Tag: yadda ake

  • Maƙala Mai Taken Tsattsafin Fanɗare wa Addinin Musulunci: Wata Yasasshiyar Gona a Gandun Waƙoƙin Baka na Hausa

    Maƙala Mai Taken Tsattsafin Fanɗare wa Addinin Musulunci: Wata Yasasshiyar Gona a Gandun Waƙoƙin Baka na Hausa

    Tsattsafin Fanɗare wa Addinin Musulunci: Wata Yasasshiyar Gona a Gandun
    Waƙoƙin Baka na Hausa

    Adamu Rabi’u BAKURA1, Abu-Ubaida SANI
    Department of Languages and Cultures, Federal University, Gusau, Zamfara State, Nigeria

    Tsakure: Rubuce-rubucen nazari da aka yi game da waƙoƙin Hausa sun fi shurin masaƙi. Duk da haka, mafi yawan rubuce-rubucen sun karkata ne kan zaƙulo fasahohi da ke cikin waƙoƙin tare da nuna yadda suke faɗakarwa da ilimantarwa da nishaɗantarwa. Wannan takarda na da fahimtar cewa an bar wani babban giɓi wanda shi ne nazarin fanɗare wa dokokin addini cikin waƙoƙin Hausa.

    Maƙalar nan na da manufar binciko muhallan da ɗiyan waƙoƙin baka na Hausa suka keta
    dokokin da Allah ya shimfiɗa wa bayinsa. An tattara bayanai ta hanyar sauraron waƙoƙin da tsamo misalan ɗiyan waƙoƙin da abin ya shafa, tare da ciro hukunce-hukuncen da suka yi bayani kansu daga Alƙur’ani da hadisan manzon Allah.

    Binciken ya fahimci cewa, akwai tarin misalan fanɗare wa addini a cikin waƙoƙin baka na Hausa. Daga ƙarshe an ba da shawarwarin da suka haɗa da ɗaukar matakan da suka dace domin tabbatar da ire-iren waƙoƙin ba su yi tasiri wajen gurɓata tarbiya nagartacciya ba.

    Fitilun Kalmomi: Waƙoƙi, Addini, Musulunci, Fanɗarewa

    GABATARWA

    Musulmi ba a bar shi kara zube ba. An kafa masa sharuɗɗan tafiyar da rayuwa dukkanta. Ire-iren waɗannan sharuɗɗan suna ƙunshe cikin littafin Allah (Alƙur’ani) da Hadisan Annabi S.A.W. Daga cikin dokokin akwai na tilas, wato abin da Musulmi mai hankali ba zai iya rabuwa da shi ba, komai tsanani.

    Akwai kuma abubuwan ƙi, wato waɗanda ba a so Musulmin ya aiwatar da su ba. Haka akwai haramun, waɗanda aka hana mutun ya aikata su. Idan dukkannin rayuwar mutum ta kasance cikin ɗa’a, kuma ya nisanci saɓo, babu shakka ya kiyaye dokokin Allah Maɗaukakin Sarki.

    A gefe guda kuwa, kamar yadda Chiromawa, (n.d. p. 5-10) ya bayyana, ko da addinin Musulunci ya iso ƙasar Hausa ya tarar da al’ummomi da dama suna aiwatar da kaɗe-kaɗe da waƙe-waƙe nau’i-nau’i da suka haɗa da:
    i. Kiɗan sana’a
    ii. Kiɗan jawo hankali
    iii. Kiɗan lallashi (rarrashi)
    iv. Kiɗan faɗakarwa

    v. Kiɗan zaburarwa
    vi. Kiɗan ƙarfafa zuciya
    vii. Kiɗan jaruntaka
    viii. Kiɗan farin ciki
    ix. Kiɗan ibada

    Duk ire-iren waɗannan kaɗe-kaɗe akan haɗa su ne da waƙe-waƙe. Kasancewar addinin Musulunci, addini ne mai sauƙi da sauƙaƙa wa mabiyansa, bai haramta waɗansu daga cikin nau’ukan kaɗe-kaɗe ba. Ya dai kawo gyare-gyare domin kare mutunci da martabar
    mabiyansa. Ya haramta shi ne yayin da aka aiwatar da abin da Allah ya haramta a cikinsa.

    Hasali ma akwai wuraren da Musulunci ya sunnanta kiɗa da waƙa, kamar a lokuttan ɗaura aure, tamkar yadda Imamu Buhari ya bayyana a “Babin Kaɗa Ganha” a ranar aure da walima. Bayan haka, akwai ranar kai amarya ɗakin mijinta, da ranar idi da ranar suna, da ranar zuwan wani shugaba da ranar komawarsa, da ranar kaciya (kugunu/kuidu).

    Akwai hadisai waɗanda Buhari da Muslim da Tirmizi da Hakimu da Nisa’i suka rawaito da ke nuni ga halaccin kiɗa da waƙa a babin aure da sallar idi. Halaccin kan tabbata ne matuƙar bai haɗa da alfasha ko motsawa zuwa ga saɓon Allah ba. A bisa wannan ne, maƙalar ta ƙuduri aniyar yin ƙwarya-ƙwaryar bincike a muhallan da makaɗan baka na
    Hausa suka keta ƙa’idojin da Allah ya shata ta hanyar kauce musu.

    Duk wasu ɗiyan waƙa da makaɗi ya yi za a yi ƙoƙarin kawo shi tare da auna shi da ma’aunin shari’a da aka ciro daga nassin Alƙur’ani da Hadisan Annabi S.A.W. domin tabbatar da hasashen. Ana iya samun ɗiyan waƙoƙin da ke ƙunshe da gurbin fanɗara a waƙoƙin makaɗan sarauta, da na jama’a da na maza da sauransu, kamar yadda za a gani ɗaya bayan ɗaya.

    Dabarun Gudanar Da Bincike

    Kadadar wannan bincike ta taƙaita ne ga waƙoƙin baka na Hausa a farfajiyar koyarwar addinin Musulunci. A ɓangaren waƙoƙin an ɗauko ɗiyan waƙoƙi da aka tattauna kansu kai tsaye ta hanyar sauraron odiyoodiyo da kallon bidiyoyinsu.

    A ɓangaren hukunce-hukuncen addinin Musulunci kuwa, an ɗauko su kai tsaye daga cikin Alƙur’ani mai tsarki da hadisan Manzon Allah (S.A.W.) ingantattu. An kuma nazarci rubuce-rubucen masana da manazarta a wannan fannin inda suka haska hanya ga binciken.

    Fanɗare wa Koyarwar Musulunci ta Hanyar Zambo

    Makaɗan saurauta sun shahara wajen yin zambo, domin ƙawata waƙoƙinsu. Masana da dama sun bayyana ma’anar zambo gwargwadon fahimtarsu. Gusau, (1984 p. 37) ya tafi kan cewa “Akan yi zambo don adanta waƙa da muzanta wanda ke hamayya da wanda ake yi wa waƙa.” Abba da Zulyadaini, (2000 p.63) sun bayyana zambo da cewa: “… nau’i ne na muzanta mutum ta hanyar ƙasƙantar da shi, ko wulaƙanta shi, domin a baƙanta masa tare da dusashe masa kwarjini a idon jama’a.

    Mawaƙan sun fi shahara da zambo don su aibanta duk wani ɗan sarki da ke ja da ubangidansu. Muhammad, (2005) kuwa na da ra’ayin cewa zambo zagi ne kai tsaye,
    … saboda akan ba da hoton wanda ake yi wa tare da bayyana cikakkiyar sifarsa ta hanyar ambaton duk wani abu da ya dace da shi. A lokacin da aka yi ma wani zambo akan fito da hotonsa ne zahiri, ta yadda duk wanda ya san shi zai gane cewa da shi ake. Muhammad, (2005 p. 28)

    A taƙaice kenan, zambo yana ƙunshe da ma’anar ƙaga wa mutun magana wadda za ta muzanta shi ta ɓata masa suna ba tare da bayyana wanda ake yi wa ba. A dubi misalin zambon da Alhaji Musa Ɗankwairo ya yi wa wani ɗan sarautar Tsafe:

    Kun san zamanin ga ya canza,
    Ga wani ɗan sarki da kandaye,
    Ya shaho hoda kamar Delu.
    (Ɗankwairo: Waƙar Sarkin Tsahe).

    Wannan zambon da Ɗankwairo ya yi wa ɗan sarki ya kai matuƙa wajen aibanta ɗan sarkin ta hanyar kamanta shi da ɗan daudu. Hakan ba ƙaramin muzantawa da dushe masa kima ya yi a idon al’umma ba. Tabbas kuwa hakan ya saɓa wa dokokin addinin Musulunci. An umurci Musulmi da ya tsare (kame) harshensa da yin furucin abin da bai halatta ba, kamar keta mutuncin ɗan uwansa Musulmi ba tare da wani abu mai wajabtawa ba na shari’a. Allah na cewa:

    Lalle Allah na yin umurni da adalci da kyautatawa, da ba wa ma’abocin zumunta kuma yana hani da alfasha da abin ƙi da zalunci. Allah yana yi muku gargaɗi ko da kuna tunawa. (Surar Nahli: 16:90).

    Idan aka dubi wannan ayar za a tarar ta yi hani ga yi wa wani mugun baki (mugun fata), sannan ta yi hani ga alfasha. Ya kuma yi umurni da tausayawa tare da yin abu bisa gaskiya. Daga ƙarshe ta yi hani a kan ha’intar wani ta kowane ɓangare. Wannan na iya
    kasancewa ta hanyar lafazi ko a aikace. Ta la’akari da wannan ɗiyar waƙar, za a tarar mawaƙin ya kauce wa dokar da Allah ya ɗora masa.

    Annabi S.A.W. Ya Ce: Haƙiƙa, mafi sharrin mutane a matsayi wurin Allah a ranar alƙiyama shi ne wanda mutane suka ƙyale shi don ƙiyayyar alfasharsa. (Muslim ya ruwaito). Wanda duk wani mawaƙi ya yi wa zambo, to zai guje shi tare da yin kaffa-kaffa da al’amarinsa.

    Sau da yawa akan ba su kyauta ne bisa tilas don gudun zambonsu. A irin wannan yanayin idan aka nazarci hadisin, za a ga a nan ma sun kauce wa koyarwar Annabi
    S.A.W. A wani Hadisin kuwa Annabi (SAW) cewa ya yi: “Mumini bai kasancewa mai yawan suka ba ko yawan la’anta ko yawan alfasha, ko mai sakin harshe” (Tirmizi
    ne ya ruwaito shi).

    Wannan hadisin ya fito ƙarara ya bayyana mana cewa, duk mawaƙin da ya ba da gaskiya
    ga Allah da ranar lahira da manzancin Annabi S.A.W., zai kasance mai bin dokokin Musulunci kamar yadda suke. Hakan kuwa zai sanya ya guji yi wa Musulmi zambo.
    Akwai misalan wuraren da makaɗan jama’a suka yi wa abokan hamayyarsu zambo ta hanyar zagi kai tsaye.

    A irin wannan lamari ne mawaƙin jama’a kan fito da halayen mutun a fili, sannan ya zage shi. Misali, a waƙar “Gagara Badau,” Alhaji Mamman Shata cewa ya
    yi:
    Shata: Allah ya tsine ma tsohon mazinaci,
    Amshi: Gagara badau namiji tsayayyen ɗan kasuwa.
    Shata: Allah ya tsine ma da kai da iyalinka.
    Amshi: Gagara badau namiji tsayayyen ɗan kasuwa.
    Shata: Yanzu babban ɗan bai gani,
    Amshi: Gagara badau namiji tsayayyen ɗan kasuwa.
    Shata: Babban jikanshi kuma yana kama agwaginmu,
    Amshi: Gagara badau namiji tsayayyen ɗan kasuwa.
    Shata: Gida ya lalace.
    Amshi: Gagara badau namiji tsayayyen ɗan kasuwa.

    Dubi yadda Shata yake zagin wani basarake tare da nuna ɗansa ya makance, ya kuma kira jikansa ɓarawon agwagi. Wannan ba ƙaramar fanɗarewa ba ce, domin a shara’ar Musulunci an umurci Musulmi da ya kiyaye da yin zance da bai halatta ba, kamar ƙarya, da zage-zage da keta mutunci Musulmi. Allah na cewa: “…Kuma yana hani da alfasha da abin ƙi da zalunci. Allah yana muku gargaɗi ko da kuna tunatuwa.” (Alƙur’ani,
    Suratul Nahl, 16:90).

    Fanɗare Wa Koyarwar Musulunci Ta Hanyar Habaici

    Habaici ko gugar zana salo ne ko azancin yi da wani a kaikaice ta yadda sai wanda ya san shi kuma ya san abin da ake magana game da shi ne kaɗai zai iya ganewa. Habaici wata hanya ce da makaɗan baka suke amfani da shi a cikin waƙoƙinsu domin ƙara musu
    armashi, ta hanyar ƙasƙantar da wani mutun ko kuma muzanta shi ko su zage shi ko kuma su soka masa wata magana a kaikaice. Misali, a cikin waƙar Mai Dubun
    Nasara Sardauna, Alhaji Musa Ɗankwairo yana cewa:

    Ga kare ga kura kowane ya hangi wani,
    Ga aura ya koma,
    Wagga nan hanya ba mu ga wurin wali ba.
    (Alhaji Musa Ɗankwairo, Waƙar Mai Dubun Nasara, ta Sardauna).

    Yayin da aka dubi ɗiyar wannan waƙar za a ga yadda Ɗankwairo ya siffanta Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato da kura. Ya yi hakan ne domin bayyana irin ƙarfinsa kamar yadda kura ke da shi. Wannan kuwa ya shafi yadda take iya tauna ƙashi da kuma kwarjini da waibuwarta na sanya rashin kuzari ga halittar da ta tunkare ta.

    A gefe guda kuwa, sai ya kira wanda yake yi wa habaici da kare, saboda ba sa zama
    inuwa ɗaya da kura. Hasali ma kare ba ya hangen nesa sosai, kuma mai gidansa yakan yi amfani da shi ne wajen farauta. Kiran mutun kare ba ƙaramin ƙasƙantarwa ba ne
    a al’adance. Wannan ne ya sa makaɗan baka sukan siffanta waɗanda suke son wulaƙantawa da kare saboda nhalayyarsa da ɗabi’unsa.

    Musulunci ya hana keta mutuncin Musulmi ko wulaƙanta shi ko zagin sa ko laƙa masa munanan sunaye, ba tare da haƙƙin shara’a ba. Allah na cewa: “… kuma kada ku jefi juna da miyagun sunaye” (Alƙur’ani, 49:11). Idan muka dubi wannan ayar, za mu ga cewa ta hana a kira Musulmi da sunan da zai kasance tamkar zagi ne gare shi. Yin haka kuma fanɗare wa umurnin Ubangiji ne.

    Annabi S.A.W. ya ce: “Zagin Musulmi fasiƙanci ne, kuma yaƙar sa kafirci ne” (Buhari da Muslim ne suka ruwaito shi). Idan aka dubi wannan hadisin cikinsa da
    wajensa, aka kuma nazarci ɗiyar waƙar da ta gabata, za a tarar cewa, makaɗin ya kauce wa faɗar Annabin S.A.W., ya yi gaban kansa. Yin haka fanɗarewa ne ga dokokin addinin Musulunci.

    Bin dokoki da ƙa’idojin Musulunci kuwa dole ne, inda har Allah ke cewa: “Kuma abin da Manzo ya zo muku da shi, to ku riƙe shi, kuma abin da ya hane ku, to ku hanu” (Surah Al-hashr, 59:9).

    Fito-Na-Fito Da Koyarwar Muslunci

    Akwai misalan inda mawaƙa ke amfani da wasu kalmomin da suka kauce wa ƙa’idojin addinin Musulunci. Akan samu irin wannan fito-na-fito a fannonin da suka shafi sahihan aƙidojin da suka danganci ranar lahira, da matsayin mala’ikun Allah da makamantansu. Ya kuma haɗa da dokoki da ƙa’idojin addinin Musulunci ta fuskar hani da horo. Wannan
    ɓangare na aikin zai mayar da hankali wajen zaƙule irei-ren waɗannan misalai:

    Izgilanci

    Izgilanci ga abubuwan da addini ya zo da su nanuni ga halin ko-oho ga lamarin addinin. Musulunci kansa ya tsawatar da riƙo da dokokin da ke ƙunshe cikinsa ba tare da wargi (wasa) ba. Duk da haka, akan samu wuraren da mawaƙa suka yi izgilanci ga lamarin
    addini. Alhaji Muhammadu Ɗan’anace a waƙar Shago yana cewa:

    Jagora: In da lahira ana kasa dambe…
    ‘Y/Amsohi: Da Walakiri ya ji ƙwal ga gaba nai.
    Jagora: Duk wanda bai yi kallon Shago ba,
    Aradu yana da sauran kallo,
    Ya zaka duniya kamar bai zo ba,
    Kamar zuwan kare ga aboki,
    Tamkar mutum ya mari budurwa,
    Ko ya mutu ba a gafarta mai.

    In aka dubi wannan ɗan waƙar, za a tarar cewa, wannan makaɗin ba ƙaramar kasada ya yi ba. Ya nuna rashin jin tsoron aukawar wani haɗari (hatsari) ko shiga cikin abin da bai san sakamakonsa ba. Allah na cewa: “Kuma kada ka bi abin da ba ka da ilimi a kansa.” (Surar Isra’i, 17:36).

    Idan muka nazarci wannan ayar, za a ga yadda Mahaliccin sammai da ƙassai ya faɗakar da masu imani da su yi kaffa-kaffa ga dukkan lamarin da ba su san haƙiƙanin yadda yake ba. Ko bayan batu kan abin da mutum bai sani ba, batutuwan da ke ƙunshe cikin ɗiyar
    waƙar na tattare da izgilanci ga abin da ya shafi imani da mala’iku da ranar ƙiyama.

    Goyon Bayan Karuwanci

    Kalmar karuwa, suna ne na mace. Jam’i kuwa shi ne karuwai. Karuwa na nufin mace mai zaman kanta wadda mazan banza ke neman ta su ba ta kuɗi domin saduwa (zina) da ita. Zina kuwa tana nufin saduwa (jima’i) da matar da ba ta halatta ga mutum ba ta hanyar aure, wato wadda ba matarsa ba. Tun kafin bayyanar Musulunci a farfajiyar
    ƙasar Hausa, Bahaushe ya ƙyamanci zina.

    Don haka karuwanci bai samu bagiren zama ba, balle a yi zina. Duk da kasancewar akwai al’adar tsarance, a inda saurayi kan gayyaci budurwarsa ta je ɗakinsa har ma ta kwana. Sakamakon irin wannan al’adar ce, ya sanya su amfani da al’adun tsafi domin tabbatar da amarya ba ta taɓa sanin wani ɗa namiji ba (zina) kafin a yi mata aure. A irin
    wannan al’adar ce, idan yarinya ta san maza kafin a yi mata aure, za ta kunyata a cikin jama’a.

    Idan kuma ta ɓoye ba ta faɗa ba, ta mutu, kamar yadda Ibrahim, (1985 p. 5) ya nuna.
    Yayin da addinin Musulunci ya bayyana, sai ya haramta zina. Hasali ma ya sanya ta cikin manyan laifuka, bayan kafirci, wato haɗa Allah da wani da kashe ɗan Adam. Allah yana cewa: “Kuma kada ku kusanci zina, lalle ne ita ta kasance alfasha ce kuma ta munana ga zama hanya” (Alƙur’ani; Suratul Isra’i, 17:32)

    Haka kuma Musulunci ya yi ƙoƙarin toshe duk wata kafa da za ta iya zama sanadin aikata zina ta hanyar wajabta wa mata sanya hijabi. Sanya hukuncin jefe mazinaci da mazinaciya har su mutu a bainar jama’a, idan sun yi aure, ko a yi musu bulala idan ba su taɓa yin aure ba, na nuni da girman zunubin. Duk da wannan umarni na Ubangijin talikai da kuma uƙubar da aka tanadar wa mazinata, sai aka sami wani mawaƙi da ake kira Habibu Sakarci ya yi wa wata karuwa waƙa.

