Tag: yadda ake

  • Tatsuniyar ’Yan Mata Masu Kamun Kifi

    Tatsuniyar ’Yan Mata Masu Kamun Kifi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana wasu ’yan matan ƙauye suka tafi rafi su, watau kamun kifi. Suka kuma yi sa’a suka kamo kifaye, suka kama hanya suka koma gida. A kan hanyarsu ta zuwa gida sai suka haɗu da wata tsohuwa sai ta tsayar da su, ta roƙi su sammata kifin da suka kamo, ko da mai ƙaya ne.

    Sai suka hana ta. Amma sai wata budurwa daga cikinsu ta ɗeba mata kifin. Ta karɓa, ta gode mata suka tafi. Washe-gari da suka koma rafi don kamun kifi, da yawa daga cikin ’yan matan kuma sun kamo kifin mai yawa, ƙoransu cike maƙil. Da tsohuwar nan ta roƙe su, suka hana ta sai waccan budurwa da ta bai wa tsohuwa kifin jiya ta gaya mata cewa yau ba ta samu ba sai wasu ’yan ƙanana guda biyu kawai.

    Ga shi kuma tana jin tausayin ’yar tsohuwar. Saboda haka sai ta ba ta ɗaya, ita kuma ta riƙe ɗaya. Kafin su rabu, sai tsohuwar ta gaya mata in ta je gida da wannan kifi guda ɗaya da ya rage a hannunta, kada ta dafa shi ta sanya shi a cikin randar gidansu. Bayan ta isa gida sai ta saka kifin a cikin randar kamar yadda tsohuwa ta ce ta yi. Sai ta shiga ɗaki ta kwanta.

    Da gari ya waye sai ta buɗe randa don ta ɗauki ɗan kifinta, amma sai ta ga randa ta cika maƙil da manya- manyan kifaye. Ta yi ta ɗiba, amma kifayen nan ba sa ƙarewa. Bayan ’yan kwanaki ’yan mata suka koma rafi don su kamo kifi, amma wannan ranar ba su sami komai ba, sai suka koma gida babu kifi.

    Washe-gari sai aka yi shela a gari cewa Sarki yana son ya ci kifi, kuma duk budurwar da ta kamo kifi ta dafa wa Sarki ta kai masa zai aure ta. Gaba ɗayan ’yan matan ƙauyen suka fita kamun kifi, amma ba wadda ta samo sai wannan budurwa da ta taimakawa tsohuwa da kifi. Yadda aka yi ta samo kifin nan kuwa shi ne, da ta kama hanyar rafi
    sai ta haɗu da wannan tsohuwar.

    Sai tsohuwa ta ce mata kada ta je babban rafi, ta nuna mata wata hanya da za ta kai ta har bakin wani ƙaramin gulbi. Sai tsohuwa ta ce ta yashe ruwan. Da budurwa marainiya ta fara yashewa sai ta fara ganin manyan kifaye, ta yi ta ɗiba har ƙwaryarta ta cika, ta koma gida. A duk faɗin garin budurwar nan kaɗai ce ta kamo kifi a wannan rana. Bayan ta dafa kifi ta sa a cikin akushi ta kai fada, mutanen gari da Sarki suka yi mamaki.

    Nan take Sarki ya amince zai aure ta. Bayan ta koma gida sai aka gaya mata ta sanar da iyayenta, za a yi bikinta da Sarki. To da yake iyayenta duk sun rasu marainiya ce, ba ta da kowa, da ta koma gida dare ya yi ta kwanta, sai ta tashi tsakar dare tana kuka domin tana tunanin ba wanda zai yi mata kayan gara. Tana cikin wannan hali na damuwa, sai ta ga kwatsam tsohuwar nan ta ɓullo mata a tsakar ɗaki, kuma ta tambaye ta ko mene ne yake damun ta.

    Sai marainiya ta yi mata bayanin dukkan abin da yake damun ta, har ya zamanto ba ta iya yin barci. Da’yar tsohuwa ta lallashe ta sai kuma ta gaya mata za ta iya yin dukkan abin da take buƙata. Yarinya ta yi ajiyar zuciya cikin murna, ta yi wa tsohuwa godiya. Tun kafin gari ya waye, sai ta ga ɗakinta cike da kayan gara fiye da yadda take zato za ta samu, ta yi ta murna.

    Ta godewa Allah. Ana nan, ana nan, ranar bikinta ta zo, aka ɗaura musu aure ta yi ta murna. Tagode wa Allah aka yi gagarumin biki, aka kai amarya gidan Sarki. Da kayan gara ya ƙare sai tsohuwa ta sake ɓullo mata a ɗakinta, ta kuma kawo mata kayan alatu da na marmari. Tace mata kullum za ta rinka kawo mata kayan ɗadi ta rinka ba Sarki, amma kada ta gaya wa kowa.

    Yarinya ta ce ba za ta gaya wakowa ba. Suka yi sallama tsohuwa ta tafi. Bayan ’yan kwanaki sai matan Sarki suka fara tsegumi cewa amarya ba ta da kowa, amma kullum Sarki yana ƙara son ta fiye da sauran matansa, kuma kayan alatu da take ba Sarki wa yake ba ta? Suka yi ta bincike, amma ba su gano bakin zaren ba, sai suka haƙura, suka bar ta.

    To shi Sarkin bai taɓa haihuwa ba, duk sanda matansa suka ɗauki ciki, sai ya zube. Rannan bayan ’yan shekaru da auren marainiya da Sarki, sai ya tara matansa, bayan ya tabbatar kowacce tana da ciki. Ya ce da su kowacce ta tafi gidan iyayenta, kuma kada ta dawo sai ta haihu. Bayan kowacce ta kama hanyar gidansu, sai ita kuma amaryar
    Sarki marainiya ta tafi gindin wata tsamiya ta zauna, ta kama kuka, tana waƙa tana cewa:

    “Wa zai ba ni yaro a yau?
    Wa zai amshi haihuwa a yau?
    Ni ba ni da uwa, ni ba ni da uba?”

    Tana cikin wannan hali sai tsohuwa ta zo ta sake tambayar ta abin da yake damun ta. Sai ta kwashe labarin yadda suka yi da Sarki ta gaya mata. Sai tsohuwa ta ɗauke ta, ta kai ta gidanta, ta cigaba da kula da ita, tana yi mata albishirin cewa in Allah ya yarda, za ta haihu, cikin ba zai zube ba.

    Suna nan tare da tsohuwahar ranar haihuwa ta zo, ta haifi ɗanta lafiyayye, kowa ya gan shi ya ga ubansa. Amma sauran matan Sarki kuwa ba su sami haihuwa ba, sai ɗaya daga cikin kishiyoyinta ta sami labarin haihuwar amaryar Sarki marainiya. Sai ta fara bin ta a sace, har ranar da aka sa za su koma gidan Sarki. Rannan sai amaryar Sarki ta tafi bakin rafi donta yi wanka tare da ɗanta.

    Da ta je bakin rafin sai ta ajiye jaririn, ta shiga wanka. Sai kishiyar nan tata ta zo ta sace yaron, ta gudu da shi.Da suka koma fada sai amaryar Sarki marainiya ta je ta gayawa Sarki cewa ta haihu, amma an sace abin da ta haifa. Sai aka ƙi yarda da wannan magana. Da kishiyarta wadda ta sace yaron ta zo, sai suka ce ita ce ta haifi yaron.

    Ita kuwa matar Sarki marainiya sai aka sa fadawa da yaran Sarki suka kafa mata ɗaki irin na dawaki, aka ajiye ta a can, bisa cewa ta yi wa Sarki ƙarya. Da kishiyarta ta ba yaron nono sai ya ƙi kamawa. Aka yi juyin duniyar nan, jaririn nan ya ƙi shan nono, sai aka rinƙa ba shi madarar shanu, har ya girma. Ana nan, ana nan, wata rana sai ɗan duba watau Sarkin bokayen Sarki, ya gaya wa Sarki cewa wannan ɗan nasa matar da ta rene shi ba ita ce uwarsa ba.

    Mamaki ya kama Sarki, sai ya nemi Sarkin bokaye da ya gaya masa ta yadda zai gane uwar yaron. Sai mai duba ya ce ya tara matansa ranar kasuwar garin, kuma a tara mutane a fada, sannan duk matansa su yi abinci, su kawo shi bainar jama’a, kuma su jeru a fada. Idan an yi haka, sai a ce da yaron ya zaɓi abincin da matan Sarki suka kai wurin, to duk abincin da yaron ya zo ya ci, tabbas mai wannan abinci ita ce uwarsa.

