai da gamewa,

    Idan larura ta zo wa,

    Wani guda ba kasawa,

    Taro ake don a kawarwa,

    Cike da ƙauna tausawa.

     

    15. Yara biyayya sunke wa,

    Duk babbuna babu rabewa,

    Yi na yi bar shi su dainawa,

    Su kuwa manya tausawa,

    Ga yara sunka zamo yowa.

    16. Kaɗan na yo lissafawa,

    Na kyan zamewar Hausawa,

    Da munka gada da daɗewa,

    Da ya wajabtu mu danƙewa,

    Domin na baya su tararwa.

     

    17. Abin takaici da ƙiyawa,

    Halin ga ‘yan yau ka gujewa,

    Na martabarmu ta nunawa,

    Don taƙamar sun wayewa,

    Hanyar ba za tai ɓullewa.

    18. Dolenmu mui jajircewa,

    Ga raya tada mu riƙewa,

    Shi ne tafarkin burgewa,

    Kayan aro mu yi watsarwa,

    Don katara ba shi rufewa.

     

    21. Allah ka ba mu amincewa,

    A nan da ranar komawa,

    Duk laifukanmu ka yafewa,

    Don Musɗafa mai shiryarwa,

    Manzo da ka zam aikowa.

    22. Nasiru G. suna nawa,

    Ɗan Ahmad babu musawa,

    Birnin Kano na zamtowa,

    Nai shukura na yi daɗawa,

    Waƙar a nan ta yi tuƙewa.

    Wannan waƙa an ciro ta ne daga littafin TASKIRA wanda Nasiru G. Ahmad Ya wallafa.

    Karanta Waƙa Mai Taken Ɗan Achaɓa