    A cikin ɗiyan waƙar yana cewa:
    Jagora: Shehuwar mata Safiya Kano, Ta gidan ‘Yajja
    Safiya Kano.
    Jagora: ‘Yan birni roƙo suke, Allah ba mu jaka bakwai,
    Mu gano ɗakin Safiya Kano.
    Jagora: Direbobi ma roƙo suke, Allah ba mu jaka
    bakwai, Mu gano ɗakin Safiya Kano.
    Jagora: Mutan birni yanga suke, Domin darajar Safiya
    Kano.

    Yayin da aka nazarci ɗiyan waƙar, za a ga cewa Habibu Sakarci yana tallar wannan karuwa ta hanyar bayyana ta a matsayin ƙasaitacciyar karuwa. Har ma ya nuna ‘yan birni da dirobobi na burin Allah ya ba su kuɗi masu yawa, don su tafi ɗakinta. Hasali ma ya bayyana ta fi sauran karuwan birnin kyau. Wannan ba ƙaramar fanɗara ba ce da keta dokokin Allah.

    Ya zo cikin hadisi
    Annabi S.A.W. yana cewa: Lalle ana rubuta wa ɗan’adam rabonsa daga
    zina, kuma lalle mai risker sa wancananka ne babu makawa. Idanu zinarsu ita ce kallo, kunnuwa kuwa zinarsu ita ce sauraro, harshe kuwa zinarsa ita ce zance. Hannuwa kuma zinarsu ita ce damƙa, ƙafa kuma zinarta ita ce taku, zuciya kuwa saƙa soye-soyenta ne, kuma tana guranta su, farji yana gaskata wancananka ko ya ƙaryata (Buhari da Muslimu ne suka ruwaito hadisin).

    Duk da irin waɗannan nassoshin Alƙur’ani da hadisan Annabi S.A.W., sai ga ya makaɗa na fanɗare musu ta hanyar gayyatar al’umma zuwa ga aikata fasiƙanci. Shi ma Alhaji Mamman Shata ya yi makamanciyar wannan waƙar, a inda ya yi wa wata mata da ake kira Karo Oma:
    Jagora: Duk ɗan birnin da ya riƙa,
    Ni kar ya yi mini yanga,
    In yana so ya isa
    In gan shi gidan Kara Oma.
    (Alhaji Dakta Mamman Shata: Waƙar Kara Oma)

    A nan Shata ya fito ƙarara ya tura ‘yan birni su tafi gidan wannan karuwa idan har sun isa. A ɗaya ɓangaren kuwa cicciɓa ta ya yi da cewa, sai manyan mutane wayayyu ne kawai suka isa su yi hulɗa da ita. Wannan waƙar ba abin da ya raba ta da fanɗare wa
    dokokin Allah da ya shata wa Musulmi.

    A shara’ar Musulunci, an san Musulmi da kunya. Hasali ma kunya tana cikin halayensa, kuma tana daga cikin Imani. Imani kuwa shi ne aƙida da rayuwar Musulmi. Manzon Allah yana cewa: “Kunya da imani suna zozozo da juna. Idan babu ɗayansu, ɗayan ma ba za
    a same shi ba” (Buhari da Muslim ne suka ruwaito shi).

    Goyon Bayan Shan Giya

    Giya, kalmar suna ce da ke cikin jerin sunaye jinsin mata. Ita kuma nau’i ce da ake yi da hatsi ko alkama ko inibi wadda ake sha a yi maye. Ana kuma kiranta barasa, kamar yadda ƙamusan CNHN (2006 p.168) ya nuna. Shan giya a tsakanin al’ummar Larabawa kafin bayyanar Musulunci abu ne sananne. Shi ne ƙashin bayan doron ginin tattalin arzikinsu, kuma giya na daga cikin kayan fataucinsu.

    Har matansu sun kasance shahararru wajen haɗa ta. Hasali ma kowane gida akan
    same ta. Wannan ya sa har suna yabon giya a cikin waƙoƙinsu. Su ma al’ummar Hausawa ba a bar su a baya ba, domin sun mayar da shan giya musamman a lokuttan
    bukukuwan aure da na haihuwa tamkar ƙawa. Yayin da suka samu rabauta na karɓar addinin Musulunci, sai suka guje ta a sakamakon hanin da addinin ya yi gare su.

    Kasancewar Musulunci addini ne mai sauƙi da ke ƙunshe da dabarun magance abubuwan da ke haifar da fitsara da ta’addanci a tsakanin al’umma, sai ya fara bayyana wa muminai rashin kyanta. Daga nan kuma ya hana kusantar wurin ibada yayin da aka sha ta Daga ƙarshe ne kuma ya sauƙar da hani kai tsaye game da shan giya inda aka ce:
    “Ya ku waɗanda suka yi imani, ku sani cewa, giya da caca da gumaka da ƙyaurayen duba ƙazanta ne daga aikin shaiɗan, sai ku nisance su don ku rabauta
    (Alƙur’ani; 5:90).

    A wannan ayar an bayyana wa masu imani munanan ayyuka da ake buƙatar mumini ya nisance su. Kuma duk al’ummar da ta rungume su za ta faɗa cikin masifa da rashin kwanciyar hankali. Ayar ce kuma ta zo da haramcin shan giya kai tsaye. Akwai hadisai da dama da suka tabbatar da haramcin shan giya da kuma abin da ake kira da giya.
    Annabi S.A.W. yana cewa: “Duk abin da ke bugarwa giya ce, kuma kowace irin giya haramun ce” (Muslim ne ya ruwaito shi).

    A Wani Hadisin Kuwa Cewa Ya Yi: Allah ya tsine wa giya, masu shan ta, da waɗanda suka zuba ta, da waɗanda suka sai da ita, da waɗanda suka saye ta, da waɗanda suka tatso ta, da waɗanda suka ɗauki kayan da ake tatsarta, da waɗanda suke ɗauke ta, da waɗanda aka kai wa ita, da waɗanda suka samu kuɗi a gare ta” (Abu Dawuda, da Al-Hakem a isnadi ingantacce, suka kawo shi)

    Yayin da aka dubi waɗannan nassoshi, za a tarar cewa, ƙin bin su sau-da-ƙafa keta shara’ar Musulunci ne, wato fanɗarewa faɗar Allah da annabinsa ne. Duk da haka, an ci karo da waƙoƙin da suka yi kira da a sha gida. Alhaji Mamman Shata Katsina ya waƙe giya. Har ma cewa ya yi:

    Jagora: Ka ji karatun masu bugun ruwa, Waɗanda…
    ‘Y/Amshi: Ke zikiri a Kuloniya, A sha ruwa ba laihi ba ne.
    Jagora: A nan muke sallarmu ta Juma’a, Mu tattara kayanmu mu kai Neja, Ku sha ruwan nan…

    Y/Amshi: Ba laihi ba ne, A sha ruwa ba laihi ba ne.
    Jagora: Ruwa na kwalba ba laihi ba ne, Ai kun ga…
    ‘Y/Amshi: Alhaji Shata sha yake. A sha ruwa ba laihi ba ne.
    Jagora: Yara mu koma wasa Kuloniya, Mu tashi kana
    mu koma Neja,
    ‘Y/Amshi: Nan ne muke zikirinmu na Juma’a. A sha
    ruwa ba laihi ba ne.
    Jagora: Malam ka sha ai ba laihi ba ne, Ga taka ga tau…
    ‘Y/Amshi: Kowa ya aje. A sha ruwa ba laihi ba ne.

    Idan muka nazarci waɗannan ɗiyan waƙar za a ga yadda mawaƙin ya yi fito-na-fito da dokokin Allah da Manzonsa. Allah ya haramta, shi kuma ya halatta. Dubi yadda mawaƙin ya ce a sha giya ba laifi ba ne, bayan Annabi S.A.W. ya ce kada a sha, a inda yake cewa:
    “Kada ku haɗa fulawa da dabino gaba ɗaya, kuma kada ku haɗa busasshen tafarnuwa da dabino sam-sam, ku bar su idan an niƙa su.”

    Yayin da aka niƙa su, nan take suna bugar da wanda ya sha su. Don haka ne Annabi ya umarci masu imani da kada su sha a haɗe yayin da suke niƙe, kamar yadda Munhajul Muslimu Jadawali na uku: Abinci da Abinsha ya nuna. Hasali ma mawaƙin ya bayyana cewa shi ma yana shan giyar tare da yaransa. Akwai hadisai da dama da suka nuna haɗarin Musulmi ya mutu yana shan giya, ko da bai halatta ta ba.

    To ina ga wanda ya halatta shan ta? Daga cikin ire-iren waɗannan hadisai akwai wanda
    Ibni Abbas ya ce: Manzon Allah S.A.W. ya ce: Duk wanda ya mutu yana cikin ɗabi’ar shan giya bai tuba ba, zai tarar da Ubangiji Allah Maɗaukakin Sarki tamkar wanda ya bauta wa gumaka (Muslim ne ya ruwaito wannan hadisin).
    A wata waƙar ta mawaƙin da ake kira Horo/Horu, an ga baitukan da suka nuna ba laifi ba ne shan giya da ma cin mushe. Mawaƙin na cewa:

    Jagora: Arnaaa ku sha giya ku ci mushe, Aljanna mai rabo zai sama.

    A wani wuri kuwa, har ya nuna ma kashi ne ga mutum ya sha giya ‘yar kaɗan kuma ta wahalshe shi. Yana cewa:

    Jagora: Kowa ya sha giya yai yi amai, Ba ɗan halas ba ne, shege ne!
    Jagora: Su wane ‘yan giyan ƙarya ne, Shegu, kwalba guda take ka da su.

    Don karanta Tarihin Garin Rimin Gado danna nan

    Goyon Bayan Sata

    Abubakar (2015, p. 431) ya bayyana cewa, sata “tana nufin ɗaukar abin wani ba da saninsa ko izinin ba. ”Sata na nufin ɗaukar wani abu da hukuncin shari’a ko hankalin tuwo bai mallaka wa wanda ya ɗauka ba, tare da amfani da shi ko musanyensa da wani abu mai daraja kwatankwacin na kuɗi ko kuma mai amfanarwa, ba tare da izinin wanda ko waɗanda ke da mallakin abun ba.

    Sata ta kasu zuwa nau’uka daban-daban. Sun fi danganta da salon yadda aka gudanar da satan. Fitattu daga cikinsu sun haɗa da:
    i. Cuta
    ii. Damfara
    iii. Fashi
    iv. Fizge/Wabce/Fauce
    v. Ƙwace
    vi. Sane

    Sata babbar abar ƙyama ce a farfajiyar Hausa da Hausawa, tun ma kafin bayyanar addinin Musulunci. Sauyawan al’amurra da cuɗanyar Hausawa da baƙin al’ummu sun wanzar da taɓarɓarewar tarbiyya da ƙoƙarin neman tara abin duniya ido rufe. Ta kai ga
    fanɗararru marasa kishin kansu cikin al’umma sun tsunduma a fagen wannan ta’addanci.
    Yayin da addinin Musulunci ya bayyana a ƙasar Hausa, sai ya ƙara ƙarfafa wa Hausawa ƙyamar wannan muguwar sana’a.

    Musulunci ya zo da dokoki domin kawar da duk nau’o’in sata. Allah na cewa:
    Ɓarawo kuma da ɓarauniya sai ku yanke hannayensu ya zama sakamako ne na abin da suka aikata, (wannan horo ne) daga Allah. Allah kuwa mabuwayi ne Gwani. (Alƙur’ani, 5:38). A addinin Musulunci ta kowace fuska ana ƙoƙarin kare dukkanin al’umma ta yadda za a zauna cikin aminci game da dukiyoyi da rayukan al’umma.

    Ita kuwa sata, mugun hali ce da ke haifar da rashin kwanciyar hankali da salwantar rayuwa a tsakanin al’umma. Don haka ne shari’a ta tanadar da hukuncin yanke hannun
    ɓarawo wanda zai hana watsuwar irin wannan muguwar ta’asa a tsakanin al’umma [14]. Allah na cewa: “Kuma kada ku ci dukiyoyinku a tsakaninku ta hanyar cuta ”(Alƙur’ani, 2: 188).

    Ayar tana tabbatar wa masu imani cewa, cuta haram ce. Ba ya halatta ga Musulmi ya yi zalunci ta hanyar zaƙin baki ko dabara. Haka kuma, bai halatta ya yi jagora don a cuci wani ba. Duk da irin waɗannan dokokin da Allah Maɗaukakin Sarki ya shimfiɗa domin samar da kyakkyawan zamantakewa da aminci a doron ƙasa, an samu gungun mawaƙa da ke jayayya da dokokin cikin lafuzzan waƙoƙinsu.

    Bunza, (2014) ya kawo baituka da dama daga bakin Alhaji Muhammadu Gambo Fagada.
    Gambo ya bayyana ƙarara cewa:
    Jagora: Don Waɗanda ka sata nay yi ganga, Ba do wani sarki mai naɗi ba.
    (Alhaji Muhammadu Gambo Fagada: Tsoho Tudu)
    A cikin waƙarsa ta Nazaƙi kuwa, an ga yadda hirarsu ta gudana da Nazaƙi bayan ya tuba daga sata.

    Sannu a hankali har Gambo ya sake zuga shi yadda har sai da ya dawo satan. Gambon da kansa ya bayyana cewa:
    Ɓarawo in ina kusa ba tuba yakai ba,
    Ko ya aje gemu, ko ya yi saje,
    Ko ya fidda farin gashi ga kaina,
    In Gambo na kusa ba tuba yakai ba,
    Ba ko batun shegantaka ba.
    (Alhaji Muhammadu Gambo Fagada: Waƙar Nazaƙi)

    A wannan ɗiyan waƙa, sai da ya jaddada cewa, batunsa ba “batun shegantaka” ba ce kawai. Wato dai haƙiƙanin gaskiya yake faɗa cewa idan yana kusa ɓarawo ba ya tuba domin kuwa zai ziga shi ya hana shi tuban. Wasu makaɗan sukan yi waƙoƙin yabo ne ga
    ɓarayin. Misali Alhaji Mamman Shata ya yi wa wani ɓarawo mai suna Mamman Ɗan’yarbayye waƙa, a inda yake cewa:

    Jagora: Mai hannun taɓa ƙofa in an bacci,
    Masu samame baƙon Ɗanmani.
    Na faɗa maka Mamman.
    In dai ka ɗauko sa’a,
    Har ka buɗe ƙofa,
    Ka tarar an bacci,
    To zari akwati tsakiyar shi ya fi kaya.
    Na saman hoto ne,
    Na ƙasan maganin ƙwari ne.
    Tafi zari akwatin tsakiyar shi ya fi kaya.
    Na Abdu ƙyale dangi sai an bacci,
    Iyalin Mamman, waɗanda ba su so a yi haske,
    Su sun fi so a tabka duhu da ruwa yaf-yaf-yaf.
    Wani don ya taka kara bai mai ƙara ba,
    Sannan ganyen ganji duk ya bi ƙasa.
    (Alhaji Dakta Mamman Shata: Mamman
    Ɗan’yarbayye)

    A waɗannan ɗiyan waƙar, mawaƙin ya yabi ɓarawon tare da ba shi shawarar yadda zai gudanar da sana’arsa ta sata. Wannan ya haɗa da yi masa ishara ga irin lokuta da yanayi da dabarun da zai bi wajen yin satar, da kuma nau’in abin da zai sata da ya fi saura daraja.

    Hakan kuwa karan-tsaye ne ga dokokin addini. Hadisin Manzo (S.A.W.) ya bayyana cewa: “Ɓarawo ba ya sata a lokacin da yake da imani” (Buhari ne ya ruwaito
    hadisin). Allah Maɗaukakin Sarki ya kawo nau’in hukuncin da ya dace a zartar wa masu fashi da makami, a inda yake cewa:

    Ba wani abu ne sakamakon waɗanda suka yi wa (Musulmi masu bin) Allah da manzonsa fashi ba, kuma suke tafiya a bayan ƙasa da ɓarna ba, sai kawai a kashe su ko kuma a tsire su ko a yanke hannayensu da ƙafafuwansu a tarnaƙe, ko kuma a kore su daga ƙasa. (Yin) wancan ƙasƙanci ne a gare su a duniya, a lahira kuma suna da azaba mai girma. (Alƙur’ani, 5:33).

    Allah ya bayyana mana cewa masu yin fashi da makami suna ƙoƙarin ɓata tsarin Allah da Manzonsa ne, saboda aiwatar da fashi ya kauce wa hanyar gaskiya da adalci, waɗanda Musulunci ke ƙoƙarin tabbatar da su a doron ƙasa. 3.5 Goyon Bayan Kisan Kai Kisan kai na daga cikin manyan zunubai masu matuƙar muni a Musulunci. A cikin Suratul Nisa’i, Allah na cewa:

    Wanda kuma ya kashe mumini da gangan, to Jahannama ce sakamakonsa, yana madawwamini a cikinta, kuma Allah ya yi fushi da shi, ya kuma tsine masa, kuma ya
    tanadi azaba mai girma a gare shi (Alƙur’ani, 4:93).

    An jiyo Makaɗa Muhammadu Bawa Ɗan’anace ‘Yar Tsakkuwa, Gandi, Sakkwato yana ziga fitaccen ɗan damben nan Shago domin ya yi kisa. A cikin Bakandamiyar Shago, yana cewa:
    Bayarwa: Yanzu inai maka kuka,
    Ba kukan tuwo ba, Ba na hura ba…
    ‘Y/Amshi: Kukan Ɓaleri ya raga bayi, Suna kirarin banza.
    Bayarwa: Ɗan Abdu ko ga girbin
    ‘Y/Amshi: Gero, bara-bara ta na hana wake….
    A wani wuri yana cewa:
    Bayarwa: Ɗan Abdu kashe mutum a gafarta ma. Ɗan Abdu…
    ‘Y/Amshi: Kashe mutum a gafarta ma.
    (Muhammadu Bawa Ɗan’anace: Bakandamiyar Shago)

    Ba za a ce maganar kisa a nan ta taƙaita ga buge mutum a dambe ba kawai. Ya haɗa da kashewa har lahira. Hakan zai ƙara tabbata yayin da aka yi la’akari da lafuzza da ya riƙa amfani da su cikin waƙar da suka haɗa da:
    i. Kusheyi
    ii. Lahira a kai miki gawa
    iii. Lahira tana yin baƙo
    iv. Uwar mutum ta haifi wani, da sauransu.

    Gambo ma ya yi makamanciyar zigar nan inda yake ziga inda yake cewa:
    Bayarwa: Duw wanda ya ishe mai kuɗi lahiya lau,
    Ya yi sata yab bar mai kuɗi da rai nai,
    In yaz zaka Allah ya isam min za ni ce mai,
    Don wagga ba sata ta ba Gambo.
    (Alhaji Muhammadu Gambo Fagada: Waƙar Kashe Mace)

    A nan, ko bayan ziga zuwa ga yin sata, mawaƙin ya nuna cewa satar ba ta cika har sai an yi kisan kai. Wannan kuwa fanɗarewa ne daga koyarwar addinin Musulunci.

    Goyon Bayan Kisan Kai

    Kisan kai na daga cikin manyan zunubai masu matuƙar muni a Musulunci. A cikin Suratul Nisa’i, Allah na cewa: Wanda kuma ya kashe mumini da gangan, to Jahannama ce sakamakonsa, yana madawwamini a cikinta, kuma Allah ya yi fushi da shi, ya kuma tsine masa, kuma ya tanadi azaba mai girma a gare shi (Alƙur’ani, 4:93).

    An jiyo Makaɗa Muhammadu Bawa Ɗan’anace ‘Yar Tsakkuwa, Gandi, Sakkwato yana ziga fitaccen ɗan damben nan Shago domin ya yi kisa. A cikin Bakandamiyar Shago, yana cewa:
    Bayarwa: Yanzu inai maka kuka,
    Ba kukan tuwo ba, Ba na hura ba…
    ‘Y/Amshi: Kukan Ɓaleri ya raga bayi, Suna kirarin banza.
    Bayarwa: Ɗan Abdu ko ga girbin
    ‘Y/Amshi: Gero, bara-bara ta na hana wake….

    A wani wuri yana cewa:
    Bayarwa: Ɗan Abdu kashe mutum a gafarta ma. Ɗan
    Abdu…
    ‘Y/Amshi: Kashe mutum a gafarta ma.
    (Muhammadu Bawa Ɗan’anace: Bakandamiyar Shago)

    Ba za a ce maganar kisa a nan ta taƙaita ga buge mutum a dambe ba kawai. Ya haɗa da kashewa har lahira. Hakan zai ƙara tabbata yayin da aka yi la’akari da lafuzza da ya riƙa amfani da su cikin waƙar da suka haɗa da:
    i. Kusheyi
    ii. Lahira a kai miki gawa
    iii. Lahira tana yin baƙo
    iv. Uwar mutum ta haifi wani, da sauransu.