    Ba tare da nuna wata shakka ba, Sarki ya ce a yi haka ɗin. Sarki ya umarci matansa a kan abin da ake so kowacce ta yi. Duk matan suka yi dafe-dafen kayan daɗi. Ranar kasuwa ta zo, mutane suka taru, fada ta cika ta batse. Amma ita amaryar Sarki marainiya, kuma uwar yaron ta gaskiya, ba ta da abin da za ta dafa.

    Hasali ma tun ranar da aka kai ta ɗakin dawaki ba ta cin komai sai in an zuba wa doki dusa ta ɗiba, ta dama ta sha, ko ta yi tuwo da ita. Da aka ce har ita ma sai ta yi abinci, sai ta ɗebi dusar da aka kai wa dawaki kamar yadda ta saba, ta kama gafiya ta yanka, ta gyara ta da kyau, ta ɗauka ta kai fada.

    Da ta isa fada sai ta tarar duk sauran matan Sarki sun jeru, suka shiga yi mata kallon reni da nuna mata ƙyama. Can da ɗan Sarki ya zo a kan doki aka ce ya zaɓi abincin wadda zai ci daga cikin matan Sarki, sai kawai ya ƙarya linzami ya doshi inda mahaifiyarsa marainiya take. Da zuwa sai ya kama cin abincin dusar nan da ke gabanta.

    Da mutanen da suka yi cincirindo a fada suka ga haka, sai mamakin yadda al’amarin ya kasance ya kama su.Da Sarki ya ga alama lallai gaskiya ce ta yi halinta, sai yasa aka kama matar da ta sace yaron ta ce nata ne, aka fille mata kai. Ita kuwa mahaifiyar yaron ta gaskiya sai Sarki ya ba ta haƙuri, ya nemi ta gafarta masa.

    Ba a daɗe da yin wannan abu ba, Sarki ya kamu da rashin lafiya, wadda ta zama ta ajalinsa. Bayan an gama zaman makokin rasuwar Sarki, sai aka naɗa shi ɗan marainiya a matsayin sabon Sarki. A cikin ikon Allah yaro ya hau karagar mulki. Ya ci gaba da tafiyar da harkar mulki kuma ’yar tsohuwar nan da uwarsa zumuncin da yake tsakaninsu ya ƙara ƙarfi. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Alheri danko ne ba ya faɗuwa ƙasa banza.
    • In Allah ya rufa maka asiri, ba mai tonawa.
    • Karya fure take ba ta ’ya’ya.

    Wannan tatsunya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Biyu)

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Biyu)

    Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Biyu)

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana ’ya’yan Kura sun je yawo gidan Kurege sai suka tarar an yi farfesun Biri. Sai aka ba su suka ci. Da babban cikinsu ya ji daɗin farfesu sai ya ɗebi romon ya shafa a kan gashin kansa ya tafi gida. Da suka koma gida, sai ya je wurin babansa Kure ya ce: “Baba ka dafa kaina mana. ”Da uban ya ji haka sai ya dube shi ya ce: “Ka taɓa jin an cewa uba ya dafa kan dansa ne?

    ”Sai ɗan ya nace shi dai uban ya dafa kansa. Sai ya dafa kan, ya ji danshin romo, ya sa harshe ya lashe. Da ya ji zaƙin romo, a nan take ya tambaye su a inda suka sami wannan abu mai daɗi. Suka amsa masa da cewa a gidan abokinsa Kurege aka ba su. Sai Kure ya sa takalminsa ya tafi gidan Kurege ƙwalama. Da ya isa gidan Kurege sai ya tarar saura kaɗan a tukunya.

    Kurege ya zuba masa ya ci. Da ya ji daɗi sai ya ce da Kurege: “Ina kake samo wannan nama mai daɗi haka?” Sai Kurege ya amsa masa da cewa: “Muna wasa ne a ruwa kullum tare da birrai, sai in daura tarko a ƙafata. Idan mun shiga mun fara kurme a ruwa sai in kama ƙarami a cikinsu, in danne a ruwa har sai ya sha ruwa sosai ya mutu. In sun tafi sun bar shi, sai in ɗauka in yanka mu yi farfesu a gidana.

    ”Da Kure sarkin kwaɗayi ya ji haka sai ya ce: “To in gari ya waye gobe zan bi ka.” Sai Kurege ya amince. Da Kure ya tafi gidansa sai ya kasa barci, ya ƙagara gari ya waye. Can dai da ya ga kamar gari ya ƙi wayewa, sai ya hura wuta ta haske ko ina. Daga nan ya je ya faɗa wa Kurege wai gari ya waye, sai Kurege ya ce: “Haba Kure, ka hura wuta a kan dakinka ka ce gari ya waye?

    Ai gara ka koma gida sai gari ya waye.” Bayan ya koma gida ya ɗan jima gari bai waye ba, sai ya kama zakara ya rinƙa matsa shi har ya rinƙa yin cara. Da Kurege ya fito sai ya ce: “Haba Kure yaya kake damun kanka haka ne? Na gaya maka sai gari ya waye.” Haka dai Kure ya haƙura ala tilas har sai da gari ya waye. Da sassafe ya shirya ya nufi ƙofar gidan Kurege.

    Suka kama hanyar rafi har suka isa, suka tarar da birrai a bakin rafi. Sai Kure da Kurege suka yanke shawarar su shiga cikin ruwa su yi wasan kurme. Da suka shiga tare da birrai sai Kurege ya faki ƙarami daga cikinsu ya danne a ruwa. Shi kuma Kure maimakon ya faki ɗan ƙarami, sai ya nufi kan babba, ya sa masa igiya ya danne shi. Da ya ji Kure zai halaka shi, sai ya yi ƙara, har sauran suka ji, suka watse da gudu.

    Kure da Kurege dai kowa ya kaso Biri daya, amma sai Kuregeya ce: “Kai kuma Kure da muka yi da kai za ka kama karami donkada su gane, sai ka kama babban cikinsu?” Sai Kure ya dubi Kurege ya ce masa ai ƙarami ba zai ƙosar da shi ba, shi ya sa ya kama babba wanda idan ya yi farfesu da shi zai sha ya ƙoshi ya more.

    Washe-gari da suka koma tun safe har yamma suna jira a bakin rafi babu Birin da ya fito bakin rafi. Sai Kurege ya dubi Kure yace da shi: “Kai ka yi mana wannan ɗanyen aiki.” Rannan dai haka suka koma gida, ba su sami nama ba. Sai Kurege ya gaya wa Kure gobe da safe za su je unguwar birrai su gaishe su domin rashin da suka yi na babbansu.

    Da ma birrai sun aika wa Kurege da Kure za su yi taro domin ba su sani ba cewa ko Kure da abokinsa Kurege ne suka kashe musu’yan’uwa. Da gari ya waye suka shirya, sai Kurege ya ce zai hau doki, shi kuma Kure ya hau ɓera. Sai Kure ya ƙi, ya ce tun da shi ne babba shi zai hau doki shi kuma Kurege ya hau ɓeran.

    Haka aka yi; suka kama hanya, kafin su isa sai Kurege yace in sun je shi zai ɗaure abin hawansa a jikin bishiya, sai Kure yace shi ne zai ɗaure a jikin bishiya, domin shi ne babba. Sai Kurege yace to shi zai ɗaure nasa a jikin ciyawa. Da suka isa garin birrai aka yi musu maraba, aka ba su masauki, shi Kure ya ɗaure abin hawansa a gindin bishiya, shi kuma Kuregeya ɗaure nasa abin hawan a jikin ciyawa.

    Suna zaune a masauki aka ce za a kawo musu giya don liyafar baƙunta. Kafin a kawo sai Kurege ya ce ya kamata su yi waƙa. Suka fara waƙa. Kurege yana rerawa yana cewa: “Ni da ƙananan nake wasa, Da ƙananan nake abota.” Shi kuma Kure yana waƙa yana cewa: “Ni da babban nake wasa, Babba na kama, A wasan ruwa mai daɗi” Sai manyan birrai suka ji abin da Kure yake faɗa, sai suka kawo musu giya a ƙwarya.

    Kure yana ta sha, Kurege kuma ya yi kamar tare suke sha amma in ya zuba a ƙoƙo sai ya kwara a jikin shinge, shi kuma Kure ya yi ta shan giya har ya yi tilis. Su kuma manyan birrai suna ta shiri don su rama abinda Kure da Kurege suka yi musu. Nan take birrai suka ƙwala ihu, suka ce a kawo sanduna za su ɗauki fansa. Suka ɗebo sanduna suka nufi kan Kurege da Kure.

    Shi kuma Kure ya riga ya yi tilis da giya ta yadda ba ya jin abinda ake faɗa. Sai ya tambayi Kurege ko me suke cewa a waje? Sai Kurege ya gaya masa cewa an ce a kawo musu farfesun ƙashi da nama. Da Kure ya ji haka sai ya gyara zama, yana dariya da murna wai za a kawo musu nama da ƙashi. A daidai lokacin da birrai suka shigo da sanduna za a fara ma Kurege da Kure, sai Kurege ya kutsa ta jikin shinge, inda yake kwarar da giya, ya gudu.

    Kure kuwa ba zai iya gudu ba, saboda haka suka yi ta jibgar sa. Bayan Kurege ya fita ta baya, kafin su biyo shi har ya hau kan ɓera. Yana taɓa shi sai ya fara gudu. Shi kuma Kure kafin ya fito ya kwance dokinsa daga jikin bishiya, ya rigaya ya sha sanduna har ya faɗi ya suma. Suka ɗauke shi, suka ɗora shi a kan dokinsa, suka kora shi gida. Ya isa gida a galabaice, ya yi ta jinya da kyar ya warke. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Son zuciya, ɓacin zuciya

    Wannan tatsunya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Daya)

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Daya)

    Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Daya)

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Kurege da Kura suna yawo, sai suka tsinci ƙyallen fatari. Sai Kurege ya ce, bari ya je ya ɗinka musu riguna da shi. Ya je ya ɗinko riguna biyu, amma girmansu ɗaya. Ya bai wa Kura ɗaya. Da Kura ta saka sai rigar ta matse ta, ta shaƙe mata wuya saboda ta yi mata kaɗan.

    Sai Kurege ya ce da Kura tun da rigar nan ta yi mata kaɗan, sai ta bar masa ita. Da Kura ta ji haka sai ta ce masa: “Daman ka cuce ni ne tun da ka ɗinka rigata daidai da taka, sai ka ɗauka.” Kurege ya haɗa duka biyun, suka shiga jeji don su farauto abinda za su ci. Da suka kamo namun daji da yawa sai suka dawo gindin wata bishiya, suna hutawa.

    Kurege yana so ya cinye namanshi kaɗai, amma ya rasa yadda zai yi. Can sai ya hango wasu ‘yanmata a bakin rafi, sai ya dubi Kura ya ce: “Ga ‘yan mata can, mu je mu yi musu magana. “Sai Kura ta yarda, suka je suka tarar da ‘yan matan suna hira. Suka zauna suna sauraron hirar.

    Da Kurege ya ga hira ta fara yin daɗi sai ya ce da Kura su je su dafa naman nasu. Sai Kura tace ita tana nan a wurin hira, ba za ta je ba. Shi kuwa Kurege sai ya je domin ya dafa musu naman. Ashe ya sami abin da yake so, wato sai ya zaɓi nama mai kyau ya zuba a jakarsa, ya ɓoye. Sai ya samo naman mushe ya dafa, ya ajiye wa Kura. Bayan ta dawo sai ya miƙa mata nama.

    Kura ta hau ci ba ta san mushe ya dafa mata ba. Ta ci nama, irin cin haɗama, amma ta ɗan rage ta ɓoye a jakarta. Kura ba ta da masaniyar cewa Kurege ya ɓoye nama mai kyau, ya ba ta mushe. Saboda wayo irin na Kurege, sai ya dubi Kura ya ce: “Kura ki rage mini naman mana. Saboda haɗama irin ta Kura ita ma sai ta harari Kurege tace:
    Ni ba zan ba ka ba tun da kai ne ka dafa, na san sai da ka zaɓi inda ya fi ko ina daɗi ka ci ka ƙoshi, ba zan ƙara maka ba.

    Da rana ta faɗi, kuma dare ya yi sai suka samu wata bukka suka kwanta, can cikin dare sai zawayi ya kama Kura. Ta nemi Kurege ya raka ta, sai da rana ta faɗi, kuma dare ya yi sai suka sami wata bukka suka kwanta ki, ya ce in zawayin yana damunta, to ta fita waje. Ya ƙara da cewa: “Idan ma abin ya dame ki ai sai ki yi shi a kwance ba sai kin tashi ba.

    Amma idan na ji ihu to babu lafiya, idan kuma abin ya yi tsanani, idan kuma kin yi shiru to lafiya kenan. Sai Kura ta fita waje ta yi kwanciyarta. Jim kaɗan sai kunama ta harbe ta. Kura da raki sai ta ƙwala ƙara, haka dai ta kwana tana zawo. Wayewar gari ke da wuya, sai ta je ta faɗa wa Kurege cewa jiya da daddare kunama ta harbe ta.

    Sai Kurege ya ce: “Ai dama mun yi da ke idan na ji shiru lafiya ta samu, idan kuma na Ji ihu to ta yi tsanani sai in fita in taimaka miki. “Bayan Kura ta ji bayanin Kurege, sai ta ce: “To shi ke nan.” Da suka gama maganganunsu, sai Kurege ya rasa yadda zai yi ya ɗauki naman da ya ɓoye ya kai gida, domin ya sani idan Kura ta gani za ta ƙwace. Sai ya yi dabara ya ba Kura shawara ta je ta sha ruwa, ta wanke jikinta kafin su tafi gida.

    Ba tare da zaton wani abu ba, sai ta kama hanyar rafi. Da Kurege ya ga ta tafi rafi, sai ya ɗauko namansa a inda ya ɓoye, ya saka shi a jakar Kura, shi ma ya shiga cikin jakar. Da ta dawo daga wanka, sai ta ɗauki jakarta ta rataya. Ba ta san Kurege yana cikin jakar ba, sai ta kama hanya. Daɗin waƙa ya sa ta kama hanyar gida ta fara tafiya, ta manta da Kurege.

    Tana cikin tafiya sai ta fara yi wa Jakarta waƙa tana cewa. “Sai ni Kura durungu, Na yi farauta, Na cika jakata da nama, Nama sai mun ture, Ga shi a cikin jakata.” Haka ta rinƙa yi wa jakar waƙa. Sai da ta isa gida ta tuna ta bar cikin jakar Kura, riƙe da namansa ya gudu zuwa gidansa. Shi ya sa duk wanda ya je daji zai ga Kura tana ta yawon nema nai. Shi kuma da za ku je gidansa, za ku tarar da gidan cike yake da nama mai kyau, wanda yake ci ya more. Da babu Gizo da na yi muku ƙarya. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Karamin mai hankali ya fi babba mai wauta.
    • Wauta mai janyo wuya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kishiyoyi Biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kishiyoyi Biyu

    Tatsuniyar Kishiyoyi Biyu

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wasu kishiyoyi biyu masu zaman lafiya a tsakaninsu a wani gari. Ba su taɓa ɓata wa juna rai ba. Suna nan, sai wata rana ɗaya daga cikinsu ta kwanta jinya. To da ma kowaccensu tana da ’ya mace, ’ya’yan kuma sun yi kama da juna ainun, yadda ba kowa ne zai iya bambance su ba, tamkar dai ’yan biyu.

    Da mai jinyar nan ta ga alamun ciwon nata ba na tashi ba ne, sai ta kira kishiyarta, ta ba ta amanar ’yarta. Kishiyar ta karɓa, kuma ta yi alƙawari za ta kula da duka yaran biyu kamar ita ta haife su. Da mai jinyar ta rasu, sai kishiyar ta ci gaba da kula da yaran har suka girma, suka zama ’yan mata.

    To amma saboda tsabar so da adalci da take yi wa ’yar kishiyarta, sai ya zamanto ba ta iya gane ’yarta daga cikinsu, domin kamanninsu ɗaya. Sai wata tsohuwa ta ziyarce su da ta lura da yanayin matar ta hanyar adalcin da take nunawa a tsakanin yaran, sai ta rinƙa yi mata faɗa a kan yaya za ta riƙi ɗan wani kamar nata.