    Gambo ma ya yi makamanciyar zigar nan inda yake ziga inda yake cewa:
    Bayarwa: Duw wanda ya ishe mai kuɗi lahiya lau,
    Ya yi sata yab bar mai kuɗi da rai nai,
    In yaz zaka Allah ya isam min za ni ce mai,
    Don wagga ba sata ta ba Gambo.
    (Alhaji Muhammadu Gambo Fagada: Waƙar Kashe Mace)

    A nan, ko bayan ziga zuwa ga yin sata, mawaƙin ya nuna cewa satar ba ta cika har sai an yi kisan kai. Wannan kuwa fanɗarewa ne daga koyarwar addinin Musulunci.

    Hani Ga Bautar Ubangiji

    Ko bayan kira zuwa ga aikata ɓarna da fasadi, akwai misalan ɗiyan waƙoƙi kuma da ke kira ga barin bautar Ubangiji. Na biyu a cikin shika-shikan Musulunci ita ce salla. Tana da matuƙar muhimmancin da har ya kasance kadarko tsakanin mutum da kuma shirka da
    kafirci. Duk da haka, sai ga ɗiyan waƙa da ke hani ga yin salla:

    Bayarwa: Ɗan Abdu ban da sallas swahe,
    ‘Y/Amshi: Domin yawan sallan nan yana rage maka ƙarhi.
    (Muhammadu Bawa Ɗan’anace: Bakandamiyar Shago)

    Sakamakon Bincike

    Ta la’akari da nassoshin Alƙur’ani da Hadisan Annabi S.A.W. da kuma ƙumshiyar wasu waƙoƙin baka na makaɗan Hausa, za a a iya cewa, mawaƙa na wuce gona da iri a waɗansu lokuta. Yawanci hakann na faruwa ne yayin da suka yi ƙoƙarin adanta waƙoƙin nasu domin burge wanda aka yi wa waƙar da kuma sauran masu nsauraro.

    A haka ake samu ɗiyan waƙoƙin sun yi wa dokokin Musulunci karan-tsaye. A wannan nazarin an fahimci cewa duk wani aikin da ɗan’adam ya aikata wanda Allah da manzonsa
    suka yi hani da shi, yin haka nau’i ne na fanɗare wa dokokin Allah. Ya zama tilas kowane Musulmi ya nemi ilimin duk wani lamarin da ya shafi rayuwarsa, (kamar yadda mai Ahalari ya bayyana) don gudun auka wa fushin Ubangiji.

    An kuma fahimci cewa, a Musulunci kowane irin al’amari an ɗora shi a kan mataki-mataki. Wannan ne ya wajabta wa kowane Musulmi ya yi umurni da aikata alheri da kuma hani ga mummunan aiki gwargwadon ƙarfin ikon mutun.

    Kammalawa

    Yin fice da waƙoƙi suka yi wurin ilimantarwa da faɗakarwa da nishaɗantarwa, ba shi ke nuna ba a samun fanɗarewa a cikinsu ba. Nau’ukan fanɗarewa da ake samu cikin waƙoƙin Hausa sun shafi ziga zuwa aikata abin da Ubangiji ya hana, ko izgilanci ga
    abubuwan da Musulunci ya zo da su, ko kuma hani ga abin da Ubangiji ya yi umarni da a aikata.

    Abu ne mai kyau manazarta su riƙa zaƙulo ire-iren fanɗarewa da ake samu a cikin waƙoƙi domin faɗakar da al’umma da su kansu mawaƙan. Malamai da ke jagorantar nazarcenazarcen waƙoƙi a makarantu kuwa, ya kamata su mayar da hankali wajen yin shiri na musamman na faɗakar da ɗalibai ta fuskokin da suka dace yayin da aka ci karo da ire-iren baitukan fanɗarewa a cikin waƙoƙin da suke nazarta.

    Gwamnatoci da hukumomin da abin ya shafa ma na da rawar takawa wajen samar da ƙa’idoji da tsaretsaren tace waƙoƙi kafin sakinsu. Haɗakar waɗannan za su tabbatar da al’umma ba ta rinjayu da kiraye-kirayen waƙoƙin fanɗara ba zuwa taɓewa.

    MANAZARTA

    • Abba, M., & da Zulyadaini, B. (2000). Nazari kan
    waƙar baka ta Hausa. Gaskiya Corporation Limited.
    • Abubakar, A. (2015). Ƙamusun Harshen Hausa.
    Zaria: Northern Nigeria Publishing Company LTD.
    • Al-Munajjid, M. S. (2004). Muharramat: Forbidden
    matters same people take lightly. International
    Islamic Publishing House, Saudi Arebia.
    • Bunza, A. M. (2014). In ba ka san gari ba saurari
    daka: Muryar nazari cikin tafashen Gambo Elkods
    Printing Hausa.
    • Chiromawa, U. A. U. (n.d.). Dalilin kiɗa a cikin
    Alƙur’ani da hadisi.
    • Gusau, S. M. (1984). Nazarin zaɓaɓɓun waƙoƙin
    makaɗan baka na Hausa, littafe na ɗaya.
    • Ibrahim, M. S. (1983). Kowa ya sha kiɗa. Longman
    Nigeria Limited.
    • Magaji, A. (2016). Kassu Zurmi da waƙoƙinsa.
    Spectrum Books Limited.
    • Muhammad, Y. M. (2005). Adabin Hausa. Ahmadu
    Bello University Press Limited.
    • Sani, A. U., & Jaja, M. B. (2019). Zamani Riga:
    Akalar Magungunan Gargajiya a Hannu Addini da
    Zamani. In The Nasarawa Journal of Humanities, 7,
    (1-2), 257-268. ISSN: 1118-6887.
    • Shehu, M., & Sani, A. U. (2019). Intra-Religious
    Conflicts within the Hausa Hausa-folk. In EAS
    Journal of Humanities and Cultural Studies, 1(3),
    145-150. ISSN: 2663-0958 (Print) & ISSN: 2663-
    6743 (Online) Available at:
    https://www.easpublisher.com/get-articles/344.
    • Umar, M. B. (1987). Dangantakar adabin baka da
    al’adun gargajiya. Kamfanin “Triumph” Gidan
    Sa’adu Zungur

    Danna nan don karanta Nazarin Hanyoyin Adana Kayayyakin Hausawa Na Gargajiya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Budurwa Marar Tabo

    Tatsuniyar Budurwa Marar Tabo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wata yarinya kyakkyawa, wadda ko tabo ɗaya babu a jikinta. Shi ke nan, sai ta ce ita fa ba za ta auri wanda yake da tabo ko da ɗaya ne tak a jikinsa ba. Manema wannan ya zo, wancan ya zo, amma duk suna da tabo.

    Ana nan, sai ga wani saurayi wai shi Ɗandisheri wanda ba shi da tabo a jikinsa, in ban da wani ƙarami a kan ɗan yatsansa, shi ma ya je saran itace ne ya yi sartse. Da ya je, sai ta ce ba ta son sa. Ya haƙura.

    Rannan sai wani maciji ya ji labarin halin wannan budurwa, ya gayawa abokansa, suka rikiɗa suka zama mutane samari kyawawa, waɗanda ba ɗaya daga cikinsu wanda yake da tabo ko ɗaya a jikinsa. Sai suka je wurinta, ta bincike kowannensu sarai, ta ga babu tabo a jikinsa.

    Nan take ta ce ta yarda ɗayansu ya aure ta. Aka taru aka ɗaura aure da ɗayansu. Shi ke nan ta tattara kayan ta suka tafi da amaryarsu. Da suka je jeji sai suka ce: “Yawwa mun iso gida.” Ita ko tace: “Ina gidan a nan?” Sai suka ce da ita: “Ai nan ne gidan. Amarya ta yi zuru-zuru, babu yadda za ta yi domin ta riga ta auri ɗayansu.

    Kuma ga shi sun kai ta dokar daji, inda ba za ta iya komawa gari ba. Daga nan suka saka ta a kogon bishiya, suka rikiɗe macizai suna lasar jikinta har ta zama fara fat, babu kyan gani, kuma abin ƙyama. Ana nan kwanci-tashi har ta sami ciki. Bayan wani lokaci mai tsawo, sai wata rana Ɗandisheri suka yi ƙarancin ciyawar akuyarsu, sai ya tafi can cikin ƙungurmin jeji yana yankan ciyawa.

    Sai matar macizai ta hango shi, ta fara rera masa waƙa tana cewa:

    “Ɗandisheri – Ɗandisherina,

    Ɗandisheri ƙanin Babati.

    Idan ka je gida ka gai da iyata,

    Idan ka je gida ka gai da Babati.

    Ni mai zaɓar maza babu tabo,

    Ga ni yau a kogon kukati,

    Maciji na lasa ta mulai,

    Kunama na harbi na mulai.

    “Sai Ɗandisheri ya ɗau waƙa, ya amsa mata yana cewa:

    Ina ruwan Ɗandisheri,

    Daga fari ke aka bai wa ni,

    Daga gani sai kika raina ni,

    Domin tabon ɗan yatsana.

    Da ya je gida sai ya gaya wa iyayenta halin da take ciki. Da suka ji labari, sai suka yi shiri domin su je su gani. Da suka je sai suka same ta a cikin kogo. Suka rasa yadda za su fito da ita. Dole aka sare bishiyar, aka fitar da ita, iyayen suka tafi da ita gida.

    Daga baya ta haifi ɗa namiji, rabin jikinsa ɗan mutum, rabi ɗan maciji. Da mazanta macizai suka ji ta haifu sai suka ƙara zama mutane, suka zo karɓar ɗansu. Da suka isa gidan, sai danginta suka tona makeken rami, aka shimfiɗa musu tabarma a kai, aka kuma hura wuta a ƙarƙashi, aka yi wa ɗansu wanka aka yi masa kwalliya aka kira su, suka zauna suka karɓi ɗansu.

    Suna cikin hira sai su ji ‘nyas-nyas,’ sai suka ce: “Kai akwai abin cizo a gidanku?” Masu gida suka ce: “E wallahi. Jim kaɗan sai tabarma da yayin suka kama wuta, su da shimfiɗar suka faɗa cikin wutar. Yayin da suke ƙonewa sai suka wurgo yaron sama, aka cafe shi, aka ƙara wurga musu, haka dai suka yi ta yi har suka ƙone rumus da su da ɗansu.

    Da ba domin Gizo ba da na yi muku ƙarya. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Mai ruwan ido gama kasuwa da yawo.
    • Jiki magayi.
    • Ƙarya fure take ba ta ‘ya’ya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Jarumin Sarki

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Jarumin Sarki

    Tatsuniyar Jarumin Sarki

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani jarumin sarki wanda a fagen yaƙi ba ya ja da baya. Duk inda ya sa gaba sai ya sami nasara. Yana da mata uku: amaryarsa kitse ne, sauran kuma mutane ne. To Sarkin nan ya fi son Takitsen. Duk lokacin da zai je yaƙi sai da ita yake tafiya.

    Ana nan, sai wata rana wani yaƙi mai haɗari da zafi ya taso. Sai ya yanke shawarar cewa wannan yaƙin ba irin wanda zai je da mata ba ne. Amma kuma yana tsoron barin amaryarsa a gida. Da sauran matansa biyu suka ji haka, sai suka ce ya bar ta a gida, babu komai za su kula da ita kamar yana nan.

    Sai ya amince da alƙawarin da suka yi, ya hau shi da barade suka dunguma zuwa filin daga, ya bar amaryarsa a gida. Bayan tafiyar Sarki sai matan nan suka sa amarya girki. Tana nufar murhu sai ta narke saboda zafin wuta. Ganin haka fa sai suka fara kuka, suna cewa: “Takitse ta narke ta zama ruwa.

    “To daman akwai wani tsuntsu a gidan Sarki. Da ya ji abinda matan Sarki suke faɗa a cikin kuka, sai ya tashi ya nufi wajen yaƙin, yana cewa;

    Sarki. Sarki. Sarki ka mai da yaƙi baya,

    domin Takitse ta narke ta zama ruwa.

    Haka ya yi ta yi, har Sarki ya kasa kunnensa, ya ji ana cewa ya bar yaƙi ya koma gida, domin matansa suna can a gida suna yin kuka. Fadawa da baraden Sarki ma suka tsaya, suka ji abin da tsuntsu ke cewa. Sai ya tambaye su abin da suka ji daga bakin tsuntsu, sai suka ce, ai Takitse amaryarsa ce ta narke.

    Nanda nan Sarki ya karya linzami, aka koma garinsa. Da ya isa fadar, sai ya shiga cikin turakarsa, ya sa Jakadiya ta kira matan, ya dube su ya ce: “Wace ce ta sa Takitse girki?” Sai matar Sarki tatsakiyarta yi farat ta ce: “Uwar gida ce. A fusace, Sarki ya umarci dogarawa su sare mata kai. Nantakesuka fille mata kai. Ba a wasa da umarnin Sarki. Kurunkus.

    Abubuwvan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Karya al kawari cin amana ne.
    • Soyayya amanar zuciya

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Ɗankaɗafi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tarihin Garin Kudan 2

    Tarihin Garin Kudan 2

    BABI NA HUƊU

    Rana ta fara haskawa a sararin samaniyar garin Kudan, tamkar zinaren take  ɗauke da albarkatu. Mutane sun tashi suna jin wani sabon ɗumi a zuciyarsu, ɗumin da ake ji, idan aka ga alheri yana gab da farawa. Kamar yadda ake cewa:

    “Idan gari ya fara motsi, ko tsuntsaye sukan san akwai abun da ake nema.”

    A wannan rana an fara da al’amura guda  uku:  tsaro, haɗin kai, da bunƙasar arziki. Wannan shi ne ginshiƙan sabon ginin da aka fara a Kudan.

    1. Dabarar tsaro (Jagorancin haziƙan mutane)

    A ƙofar kasuwar Kudan, matasa sun taru ƙarƙashin jagorancin Salmanu Faris da Nuhu Baushe, Nawalmu da Garba Ode. Sun kafa Kudan Community Watch, wata ƙungiya da ta haɗa matasa masu kishin gari.

    Salmanu ya tsai da kansa a gaban jama’a ya ce:

    “Tsaro ba na gwamnati kaɗai ba ne. Tsaro tamkar alwala ne, kowa ya tsarkake nasa ɓangaren.”

    Nuhu Baushe, fitaccen mafarauci mai hikima, ya ƙara da cewa:

    “Mutum da ke iya bin sawu a daji, ba zai kasa gano matsala cikin gari ba.”

    Sun rarraba matasa zuwa rukuni-rukuni:

    1. Rukuni na dare, ‘yan sintiri masu bin layi har da mafarauta.

    2. Rukuni na kasuwa,  waɗanda ke kula da kasuwar gari.

    3. Rukuni na hanya, masu taimakon mata da yara wajen tsallaka tituna, musamman a lokacin cankuso.

    Garba Ode, wanzamin gari, ya zama mai lura da lafiyar matasa. Kullum yana cewa:

    “Idan ka so ka yi gudu mai nisa, to ka ci gaba lafiya.”

    Mutane suka ji daɗi, suka fara hango kwanciyar hankali.

    A farfajiyar babban masallacin Juma’a na Kudan, malamai suka fara gudanar da babban taron da ya tattara ɗalibai, matasa da manya. Malam Aliyu ya tashi ya fara magana cikin nutsuwa:

    “Haɗin kai tamkar tukunya ce; ko an yi girki mai daɗi, ba za ku ci ba , dan tukunya ta karye.”

    Daga nan malamai suka kafa shirin da suka kira “Tattalin Zumunci” , inda kowane gida zai ziyarci wani gida a kowane mako, domin sada zumunta. Wannan ya rage rigingimu da rashin fahimta. Sannan kuma duk Alhamis ɗin ƙarshen wata, malamai zasu dunga taru wa a masallacin Juma’a na cikin gari, don yin musaffa tare da addu’o’in zaman lafiya da ci gaban gari.

    Mal. Auwal da Mal. Salim suka shigo da darussan boko, cewa matasa su koyi rubutu, fasaha, kimiyya da ilimin zamani. Suna yawan cewa:

    “Karatu shi ne ido, idan ka rasa shi, koda kana da ƙafa za ka yi tafiya cikin duhu.”

    Malam Abdulhafiz ya koyar da matasa dabarun tattaunawa da sauraro.

    Malam Yasir ya koyar da “Tsarin gina gari ga matasa”.

    Malam Salisu ya shigo da dabarun zama lafiya.

    A hankali, mutane suka fara fahimtar cewa:

    Haɗin kai ba maganar baki ba ce. Aiki ce.

    BABI NA BIYAR

    A kasuwar Kudan, ana ta hayaniya cikin nishaɗi. Abubakar mai kamfanin shinkafa ya kawo sabuwar na’urar tacewa. Ya ce:

    “Shekara da yawa muna da fili, kuma muna samun amfanin gona mai yawa, amma ba mu da fasahar sarrafawa ta zaman, wacce za ta tace mana kayan amfanin gonan mu cikin sauƙi da kuma tsabta”.

    Nan take sai ya ɗauki matasa 25 suka zama ma’aikatansa, mata 10 suka zama masu tace shinkafar da aka noma, sauran mutane 15 kuma masu noma kayan amfanin gona gami da samar da taki mai inganci.

    Muzammil da Mas’ud suka haɗa ƙungiyar mazauna garin da ke noma.

    Nafi’u da Isma’il suka fara shirin Noman Zamani da amfani da injina.

    Mutane suka fara jin cewa tattalin arziki zai farka daga sumar da ya yi. Kasuwa ta zama wuri mai cike da motsi.

    Mutum ya je kasuwa ya ji ana cewa:

    “Kudan ta tashi, Wallahi Kudan ta tashi tamkar aure da ya zo da annuri.”

    Ƙungiyar Mawaƙa

    A gidan Labaran Adamu, aka yi zaman mawaƙa. Su Ashiru, Salahu, Ali Na Annabi da Rabilu sun rubuta sabuwar waƙa mai taken: “Uban arziki ”

    Waƙar ta kama hankalin mutane sosai. A cikin baitocin waƙarsu akwai karin magana mai zurfi:

    “Idan rana ta fito a gefenku, kada ku ce ba ku dace ba, ku tashi ku yi aiki.”

    Wannan waƙa ta zama tamkar tutar motsa zuciyar al’umma.

    Daga Ƙarshe

    Yayin da rana ta doshi yamma, mutane suka tsaya a kan ƙaramin tudu suka kalli hasken rana tana faɗuwa. Kamar furen da ya buɗe, zukatan al’umma suka yi fari.

    Farfesa Mu’azu ya tsaya ya ce: “Daurin mu a yau ya zama ginshiƙin gobe. Idan mu ka dage, Kudan zata zama abin koyi.”

    Salmanu Faris ya ce: “Gari ba ya giɓi idan kowa ya ɗora nasa tubalin.”

    Mutane suka ce gaba ɗaya: “Mu tashi, mu gina Kudan! Don tuƙa Tuwon gobe lafiya”.

    Yayin da tashin hankali ya fara raguwa

    A kwanakin da suka biyo baya, garin Kudan ya fara samun nutsuwa fiye da da. Ayyukan Salmanu Faris da tawagarsa: Nuhu Baushe, Nawalmu da Garba Ode, sun riga sun bazu a cikin gari kamar wutar daji a zukatan mutanen gari. Kowa ya fara kallon gaba, domin an fara ganin tabbas gari ya fara komawa bisa turba.”

    A daren ranar Asabar, bayan taron tsare-tsare da suka gudanar a unguwar Kintonho , suka fito suna tafiya cikin farin wata mai haske. Kamar yadda Hausawa ke cewa:

    “Idan dare ya yi tsawo, sai ya kai ga wayewar gari.”

    Wannan kenan. Wayewar gari ta kusa.

    Ginin Sabon Masallacin Juma’a

    Washegari da safe, jama`a suka taru a babban fili yayin da ake ƙaddamar da ginin babban Masallacin Juma’a da Rt. Hon. Isa Ashir ya ɗauki nauyi. Ya yi wani jawabi wanda ya cika zukatan mutane:

    “Garin da ya rasa tsaro, ya rasa komai. Amma garin da ya nemi ilimi, tarbiyya da haɗin kai, to ya kama sahun cigaba.”