    Sannu a hankali, har dai ta fara karkata ga zancen tsohuwa, to amma sai tace ba za ta iya gane ɗiyarta daga cikin yaran ba. Sai tsohuwar nanta ba ta shawara da cewa in sun je ɗaukar ruwa kafin su dawo, ta dafa dambu, ta ajiye a bakin randa, in sun dawo suna jin yunwa za su fara ci.

    To sai ta bari sai sun fara cin dambun sai ta daka musu tsawa, tana cewa: “Kun san yadda yake ne, ba ku tambaya kafin ku fara ci? ”Tsohuwa ta ce mata ta lura da kyau, domin wadda ta fara cire hannunta daga akushin dambun to ita ce ’yar kishiyarta. Wadda taƙi cire hannunta, kuma ta ce suna jin yunwa ne, to ita ce ’yar cikinta.

    Sai kuwa matar nan ta yi hakan. Bayan yaran sun dawo daga ɗaukar ruwa sai suka hangi dambu a bakin randa, suka nufi bakin randa da gudu, suka fara cin dambu. Nan take sai ta daka musu tsawa, tana cewa: “Kun san yadda dambun yake ne, ba ku tambaya ba kafin ku fara ci? ”Nan da nan suka razana, sai ’yar kishiyarta ta cire hannunta daga cikin akushin dambu, ita kuma ’yarta ta cikinta, ta dubi uwarta ce: “Haba mama, muna jin yunwa ne fa.

    ”Daga nan sai ta kama ’yarta ta kai daki, kuma ta kama’yar kishiyarta ta yi mata tsaga a fuska. Daga nan fa sai ta fara gana wa ’yar kishiyar nan tata azaba iriiri, har ya kai ga in za su ci abinci, sai ta ƙi zuba wa ’yar kishiyarta nata abincin a akushi, sai ta zuba mata a ƙasa. Amma kuma maimakon ’yar kishiyar nan ta rame ko ta damu, sai ƙiba kurum take yi.

    Daga nan sai ta daina ba ta abincin sam-sam, har ma dai takore ta daga gidan, wai ta je can kabarin uwarta ta karbi abinci. Da yarinya ta ji haka, sai ta yi ta kuka, ta kama hanya ta tafi bakin kabarin uwarta tana kuka. Ana haka, ana haka, wata rana da ta je kabarin uwar tana kuka, sai uwar ta fito ta rarrashe ta, ta ba ta abinci, ta ci ta ƙoshi.

    Haka dai, kullum sai ta je bakin kabarin uwarta, ta fito ta ba ta abinci. Nan da nan ta sake yin ƙiba, ta yi kuma kyau, ta goge, abin gwanin ban sha’awa. Ita kuwa mai uwa a murhun, sai ramewa take yi. Uwarta ta rasa abin da za ta yi. Wata rana sai wasu samari suka je tambayar uwar cewa ɗaya daga cikinsu yana son ya shiga neman auren marainiyar.

    Maimakon ta yi abin da samarin suka nema, sai ta ce sai dai su auri ’yarta. Su kuma suka ce waccan mai tsaga a fuska suke so. Amma sai ta hana su, ta mare su, ta gaya musu kada su sake zuwa gidan neman aure in ba ’yarta suke so ba. Da marainiyar nan ta ga haka, sai ta gudu, ta shiga uwa duniya. Tana cikin tafiya a dokar daji, sai ta ga shinkafa da nama.

    Sai shinkafa ta yi wa budurwar nan magana, ta ce idan tana jin yunwa ta zauna ta ci. Amma sai yarinya ta ce ta ƙoshi, kuma ta ci gaba da tafiya. Can kuma sai ta ga naman kaza, sai naman ya yi mata tayi, amma sai ta ƙi ci, ta ci gaba da tafiya. Haka ta rinƙa haɗuwa da kayan daɗi iri-iri, amma ta ƙi amsa tayinsu, ta haƙura da yunwar da take ji, ga baƙin cikin da ke damunta.

    Tana cikin tafiya sai ta ga hadari ya haɗu, ita kuma babu inda za ta fake. Ta duba nan, ta duba can, sai ta hangi wata ’yar bukka, nan take ta nufe ta a guje, ta buɗe ta shiga. Bayan ta zauna sai ta ga wani babban kumurci a gefenta. Sai macijin nan ya sulalo ya nufo wurinta, amma ba ta ji tsoro ba sai kallon sa take yi.

    Da ya ji bayaninta, sai ya tambaye ta tana iya gane garin, sai tace ta sani. Ba tare da ɓata wani lokaci ba, sai ya ce ta shirya su je su kai musu ziyara. Jin haka ya sa ta shiga murna da shirye-shiryen tafiya. Ta tanadi kayan sutura da sauran kayan masarufi. Da ranar da suka sa ta zo, sai Sarki ya sa aka haɗa su da dawakai da ’yan rakiya masu yawa, sai ka ce ita ce matar Sarki, suka kama hanya.

    Da suka isa garin, sai ita da mijinta da ’yan rakiyarsu suka nufi gidan iyayenta, suka shiga gidan, mutanen gari kuma suna ta mamakin yadda wannan yarinyar da aka ba wuya a baya ta koma. Da ’yar’uwarta ta gan ta sai ta rungume ta, amma da kishiyar uwarta ta fito sai ta ce ba ita ce ta ɓata ba, to amma saboda tsagun fuska da ta yi mata, sai ta gane ta.

    Nan take suka rungume juna cikin murna. Bayan amarya ta huta sai suka fara hira, ta kwashe labari tun daga barinta gida har zuwa lokacin da ta auri ɗan Sarki. Data gama ganin dangi, sai ita da mijinta suka yi musu sallama, suka kama hanya tare da ’yan rakiyarsu, sai garin mijin.

    Bayan tafiyarta sai kishiyar uwarta ta ce lallai ita ma ’yarta ta je ta auro ɗan Sarki. A kan dole yarinya ta amsa. Da ta kama hanyar tafiyar neman ɗan Sarkin da za ta aura, kamar dai yadda ’yar’uwarta ta yi, tana shiga daji sai ta ga shinkafa da nama. Tun kafin ma a yi mata magana sai ta tsuguna ta fara ci. Sai shinkafa ta ce da ita: “‘Yan mata zo ki ci shinkafa.

    ”Da budurwa ta ji haka sai ta dubi shinkafa ta mayar mata da jawabi: “Da ma ko ba ki yi magana ba, ai ina jin yunwa.” Sai ta ci gaba da cin shinkafa har ta ƙoshi. Daga nan sai ta kama hanyar ta fara tafiya. Ba ta yi nisa ba kuma sai ta haɗu da naman kaza. Nan ma ta zauna ta ci har ta ɗebi cinya da fukafukai da ƙirjin kaza a hannunta, ta yi guzuri. Ta sa kai ta fara ci gaba da tafiya tana lasar baki.

    Ba jimawa sai hadari ya taso, ta rasa yadda za ta yi. Gashi ba gari kusa a baya, kuma ba ta san inda ta dosa ba. Can sai ta hangi wata ’yar bukka, ta ruga a guje ta shiga, sai ta ga wani shirgegen maciji. Tana ganin macijin nan sai ta ƙwala ihu, tana neman hanyar gudu. Sai ɗan yaro ya ɓullo ɗauke da abinci, ya ce ta ba macijin abinci.

    Sai ta ce: “Tabɗi! Ta yaya ina jin yunwa in ga abinci in ba wani maciji?” Sai ta kama cin abinci, ta yi watsi da maciji. Jim kaɗan sai macijin ya fara rikiɗa. Tana ganin haka sai ta faɗi sumammiya, watau ba ta ga ɗan Sarki ba, balle ta san kamanninsa. Bayan ta farka sai ta gan ta a gidan wasu masu sarauta, amma talakawane da wani ɗan yaro ya zo ya gaya mata cewa za a zo a yi mata kitso, amma idan makitsiyar ta ba ta abin ƙwalama kada ta ci.

    Tana cikin haka da macijin nan, sai wani ƙaramin yaro yaɓbullo ɗauke da kayan abinci, ya gaya mata ta ba macijin nan abinci. Nan da nan ta ba shi ruwa ya sha, kuma ta ba shi abinci ya ci. Da ya ƙoshi sai ya rufe baki. Bayan ta kammala ciyar da macijin nan da shayar da shi ruwa, sai yaron ya tambaye ta ko ita ma za ta ci abincin ne.