    Sadaukarwarsa ta ja hankalin kowa. Salmanu ya kalli masallacin yana murmushi. Ya ce a zuciyarsa:

    “Ginin masallaci ba katanga ba ce kaɗai. Gina zuciyar al’umma ne.”

    Makarantar Sana’o’i ta Tashi Tsaye

    Ranar da suka fara shigar da kayan aiki makarantar koyon sana’o’i, sai yaran gari suka yi tsalle da murna. Wani yaro mai suna Zailani Sambo ya ce:

    `Wallahi zan koyi gyaran waya in taimaka wa iyayena!”

    Nawalmu ya yi murmushi yace:

    `Ai haka ake so! Sana`a kamar garkuwa ce, mai shi baya jin yunwa.

    Bisa ga dalilin haka,sai aka samar da wasu rassa kamar: gyaran lantarki, ɗinki, walda, girki da fasahar kwamfuta. Gari ya fara cika da hayaki na cigaba, ba na rikici ba.

    Makarantar ƴan Sanda (Police Academy)

    Garba Ode, wanda ke da ƙwarewa a ilimin ladabtarwa, shi ne aka ba alhakin tsara tsarin horo. Ya ce wa Salmanu:

    “In an so zaman lafiya, dole a gina jami’an tsaro masu hankali, ba masu daga bindiga kawai ba.”

    A can an samar da aji-ajin koyar da:

    1. Magance rikici.

    2. Dabarun tattaunawa.

    3. Kare haƙƙin ɗan adam.

    4. Sahihiyar bincike.

    Ginin ya zama tamkar wuta da ake iya ganin hasken ta daga nesa.

    Asibitin shakatafi (Primary health care)

    Rt. Hon. Isa Ashir ya kuma aika injina da ma’aikata wurin gina sabon asibiti, domin ya ce:

    “Ba tsaro ba tattali idan babu lafiya.”

    An kafa sashen haihuwa, daakin tiyata, da ɗakin taimakon gaggawa. Dattawa suka yi addu’a, mata suka yi hawaye na farin ciki. A wurin ƙofar asibitin wani dattijo ya ce:

    “ Turakun gari sun fara zama.”

    BABI NA SHIDA

    Matasa kuwa sun yi murna fiye da kowa da ginin filin ƙwallo na zamani. A ranar da aka fara dasa harsashin ginin wajen,ɗaruruwan mutane suka taro a wajen, don murna.

    Nuhu Baushe ya ce:

    “Matasa da ba su da abin yi, fitina na kiransu. Amma idan ka basu filin wasa,ka rage yawan ɓarna.”

    Filin ya zama wajen taron matasa, wuri mai ɗauke da annashuwa maimakon hayaniyar rikici.

    Sabon Tituna,

    An fara shimfiɗa tituna masu faɗi a manyan lunguna. Hakan ya sauƙaƙa zirga-zirga, ya hana ‘yan fashi yin ƙwanton-bauna.

    Salmanu ya ce lokacin da suka tsaya kallon injinan da ke aiki:

    “Idan ka gyara hanya, ka gyara zuciya. Domin hanya ta haɗa ɗan Adam da ɗan Adam.”

    Nawalmu ya ƙara da cewa:

    “Hakika! In aka samu hanya, ko rikici na iya tserewa!”

    Yayin da rana ta faɗi kan sabbin gine-ginen da suka ƙawata garin Kudan, Salmanu Faris ya kalli Nuhu Baushe, Nawalmu da Garba Ode, sai ya ce:

    “Haɗuwar al’umma waje ɗaya, da shawo kan rikic, shi ne jigon abin da zamu sa a gaba. Mu ci gaba, kar mu tsaya.”

    Gari ya yi shiru mai cike da salama. A cikin wannan shiru akwai wata magana ta gargajiya da ta dawo masa daga zuciya:

    “Gari da alheri ya bunƙasa, ko tsuntsu na leƙen damar zama.”

    Wɗancan dalilai sun sa garin Kudan ya samu cigaba fiye da shekarun baya. Saboda garin ya kafu shekaru ɗari biyu tun kafin jihadin Usman Ɗanfodiyo, wato a ƙarni na goma sha huɗu, wanda a yau (2025) garin ya samu shekaru ɗari shida da ashirin da biyar da kafuwa (625).

    A makonnin da suka biyo baya, sabuwar duniyar Kudan ta fara bayyana a fili. Mutane suna yawo cikin kwanciyar hankali, yara na wasa a sabbin tituna, mata na fita kasuwa cikin kwanciyar hankali, dattawa na zama ƙarƙashin inuwa suna tattaunawa da nishaɗi.

    A wani yammaci, Salmanu Faris ya tsaya a saman wani ɗan tudu yana kallon garin. Yana jin wani irin shauƙi da jin daɗi a zuciyarsa. Nuhu Baushe ya taho daga baya ya ce masa:

    “Kai Salmanu, garin nan ya zama abin kallo! Haka ake so, idan rawani ya yi kyau, sai a yabawa mai ɗaure shi.”

    Salmanu ya yi murmushi:

    “Mu dai mun yi niyya ne, Allah ya daidaita. Kowa ya bada gudunmawa.”

    A kwanakinnan, an ga wani sabon yanayi na haɗin kai wadda ba a saba gani ba.

    Matasa suna taimakon juna wajen tsaftace titi. Mata suna koyon sana’o’i a makarantar horo. Dattawa na bada shawarwari a majalisa.

    Kowane yanki na gari yana kama da sabon fure da ya fara buɗewa.

    Ƙofar Arewa, Ƙofar Gabas, Ƙofar yamma (Kintonho), Ƙofar yamma ko Zaria.

    Har’ila yau, kuma an kafa kwamiti na kowace unguwa, don tabbatar da tarbiyyar yaran unguwar gami da warware matsalolin zamantakewar auratayya. Waɗancan unguwannin sun haɗa da: Unguwar Makera (farfaru), unguwar Maƙera (babbaƙu), Ƙofar Arewa, Saidawa, Unguwar Zaɓi, Ƙofar Gabas, Unguwar Liman, Unguwar Bela, Juga (Kintonho), Yan Gishiri, Unguwar Malamai, Unguwar Ƴan Takalma, Tudun Wada, Ƙofar Fada, Sabon garin Kudan, Unguwar Malam Talatu, Rimin Baima, Kuka, Tartibu, Unguwar Tsauni, Unguwar Ma’aji, tsohuwar Kasuwa, Shagari Quarters da sauransu.

    Garba Ode, wanzamin gari kuma ɗaya daga cikin shugabannin ci gaban al’umma, ya tsaya gaban jama’a a kasuwa ya yi magana cikin hikima:

    “Idan mutum ya ceci mutum guda, tamkar ya ceci duniya ne. Mu ci gaba da taimakon juna ko kaɗan ne. Da kaɗan-kaɗan ne ake tara tsaba a rumbu.”

    Kowa ya yi dariya, domin Garba Ode yana da hikima mai fara’a.

    Ginin masallacin Juma’a, asibiti, makarantu da tituna sun ba mutanen Kudan sabon yanayi. Mutane suna yawan cewa:

    “Ashe idan mutum mai hangen nesa yana mulki, gari ya kan yi kyau kamar hatsi a kwando!”

    Rt. Hon. Isa Ashir ya sake ziyartar wuraren da ake gine-gine. Yara suka ruga suna ta murna suna kiran sunansa. Ya tsaya ya ce:

    “Na gina gine-gine, amma ku kun gina haɗin kai. Ku ne jarumai.”

    Kalmar nan ta sanya mata da maza yin kabbara da farin ciki.

    A wata laraba, an gayyaci Salmanu Faris zuwa babban taron Majalisar ci gaban Kudan.

    Duk jama’a suna jiran jin me za a ce masa.

    Shugaban majalisa ya miƙe ya ce:

    “Mutumin da ya jagoranci zaman lafiya, ya haɗa matasa, ya haɗa dattawa, ya ƙarfafa tsaro, ya samar da cigaba, ba wanda ya cancanci yabo kamar Salmanu Faris.”

    Jama’a suka yi tsalle da tafi.

    Salmanu ya miƙe cikin ladabi. Ya ce:

    “Na yi abin da na iya ne kawai. Gari ba na mutum guda ba ne, gari tamkar tabarma ne, kowa zai iya samun zama.”

    Jama’a suka amsa da cewa:

    “Hakane! Gaskiya ka faɗa!”

    Wannan dare, a ƙofar masallacin Juma’a, an shirya liyafar godiya. An kunna fitilu, yara suna murna, matasa suna ta kabbara.

    An miƙa kyaututtuka ga jarumai uku na gari:

    1. Nuhu Baushe, saboda tsayuwar tsayin dakan da ya nuna wajen kare jama’a.

    2. Nawalmu, saboda hikimarsa gami da ƙwazon, wajen bincike gami da tabbatar da zaman lafiya.

    3. Garba Ode, saboda basirarsa da kuma ƙwarewarsa wajen ladabtar da mutanen marasa jin magana.

    Dukkaninsu sun yi jawabi ɗaya bayan ɗaya.

    Nuhu Baushe ya ce:

    “Rana ɗaya bata ƙona duka jirgi, haka rikici ba zai ɗauki gari gaba ɗaya ba idan muna tare.”

    Nawalmu ya ce:

    “Hikima tamkar haske ce; idan ka kunna ta, duhu ya gudu.”

    Garba Ode ya yi dariya ya ƙara da :

    “Ai ni Garba Ode, na saba da aiki da mutane. Idan kana so su nutsu, ka fara nutsuwa da kanka.”

    Jama’a suka yi banƙwana da dariya.

    Fitilu suna haske, tituna suna sababbi, masana’antu sun tashi, gidaje sun gyaru, kasuwa ta bunƙasa, matasa na neman ilimi da sana’a.

    A hankali, mutane na ko’ina suna cewa:

    “Kudan ta dawo.”

    Salmanu ya tsaya gefe yana kallon wannan canji. Yana jin kamar an saka masa nauyin al’umma a kafaɗarsa, ba nauyi mai wahala ba, amma na alfahari.

    Ya ce a zuciyarsa:

    “Idan mutum bai yi wa gari ba, gari zai yi masa.”

    Saboda haka ya yi addu`a:

    “Allah ka saka da alheri, ka dauwamar da zaman lafiya.”

    Fitilar gari ta haska fuskarsa, kamar wani sabon jarumi da zai ci gaba da jagorantar al`umma zuwa gobe mai haske.

    Salmanu Faris, ya tashi tsaye cike da murna. Sannan yace ” al’ummar wannan gari mai albarka, na shirya wata waƙa, don taskance unguwanninmu da kuma wasu ayyuka na mu”. Ga waƙar nan kamar haka:

    1.

    A ƙasar Kudan mai daraja, mai farin taurari a samanta,

    Tarihi ya haɗa ƙofofi huɗu, kowacce na ɗauke da alherinta,

    Ƙofar Arewa mai kwanciyar hankali da nutsuwa babu tata,

    Ƙofar Gabas mai mazan jiya, uwa ce ga arziki da rabonta.

    2.

    Ga Ƙofar Yamma, wurin jarumai tun kaka da kakanta,

    Zaria ce ta gefe, mahaɗar ilimi da sadar da zumunta,

    Duk mai shiga sai ya ji ƙamshi mai daɗi daga gadonta,

    Kofofi mai tarihi, wanda ba ta gushewa har lokacinta.

    3.

    Makera farfaru,masu fasaha tun da, fitila ce ga sana’arta,

    Makera babbaƙu, masu hikima wanda ba sa yin gorinta,

    Saidawa da Zaɓi, unguwanni masu sana`a da himmata,

    Unguwar Liman, Bela, da Juga,suna ɗauke da kamalarta.

    4.

    Yan Gishiri, unguwar arziki, mai ƙara armashi a miyarta,

    Unguwar Malamai, maɓuɓɓuga ilimi, haske ke iliminta,

    Unguwar Ƴan Takalma, ƙwararru ne masu zaratar fata,

    Tudun Wada da Ƙofar Fada, wuraren mutunci da nagarta.

    5.

    Sabon Gari, sabuwar duniya mai ci gaba da inganta.

    Rimin Baima, Kuka, Tartibu, kowacce tana da hikimarta,

    Unguwar Tsauni da Ma’aji,wuraren tarihi masu basirarta,

    Tsohuwar Kasuwa da Shagari Quarters, wurare masu limanta.

    6.

    An kafa kwamiti a kowanne yanki, don lafiya ta tabbata,

    Tarbiyyar yara, warware matsalolin aure ban da salwanta,

    Dattawa da dattijuwa na ba da shawara cikin tafiyarta,

    Domin ƙauye ba na mutum ɗaya ba ne,” don cigabanta.

    7.

    Salmanu Faris ne ya tsara wannan waƙa mai nagarta,

    Domin tunatar da sanin darajar unguwanni da ƙauyenta,

    Duk inda ka juya, alheri yana haskawa tamkar alfijir a wajenta,

    Allah Ya kare Kudan, Ya tsare ta da kwanciyar hankalinta.

    BABI NA BAKWAI

    Washe gari bayan taron godiya, garin Kudan ya tashi cikin nishaɗi da annashuwa. Mutane har suna cewa: “Gari idan ya samu shugabanni masu gaskiya da jama’a masu haɗin kai, sai ya zama kamar rijiya: kowa zai sha, amma ba ta bushewa.

    A wannan safiya, Salmanu Faris ya samu kira daga Farfesa Muazu wanda ya ce: “Salmanu, lokaci ya yi da za mu tattara tarihinku tun daga zaman lafiya zuwa gyaran gari. Ba a barin tarihi ya yi bacci. Sun zauna a cikin Babban Masallacin Juma’a, gini sabo, fenti sabo, ƙamshi yana tashi kamar sabon harsashi. Farfesa ya ce:

    “Wannan ginin da ka ke gani ba bango ba ne kaɗai. Al’umma ta gina shi da addu’a, haɗin kai da gaskiya.” Salmanu ya gyaɗa kai, yace ” gaskiya ne”. A gefen masallacin, yara suna fitowa daga sabuwar makarantar koyon sana’o’in dogaro da kai. Wacce ake koyar da:

    1. Ɗinki.

    2. Walda.

    3. Gyaran waya.

    4. Noman zamani.

    5. Tsabtace muhalli.

    Nawalmu da Nuhu Baushe su ne jagororin tsaro a wajen. Nawalmu ya ce:

    “In ka koya wa matashi sana’a, ka cire masa yunwa da rashin aikin yi a lokaci ɗaya. Tsaro ya fara da cikakkiyar” Mutane suka yi murmushi, domin kalamansa suna da kaifi, amma mai zaƙi.

    A gabas da gari kuma, titin da Rt. Hon. Isa Ashir ya gina ya sake raya kasuwanci. Baburan haya suna yawo, masu sana’ar shinkafa suna kai kaya, manoma suna kawo hatsi. Garba Ode yana tsaye da wuƙarsa a gefe yana karɓar biki. Ya kalli sabuwar hanya ya ce:

    “Kai! Idan hanyar mutum ta gyaru, al’amuransa sukan gyaru. In ka gyara hanya tsakaninka da mutane, ka gyara zaman duniya.” Mal. Mujaheed da Auwal, Salim da Abdulrazaƙ suna koyar da matasa darussan:

    1. Yadda ake kawo rahoto cikin ladabi.

    2. Yadda ake lura da abin da ya saɓa da al’ada.

    3. Yadda ake guje wa hayaniya da tada husuma.

    4. Yadda ake tsare unguwa ta hanyar sa-ido da bin doka.

    Shi kuma Nuhu Baushe yana kula da masu sintiri daga maraice zuwa safiya. Yana kiran wannan aiki: “Kayan kwana tamkar halacci kare gari. Idan gari ya kwana lafiya, kowa ya huta. A asibitin da sabuwar na`ura ke aiki, Furaira (Hajiyayye) da Sha`awanatu suna kula da marasa lafiya.

    Mutane sun saba cewa: “Asibiti tamkar zuciya ce ga gari. Idan zuciya ta yi ƙarfi, mutum ba ya faɗuwa.” Likita ya ce Salmanu ya kawo rubutu kan yadda aka inganta aikin jinya. Salmanu ya amince.

    A ɓangaren ɗaya kuma, lokacin da ranar ta yi sakaliya, filin ƙwallon da Rt. Hon. Isa Ashir ya gina ya cika da mutane. Matasa suna motsa jiki, yara suna kallo. Muryar masu ihu ( zuga) tafi tana ƙara karaɗe garin, a lokacin da Ibrahim (Henry) da Zubairu ( Eto) suka ci wata ƙwallo ta ban al’ajabi. Isma’il ya kalli Malam Mujaheed ta yi murmushi:

    “Ka ga idan matasa suna motsa jiki, ba su da lokacinnda za su bi maganganu marasa amfani.

    Karanta Tarihin Garin Kudan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Asalin Kishi Yake

    Yadda Asalin Kishi Yake

    GABATARWA

    A shekarar 2013, wani rahoton binciken masana da Farfesa Daniel Freeman na Jamiar Oxford tare da marubuci Jason Freeman suka wallafa a jaridar ‘The Guardian’ ta ƙasar Amurka, mai taken ‘Jeolousy: It’s in your gene’, ya nuna cewa kishi gadajjen abu ne wanda kowanne ɗan adam ke tare da shi a cikin ƙwayoyin halittar sa.

    Binciken da masana suka gudanar  ya nuna cewa mata sun fi bayyana kishi sama da maza, wannan kuwa a kimiyyance muna iya danganta shi da yanayin mutumtakar jinsinan biyu wajen jure yanayai na zuciya da ɗaukar matakai a game da su.

    Mujallar BBC Science Focus ta taɓa yin nazari game da dambarwar masana a kan ‘shin kishi abu ne da ɗan Adam ya yo gadon sa ko wanda ya koya bisa zamantakewar sa a muhallin sa?’.

    Shi ne har suka kawo hujjojin kowanne ɓangare, ciki har da masu kallon yadda wasu sarakuna a zamanin baya su ke bai wa baƙinsu matayen su don su tara da su, da yadda wasu ke faɗin cewa ba su taɓa jin kishi game da abokan tarayyar jima’in su ba, sai dai bisa la’akari da hujjojin masu cewa ‘gadon kishi ɗan Adam ya yi’, waɗanda suka haɗa da yadda maza a mafi yawan lokuta suke son kyakkyawar mace (satirical theory) mai jiki sama da sauran mata, da yadda wannan soyayyar ta maza kan haifarwa da mata daraja musamman daga ‘ƴa’ƴayen da dangantakar ta samar musu saboda tarawar jima’i.

    Sai ya zamana wajibi ga mata su fi buƙatuwar samun kaɗaitacciyar dangantaka wadda za ta ba su ‘ƴa’ƴaye, wanda hakan kan tilasta jikkunan su samar da ƙwayoyin halittun da za su fi son wanzuwar su kaɗaitattu ababen so a wurin abokanan zaman su (maza).  Wannan ne silar samuwar kishi a ɓangaren mata, wanda kan faru da zarar mace ta hangi yiwuwar faruwar wani abu wanda zai iya dakushe mata wancan muradi nata da ta yi gado daga ƙwayoyin halittu.

    Sai kuma yadda aka lura da samun ɓurɓushin kishi daga wasu dabbobi misalin Gibbon waɗanda dangantakar su ta ƙwayoyin halittu ke tuƙewa da ɗan Adam, don haka aka fi danganta kishi ga ‘Natural Selection’, watau watsuwar ƙwayoyin halittu.

    Ƙarin hujja a kan haka shi ne yadda a baya-bayan nan wani rahoton bincike ya tabbatar da cewa kishi shi ne silar da yara ƙananu ke yawan kuka/rikici da dare domin kange mahaifansu daga tarawa wadda za ta kai su ga samar musu da ƙani ko ƙanwa, da kuma yadda yara ke ƙara yawaita rikici bayan mahaifiyar su ta sake haihuwa.

    Mutane da yawa da zarar an ambaci kishi sun fi danganta shi a tsakanin ma’aurata, musamman tsakanin kishiyoyi, amma a zahiri kishi ya wuce haka. Don haka a taƙaice, wannan ɗan rubutu zai kalli wasu daga taƙaitattun zantuka game da asalin kishi a kimiyyance da tasirin sa gami da yadda ya kamata a tunkare shi.

    MA’ANAR KISHI

    Masana da dama sun fassara ma’anar kalmar kishi gwargwadon fahimtar su, amma bisa tamu fahimtar, kishi na nufin wani yanayi na zuciya wanda yake cike da tsoro da firgici da tsana da ƙyamata, wanda ya ke bijirowa a duk sa’ar da wani ya fahimci samuwar wani abu mai barazana ga darajar sa ko matsayin sa, ko damar sa, ko mabiyan sa ko wani abu muhimmi da yake tutiya da shi.

    ASALIN KISHI

    Ko da yake, masani mai bincike Emanuel Eisner ya faɗi cewa ƙwayoyin halittar mu kusan ɗaya suke da na kakannin mu waɗanda suka rayu kimanin shekaru 600 da suka gabata, amma haɓakar yanayin kishi a zuciyoyin mu yana da alaƙa da sauyawar abubuwan da suka rinƙa faruwa ga ɗaukacin jikkunan mu na tsawon waɗancan shekaru, wanda hakan ke nufin cewa akwai ɗaukacin banbanci a tsakanin abinda mutumin yanzu zai yi kishi a kansa da na mutumin da ya rayu shekaru 600 baya.

    Wannan ya samu ne daga sauyawar muhallai, da buƙatu da muradun mu ne, amma kuma ɗaukacin jigon kishin sam-sam bai sauya ba. Masani Aaron Sell na jamiar Griffith da ke Australia, ya yi nazari a kan asalin kishi, inda har ya gano kishi ne silar aikatuwar wasu munanan laifuka da rashin zama lafiya irin wanda ake fama da su a halin yanzu.

    Misali a kan haka shi ne KISA

    Kimanin kashi 90% na kashe-kashe da ake yi a wannan duniyar maza ke aikata su, amma an lura da cewa mata ne a kan gaba wajen kashe ƙananun yara (Infanticide) da kuma abokanan auratayyar su (spousal homicide).

    Mu kalli Spousal Homicide: Wananan kalma na nufin yanayin kisan kai da kan faru tsakanin ma’aurata, walau miji ya kashe matar sa, ko mata ta kashe mijinta. Bincike ya tabbatar da cewa mata aka fi samu da kashe mazajen su.

    Haka nan, Bincike ya nuna cewa sama da dubunnan shekaru, mazajen da suka rayu a wannan duniyar suna cike da kishin matayen su, don haka sun kasance cike da ƙoƙari wajen ganin sun mallaki akalar matayen su, watau sun kange su daga tarayyar da ba sa so.

    Wasu mazan kan yi haka ta hanyar tsoratarwa, ko nuna ƙarfi ga mata waɗanda akasari su ne a ƙarƙashin su, wannan ya sa har zuwa yanzu akan samu yanayan da namiji zai saki mace, sannan ya bi sabon mijin da ta aura ya kashe ko ya yi wa lahani, saboda ya sake ta ne cikin fushi, yana mai burin ta shiga wani yanayi wanda zai sa ta yin nadamar rabuwa da shi ba don ba ya son ta ba, amma da zarar ya ganta cikin yanayi mai daɗi saɓanin yadda ya yi muradi, sai kishi ya taso masa, wanda a wasu lokutan ya kan zama silar aikata munanan ayyuka.

    Su kuwa mata kasancewar su raunana ga maza, sai suka fi amfani da kisa a ɓangaren su wajen gudanar da nasu kishin na kange mazajen su daga tarayyar jima’in da ba sa so. Duk da cewa an lura da cewar mata masu ƙarancin shekaru kuma waɗanda ba su haihu da yawa ba ne suka fi aikata hakan, amma sau tari ɓacin ran da ke tunkuɗa su aikata wannan mummunan aiki daga gundarin kishi ya ke.

    Mai bincike Anne Campbel ta gudanar da cikkaken bincike game da silar rikicin mata, abinda ta tafi a kai shi ne mata sun ɗora rayuwar su kachokan ne a kan maza (uba, ɗan uwa, miji da sauran su), don haka matsawar mace tana da namijin da zai mata yaƙi, ba za a ganta cikin rikici ba.

    Saboda haka ana iya cewa babban abinda ke tunkuɗa mata aikata wancan ta’addancin na kashe mazajensu bai wuce yadda suke ɗaukar tozarci ne a gare su idan har suka samu raguwar daraja ko kawar da kai daga wanda suka ɗorawa so da aminci a garesu, don haka sukan gwammace halaka mazajen su duk a cikin kishi.

    Amma a game da kisan ƙananun yara da mata kan yi (infanticide), shahararrun masanan nan Martin Daly da Margo Wilson sun yi bincike a kai, inda suka bayyana cewa samuwar kishiyar uwa a gida na sanya yaro cikin haɗarin fuskantar kisa a ƙalla da kashi saba’in, da kuma haɗarin fuskantar cin zarafi da kashi 40. Wannan ma duk kai tsaye ana iya cewa daga kishi ne wanda ke faruwa a tsakanin matan gida wanda kuma yake shafar yaran.

    Don haka, a ƙarshen binciken Masani Aaron ya tafi a kan cewa ɗan Adam bai ginu da ƙwayoyin halittun yin kisa don kange wanda yake so daga wata tarayya da ta saɓawa son zuciyar sa ba, sai dai kisan ya kasance a matsayin makami da wasu yanayai munana na zuciya kan tunkuɗa wasu mutane su yi riƙo da shi gwargwadon juriyar su ga wutar kishin da ke ruruwa a zukatan su. Wannan kuwa yanayi akan same shi a sauran sassan rayuwa ba ga auratayya ba kaɗai.

    Haka nan, masana sun kalli yawaitar tashe-tashen hankula tare da danganta su da kishi, wanda yake faruwa sabili da tarayya a kan abu guda da wasu mutane ke son mallaka, ko kaɗaituwa da shi da makamantan irin haka, don haka duk wanda ya ga akwai yiwuwar ya rasa wata martaba da yake tinƙaho da ita ko wani na son tarayya da shi ko kuma wani ya hau turbar fifita a wani lamari sama da nashi, sai kawai ya yi martani da ayyuka waɗanda suka saɓawa hankali.

    Akwai irin waɗannan abubuwa da yawa a cikin kasuwanci, siyasa, malantaka da sauran lamurori na zamantakewar al’umma. Akwai ƙarin hujjoji masu nuni da cewa kishi daɗaɗɗen abu ne da ke cikin jini wanda yake yawatawa a jijiyoyin ɗan Adam, daga misali shi ne kisan farko da ɗan adam ya soma aikatawa a duniya, watau tsakanin Ƙabila da Habila (Cain da Able), da kuma yadda ya zo a tarihi wurare daban daban inda ɗan’uwa ya kashe ɗanuwansa bisa wani dalili mai tuƙewa da kishi.

    Susan Dudley, masaniya ce mai bincike, ta gudanar da wani bincike dangane da wasu tsirrai (American sea rocket) wanda ya ƙara mana fahimta a game da asalin kishi. Susan ta ware wasu tukwane guda biyu ne, sannan a tukunya ta ɗaya ta shuka jinsin tsirrai guda guda biyu ‘ƴan uwan juna, a tukunya ta biyu kuwa sai ta shuka mabanbantan jinsinan tsirrai.

    Bayan tsawon lokaci sai ta samu cewa tsirran da aka shuka a tukunyar da ke ɗauke da mabanbantan tsirrai sun fi saurin girma fiye da ɗayar. Wannan na nuna cewa akwai kishi har a tsakanin tsirrai, domin ga shi tsirran da suke da alaƙa da juna sun hana junan su girma yadda ya kamata. Wannan fa ya faru ne a tsakanin tsirrai wanda kowa ya sani kashi 25 zuwa 30 na ƙwayoyin halittar su ɗaya yake da na bil’adama. Ina ga shi kansa ɗan Adam?

    Don haka fahimtar ainihin yadda kishi ya samo asali na da buƙatar dogon nazari mai tuƙewa da asalin samuwar ɗan Adam, amma dai a mafi rinjaye, ƙwayoyin halittar ɗan Adam ne ke ɗauke da shi.

    A INA AKE SAMUN KISHI

    An fi samun kishi a tsakanin abubuwa biyu masu alaƙa da juna. Misali, mutum ya fi kishi da mutum, dabba ta fi kishi da dabba, haka ma tsirrai sun fi yi a tsakanin su. Haka kuma, ko a cikin mutane, yawan zurfin alaƙa ke nuni da yiwuwar samun zuzzurfan kishi.

    Ko kuma a ce, kishi ya fi samuwa a tsakanin wasu mutane da suke tarayya da wani abu, misalin jinsi, ƙabila, harshe, gari ɗaya ko ƙasa ɗaya, ko ‘ƴanuwa da abokanai, ko a tsakanin wasu rukunin al’umma masu aiki ko sana’a iri ɗaya, da dai makamantan su.

    Don haka za a ga cewa mace ta fi kishi da mace ‘ƴaruwarta sama da namiji. Haka kuma sau tari, Bahaushe ya fi jin kishi ga abinda ya shafi ɗan’uwan sa Bahaushe. A wani yanayin ma akan samu cewa mutum ya fi samun maƙiya daga ƴanuwan sa na jini .

    AMFANIN KISHI

    Masana sun kalli tasirin kishi, sun kuma tabbatar da cewa abu kamar sa wanda ya daɗe a duniya yana ta bibiyar ƙwayoyin halittar ɗan Adam ba zai taɓa kasancewa mara amfani ba. Babban amfanin da aka fi dangantawa kishi shi ne; ankararwa da kuma zaburarwa domin tashi tsaye bisa naƙasun da akan iya haɗuwa da shi a lokacin da buƙatar hakan ta taso.

    Don haka, ɗan kasuwar da ya fahimci yiwuwar wani abokin kasuwancin sa zai danne shi a fannin kasuwanci, zai ji kishi a zuciyar sa, wanda hakan na nufin ya zaburar da shi domin fahimta gami da gyara abubuwa na kuskure da yake aikatawa gami da ɗorarwa a kan ayyukan da za su ƙara riƙe masa martaba a kasuwancin sa. Irin haka ne ga kishiya ta aure, ko malanta, ko ta duk wani abu da kishi kan iya bijirowa a cikin sa.

    Saboda haka kyakkyawan kishi abu ne da aka lura da cewa zai iya samar da cigaba ga mutane ko ga yankuna ko ga duk wani abu da ake kishi a kan sa matsawar an yi amfani da shi bisa tsari kyakkyawa yadda ya kamata.

    ILLAR KISHI

    Mutane da yawa suna faɗawa cikin munanan ayyuka sabili da kishi. Wani kan kashe wanda yake kishi da shi, ko ya bi wasu hanyoyi da yake gani zai iya  wargaza lamurran abokin kishin sa. Wanda akan haka, wasu kan rasa rayuwar su, ko matsayi ko darajar su ko imanin su da Allah maɗaukakin sarki. Wasu ma na tsintar kawunan su a kurkuku ko a wani yanayi mara daɗi tun a nan duniya duk bisa mummunan aikin da aka aikata saboda kishi.

    Babban illar kishi ga ɗan Adam shi ne; hana girma ko haɓaka. Sau tari, mummunan kishi ne silar durƙushewa da rashin cigaban al’umma. Shi ne kuma kan zama silar yawaitar munanan ayyuka da rashin zama lafiya.

    MAFITA GAME DA KISHI

    Yana da kyau a sani cewa babu wani ɗan Adam da ba ya jin kishi matsawar yana da lafiyar ƙwaƙwalwa. Sannan babu wata ni’ima ko fifiko da Allah zai yi ga wani ko wata wadda ba za ta sanya kishi a zukatan mutane musamman masu wani abu iri ɗaya da shi ba. Mafitar ɗaya ce; a mayar da dukkan lamurra ga Allah.

    Masani Berit Brogard yana da dabarar ‘normalism the feelings’ wajen kashe mummunan kishi, watau ɗaukar irin waɗannan yanayi a matsayin abu gama gari wanda bai kamata a tayar da hankali a kan sa ba.

    Don haka da zarar tunanin sa ya bijirar masa da wani abu na kishi, sai ya kwantarwa da zuciyar sa hankali, ya faɗa mata wannan abin fa ‘is normal’ ba abu ne mai buƙatar ɗaga hankali ba.

    Sanin kowa ne cewa kowanne ɗan Adam yana da ƙaddarar sa, wani mai kyau wani mara kyau. Don haka, sunnar rayuwa ce irin abin nan da ake cewa ‘yau gareka gobe ga wanin ka’. Wato komai na tafiya da lokaci. Idan yanzu kai ne ke sharafi, to ai a baya ba kai ba ne, don haka nan gaba ma wani ne zai yi ba kai ba.

    Abu na gaba shi ne buƙatar rage abinda masana ke kira ‘endowment effect’, wato yanayi da kan sa mutum ya ji cewa shi kaɗai ya isa da abu kaza ko jin cewa abu kaza mallakin sa ne shi kaɗai tilo, kamar yadda aka fi samu a tsakanin ma’aurata.

    Ya kamata mace ta sani cewar an halartawa namiji ƙarin aure a duk sanda ya samu sukuni, haka shi ma namiji ya sani cewar mace na da damar samun annushuwa da wanin sa idan ƙaddarar rabuwa ta auku a auratayyar su.

    Kuma ya kamata kishi ya zamo silar zaburar da mutane aikata kyakkyawan ayyuka ba munana ba. Sannan mutum ya ɗora faruwar lamurra dukkan su ga Allah maɗaukakin sarki, walau ga kansa ko ga wanin sa.

    Ƙarshen wannan muƙala kenan.

    Ina mai adduar Allah ya jikan babban marubuci Alh Bashir Usman Tofa wanda aka yi jana’izar sa a yau litinin 2/1/2022.

    Ga masu buƙatar ƙara samun sani game da wannan muƙala, akwai kwas mai taken ‘Introduction to Mental Health’ wanda muka samar kyauta a kwalejin Hausa ta yanar gizo mai suna AAGHOLI a kan adireshin (https://www.aagli.com.ng)

    Nine naku Sadiq Tukur Gwarzo (Public Health Nurse, mamba Global Goodwill Ambassadors)

    Danna nan don karanta Kimiyyar Siyasar Uban Gida: Tasiri, Makoma Da Silar Rabuwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Nazarin Hanyoyin Adana Kayayyakin Hausawa Na Gargajiya

    Nazarin Hanyoyin Adana Kayayyakin Hausawa Na Gargajiya

    TUN KAFIN A HAIFI UWAR MAI SABULU, BALBELA TAKE DA FARIN GASHINTA: NAZARIN HANYOYIN ADANA KAYAYYAKIN HAUSAWA NA GARGAJIYA

    Daga

    Magaji Ahmad Gaya PhD

    Sashen Koyar Harsunan Nijeriya,

    Jami’ar Northwest, Kano

    magaya@nwu.edu.ng /magajiahmadgaya@gmail.com

    08066009039

    Takardar Da Aka Gabatar A Taron Makon Hausa Wanda Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya Jami’ar Arewa Maso Yamma (Northwest) Kano Ta Shirya. Wanda Aka Gabatar A Babban Ɗakin Taro Na ‘Yanganau Da Ke A Farfajiyar Jami’ar. Ranar Alhamis 29/01/2026

    Tsakure

    Al’ummar Hausawa, mutane ne waɗanda tun fil’azal suna da hikimominsu da suka gada tun iyaye da kakanni, waɗanda suke aiwatar da su har ya zuwa yau. Suna amfani da fasahohinsu da hikimimominsu da basirarsu ta hanyar sarrafa albarkatun da suke kewaye da muhallansu, waɗanda suka haɗa da adana kayayyakin Hausawa na gargajiya domin su samar da kayayyakin amfanin kansu.

    Manufar wannan takarda ita ce bayyana wasu hanyoyin adana kayayyakin gargajiya wanda suke amfani da su tun kafin haɗuwar su da baƙin al’ummu. An yi amfani da hanyoyin gudanar da bincike, waɗanda suka haɗa da tattaunawa da ziyarar gani da ido da karantawa daga wasu rubutattun bayanai.

    An ɗora wannan bincike ne bisa ra’in Adana Al’adu da Cigaban Al’umma wato (Cultural Sustainability Theory), shi ya fi dacewa da wannan bincike. Gusau (2015:55) ya kira makarantar da ta fito da wannan ra’i da suna ‘‘Mazahabar Adana Al’adu’’. Shi kuma Sha’aibu (2013:78), ya kira makarantar da ke da’awar wannan ra’i na Adana Al’adu da suna “Mazahabar Muhafaza”.

    Sakamakon takardar ta nuna cewa al’ummar Hausawa suna da hanyoyin adana kayayyakinsu a gargajiyance waɗanda suka gada tun kafin zuwa ko haɗuwa da baƙin al’ummu. Hausawa suna amfani da su wajen adanawa tare taskacewa don gudun lalacewa ko salwanta.

    Muhimman Kalmomi: Adana da Kayayyaki da Hausawa da Gargajiya.

     Gabatarwa

    Wannan takarda za ta yi duba ne a kan kayayyakin da al’ummar ƙasar Hausa suke amfani da su wajen adanawa. Waɗannan kayayyakin gargajiya da za a yi nazari a kansu, na su ne, kuma har gobe suna amfani da su wajen aiwatar da ajiye-ajiye da aikace-aikace. Akwai tarin fasahohi da hikimomi ta yadda Hausawa suka samar da su, musammanma idan aka yi la’akari da yadda suke taimaka musu wajen adana kayayyakinsu cikin sauƙi, ba tare da wata matsala ba.

    Haka kuma, an nazarci yadda masu sana’ar suke amfani da su, kuma an kawo bayanin yadda suke  samar da su da kuma nau’o’in aikace-aikacen da ake yi da su. Hausawa sun inganta wasu kayayyakin, domin su dace da buƙatun mutanan, da ma na wannan zamani. Har ila yau sun yi ƙoƙari matuƙa wajen rage tsofaffin kayayyaki, waɗanda maimakon su yi wasarere da su gaba ɗaya, akwai buƙatar ƙara inganta su domin tafiya da zamani.

    Manufar Gudanar da Bincike

    Manufar wannan takarda ita ce, bayyana wasu hanyoyi  da al’ummar Hausawa suke amfami da su wajen adana ko taskce kayayyakinsu domin gudun lalacewa ko salwanta ko kuma domin tarihi da makamantansu.

    Haka kuma, wata manufar ita ce, domin bayyana ko fayyace wasu tsofaffin kayayyakin da ake adanawa haɗi da amfani da su. Sannan kuma, wata manufar ita ce, domin fito tare da bayyana alfanun da kayayyakin suke da shi wajen adanawa da kuma mai da hankali wajen nazarinsu ga masu bincike domin gujewa gushewarsu.

    Ra’in Bincike

    Wannan bincike an ɗora shi ne a kan Ra’in Haƙiƙa, wannan bincike ya bibiyi ra’o’in binciken al’adun Hausawa daban –daban don tantance wanda ya dace da wannan bincike: inda aka gano cewa Ra’in Adana Al’adu da Cigaban Al’umma wato (Cultural Sustainability Theory), shi ya fi dacewa da wannan bincike.

    Gusau (2015:55) ya kira makarantar da ta fito da wannan ra’i da suna ‘‘Mazahabar Adana Al’adu’’. Shi kuma Sha’aibu (2013 :78), ya kira makarantar da ke da’awar wannan ra’i na adana al’adu da suna ‘‘Mazahabar Muhafaza’’.

    Salsalar Ra’i

    Wannan ra’i ya samo asali ne ta hanyar gudummawar masana da hukukmomi da ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa, wanda John Hawkes ya assasa a matsayin jagoran wannan ra’i.

     Mabiya Ra’i

    Ko da yake John Hawkes ne ya fi shahara wajen gabatar da wannan ra’i, amma akwai masana da hukumomi da dama da suka rungumi tare da bunƙasa wannan ra’in na adana al’ada. Wasu daga cikinsu su ne:

    • Unesco da UNDP (United Nations Development Programme)
    • David Throsby,
    • Jown Hawkes Australian Coucil For the Art
    • Katrilna Soini & Inger Birkeland
    • Nancy Duxbury
    • Keith Nurse
    • Graham Fairclough

    Ayyukan da aka Ɗora Ra’in a kai

    Akwai bincike masu dama da aka gudanar a baya, waɗanda suka yi amfani da wannan ra’i na adana al’ada daga cikin su akwai John Hawkers (2001) ya yi littafi mai suna The Fourth Pillar of Sustainability: Cultures Assencial Role in Public Planning. Ya jaddada cewa dole ne a haɗa al’adu cikin tsare-tsaren cigaba.