    Sai tace ta ƙoshi. Sai macijin nan ya sake yin ƙoƙarin razana ta, amma sai tace ita komai ya ga dama ya yi mata, domin ba ta da wurin zuwa, kuma ta riga ta sadaukar da rayuwarta. Da jin haka, sai macijin ya shiga rikiɗa, yana zama namun daji daban-daban, amma duk da haka ba ta razana ba. Maimakon haka ma, sai ta gyara zama tana kallon ikon Allah, har dai macijn nan ya rikiɗa, ya koma yaro matashi kyakkyawa.

    Yarinyar ba ta sani ba, ashe macijin nan ɗan Sarki ne yake neman aure, amma sai ya bi wannan hanya don ya sami mace mai hankali, mai amana. Nan da nan ya sa aka ɗauke ta a kan doki, akakai ta gidan Sarki, aka ɗaura mata aure da shi, aka sha biki. Bayan an gama biki sai aka tura yaro ya gaya wa amarya za a zo a yi mata kitso, to amma matar da za ta yi mata kitson mayya ce, kuma za ta zo da kayan ciye-ciye a hannunta, idan ta ba ta kada ta ci.

    Yaron ya ce mata ta riƙe duk abin da za ta ba ta a hannunta, ko sau nawa ta ba ta kuwa kada ta sa a baki. Yaro ya ƙara bayyana mata cewa, bayan wannan mayya ta gama kitso za tayar da matsefata a gidan, amma kada ta gaya mata, ta kyale ta ta tafi. Bayan ta tafi kuma za ta dawo ta tambayi matsefatar, to sai ta miƙa mata haɗe da kayan ciye-ciyen da ta ba ta.

    Amaryar ta amince. Da makitsiya ta zo gidan, sai aka ce ta je ta yi wa amarya kitso. Da ta fara kitso sai ta miƙa wa amarya kayan ƙwalama, wai ta ɗan lashe bakinta da shi, sai amarya ta karɓa kamar za ta ci, amma sai ta riƙe a hannunta. Jim kaɗan kuma sai
    ta sake miƙa mata wani abincin, sai amarya ta karɓa ta haɗa su a hannunta. Haka dai har sai da suka gama kitso, makitsiyar ta tashi za ta tafi, sai ta yar da matsefin da ke hannunta a tsakar ɗakin amarya, amma amarya ta ƙi gaya mata.

    Makitsiya ta kaɗa kai ta yi tafiyarta. Bayan wasu ’yan sa’o’i da tafiyarta sai ta dawo, wai ta manta matsefinta a gidan, sai amaryata ɗauko mata, ta haɗa mata da kyautar da ta ba ta ta kayanƙkwalama a lokacin da take yi mata kitso. Da mayyar nan ta ga an dawo mata da tarkacenta, sai kawai ta fara zage-zage, ta kama hanya a fusace ta fita abinta. Amarya da mijinta ɗan Sarki suka ci gaba da zamansu cikin jin daɗi.

    Wata rana sai amarya ta kwanta a ɗaki ita kaɗai tana ta rusar kuka. Da mijinta ya shigo sai ya tambaye ta abin da ya faru, sai tace tana tunanin gidansu ne da mahaifinta da kuma kishiyar mahaifiyarta wadda ta riƙe ta. Ta kwashe labarinta gaba ɗaya ta gaya masa. Tana jin wannan ƙa’ida sai ta ce: “Tabdi! Ai ni in har na ga abin daɗi ba zan ƙyale shi ba sai na ci.

    …..”Da makitsiya ta zo ta fara kitso sai ta miƙa wa yarinyar abin ƙwalama, sai ta karɓa ta kai baki ta cinye. Da ta sake miƙa mata na biyu sai ta sake lanƙwamewa. Bayan sun gama kitso sai makitsiyarta yar da matsefinta, sai ta ce da ita: “Ai kin manta matsefinki.” Sai ta juya ta karɓa, ta tafi tana dariya. Bayan wasu ’yan kwanaki sai yarinyar nan, abin tsautsayi ta kamu da cuta, wadda ta zama ajalinta aka binne ta, ba tare da ta auri ɗan sarkin ba. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Munafunci dodo ne, yakan ci mai shi.
    • Mai rabon ganin baɗi ko ana ha maza ha mata sai ya gani.
    • Hassada ga mai rabo taki ce.
    • Mahakurci mawadaci.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta  Tatsuniyar Ƙawancen Kyanwa Da Bera

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Na-Goma

    Tatsuniyar Na-Goma

    ‎Ga ta nan ga ta nan ku.

    ‎Wata rana, an yi wani mutum wanda ya ke da ‘ya’ya goma. Shi kuwa maharbi ne. Kullum ya je daji yawon harbi sai ya kamo tsuntsu guda ɗaya. Shi ke nan kullum ya kamo tsuntsun sai ɗansa Na-Goma ya gasa shi ya cinye shi kaɗai. Kullum haka, kullum haka.

    ‎Ran nan sai ubansu ya ce a tafi kogin rantsuwa a yi rantsuwa a ga wanda ya ke cinye tsuntsun da ya ke kamowa kullum. ‎Shi ke nan. Sai suka ce, ‘To.’ Suka bi shi zuwa kogi. Da suka je kogin, sai na farkon, watau Na-Ɗaya, ya shiga ya ce:

    Ni Na-Ɗaya, na ɗayan Babaye.

    ‎In ni na ci tsuntsun Babaye,

    ‎Ruwa tafi da ni kar ka dawo da ni.

    ‎Sai ruwa ya ƙi tafiya da shi. Sai ya fito. Na-Biyu kuma ya shiga ya ce:

    Ni Na-Biyu, na biyun babaye.

    ‎In ni na ci tsuntsun babaye,

    ‎Ruwa tafi da ni kar ka dawo da ni.”

    ‎Sai ruwa ya ki tafiya da shi shi ma, ya fito. Duk sauran suka yi ba su nutse ba har aka zo kan Na-Goma wanda ya ce:

    Ni Na-Goma, na goman babaye.

    ‎In ni na ci tsuntsun babaye,

    ‎Ruwa tafi da ni kar ka dawo da ni.”

    ‎Shi ke nan. Sai kuwa ruwa ya tafi da Na-Goma.

    ‎Sai ‘yan uwansa suka ce, “To, baba, ka ga wanda ya ke cinye maka tsuntsu.” Uban kuma ya ce, “Na gani. Ku mu tafi gida. ‎Da suka je gida, suka shaida wa uwarsu wannan labari, sai ta fashe da kuka. Ta yi kukanta ta gaji ta share hawaye ta ce, ‘Ba kome. Allah ya ji kansa.’

    ‎Shi ke nan. Ruwa yana cikin tafiya da Na-Goma, sai ya zo gaɓar kogi. A nan ne fa ya ga wata dodonniya tana ta cin kwaɗi. Sai ta kama shi ta ce, ‘Kai yaro mutum ne, ko dodo irina?’ Sai yaro ya ce, ‘Ni mutum ne. ‘Sai ta ce, ‘Kai kuwa me ya kawo ka nan? ‎Sai ya ce, ‘Abin da ya sa na zo nan, shi ne, kullum kullum ubana ya kamo tsuntsu ya kawo gida, sai in ɗauka in gasa in cinye ni kaɗai, ba wanda ya sani.

    Shi ke nan, sai ran nan ya gaji ya ce mu je kogin rantsuwa tare da ‘yan uwana a gwada a ga wanda ya ke cinye tsuntsun da baba ya ke kamowa. Da muka je muka yi rantsuwar, shi ne kogin ya cinye ni ya kawo ni nan. ‘Sai ta ce, ‘To, yanzu ka ga ni dodonniya ce. In cinye ka ko in ƙyale ka?’

    ‎Sai ya ce, ‘Ni dai ina so ki yi mini arziƙi in zama ɗanki. ‘‎Shi ke nan, sai ta ce, ‘To, tashi mu tafi gida. Sai suka tafi gida. Da suka isa gidan, sai ta soma yi masa abubuwa yana sayarwa. Tana yi masa ƙosai yana talla. Kullum haka har yaro ya girma. Sai ta sai masa doki da kayan doki yana hawa yana tallan ƙosai a kai.

    In lokacin cin abinci ya yi, sai ta samo masa irin nasa na mutane. Ita kuma ta samo irin nasu na dodonni. ‎Shi ke nan. Kullum haka, kullum haka, sai rannan ‘yan’uwan Na-Goma suka gan shi yana tallan ƙosai a kan doki. Suka ce, ‘Wannan kamar Na-Goma,’ a zuciyar su. Shi ma kuma ya shaida su. Sai suka ce, ‘Kai mai ƙosai!’