    Sannan da David Throsby (2008-2010), Linking Cultural and Ecological Sustainability. The Economic of Cultural Policy: ma’ana dangantakar da ke tsakanin Al’adu, Tattalin Arziki da Ɗorewarsu. Sannan kuma akwai binciken da UNESCO ta tallafa a shekara ta (2003-2015), mai taken “Al’adun Gargajiya Marasa Ganuwa (Intengible Cultural Heritage), da ilimin gargajiya na asali, sai kuma Harsuna da suke fuskantar shuɗewa.

    Haka kuma akwai binciken da aka gabatar a jami’o’in gida a kan al’adun Hausawa da suka haɗa da:

    • Aminu Lawan, ya yi bincike a kan “Ɗorewar al’adun Hausawa a Zamanin Zamani”. Jami’ar Bayero, Kano.
    • Zainab Sadiq, ta yi bincike a kan “Rawar Bukukuwan Gargajiya Wajen Raya Al’adu”. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sokoto.
    • Abdullahi Musa. ya yi bincike mai taken “Tasirin Zamani da Adabin baka na Hausa”. Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya
    • Hadiza Bello, ta yi bincike mai taken ‘‘Rawar ‘Yammata Wajen Kare da Ɗorewar Al’adu a Arewacin Najeriya”. Jami’ar Ilorin
    • Sani Ibrahim, ya yi bincike a kan “Gudummuwar Sarautun Gargajiya Wajen Ɗorewar Al’adu”. Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’adua Katsina.

    Dangantakar Ra’i Da Nazari

    Bayanan cikin wannan ra’i suna da dangantaka ta kai tsaye da wannan nazari, sannan za su zamo wani dandamali da wannan bincike zai taka ya hau har wannan bincike ya samu kammaluwa. Saboda ra’in yana bayani ne kan yadda za a tseratar da al’adu daga salwanta, wanda wannan shi ne ƙudirin wannan bincike da za a gudanar.

    Hanyoyin Gudanar da Bincike

    Kamar yadda aka sani, babu aikin da za a yi ba tare da bin wasu hanyoyi na gudanar da shi ba. Fayyace waɗannan hanyoyi a bincike irin wannan yana da matuƙar muhimmanci, domin zai taimakawa wajen tabbatar da sahihancin bayanan da aka kawo a cikin aiki.

    Ba a bar wannan binciken a baya ba ta wannan fuska, domin shi ma an yi amfani da wasu hanyoyi wajen tattara bayanan da suka taimaka wajen aiwatar da shi. Daga cikin hanyoyin, akwai tattaunawa da mutanan da aka samu damar tattaunawa da su domin samun nasarar wannan bincike.

    Wajen gudanarwa an yi la’akari da matsayi da kuma shekaru. Mutanen da aka tattauna da su sun haɗa da tsofaffi maza da mata, waɗanda suka taimaka wajen fito da wasu muhimman bayanai na waɗannan kayayyakin aiki. An kuma kai ziyarar gani da ido, inda kai tsaye aka ziyarci masu gabatar da ayyukan kaba da maginan ƙasa da fatu da sauransu, kuma aka tabbatar da wasu bayanan da aka samo daga gare su.

    Baya ga waɗannan hanyoyi, an kuma tuntuɓi masana na sana’o’in gargajiyar Hausawa, kuma an bibiyi rubuce-rubucen magabata inda aka samu tarin bayanai da suka taimaka wajen rubuta wannan takarda.

    Nazarin Hanyoyin Adana Kayayyakin Hausawa Na Gargajiya

    Akwai hanyoyin da ake amfani da su wajen adana kayayyakin Hausawa na gargajiya masu yawan gaske, waɗanda lokaci ba zai bayar da damar kawa su gaba ɗaya ba, sai dai a kawo misalan wasunsu tare da bayani.

    Rumbu

    An bayyana kalmar rumbu da shi ne, “ɗakin da ake ginawa da ƙasa ko karan dawa ko gamba domin adana hatsi” (Sa’id, B. da wasu 2006). Ana saƙa rumbu ne da ciyawar gamba wadda take da tsawo da ƙwari, akan ɗora bisa dirkoki ko kuma manyan duwatsu saboda gudun  ƙwari ko ɓeraye.

    Akan ɗora masa  ɗan boto a sama a matsayin murfi domin adana kayan amfanin gona irinsu gero ko dawa ko gyaɗa ko wake ko ɗauro cikin zangarniya. Idan ana buƙata sai a tsakura ko kuma a ɗebo domin biyan bukatar yau da kullum.

    Randa

    Wannan wani mazubi ne da ake ajiye ruwa a cikinta.  Sa’id da wasu, (2006) sun bayyana ta da cewa” “Wata ƙatuwar tukunya da galibi ake zuba ruwa a cikinta ko kuma ta zamanto taskar ajiye kuɗi. Har ila yau tana iya zama rijiyar karofi ta rini. Randa tana daga cikin kayayyakin da Hausawa suke amfani da ita, magina ƙasa ne suke gina randa.

    Yayin da za a gina ta magina, suna samo taɓo da ƙasa ta jangargari haɗi da ruwa a cakuɗa har dai a samar da ita. Yayin da aka samar da ita akan ajiye ruwan sha da kuma adanawa domin tanadin abubuwan da za su iya tasowa haɗi da abubuwan yau da kullum.

    Ruzu

    Wata irin ƙaramar jakace saƙaƙƙiya. Ruzu wata jaka ce wadda ake saƙa ta da kaba ko zare, tana da ɗan faɗi da tsayi sannan tana da maratayi, ana rataya ta a kafaɗa, mafarauta sukan saka naman daji idan sun kamo a ciki, yayin da suka fita farauta ko sharani ko ƙuloto. Sannan idan suka dawo gida akan ajiye naman da suka samo a cikinsa (Tattaunawa da Baba Sayyadi).

    Taskira

    Ana saka ta dominn aikin kaɗin zare da abawa, tana da faɗi kamar faranti ƙarami ko filet na zamani, sai a shimfiɗa mata fatu riɓi-riɓi kamar talatin ko talatin ko ashirin, mai ɗakin kan ajiye wasu abubuwa masu muhimmanci da suka haɗa da; kuɗi da ‘yankunnaye da sarƙoƙi da sauransu.

    Ana yi wa taskira kirari da: “Taskira Asirin Mai Ɗaki. ”Don haka za a iya cewa, taskira, wani ɗan ƙaramin kwando ne da aka saƙa da kaba wanda mata ke amfani da shi wajen zuba auduga da mazari da alli don yin kaɗi (Sa’id, B. da wasu 2006).

    Gajiran/Gajirami

    Wannan shi ma wata ma’ajiya ce ta gargajiya wadda Hausawa, suke ginawa tare da jera su a ɗaki. Akan yi rami matsakaici kamar yadda tukunya ƙarama za ta shiga cikin ramin sai a layanta su a bango da ƙasa, sai kuma abinne amma bakinsu yana kallon sama, akan adana wake ko gyaɗa ko riguna ko zannuwa ko hatsi da sauransu, wasu ma har kuɗi suke ajiyewa (Tattaunawa da Maisalati Durɓindai).

    Adudu

    Wannan kuwa, ya kasance ɗaya daga cikin kayayyakin da Hausawa suke amfani da shi musamman wajen ajiye ko adana wasu hajoji da nufin kaucewa salwanta ko kuma lalacewa. Wata ma’ ajiyin sutura mai zurfi da kuma murfi wanda ake yi da kaba (Sa’id, B. da wasu 2006). Adudu wata fasahar Hausawa ce, wanda ake amfni da kaba da gazari wajen saƙa shi domin adana sutura domin kaucewa ɓarnar ƙwari.

    Lefe

    Mazaubi ne da ake saƙawa da kaba don kaɗar auduga ta zama zare. Yayin da Sa’id da Wasu (2006) suka bayyana shi da cewa: “Wani makai da ake saƙawa da kaba don saka ko ajiye kayan kaɗi ko zuba kayan aure”. Haka kuma, wannan ya sanya Hausawa suke zuba sutura a ciki don kai Toshi gidan su amarya kafin a yi aure.

    Kuratandu

    Kuratandu wani ɗan ƙaramin tandu ne ake yinsa da jemammiyar fatar akuya ko tinkiya ko wata ƙaramar dabbar domin sa kwalli da mishiyi da akan sa kwallin da shi. Sannan kuma a sa matashi haɗi da murfi domin gudun ka da ya zube ko kuma ya salwanta.

    Akurki

    Akurki ana saƙa shi ne da itacen geza, za a zubar da ganyayyakin da ke maƙale a jikin itacen, sai kuma a tsaga itacen gezar gida biyu ko uku a tsaye. Ana saƙa kamar yadda ake kife ƙwarya, ana yi masa ƙofa daga ƙasa, yayin da aka kammala sai a samo kashin shanu sai a baibaye shi ciki da waje.

    Yana daga cikin kayyakin Hausawa na gargajiya da ake amfani da shi musamman wajen ajiye da kuma adana tsuntsaye nau’in kaji ko agwagi da zabbi da agwagi da makamantansu. Yayin da aka saka su ciki ko kuma suka shiga da daddadare sai a saka murfi a rufe ƙofar ta yadda wani abin cutarwa ba zai sami damar cutar da su ba irin su maciji ko muzuru ko cimola da makamantansu.

    Cali

    Wannan wani abu ne raga-raga, wanda ake saka tuluna ko ƙore da makamantansu. Wasu lokutan akan ɗora wa jaki idan za a kai su kasuwa. Sannan kuma a wasu wuraren cali kan kasance mazubin kayan amfanin gona kamar albasa ko yalo, ana saƙa shi ne da igiya, yana da ƙofofi don kayan su sha iska. Ana amfani da cali a ɗora kan jaki ko takarkari don ɗaukar kaya.

    Taiki

    Mazubi ne na jemamiyar fata wadda ake ɗinkawa, wadda za a ɗura tsabar gero ko dawa ko shinkafa wadda zai kwanta kan jaki ko takarkari mai siffar mangala domin kai kayan amfanin gona kasuwa ko kuma wurin da ake da buƙata. Akan zuba tsabar gero ko dawa ko rimi da makamantansu.

    Kwatanniya

    Kwatarniya wani matsakaicin mazubi ne wanda masu sana’ar ginin ƙasa suke samarwa. Ana samun taɓo da jangaggari da ruwa sai a haɗa a kwaɓa, sai kuma a samo wata tsohuwar kwatarniyar a mamaye bayanta da wannan taɓon da jangargarin da aka kwaɓa, ana bi ana bugawa kaɗa-kaɗan har ta zama ta yi kwafin ta farko, sai a bi a gyaggyara har ta zama abin da ake so.

    Ana zuba ruwa musamman idan za a yi wankan jego, haka kuma ana amfani da ita wajen wanki ko wankin kalwa. Haka kuma ana ajiyewa dabbobi irinsu awakai da tumakai ruwan da za su sha idan sun dawo gida daga kiwo. Ana yi mata kirari da cewa: “Kwatarniya kin fi arfin roro”.

    Akushi

    Akushi kwanon da ake cin abinci ne da shi ne a gargajiyance, sai dai shi ana sassaƙa shi ne da gungumen itace, ana zuba abinci a cikinsa kamar tuwo da miya, kasancewar itacen mai kauri ne yakan sa abincin ya daɗe bai huce ba.

    Ƙwarya

    Ƙwarya ana samunta ne daga ɗan duma, yayin da ya zama babba ya riƙa. Bayan an ɗebe kayan amfanin gona, sai masu sana’ar fafar ƙwarya su raba ta biyu, inda za su fitar da totuwar da take cikinta, sai kuma su fafe ciki sarai  sannan a barta har ta bushe, sai kuma a sake fafewa yayin da za a fitar da dukkan wata totuwar da take cikinta.

    Ita ma ana amfani da ita wajen adana kayyayaki masu yawan a gargajiyance, misali dawa ko gero ko wake ko deɓo hatsi daga rumbu, sannan kuma ana amfani da ita wajen shiqar hatsi idan an yi casa ko kusa zuba mararrakin tuwo idan an kwashe.

    Tallen Miya

    Maginan gargajiya na Hausawa su ne suke gina tukwanen ƙasa. Tallen tukunyar ƙasa, na daga cikin kayayyakin da ake amfani da su wajen adana ko ajiye kayayyaki wanda Hausawa suke saka suturarsu ko kuɗi ko ko kuma abinci domin gudun salwanta ko ɓata.

    Kamar yadda, Sa’id, da wasu (2006). Suka tabbatar cewa, makai da aka gina da laka aka gasa don dafa abinci ko zuba ruwa ko ajiyewa wani lokaci ma da adanawa. Shi kuwa Talle, wata ƙaramar ‘yar ƙaramar tukunya ce da ake dafa miya a cikinta.

    Ya kasance kamar tukunya sai dai, bai kai ga tukunya girma ba, da shi ake amfani wajen yin miyar abinci, yayin da aka gama miya akan ajiye ta saboda ka da ta lalace ko kuma ta salwanta wasu lokutan akan adana saboda akuya ko yaro ko wata dabbar ta zubar da ita.

    Asusu

    Wannan ya kasance wurin ajiyar kuɗi da ake ginawa a jikin bango ko ɗan kurtun yamɓu mai ƙaramar tsaga, ko gwangwani da aka yi masa ‘yar tsaga. Asusu wata ma’ajiya ce da Hausawa suke samarwa ta hanyar sarrafa ƙasa ta yumɓu haɗi da sauran kayyayakin samar da shi.

    Za a yi masa ‘yar ƙofa kaɗan yadda hannu ba zai iya shiga ba, duk abin da aka zura cikinsa ya shiga ke nan idan har ana da buƙata sai dai a fasa ko kuma a ɗauki lokaci mai tsawo kafin wani abu ya fito, sannan kuma daga sama ana yi masa mariƙa ta ƙasa. Akan zuba kuɗi domin yin ajiya (Tattaunawa da Mukhtar A. Isma’ila).

    Ragaya

    Ita ma hanya ce da Hausawa suke amfani da ita wajen ajiye tare da adana kayayyaki domin gudun salwanta ko lulubewa. Sa’id, B.da Wasu (2006). Sun ce: “Ragaya ita ce maratayin ƙore ko kaya da ake ɗaurawa ko ajiye wani a jinkar ɗaki daga ciki, wanda kuma ake saƙawa da tufkarkiyar kaba ko yawa.” Ragaya ita ce wadda ake saka ƙoƙuna ko akusai a ciki, yadda za ta zama an sarrafa ta da kaba sannan a yi mata gida-gida ko kuma hawa-hawa musamman domin ajiyar wani abu.

    Kula

    Kula ita ce babbar butar ƙasa da ake zuba ruwan sha a ciki domin ya yi sanyi. Ta kasance tana daga cikin jerin kayayyakin ajiyar Hausawa na gargajiya. Ana yin ta da taɓo da jangargari da ruwa. Maginan tukwane da sauran nau’o’in sarrafa ginin ƙasa ne suke samar da ita.

    Kula ita ce butar da ake yi da ƙasa, akwai ƙarama sannan kuma akwai manya, ƙananan su ne ake amfani da su wajen sayar da ruwan alwalla a kasuwannin ƙauyuka, Manyan kuma su ake zubawa ruwan sha domin ya yi sanyi, musamman a lokutan bazara yayin da ake tsananin rana. A lokutan sanyi kuwa akan ɗora ta a kan garwashin wuta don a sami ruwan xumi. (Tattaunawa da Muhammad Sani ).

    Ƙaho

    Ƙaho ya kasance wani abu ƙashi-ƙashi guda biyu da yakan fito a kan dabba, kamar saniya ko rago ko akuya ko barewa (Sa’id, B. da wasu 2006) musamman ma ƙahon rago ko kuma ƙahon wata dabbar daban, sukan sanya layun da aka rufa su da fata ko farin ƙyalle su rataya shi inda suke buƙata kamar a ƙofar gida ko a tsakar gida ko a binne domin yin kafi ko kuma wani muhimmin dalili, domin neman kariya daga al’ajanu ko ɓarayi da dai sauransu.

    Adada

    Wannan wata rumface wanda ake yinta a tsakar gidan Bahaushe, ana yin ta da gwafanni da bunu ko ciyawa, wasu lokutan kuma akan haɗa da zana da igiya da sauransu, akan ajiye kayayyaki irin su fatun buhuna ko kayayyakin aikin gona da suka haɗa da; magirbi da sungumi da garma da fatanya da gatari Har ila yau akan ajiye karbi da dai sauran kayyakin da ake da buƙata a ajiye (Tattaunawa da Kawu Mu’azu).

    Batta

    Wani ɗan kuttu ne na ƙirgi wanda ya ɗan ɗara girman kuratandu wanda ake zuba taba gari a ciki ( Sa’id, B. da wasu 2006). Shi ma yana ɗaya daga cikin kayayyakin Hausawa da suke yin ajiya haɗi da adanawa domin ka da su salwanta. Haka kuma matan Hausawa sukan yi ajiyar kayan kwalliya da sauran wasu abubuwa muhimmai, kamar tozali, gyatuma raɗau ko kuma aɗaɗa ko janbaki ko hoda ko jar koya da makamantansu.

    Don haka Batta tana da siffa kamar haka, akan shirya da tsara ta tare da yenta kamar siffar adaka, sai dai da katako ko kuma itace, sai kuma a lulluɓe ta da fata wanda Dukawa wato masu sana’ar sarrafa fata suke samar da ita (Tattaunawa da Malam Gambo.)

    Angara

    Kamar sauran kayyayin ajiyar Hausawa, Angara ta kasance wata ƙaramar jaka ce mai kama da zabira ta wanzamai, galibi maharba ne suka fi amfani da ita, domin adana kayayyakin harbinsu kamar, ’ya’yan date da toka da tsakuwa da ashana da sauransu. Dukawa ne suke samar da ita, saboda ta kasance ta fata ta kowace dabba in dai ta kasance mai faɗi (Tattaunawa da Malam Gambo).

    Akwatsa

    Wani ɗan ƙaramin wuri ne da ake samarwa mai kama da kanta, sai dai bai kai kanta girma ba, wani lokacin ma ana yin ta daf da ƙofa daga cikin ɗaki ko kuma daga waje. Akan yi ajiyar kayyayakin buƙata kamar su guntun manguli da ashana da kuka da manda da kanwa da gishiri da barkono da sauransu (Tattaunawa da Sa’idu Nakande).

    Bankaɗe

    Yana daga cikin kayayyakin da Hausawa suke yin ajiya a cikinsa, sannan ya kasu gida-gida akwai bankaɗen tabarma da bankaɗen gado da bankaɗen lefe da bankaɗen mataki da bankaɗen faifai da sauransu. Hausawa sukan yi masa waƙa da cewa: “Bankaɗan lefe na ka zuba mini ba ni bari sallah ta wuce ni” (Tattaunawa da Adamu Isyaku).

    Kuikuita

    Wata hanya ce ta Hausawa da suke yin ajiya a ciki, ana yin ta da kaba, sannan tana da siffar kuttu, sai dai ba ta kai kuttu girma ba.  Kuikuita tana da ɗan zurfi kaɗan, tana da murfi, sannan akan yi mata ‘yar mariƙa kamar yadda jaka take. Akan adana kayan kwalliyar mata kamar ‘yan kunnaye da barima da’yan hanci da duwatsu da murjani da sarƙa da awarwaro da zobba da tagulla da azurfa da sauransu (Hira da Maisalati Durɓunde).

    Salka

    Wata sarrafaffiyar fata ce da mahauta kan yi wa dabba fiɗar zuga-zugi, inda za su zare fatar ba tare da an yanka ta ba, musamman daga wuya zuwa ƙasa. Yayin da su kuma Dukawa suke jeme ta, wato su kawar da gashin da take ɗauke da shi, sai kuma su rina ta don ta bayar da kalla.

    Sai kuma a ɗaure dukkanin ƙofofin ƙafar ko a ɗinke su domin ka da abin da aka ajiye ko adana su zube. Akan ajiye muhimman abubuwa kamar ruwa da mai da hatsi da gari da sauransu. Sannan kuma a wasu lokuta matafiya ko kuma fatake  kan yi jagami da ita, ko kuma su ɗora a kan jakuna ko alfadarai (Hira da Maisalati Durɓinde).

    Sanho

    Shi ma yana daga cikin  kayayyakin da ake yin ajiya ko adanawa wasu muhimman abubuwa wanda al’umar Hausawa suke amfani da shi a cikin al’amuransu na yau da kullum.

    Sanho wata saƙaƙƙiyar kaba ce da masu sana’ar saƙar kaba suke samarwa, yana da siffar saƙa irin takumkumi, amma ya kasance ba shi da ƙofofi ko raga irin ta takumkumi, ya kasance haɗaɗɗiyar saƙa ce irin ta mangala. Akan ajiye kayayyakin amfani gona kamar su gero da dawa da alkama da dankali da wake da sauransu (Hira da Abdullahi Madaki).

    Kammalawa

    Wannan takarda ta karkata akalarta ne a kan kayayyakin da ake amfani da su wajen adanawa ta hanyar gargajiya, inda aka kawo bayanansu da kuma yadda Hausawa suke amfani da su a lokacin da buƙatar hakan ta taso. Kayayyaki ne na gargajiya, kuma suna da inganci da sauƙin samuwa haɗi da sauƙin sarrafawa.

    Amfani da waɗannan kayayyaki ya haifarwa Hausawa samun hanyoyi masu yawan gaske wajen adana kayayyakinsu domin amfanin yau da kullum. Takardar ta mayar da hankali kan kayyayaki da ake amfani da su wajen adanawa da kuma bayyanawa masu nazari da ‘yan baya masu tasowa su san su don ka da su wofantar da su.

    Sakamakon Bincike

    Bayan kammala wannan takarda. Babu aiki mai manufa da za a gudanar a kasa samun sakamakon da ya haifar ba. Daga cikin sakamakon da aka samu bayan kammaluwar wannan maƙala, sun haɗa da yadda aikin ya gano waɗansu hanyoyi da Hausawa suka bi cikin hikima da fasaha suka ƙirƙiri kayayyakin aikinsu waɗanda suka dace, kuma suka yi daidai da yadda za su yi amfani da su, ba tare da wata barazana ba.

    Da farko, takarda ta gano cewa ta hanyar amfani kayayyakin da ake yin ajiya ko kuma adanawa ake samar da wasu abubuwan da suke taimakawa wajen taskacewa don gudun lalacewa ko salwanta. Misali, kamar sanho da randa da rami da makamantansu.

    Haka kuma, takardar ta ƙara fito da sunayen wasu kayayyakin gargajiya masu amfani waɗanda ake samarwa, sannan kuma al’umma suke amfani da su don gudun ɓacewarsu. Misali kuikuito da salka da sanho da rumbu da makamantansu.

    Haka kuma takardar ta gano cewa mutane masu sarrafa kayayyakin adanawa ko ajiyewa suna bayar da gagarumar gudummawa wajen kyautata al’adu da kuma haɓaka tattlin arziƙin ƙasa. Domin sakamakon amfani da su na samar da abubuwan gargajiya don amfanin yau da kullum.

    Bayan nan kuma, takardar ta lalubo waɗansu kayayyaki waɗanda a yau Hausawa sunayensu kawai suka sani ko suke ji. Amma a da suna ganinsu tare da amfani da su yadda ya kamata. Misalin irin kayayyakin su ne irin su: zunguru da akwasa da tulu  da sauransu.

    Bayan da aka ƙare wannan takarda, an gano cewa har ma gwamnati da sauran hukumomin gwamnati na sayen wasu kayayyakin da aka sarrafa na gargajiya, suna adanawa a gidajen adana kayan tarihi na jihar Kano da sauran jahohin ƙasar nan da  nuna su a wajen taron baje kolin al’adu ko lokatan nunin kayan amfanin gona da ma sauran tarurruka.

    Shawarwari

    Wannan takarda tana bayar da shawara ga wasu rukunnan al’umma da ƙungiyoyin cikn al’ummar ƙasar Hausa kamar haka:

    Da farko, ana bayar da shawara ga al’umma, musamman waɗanda suke amfani da waɗannan kayayyakin a cikin gonaki da gidaje baki ɗaya, da su ci gaba da amfani da su. Dalili kuwa shi ne, rashin amfani da waɗannan kayayyaki zai iya janyo  sakaci da lalaci da karya gwiwar masu yin su wanda daga ƙarshe ma suna iya yin fatali da su baki ɗaya.

    Haka kuma, ana bayar da shawara ga hukumomi da mahukunta, musamman gidajen tarihi da gidajen sarauta da cibiyoyin koyar da al’adun Hausawa da cibiyoyin ilimi na kwalejojin ilimi da jami’o’i na jihohi da na tarayya da su riƙa ba masana da manazarta ƙwarin gwiwa da goyon baya a duk lokacin da suka je yin irin wannan bincike a wurarensu.

    Haka zalika, ana bayar da shawara ga ɗaliban ilimi, musamman matasa masu jini a jika da su tashi tsaye, tsayin daka, su ba da himma da ƙwazo wajen yin nazari da bincike dangane da abin da ya shafi irin wannan ɓangare. Dalili kuwa mafi yawan ɗalibai sun karkata ne a kan jigo da salo da sarrafa harshe. Abin, ya kamata mu fuskanci al’adunmu na gargajiya kar mu guje su mu faɗa ga na waɗansu.

    Bayan haka kuma, wannan takarda tana shawartar masana da manazarta da su ƙara ba ɗalibai ƙwarin gwiwa dangane da yin nazarce-nazarce waɗanda suka danganci irin waɗannan al’adu musamman amfani da kayayyakin da ake adanawa, don ta yin haka ne za a gano waɗansu abubuwa da aka riga aka manta da su. Sannan a san waɗansu sababbi waɗanda ba a san da su ba. Amma hakan ba zai yiwu ba har sai  an zurfafa bincike a wannan fage. Sannan za a iya cim ma wannan buri.

    Wata shawarar ita ce ga gwamnati da masu hannu-da-shuni da su tallafa wa masu irin waɗannan sana’o’i na sarrafa kayayyakin da ake amfani da su, a riƙa ba su tallafi na jari ko kayan aiki, za a samu ci gaban da ba a tunani.

    Haka kuma, gwamnati ita ce ya kamata ta tabbatar da aiwatar da koyar da sana’o’in gargajiya a manhajojin ilimi tun daga matakin firamare har ya zuwa matakin jami’a, wannan zai ƙara haɓaka sana’o’in gargajiya da bunƙasa al’adu da tattalin arziƙi baki ɗaya.

    Manazarta

    Ado, A. (2019). Ra’o’in Bincike Kan Al’adun Hausawa. Katsina: Government Printing Press, Nigeria.

    Akodu, A. (1985) A Comparative Study of The Traditional and Contemporary Arts of The Maguzawa of Kano and Kaduna states Ph.D. Thesis, Department of Fine Arts, Faculty of Enviroment Design. Zaria: Ahmadu Bello Uniersity.

    Alhassan H. Da Wasu, (1982).Zaman Hausawa. Bugu na Biyu, Kaduna: Islamic Publication Bureau.

    Bargery, G.P.(1934).English Hausa Vocabulary. London: School of Oriented Studies, University Press.

    Bunza, A.M. (2006). Gadon Fexe Al’ada. Lagos: Tiwal Publication Company.

    Sa’id, B. da wasu,(2006).Qamusun Hausa.Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Kano: Jami’ar Bayero.

    Muhammad, M.S. (2020).Bahaushiyar Al’ada.Tetfund. Kano: Bayero University Press.

    Soba, S. A. (2012). “Muhallin Bahaushe Jiya da Yau”.Kundin Digiri na Biyu da Aka Gabatar ga Sashen Harsunan Nijeriya.Sokoto:Jami’ar Usman Xanfodiyo.

    MUTANEN DA AKA TATTAUNA DA SU

    Lamba Suna Shekaru Sana’a Gari Rana
    1. Saidu Nakande 60 Manoni Ɓangashe 20/1/2026
    2. Ibrahim Abubuakar 65 Manomi Aku 21/1/2026
    3. Mustapha Ibrahim 40 Maƙeri Gaya 2/1/2026
    4. Malam Gambo 65 Baduku Gaya 13/1/2026
    5. Tabawa Adamu 61 Sana’ar Kaba K/ Gabari 11/1/2026
    6. Baba Sayyadi 43 Maƙeri Gaya 5/1/2026
    7. Mukhtari A.Isma’ila 45 Magini Ƙwanadroso 11/1/2026
    8. Dr. Abdullahi Madaki 62 Malamin Jami’a Gaya 6/1/2026
    9. Kawu Mu’azu 57 Wanzami Tarauni 3/1/2026
    10. Maisalati Durɓindai 58 Sana’arTukwane SRCOE 1/1/2026
    11. Adamu Isyaku 68 Masanin Al’adu Gamoji 15/1/2026
    12. Sadiya Sabo 60 Saƙar Kaba Aku 29/1/2026
    13. Dauda Yusif 50 Manomi Gaya 26/1/2026
    14. Muhammad Sani 65 Sana’ar  Fafa Shagogo 19/1/2026
        15. Mu’azu Adamu      72 Mai Unguwa Matamawa 20/1/2026

     

     

    Danna nan don karanta Tarihin Dr. Magaji Ahmad Gaya (PhD)

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tarihin Garin Kudan

    Tarihin Garin Kudan

    BABI NA ƊAYA
    Allah mai yin yadda Ya so. Garin Kudan, tsohon gari ne da ya ginu bisa mutunci, tsoron Allah da kuma kishin al’umma. Tsuntsaye sukan tashi da sassafe suna rera waƙar alfijir, iska tana taɗa ganyayyaki kamar mai kiran mutane zuwa sabuwar rana. Ko da yake gari ne na tarihi, amma yana da zuciya mai sabuntawa kamar ruwan rafi da ba ya gushewa.

    A tsakiyar wannan gari ne ake samun jarumin da tarihinsa ya cika duniyar maƙwabta,wato mai girma Hakimin Kudan (Alhaji Ishaƙ Ashir), mutum mai tarbiyya, mai hangen nesa da kuma don ginshiƙin zaman lafiya. Hakimi mutum ne da ake cewa:

    “In ka ji ana yabon gida, to ka san akwai wanda ya kafa.”
    A zamaninsa, Kudan ya ɗauki salo na ci gaba, wanda ba kowa ba ne zai iya jagoranta ba. Mutanensa suna kiransa “Uban Kowa,” domin ko gida na makoki ne ko na suna, ko ɗaurin aure, ko taron al’umma, sai ka gan shi cikin mutane, ba tare da girman kai ko zunzurutun mulki ba.

    Allah ya yi masa tarin tulin baiwa ta samun ‘ƴa’ƴaye mata da maza kamar: Halima, Mariya, Hindatu, Usman (Ɗanladi), Nafi’u, Balarabe, Isma’il, Mas’ud, Gaddafi, Nasiru, Imrana, Abdulshahid, Umar, Abubakar, Yunusa, Muzammil, Sha’awanatu, Furaira (Hajiyayye), Karimatu, Aisha, Shamsiyya, Raliya… jerin sunaye da ke kamar gini-gini masu ɗora gari kan tushe.

    Hakimi kalmarsa ɗaya: “Gari ba ya ci gaba sai al’umma sun zama tamkar juna.”

    Ranar damuwa

    Ranar Lahadi, 3 ga Yuni 2024, wannan gari mai farin ciki ya shiga duhu. Rana ta fito, amma kamar ba ta da ƙarfi. Tsuntsaye ma sun yi shiru, tamkar suna jin wani abu mai nauyi na shirin faruwa. Sai labari ya bazu cikin ‘yan mintoci:
    “Hakimi ya rasu…!”

    Kalmar ta yanke zukata tamkar takobi. Mata suka zube suna hawaye, maza suka tsaya cak tamkar dutse. Kudan ta yi shiru, irin shiru mai ciwo. Wani dattijo ya ce:
    “Mutum mai kyau idan ya tafi, gari yakan yi kamar ya faɗi.”

    Mutanen garin sun yi zaman makoki, sun yi kuka, amma kuma suka yi nazari, domin Hakimi ya riga ya bar saƙon da ba ya mutuwa: al’umma su zama ɗaya.
    Bayan jana’iza, gari ya cika. Mutane sun tashi da kalmar:
    “Idan ka ga alheri ya dusashe, to ka san akwai wanda bai tsaya a kansa ba.”
    A wannan rana aka fara sabuwar tafiya.

    BABI NA BIYU

    Ranar da aka binne Hakimi, dare ya sauka da wata irin nutsuwa da ba a saba gani ba. Kafin wannan lokaci, Kudan gari ne da yake da annuri da hayaniya, amma wannan dare ya yi kamar an ɗaure shi da sarƙar jimami. Ko iska tana motsawa cikin ladabi saboda mutumin kirki ya yi hijirar da ba a dawo wa.

    Amma cikin wannan nutsuwa akwai wani haske da ba kowa ke gani ba, wato hasken da ke fitowa daga zukatan waɗanda Hakimi ya taɓa rayuwarsu da kyawawan ayyuka. Kamar wutsiyar wuta a duhun daji, hasken na neman ya tayar da mutanen gari daga dogon tunani.

    Farfesa Mu’azu (Makiyayi mai raya zukatan mutane da ilimi)

    Bayan sallar Isha’i, Farfesa Mu’azu ya zauna a gindin bishiyar ɗorawa a cikin gidansa, yana kallon taurari tamkar yana karanta tarihin mutane cikin sararin samaniya. Shi mutum ne mai nutsuwa, mai hikimar magana irin ta magabata. Ana cewa:

    “Idan ka ga dattijo yana shiru, ka sani yana magana da zuciyarsa.”
    Ya shaida rayuwar Hakimi, ya san jajircinsa, kuma ya yi imani cewa “labarin gari” ba zai kammala ba sai an rubuta tarihin waɗanda suka wakilci zuciyar jama’a. Saboda haka, ya zaro littafi ya fara rubutu cikin dare, yana cewa:

    “Ba don jarumtakarsa kaɗai ba, amma don darasin da ya bar mana.”
    Farfesa Mu’azu mutum ne da ke haɗa mutane, mai sauƙin kai, mai taimakon marayu, mai ɗaukar nauyin ɗalibai. Hakan ya sa mutane suke kallonsa tamkar hasken fitila a duhun daji. Mutane suna cewa:

    “Mai ilimi kamar ruwan sama ne; ko ka ƙi, ko ka so,idan ya sauka, ya yi maka alheri. Shi ne ya fara kiran al’umma zuwa taro a fadar masarauta, bayan kwana uku da rasuwar Hakimi.

    Malam Aliyu Labaran (Damo sarkin haƙuri)

    A cikin jama’ar Kudan, akwai gwarzon da ba shi da aiki sai ibada da ilimi, wato Malam Aliyu. Mahaddacin Alƙur’ani ne mai ladabi, mai haƙuri da juriya. Idan ya yi magana, harshensa ya yi taushi kamar ruwan zuma.

    A taron farko bayan rasuwar Hakimi, shi ya tsaya ya ce: “Gari kamar jiki ne, idan ɗaya ya ji zafi, dukkan su sun ji. Don haka mu yi aiki tare, don cike giɓi. ”Kalmar ta shiga zukata tamkar wuta a cikin busasshiyar ciyawa.

    Malam Surajo Yunusa (bango majingina)

    Kodayake Malam Surajo ya rasu tun 06/04/2017, amma mutanen gari suna yawan tuna wa da shi. Mutum ne da ya rayu wajen koyar da mutane Alƙur’ani, yana zuwa gidaje ɗaya bayan ɗaya yana cewa: “Ilimi shi ne garkuwar mai rai.”

    Rayuwarsa ta zama misali ga matasa. A wannan lokacin da ake neman sabuwar hanya, mutane da yawa suka fara tunanin yadda Malam Surajo zai yi da ya kasance a raye. Wannan tunanin ne ya fara tayar da sha`awar komawa makarantu da karatu.

    Idan ka yi tafiya cikin dare a Kudan, za ka ji matasa suna karanta Alƙur’ani a ƙananan makarantun allo da ya bari. Wani kamar ya ce: “Mutum ya mutu, amma alherensa suna raye.”

    BABI NA UKU

    A gefe guda kuma, Salmanu Faris wanda ya kasance matashi, marubuci, manomi, ɗan jarida kuma almajiri. Bayan bayan taron sai ya ɗora alƙalamin rubutu. Idanunsa sun yi ja, saboda rashin bacci, amma zuciyarsa cike take da wuta irin wutar da ta ratsa zuciyar mai son ci gaban gari. Shi ne ke cewa:

    “Idan ka ga gari ya tashi, to matasa sun ce ba za su yi shiru ba.”

    Faris ya ga mutanen gari sun shiga tunani, kuma ya yanke shawarar cewa wannan shi ne lokacin da zai tashi tsaye ya rubuta labarin mutanen gari, ya faɗaɗa tunani, ya tunzura matasa, ya yaɗa kiran ci gaba a kafafen sada zumunta da jaridun yankin.

    Shigowar Mawaƙa (Murya Mai Ƙarfafa Zuciya)

    Labaran, Ashiru, Salahu, Ali (Na Annabi) da Rabilu, su ne mawaƙa, sha’irai, kuma manoma. Sun saba da rubutu da waƙoƙi, amma wannan lokaci suka fito da wani sabon salo. Suna cewa:

    “Waƙa ba ta zama waƙa ba sai ta gina zuciya.”

    Suka shirya waƙar “Rayuwar Hakimi” wadda ta zama kamar taken sabon tafiya. Yara da matasa suka rera kanta a tituna, manya suka saurare ta cikin kukan sha’awa. Ta zama kamar ƙaho na farfaɗo da al’umma.

    Kungiyar Malamai (Garkuwar Zuciya da Ilimi)

    Auwal, Salim, Abdulrazaƙ, Abdulhafiz, Sani, Salisu, Abba, Yahaya, Abubakar, Muhammad (Prof), Yasir, su ne suke riƙe da guraben ilimi. Wanda suka kasance malamai na boko da na addini, duk masu haƙuri, nutsuwa da hangen nesa.

    Suka yi taro suka yanke shawarar:

    1. A buɗe darussa na koyar da rubutu da karatu.

    2. A ƙarfafa zaman lafiya.

    3. A koyar da matasa sana’o’in dogaro da kai.

    4. A fahimtar da al’umma mahimmancin zaman lafiya.

    Malam Auwal ya ce:

    “Idan ka ilimantar da ɗa, ka ilimantar da al’umma baki ɗaya.”

    Abubakar Suleiman (mutum na mutane)

    Abubakar, matashi mai arziki, kuma ɗan kasuwa. Ya yi na’am da wannan sabuwar tafiya. Mutum ne da ke da juriya da zuciya mai tausayin talakawa. Ya ce:

    “Ku kafa tsari, ni kuma zan tallafa.”

    Nan take ya ɗauki matasa 25 aiki, ya ba da kayan aiki, ya ba da tallafi ga makarantu da masu koyarwa. Mutane suka fara ce wa juna:

    “Gari zai tashi. Gaskiya gari zai canza.”

    Karanta Waƙa Ta 2 Ga Farfesa Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Gizo Da Ɓaure

    Tatsuniyar Gizo Da Ɓaure

    ‎Ga ta nan ga ta nan ku.

    ‎Wata rana ne dai wani sarki yana zance a zuci, yana cewa, ‘Gonata ta ɓaure ta yi kyau. Ɓauren yanzu duk ya nuna. Gara in sami wani ya je ya tsinke mini duk ɓauren, kar in bar shi ya ruɓe a banza. Amma fa wanda zai tsinke ɓauren ba zai sha ba, ko da ɗaya ma.

    Idan ya gama bai sha ba, zan ba shi ‘yata tare da gararta baki ɗaya’. ‎Shi ke nan. Kashegari sai sarki ya sa duk a yi shela a gaya wa mutanen gari sarki yana kiran su a ƙofar fada.

    ‎Mutane suka taru a ƙofar gidan sarki. Sai sarki ya ce, ‘Da ma ba wani abu ya sa na yi kiran ku ba. Gonar ɓaurena ce na ke so a tsinke min, amma ba za a sha ko ɓaure ɗaya ba. Sai dai zan ba wanda ya tsinke ɗin ladan tsinkewar. Watau zan ba shi ‘yata da gararta baki ɗaya.’