    ‎Sai ya waigo. Suka ce, ‘Ko kai ne Na-Goma? ‎Sai ya ce, ‘I. Ni ne. ‘‎Sai suka rungume juna suna ta kuka. Shi ke nan, sai suka ce, ‘To, mu tafi gidan da ka ke. ‘Sai ya ce, ‘To, ai ni babata dodonniya ce. ‘‎Sai suka ce, ‘Mu tafi haka. Ba kome.’

    ‎Sai suka je suka yi sallama. Suka gaisa da dodonniya, suka ce ‘Mun zo ne mu tafi da ɗan’uwanmu Na-Goma.’

    ‎Sai ta ce, ‘Ni ba zan ba ku shi ba.’

    ‎Sai suka ce, ‘Ki yi haƙuri ki ba mu shi.’

    ‎Sai ta ce, ‘To, ku gaya min dalilin da ya sa ya zo ya same ni a nan.’

    ‎Sai suka gaya mata kamar yadda Na-Goma ya gaya mata, tun farkon haɗuwarsu a bakin kogi. Sai ta ce, ‘To na ji. Amma yanzu sai ku je ku kawo duk irin abin da za ku iya na dangin abincina. ‘Sai suka ce, ‘To.’ Suka tafi gida suka ce wa babansu, ‘Baba, yau dai mun ga Na-Goma yana tallan ƙosai a kan doki.’

    ‎Sai babansu ya ce, ‘Kai ku tafi can masu ƙarya, wanda ruwa ya cinye ina za ku gan shi? ‘Sai suka ce, ‘Ai gaskiya mu ke faɗa. Har ma wadda ta ke riƙonsa ta ce sai mun kai mata kayan abinci, sannan za ta ba mu shi. ‘‎Shi ke nan sai uban ya ce, ‘To a kai mata taikin gero ɗari da gomiya bakwai.

    Taikin dawa ɗari da gomiya bakwai. Taikin shinkafa ɗari da gomiya bakwai. Kai da duk dai irin abincin da mutane su ke ci a yi mata ɗari da gomiya bakwai-bakwai.’‎Da aka kai mata, sai ta ce:

    Ba cina ba, Na-Goma Ba cina ba.

    Je ka ka dawo, Na-Goma Je ka ka dawo.

    ‎Shi ke nan sai suka koma suka ce, ‘Baba, ta ƙi karɓa. Ta ce ba ta cin irin wannan abincin. ‘Sai ya sa aka yi mata taikin ƙuda ɗari da gomiya bakwai. Taikin tsutsa ɗari da gomiya bakwai. ‎Taikin kyankyaso ɗari da gomiya bakwai. Haka kuma taikin su gwano, da na tururuwa, da kiyashi, da jaba, da gafiya, da ɓera, da ƙadangare ɗari da gomiya bakwai-bakwai.

    Sai aka kai mata su. Da ta ga wannan gara zango-zango, tsibi-tsibi na irin abincinta, sai ta ce:

    Ga cinan nan, Na-Goma,

    ‎Ga cinan nan.

    ‎Ga shanu nan, Na-Goma,

    ‎Ga shanu nan.

    ‎Madalladai, Na-Goma,

    ‎Madalladai.

    ‎Dau wandonka, Na-Goma,

    ‎Dau wandonka.

    ‎Sa rigarka, Na-Goma,

    ‎Sa rigarka.

    ‎Sa hularka, Na-Goma,

    ‎Sa hularka.

    ‎Hau dokinka, Na-Goma,

    ‎Hau dokinka.

    ‎Sai wata rana, Na-Goma.

    ‎Sai wata rana.

    ‎Sai wata rana, Na-Goma,

    ‎Sai ka dawo.

    ‎Shi ke nan, sai suka rabu, dodanniya tana kuka, Na-Goma yana kuka. Aka kai Na-Goma gida, ya yi zamansa. Bai sake cinye wa babansa tsuntsu ba. ‎Shi ke nan.

    ‎Kurunƙus kan ɗan ɓera. Ba don Gizo ba da nai ƙarya. Ba don ƙarya ƙarya ce ba, wa zai ci tuntuɓe da tuwon shinkafa, ya dauje baki da tsokar nama, ya faɗa rijiyar zuma, a ciro shi da nakiya da alkaki?

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafi mai taken TATSUNIYOYI DA WASANNI wadda Ibrahim Yaro Yahaya ya wallafa

    Danna nan don karanta Tatsuniya Mai Taken Marainiya

  • Tatsuniya Mai Taken Wani Sarki Da Matansa

    Tatsuniya Mai Taken Wani Sarki Da Matansa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wani Sarki ne mai mata uku, amma Allah bai taɓa ba shi haihuwa ba. Ana nan, ana nan wata rana sai ya nemi shawarar fadawansa a kan abin da ya kamata ya yi saboda wannan rashin haihuwa. Sai suka ce ya kamata ya ƙara aure. Shi ko ya ɗauki shawararsu, ya sa aka nema masa budurwa kyakkyawa ya aure ta.

    Bayan wasu ‘yan watanni sai Allah ya ba ta ciki, labari kuma ya gama ko ina, matar Sarki tana da ciki. Su kuwa kishiyoyinta sai suka shiga baƙin ciki, don sun daɗe a gidan Sarki ba tare da ko ɗaya daga cikinsu ta sami ko da ɓatan wata ba. Daga nan sai suka shiga neman hanyar da za su bi su zubar da cikin, amma abu ya gagara, har lokacin haihuwa ya zo.

    Lokacin da suka tabbatar ta kusa haihuwa, sai suka je wurin Sarki suka nemi izini su je shan iska da saran itace a jeji tare da bayinsu. Ba tare da wani mugun zato ba, sai Sarki ya ba su izini, amma da sharaɗi, ba za su je da amaryarsa mai juna biyu ba. Sai suka ce ai za su kula da ita, kuma babu abin da zai same ta.

    Da suka nace, sai Sarki ya bar su suka tafi jeji da ita. A dajin nan naƙuda ta kamata, suka kai ta gindin bishiya, suka kwantar da ita, ta haihu. Da suka ga ta haifi ‘ya kyakkyawa, kuma ba ta cikin hayyacinta, sai suka ɗauki jaririyar suka jefa a kan bishiya. Can da rana ta yi sanyi, sai su da bayinsu suka kama hanyar gida, tare da mai jego.

    Lokacin da suka isa gida, sai matan Sarki suka je turakarsa, suka gaya masa wai matarsa ta haifi wani ɗan itace ne, ba mutum ta haifa ba. Da jin wannan bayani sai ya fusata, domin ya ɗauka gaskiya suka gaya masa, ya sa aka kai amaryarsa wani gida ita kaɗai inda ba kowa, sai abin tsoratarwa, aka bar ta a can.

    Bayan wasu ‘yan watanni sai bayin Sarki suka je daji yankowa dawakin Sarki ciyawa. Suna cikin yankan ciyawa sai wata ‘yar tsuntsuwa ta zo ta sauka a kan bishiya, ta tarar da ‘yar yarinya. Sai ta fara waƙa tana cewa: “Ɗan tsuntsu kar ka faɗa kan ‘yar Sarki, Wadda kishiyoyi suka ce, Wai ɗan itace uwarta ta haifa, Suka jefa ta kan bishiya, Ba ɗan itace ba ne, ‘Yar Sarki ce.

    “Ta rinƙa maimaita wannan waƙa, har bayin Sarki suka ji wakar ‘yar yarinya ta kan bishiya. Wannan ya sa suka fita da gudu, suka koma gari. Washe-gari ma da suka koma yankan ciyawa sai suka ji waƙar. Da suka kasa kunnuwansu da kyau, suka kuma saurari waƙar ‘yar yarinya, sai suka koma gida suka gayyaci mutanen gari masu yawa, domin su ma su je jejin su ji.

    Mutanen gari suka saurari waƙar da tsuntsuwa ke yi wa yarinya. Daga nan fa suka koma gari, suka je suka sanar da Sarki abin da suka ji. Sarki ya tashi da kansa ya nufi jeji inda yarinyar take, yasa aka hau bishiya a ga ko me yake yin wannan waƙa. Da aka hau bishiya sai ga yarinya kyakkyawa mai kama da Sarki, sai ka ce kakinta ya yi.