    ‎Sai kowa ya ce ba zai iya ba, domin bauren ya cika kyau, ga kuma ƙanshi da zaƙi. Ba wanda zai iya ba tare da ya sha ba. Can, sai Gizo ya zo; ya ce wa sarki, ‘Zan iya. ‎Shi ke nan, sai sarki ya ce, ‘To. Gobe ka yi shiri ka tafi’.

    ‎Da gari ya waye, sai Gizo ya dura ruwa a jallo, ya ɗauki madubi da kuma tsinkensa na sakace. Ya je gonar sarki ya kama tsinkar ɓaure. In yana cikin yi mutane suka zo suka ce, ‘Gizo barka da aiki’; sai ya tsiri tofar da yau, yana cewa, ‘Tuf! Kai wannan ɓaure! Ko warinsa ba na so’.

    ‎Idan sun wuce, sai ya ci gaba da tsinkar ɓauren, yana sha yana zubo wani a ƙasa. Shi ke nan, ashe bai sani ba, wata ‘yar tsuntsuwa tana kallon sa. Da ya gama tsinkar ɓauren tas. Ya sauko zai tafi gida, sai ya ɗauko jallon ruwansa ya kurkure bakinsa, ya ɗauko madubin nan da tsinken sakace, duk ya ciccire ɓauren da ya maƙe masa a haƙorinsa.

    Bakinsa ya yi tas, kamar bai ci kome ba. Sai sarki ya aiko mutane don su debe ɓauren da Gizo ya tsinke. Suka zo suka sami Gizo suka ce, ‘Sannu da aiki, Gizo’. ‎Ya ce, ‘Yauwa’. ‎Suka ce, ‘Har ka gama? Sai ya ce, ‘I. Amma da ƙyar’.

    ‎na gama. Kamar na yi amai, saboda warin ɓauren nan. Warin duk ya cika mini ciki’. ‎Sai suka zuzzuba ɓauren a buhunhuna suka tafi su kai wa sarki. Da suka je gida, sai sarki ya tambaye su labarin Gizo da tsinkar ɓaure. Suka ce, ‘Ai, yallaɓai, Gizo bai sha ɓauren nan ba, domin mun ga muna zubawa a buhu yana tofad da yau..

    Kuma da muka ce da shi, ‘Me ya sa ka ke zubad da yau?’ Sai ya ce warin ɓauren ne ya cika masa ciki. Sun gama faɗin haka ke nan, sai ga Gizo ya zo gidan sarki. Sarki ya ce da shi, ‘To, Gizo. Ka yi aiki mai kyau. Sai kuma ka je gida ka gyaggyara, za a kawo amarya da gararta.’

    ‎Shi ke nan. Gizo ya je gida ya gyaggyara sarai. Aka ɗauko amarya da gara aka zo da ita gidan Gizo. Kafin ‘yan ɗaukar amarya su tafi gida, sai suka ji tsuntsuwa tana waƙa tana cewa: ‘Kai Gizo, kai Gizo, A can ka ci ɓaurenka, Har ka kurkure bakinka, Har ka manto jallonka…’

    ‎Tana ta faɗar haka har sai mutanen suka ce, ‘Kai, ku tsaya mu ji abin da tsuntsuwar can take faɗa. ‎Sai Gizo ya ce da su, ‘Kai, ku rabu da ita don Allah, shirmenta ta ke yi’. ‎Sai mutanen suka ce, ‘Wane irin a rabu da ita? Kai! Mu tsaya mu ji’.

    ‎Shi ke nan, sai ‘yan kawo gara da amarya suka ji tana cewa: ‘Kai Gizo kai Gizo, A can ka ci ɓaurenka, Har ka kurkure bakinka, Har ka manto jallonka…’‎Sai suka ce, ‘La’ila! Ashe da ma ka ci ɓauren ka ce ba ka ci ba?’

    ‎Sai suka yi ta surutu da hayaniya. Shi ke nan. Sai suka mayad da amarya da gararta gida su ka gaya wa sarki abin da ya faru.

    ‎Shi ke nan. Ƙurunƙus

    ‎Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafi mai suna TATSUNIYOYI DA WASANNI wanda Ibrahim Yaro Yahaya ya wallafa.

    Danna nan don karanta ‎Tatsuniyar Barewa Ta Auri Mutum

    Edita@rumasau-kallamu

  • ‎Tatsuniyar Barewa Ta Auri Mutum

    ‎Tatsuniyar Barewa Ta Auri Mutum

    ‎‎Ga ta nan ga ta nan ku.

    ‎Wata barewa ce, sai ta rikiɗa, ta zama mace kyakkyawa. Sai ta ɗauki ɗan kwatashinta ta ɗora a ka ta tafi tsakiyar karofi ta ajiye. Da ta ajiye, sai ta ce duk wanda ya jefa ’yar tsakuwa ta buɗe kwatashin nan, shi ne mijinta.

    ‎Sai wannan ya ɗauki tsakuwa ya jefa bai buɗe ba, wancan ya jefa tsakuwa bai buɗe ba. Sai aka sami wani ya jefa ’yar tsakuwa, sai ya buɗe. Sai ta ce ta sami miji, shi za ta aura. Sai suka tafi garin ita yarinyar, wurin iyayenta za a ɗauro mata aure da wannan mutumin.

    ‎Sai aka ɗaura musu aure ta zo ta tare gidan mijin. Kullum ranar girkinta sai a ce ta je ta ciro kuɓewa a gonar mijin ta yi miya. Da ta je gonar, sai ta yar da zanenta ta yi birgima a ƙasa ta zama barewa ta yi kiran ’yanuwanta, ta yi waƙa ta ce:

    ‎Cinkalkal, cinkalkal kalaya,

    Turmin ’yan kale ya yi fure, ceɗiya.

    Tudu na korar Tudu, Marina.

    Tudu na korar tudu da ƙaho.

    Ban da kwatsa-kwatsan.

    Ban da ƙanƙan.

    Sai ’yan uwanta su zo su taru su ciccinye kuɓewa. Sa’an nan in sun gama sai su tafi gida. ‎Ita kuma sai ta yi birgima ta komo mutum ta ɗauki zanenta ta ɗaura. Sai ta koma gida ta dinga cewa, ‘Ni da gangan aka tura ni. Ga shi nan ban samo kome ba.’

    ‎To, ran nan sai mijinta ya bi ta gonar. Sai ya gan ta tana birgima. Da ta gama birgimar, sai ya ga ta rikiɗe ta zama barewa. Sai ya ga ta yi kiran ‘yan’ uwanta bareyi da waƙa. Bareyi suka taru a gonar jingim. Duk suka cinye kuɓewa.

    ‎Suna cikin ci sai ya fasa su. Sai ya ga matarsa, ta gan shi. Ya komo gida. Sai ta ɗauko kuɓewar ta biyo shi. Ta tarad da shi a gida. Ya ce, ‘Wace ce?’ Ta ce, ‘Ni ce.’ Ya ce, ‘Ina za ki?’ Ta ce, ‘Ɗaki za ni.’ Ya ce, ‘A a, koma daji.’ Sai ta ce ta ƙi. Sai ya biyo ta a guje ya kora ta daji.

    ‎Daga nan ba ta sake dawowa  ba. Shi ke nan. Kurunkus.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin tatsuniyoyi da wasanni wanda Ibrahim Yaro Yahaya ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Gizo Da Namun Daji

    Edita@rumasau-kallamu

  • Kimiyyar Siyasar Uban Gida: Tasiri, Makoma Da Silar Rabuwa

    Kimiyyar Siyasar Uban Gida: Tasiri, Makoma Da Silar Rabuwa

    A siyasa, a ko’ina a faɗin duniya ana amfani da harshen ‘biyayya, jagoranci gami da magajin mulki’. Shugabanni da dama su kan ce suna “gina shugabannin gobe”, ko “naɗa magaji”, ko kuma “tallafawa amintattun mabiyansu na siyasa”, amma a ƙarƙashin wannan zance akwai lamari mai tsauri.

    Siyasar ubangida (godfatherism) tsari ne da ikon siyasa ke zarcewa ta hannun mutane masu ƙarfin iko bayan cikar wa’adinsu, ba lallai ta hanyar hukumomi ko dokoki ba.
    A nahiyoyi daban-daban, wannan tsari yana bin salo iri ɗaya: uban-gida ya ɗora yaronsa na siyasa, yaron nasa ya samu iko, sannan daga baya rikici ya raba kawunansu.

    Wannan maƙala tana nazarin bayanai ne na duniya da na Najeriya game da silar rikicin siyasar ubangida da kuma dalilin da yasa Siyasar ubangida ke ci gaba da aukuwa, da dalilan da yasa take karyewa, da Kuma yadda take ƙarewa a mafi yawan lokuta.

    Don haka za mu fara yin nazarin ta waɗannan sigogi:

    1. a. Siyasar Uban-Gida a Matsayin Fasahar Siyasa ta Duniya
    Siyasar ubangida ba ta keɓanta ga Afirka ko Najeriya kaɗai ba. Ita wata fasahar siyasa ce ta duniya, musamman a wuraren da:

    • Hukumomi suke da rauni, samun adalci yake da tsada.
    • Jam’iyyun siyasa suke mallakar ɗumbin magoya baya,
    • Kuma samun iko yake da mafi tsadar farashi.

    A Latin Amurka, ana kiran Siyasar Ubangida da suna ‘caciquismo’, ma’anarta shugabannin yankuna masu sarrafa ƙuri’u da makomar mutane. A wasu sassan yankunan Asiya, musamman Philippines, Siyasar Ubangida na bayyana a matsayin siyasar gado, inda wani ahali kan mamaye muƙaman da ake zaɓe a kansu na tsawon ƙarni.

    A Amurka, a farkon ƙarni na 20, ƙusoshin siyasa kamar su Tammany Hall a New York suna aiki ne ta hannun shugabanni da suke “ƙirƙirar” gwamnoni da magajin gari.
    Duk da bambancin wurare, binciken siyasa da kamanceceniyarsa ya nuna abu guda:
    “A duk inda zaɓen ’yan takara ya dogara da masu hannu da shuni fiye da masu zaɓe ko hukumomi, siyasar ubangida tana bunƙasa”.

    b. Nazari: Bayanin ƙididdiga na duniya

    Binciken ƙasashe da dama ya nuna cewa a wasu ƙasashe masu dimokiraɗiyya mai raunin tsarin jam’iyya, kashi 60–75% na muƙaman majalisa ko kujerun zartarwa suna hannun mutanen da ke da alaƙa da manyan ahali ko wasu iyayen gida. Wannan haɗuwar iko ke sa rikicin ubangida da yaron gida ya zama babbar matsala mai girgiza tsarin siyasa baki ɗaya.

    2. Me Yasa Ubangida Ke Ƙirƙirar Yaron-Gida (Kuma Me Yasa Yaron gida ke Kware Masa Baya?)

    Ubangida ba ya ɗora yaron-gida saboda tsananin biyayya, ko tausayi ko kyautatawa kawai. Ilimi ta nuna hakan wani tsari ne na dabarar siyasa: Saboda dalilai kamar haka;-

    1. Kare iko – Mai mulki na son yaga ya cigaba da tasiri ko da bayan wa’adinsa ya ƙare.
    2. Tsaron tattalin arziki – kare kasuwanci, kwangiloli, da hanyoyin samun kuɗin shiga.
    3. Garkuwar siyasa – kariya daga bincike, cin zarafi ko samun babbar daraja a tsarin siyasa.
    4. Gina tarihi – mayar da iko na mutum zuwa “ɗariƙar siyasa” ko daular siyasa Wanda tarihin zai rinka tunawa dasu.

    Amma yaron gida yana gadon muƙami ne, ba ƙarƙashin biyayya kaɗai ba. Don haka da zarar ya hau mulki, matsin lamba za ta bayyana, biyayyar da ya jima Yana yi wa Ubangidansa na iya sauyawa Saboda dalilai kamar haka:

    1. Ikon kundin tsarin mulki da zai rinƙa yi wa biyayya,
    2. Haƙƙin jama’a da ya rataya a wuyansa na zuwa da muradai mabanbanta
    3. Hamayya daga manyan masu ruwa da tsaki na kusa da na nesa,
    4. Bujirowar burika na wannan mai mulki.
    Daga nan ne tsarin ke fara tsagewa..

    3. Yanayin Najeriya: Dalilin da Yasa Siyasar Ubangida Ta Fi Zafi a tsarin siyasar Najeriya ba ya rasa nasaba da dalilai guda huɗu:
    1. Tsarin “wanda ya yi nasara ya ɗauke komai” watau samun iko a Nigeria yana nufin samun iko da dukkan albarkatu.
    2. Raunin dimokiraɗiyyar jam’iyya – ’yan takara sunfi fitowa ta hanyar sulhu ko masalaha (nune), ba zaɓen gaskiya ba.
    3. Tsadar kamfen – Tun daga zaɓen cikin Gida, kudi sunfi tasiri wajen samun kuriun daliget Sama da nagartar ɗan takara. Haka Nan uwa uba babban zaɓe, masu dangwala kuriun sun fi zaɓar Dan takarar daya basu ihsani. Don haka ’yan kaɗan ne za su iya tsayawa takara har suyi nasara ba tare da masu kuɗi sun tallafesu ba.
    4. Ƙarfafa mutum fiye da karfafa doka – rigar mulki a Nigeria tafi ƙarfafa mutum fiye da bin dokokin ƙasa.

    Binciken zaɓukan Najeriya tun 1999 ya nuna cewa yawancin gwamnoni da suka yi nasara sun samu goyon bayan manyan ubangida ko ƙungiyoyi masu ƙarfi. Amma a lokaci guda, da dama daga cikin waɗannan alaƙa sun rushe bayan samun nasara.

    4. Yadda Siyasar Ubangida ta kasance a wasu Jihohin Najeriya
    i. Jihar Rivers: Daga Gado zuwa Yaƙi

    Rikicin da ya ɓarke tsakanin tsohon Gwamnan Nyesom Wike da Gwamnan mai ci Siminalayi Fubara a Jihar Rivers shi ne mafi tsanani a wannan zamanin. Tsarin gadon mulki mai kyau ya koma:

    • Toshe ayyukan majalisa,
    • shari’o’i a kotuna,
    • tsaikon kasafin kuɗi,
    • sa hannun gwamnatin tarayya.

    Abinda hakan ya haifar: lalacewar hukumomi na dogon lokaci, sulhu na ɗan lokaci, da rabuwar bangarorin siyasa abinda za a iya cewa har abada.. sai dai wasu na ganin kwatankwacin haka Nweson Wike ya yi ga waɗanda suka raine shi a siyasa.

    ii. Jihar Kaduna: Uban-Gida ga Gwamna
    A Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya tallafa wa Uba Sani wajen zamowar sa Gwamna. Bayan da ya hau mulki, sai gwamnan ya nemi ’yancin kansa, abin da ya haifar da:

    • zarge-zargen jama’a,
    • binciken majalisa ga Gwamna El-rufai
    • yaƙin cacar baka musamman a kafafen yaɗa labarai.
    • Abubuwan da hakan suka haifar: rabuwar manyan ’yan siyasa da ɓata suna daga ɓangarorin biyu.

    iii. Jihar Kwara:
    Daular Saraki — ƙarƙashin Olusola Saraki, daga baya Bukola Saraki — ta nuna wani tsari na daban.
    Uba (Sola) ya Dora ɗansa (Bukola), bayan cikar wa’adinsa ya yunkura maye gurbinsa da Kanwar Bukola.. Amma sai Bukola ya bijerewa mahaifinsa tare da ɗora Abdulfatah Ahmed..
    iv. Jihar Kano: Tafarkin Siyasa da Sarrafa Iko

    A Jihar Kano , Jagoran darikar Kwankwasiyya Engr Rabiu Musa Kwankwaso ya gina gagarumar ɗarikar siyasa. Amma gwamnan farko (Abdullahi Umar Ganduje) daya gajeshi ya raba gari dashi, sannan a yanzu haka Gwamna na biyu (Abba Kabir Yusuf) da ya ɗora shi ma ya raba sheƙarsa ta siyasa da jagoransa Rabiu Kwankwason

    v. A takaice, an samu irin wannan salo a yawa-yawan jihohin ƙasar Nan misalin Zamfara, Borno, Yobe, Kogi da makamantansu

    5. Ƙididdigar Sakamako: Abin da Bayanai Ke Nunawa
    daga siyasar jihohin Najeriya (1999–2025).
    Taƙaitaccen bincike ya nuna:
    1. ≈Kashi 70% na alaƙar ubangida da yaron-gida tana rushewa daga ƙarshe.

    Daga cikin waɗanda suka rushe:
    kaso~40% sun ƙare da sauya jam’iyya ko sake tsayuwa da ƙafafunsu.
    kaso ~25% sun kai ga rikicin shari’a na tsawon lokaci,
    kashi ~20% sun haifar da rugujewa ko tuge injin siyasar ubangida a zaɓe,
    ƙasa da kashi <15% ne kawai suka kai ga tsananin biyaya da sulhu mai ɗorewa misalin abinda ake gani ga Gwamna Ododo da Yahaya Bello a Kogi.

    A Siyasar duniya ma, waɗannan kaso suna kama da juna a ƙasashen da siyasar Ubangida ta yi ƙarfi.

    6. Me Yasa Rabuwa Kusan Dole Ce a Siyasar Ubangida?

    A kusan dukkan lamurra, abubuwa biyar ke haifar da rabuwa:
    1. Saɓanin ra’ayi wajen iko da albarkatu; misalin kasafin muƙamai, kwangiloli da sauransu.
    2. Tsoron dusashewar tauraro – a mafi akasari, Ubangida ba ya son a manta dashi ko a daina tuntuɓarsa akan kamurori.. don haka idan ya hango haka zata faru, yana iya yunkurin sauya shugabancun daya ɗora.

    3. Sauyin halaccin mabiya – yarongida yana iya samun iko daga ɗumbin jama’ar da yake shugabanta, hakan na iya bashi damar auna ƙwanjinsa da Ubangidansa.
    4. Fargabar magajin gaba – bayan kammala waadin mulkin yaron gida, shin wake da halascin sake ɗora magaji? tayaya hakan zai amintar da babban ubangida ko yarongida?.
    5. Tasirin mulkin mai mulki wajen sarrafa kansa da muradan zuciyarsa

    A taƙaice: siyasar ubangida tana haifar da cibiyoyin iko biyu a ofishi guda sai dai ita siyasa sam ba ta lamuntar iko biyu.

    7. Yadda Siyasar Uban-Gida Ke Ƙarewa Galibi

    Shaidu daga Najeriya da duniya suna da nuni da cewa mafi yawan Siyasar ubangida :
    * Ba ta ƙarewa cikin nutsuwa.
    * Tana raunana shugabanci.
    * Tana rarraba jam’iyyun siyasa.
    * Wani lokaci tana ƙarfafa jama’a idan suka haɗu (kamar Kwara).

    Abin mamaki, tsarin da aka ƙera don rage rashin tabbas shi ne ke haifar da rashin kwanciyar hankali na dindindin.

    8. Hasashe na Ƙarshe: Rikicin Siyasar Biyayyar Ubangida

    Siyasar uban-gida tana cigaba ne saboda tana magance matsalolin gajeren lokaci kamarsu cin zaɓe, tara kuɗi, kauce wa hukumomin bincike da sauransu. Amma tana karyewa bayan dogon lokaci saboda ta saɓa da ma’anar mukamin dimokiraɗiyya.

    > Da zarar yaron-gida ya zama gwamna, to fa Allah ɗaya ne kurum, babu mai iya tabbatar da ƙarshen lamarin. Har sai jam’iyyun siyasa, kuɗin kamfen, da hukumomi sun maye gurbin ubangida a matsayin hanyar samun iko, sannan zagayen zai ci gaba: amma abinda alƙaluma suka nuna, a duk siyasar ubangida huɗu, ɗaya ce kawai ake wanyewa lafiya, sauran ukun kuwa duk da ɓacin rai ake ƙarewa saboda saɓanin fahimta da bijirowar sabbin buƙatu masu sauya lamurori.

    Sadiq Tukur Gwarzo GGA.

    Karanta Falalar Malamai Da Ta&#8217;aziyyar Masani Shehu Ahmad Bamba (Ƙala Haddasana)

    Edita@rumasau-kallamu