    Bayan an sauko da ita Sarki ya gan ta, nan da nan ya rungumi ‘yarsa, yana ta salati irin na godiya ga Allah, yana sumbatar yarinyar nan, don ƙauna irin ta ‘ya da mahaifi. Bayan wannan nuna murna ta Sarki da amsar barka da arziki daga jama’arsa da ke wurin, sai ya sa aka kawo masa doki ya hau, aka miƙa masa ɗiyarsa, suka hau doki tare, shi da ɗimbin jama’a suka kama hanyar gari.

    Da suka isa gida sai ya aika aka kawo masa uwar yarinyar da aka kai can wani gida da ke bayan gari, yana cike da nadama, amma kuma a cikin muryar bayyana farin ciki, ya ba amaryar haƙuri, ya nemi ta yafe masa horon da ya yi mata ba tare da laifin ta ba, a sakamakon makircin kishiyoyinta.

    Bayan fada ta cika ta batse da mutanen gari, sai aka bayyana musu miyagun halaye da makircin sauran matan Sarki, da yadda suka sa Sarki ya hori matarsa ba tare da ta yi masa laifi ba, da kuma yadda suka jefa da ‘yar Sarki a daji. Nan take Sarki ya umarci
    Hauni da ya fille musu kawuna, aka je aka zuba su a rami, aka binne. Sarki kuma ya ci gaba da sabuwar rayuwa shi da amaryarsa da’yarsa. Da ba domin Gizo ba da na shara muku ƙarya. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Mugun nufi ba ya kashe ɗan kurciya.
    • Ƙaiƙayi ya koma kan masheƙiya.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Ƙawancen Kyanwa Da Bera

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ƙawancen Kyanwa Da Bera

    Tatsuniyar Ƙawancen Kyanwa Da Bera

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Kyanwa da Bera dai ne suka yi ƙawance, suka kuma yi shawarar cewa ya kamata su tara kayan abinci da za su rinƙa ci idan lokacin hunturu ya zo. Suka kuwa zartar da wannan shawarar.

    Suna nan, sai rannan Ɓera ya ce da Kyanwa zai je bikin ƙanwarsa. Da ya fita sai ya nufi rumbun abincin da suka tara, ya ci har sai da ya ƙoshi. Da ya dawo gida sai Kyanwa ta yi masa maraba, ta tambaye shi, “Me aka samu ne?” Ɓera ya dubi Kyanwa ya ce: “Abin da aka samu shi ne, wuyar aiki ba a fara ba!” Aka yi murna aka watse.

    Bayan ’yan makwanni kuma Ɓera ya je wani sunan, ya bi ta rumbu ya ci har ya ƙoshi. Da dawowa gida sai Kyanwa ta tambaye shi: “Yau kuma wa aka samu?” Sai Bera ya dubi Kyanwa yana murmushi ya ce: “Yau kuma an sami kwanci-tashi ba ta bar komai ba.” Duk abin da Ɓera ke yi dai Kyanwa ba ta sani ba.

    Da Ɓera ya je gidan suna na uku ya dawo, sai Kyanwa ta nemi sanin abin da aka samu. Sai ya harare ta ya ce: “An sami ta-faru-ta-ƙare.” A tafiyar suna na huɗu Ɓera ya dawo da fuska a murtuke. Ita ko Kyanwa ta tambayi sunan jariri da goron suna. Maimakon Ɓera ya ba ta jawabi kamar yadda ya saba, sai ya fara yi mata wani kallon raini, kuma ga shi tana jin yunwa, tana jiran ya kawo mata abincin suna.

    Da ta ga alamun babu abincin nan, kuma Ɓera yana yi mata kallon raini, sai haushi ya kama ta ta fusata ta ce: “Kai ka cika surutu da fitina.” Kafin a ce haka, ta yi carab ta far masa, ta kama shi ta cinye. Ƙarya daɗin ji, amma ba na yi tun da Gizo yana nan. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ruwa ba sa’an kwando ba ne.
    • Duk wanda ya ci amana, sai amana ta ci shi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kaza Da Muzuru

    Edita@rumasau-kallamu

  • Abubuwa Goma Da Mai Azumi Ya Kamata Ya Sani

    Abubuwa Goma Da Mai Azumi Ya Kamata Ya Sani

    ZAFAFA GOMA: ABUBUWA 10 DA MUSULMI YA KAMATA YA SANI SANNAN YA KIYAYE A LOKACIN AZUMIN WATAN RAMADANA.

    GABATARWA:
    Alhamdulillahi Rabbil ‘Alamin. Tsira da amincin Allah (SWT) su tabbata ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم, iyalansa da sahabbansa baki ɗaya. Muna yi wa Allah (SWT) godiya da Ya raya mu har muka sake gamuwa da watan Ramadan, watan rahama, gafara da tsira daga wutar Jahannama.

    Ibadar azumin ramadana ibada ce wacce ta samo asali da umarni daga Allah (SWT) kuma ibada ce wacce aka umarci al’ummomin baya da ita. Dalilin haka shi ne faɗin Allah (SWT) “ya ku waɗanda suka yi imani an farlanta muku azumi kamar yadda aka farlanta ma waɗanda suka gabace ku domin ku yi taƙawa”. Duba bakara: 2:183.

    Haka kuma Allah (SWT) yana cewa “watan ramadana shi ne wanda aka saukar da alkur’ani a cikinsa domin zama shiriya ga mutane……”Duba bakara: 2:185. Haka zalika, An ruwaito manzon Allah (SWT) yana cewa: “ haƙiƙa watan Ramadana ya zo muku. Wata ne mai albarka. Allah yana lulluɓeku (da rahamar sa) a lokacin sa.

    Yana saukar da jin ƙan sa, yana kankare zunubai kuma yana karɓar addu’o’i. Allah yana kallon tsere da kuke yi ta ɓangaren kyawawan ayyukan ku sannan ya sanar da mala’iku cikin girmama ku. Saboda haka ku nuwa Allah nagartar ku. Tabbas matsiyaci shi ne wanda ya kasa samun rahamar Allah a lokacin Ramadan ”Duba “ Majma’uz-zaw’id 3:142

    Haka kuma Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yace “duk wanda ya azumci Ramadana yana mai imani da kwaɗayin samun lada, za a gafarta masa dukkan zunuban sa da suka
    gabata….”.Duba Bukhari 2014 da muslim 759-760. A wani hadisin ƙudusi Allah (SWT) yana cewa “ dukkanin aiki (mai kyau) na ɗan-adam da ya yi yana da lada goma kwatankwacinsa har zuwa ɗari bakwai amma banda azumi.

    Haƙiƙa azumi nawa ne kuma ni zany ni sakayyarsa. Shi mai azumi ya bar cinsa da shansa, da sha’awarsa saboda umarni na” manzon Allah ya cigaba da cewa “ mai azumi yana da farin ciki har guda biyu. Farin ciki lokacin da yake buɗa baki da kuma farin ciki lokacin da zai haɗu da ubangijinsa” ….Duba Bukhari 1904 da muslim 161-1151

    A cikin wannan taƙaitacciyar tunatarwa, na ambaci abubuwa goma da Musulmi ya kamata ya kiyaye domin azuminsa ya zama karɓaɓɓe mai cike da falala. Allah (SWT) ya ba mu ikon amfana da wannan tunatarwa da kuma ikon aiki da waɗanan abubuwa (ZAFAFA GOMA) domin rabauta da dacewa.

    NA FARKO: NIYYA

    Azumi ibada ce, kuma ibada ba ta inganta sai da niyya tun daga dare kafin a tashi
    da azumi. Wajibi ne mutum ya ƙulla niyyar azumi da zarar an ga wata tun kafin ya
    kwanta bacci ko kuma kafin fitowar alfijir.

    Hujja: Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce:“Duk wanda bai yi niyyar azumi da dare ba, babu azumi a gare shi.” (Abu Dawud, Tirmizi)

    NA BIYU: ƊAUKAR AZUMI DA GANIN WATA

    Azumin Ramadana yana farawa ne da ganin wata ko kuma cikar wata (sha‟aban zuwa 30) kuma yana ƙarewa da ganin wata (na shawwal).

    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce:“Ku yi azumi idan kun ga wata, ku buɗa azumi idan kun gan shi. ”(Bukhari da Muslim)

    NA UKU: TSAYAWA DA SALLOLIN FARILLA

    Ko da mutum yana azumi, idan ya raina sallah, ya jefa kansa cikin haɗari. Allah (SWT) yana cewa “ ku kiyaye sallolin ku musammam sallar (tsakiya) La‟asar….. Duba bakara 2:238

    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce:“Abu na farko da za a tambayi bawa a ranar Alƙiyama shi ne sallah….” (Tirmizi)

    NA HUƊU: YAWAITA KARATUN AL-KUR’ANI

    Ramadan wata ne na Al-Kur‟ani, don haka ake ƙwaɗaitar da musulmi da ya dage
    wajen yawaita tilawa da sauraron alkurani ba dare ba rana. Karatun alkurani shi ne
    zikiri mafi girma kuma a watan ramadana aka saukar da shi.

    Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya kasance duk watan ramadana mala‟ika Jibril yana zuwa sau biyu wajen sa domin tilawar alkurani tare da shi kuma an ruwaito sahabbai da magabata sun kasance suna duƙufa ba dare ba rana wajen raya dukkan kwanaki da karatun alkurani. Ana so mutum ya shagaltu sosai da karatun alkurani kuma ya zama shine mafi yawan ibadar sa acikin ramadana.

    Hujja: Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce:“Ku karanta Al-Kur‟ani, domin lallai shi zai zo ranar Alƙiyama yana yi wa masu shi ceto.” (Muslim)

    NA BIYAR: YAWAN ZIKIRI

    Zikiri yana rayar da zuciya kuma yana ɗaga darajar bawa.
    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce:“Kalmomi biyu ne masu sauƙi a harshe, masu nauyi a sikeli, masu soyuwa ga Rahama…” (Bukhari da Muslim)

    NA SHIDA: YAWAITA SALATI GA ANNABI صلى الله عليه وسلم.

    Salati hanya ce ta samun rahamar Allah. Don haka yawaita salati ga manzon Allah
    صلى الله عليه وسلم a kowane lokaci ibada ce mai albarka da ɗimbin lada musammam kuma a lokacin azumi.

    Hujja: Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce:“Duk wanda ya yi mini salati sau ɗaya, Allah zai yi masa sau goma.” (Muslim)

    NA BAKWAI: YAWAITA ADDU’A, MUSAMMAN A SAHUR DA BUƊA BAKI

    Mai azumi yana da matsayi na musamman wajen Allah. Lokacin da bawa ke azumi
    lokaci ne na addu’a gaba ɗaya amma kuma akwai keɓaɓɓun gurare da aka ayyana cewa
    ana so a yawaita addua kamar lokacin buɗa baki da lokacin sahur da sauransu.
    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce:“Mai azumi yana da addu‟a wadda ba a mayar masa da ita ba a lokacin buɗa bakinsa.” (Tirmizi)

    NA TAKWAS: SALLAR TARAWIHI DA TSAYUWAR DARE

    Wannan wata dama ce ta gafara da gyaran rayuwa.
    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce: “idan mutum ya tsaya domin sallar dare (tarawih ko ƙiyamul laili) tare da liman har aka ƙare sallar, Allah zai rubuta masa lada kamar wanda ya raya daren gaba ɗaya da sallah.” (Abu dawud 1375)

    NA TARA: SADAKA DA CIYAR DA MAI AZUMI

    Ramadan wata ne na tausayi da taimakon juna.
    Hujja: Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce: “Duk wanda ya ciyar da mai azumi, zai samu irin ladan azuminsa.” (Tirmizi)

    NA GOMA: I’ITIKAFI, ZAKATUL FITR DA UMARA GA MAI HALI

    Goman ƙarshe lokaci ne na ƙara kusanci da Allah da dagewa sosai domin ƙara yawaita ibadu musammam a kwanakin da ake sa ran dacewa da lailatul kadari watau daren 21, 23, 25, 27 da kuma 29. I’itikafi ibada ce mai tarin lada da samun kusanci da Allah (SWT) kuma ana shiga I’itikafi ne a goman ƙarshe a Ramadan.

    Haka, zakkar fidda kai (zakatul fitr) ibace wacce aka shar’anta ta a kan dukkan musulmi namiji ko mace, babba ko yaro ko ɗan jariri kowa ana fitar masa da zakkar
    fidda kai.
    Hujja: An rawaito cewa Annabi صلى الله عليه وسلم yana yin I’itikafi a goman ƙarshe na Ramadan.(Bukhari). Haka kuma ya wajabta Zakatul Fitr (zakkar fidda kai) domin tsarkake azumi, kuma ya ce: “Umara a Ramadan tana da ladan Hajji.” (Bukhari da Muslim).

    ‘Ƴan uwa masu girma haƙiƙa duk wanda ya kiyaye waɗannan abubuwa goma, ya yi azuminsa da ikhlasi, to da yardar Allah zai samu cikakkiyar falalar Ramadan wanda Allah kaɗai ne ya barwa kansa sanin irin tanadin ladan da zai ba shi. Allah Ya karɓi ibadunmu, Ya gafarta mana zunubanmu, Ya sa mu dace da Lailatul Qadr.
    Ameen.

    Husain M. Inuwa.
    usainiskima@gmail.com
    09042152353

    Danna nan don karanta Shan Azumi Ga Matafiya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kaza Da Muzuru

    Tatsuniyar Kaza Da Muzuru

    ‎Ga ta nan ga ta nan ku.

    ‎Kaza ce dai ta ce ba ta son kowa a cikin duk ‘yan uwanta zakaru masu nemanta. Ta dage ita sai muzuru kawai ta ke so da aure. Iyayenta ma suka ce ba za su ba ta shi ba. Ita kuma ta ce shi take so.

    ‎Da suka ga ta dage, sai suka ce, ‘To, mu dai babu ruwammu. Kada ki je ki jawo mana abin da zai hallaka mu baki ɗaya. Kaza kuwa ta ce ita dai shi ta ke so, ba za ta sake ba.

    ‎Sai aka kirawo ƙawayenta suka rarraba goron biki. ‎Shi ke nan, aka yi biki. ‎Sai ‘yammatan amarya suka je suna waka suna cewa:

    ‎Ke kaza kar ki jawo mana tserereninya da muzuru.’ Sai kaza ta ce: ‘Shi ba ya cin kaji, mhn. Shi ba zai ci kaji ba, mhn. In ji dai ni na kai kaina, mhn.’

    ‎Shi ke nan, sai suka ce da makaɗin ya sauya musu kiɗa. Shi kuwa makaɗin zakara ne, saboda a dangin amarya ya ke. Sannan ga kuma angwaye muzurai sun jeru, suna jin waƙa.

    ‎Shi ke nan, sai ‘yar ƙaramar kaza ta shiga fage ta ce:

    ‘Ni auta, autar kaza,

    In waiwaya haka,

    In muskuta haka,

    Sai na kan ji kiɗan da daɗi.’

    ‎Sai ta fita. Wata kuma ta shiga ta ce:

    ‘Ni wake-waken kaza,

    Kazar da ba a duka,

    Kazar da ba a zagi,

    In waiwaya haka,

    In muskuta haka,

    Sai na kan ji kiɗan da daɗi.’

    ‎Shi kuma makaɗin zakara, yana cewa:

    ‎’Daga baya-baya nake tsaya, In na ji kaya-kaya in naƙe.’

    ‎Sai kuma kaza ta uku ta shiga ta ce:

    ‘Ni ja-ja ja-jar kaza,

    Kazar da ba a duka,

    Kazar da ba a zagi,

    In waiwaya haka,

    In muskuta haka,

    Sai na kan ga idon muzuru!’

    ‎Daga nan fa sai angwaye muzurai suka yiwo kan ‘yan biki kaji radadada. Muzurai suka fara ciran su kai, su fafa, su fukafiki na kaji. Ita kuwa amarya sai cewa ta ke yi, ‘Kar ka cire mini fukafiki. Kar ka cire mini kai.’ Suka isa gida da ƙyar, suna cewa: Ga shi ta jawo mana tsiya. Wanda bai ji bari ba, zai ji hoho. An ce ta bari ta  ƙi.

    ‎Kurunkus kan ɗan kusu.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin Tatsuniyoyi Da Wasanni wanda Ibrahim Yaro Yahaya Ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kura Da Zomanya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kura Da Zomanya

    Tatsuniyar Kura Da Zomanya

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can cikin wani ƙungurmin daji akwai wata Zomanya mai ciki, wadda gidanta yake kusa da na wata Kura, ita ma mai juna biyu. Suna zaman lafiya da junansu irin na maƙwabta. Wata rana sai Zomanyar nan ta je wurin Kura ta ce mata: “Kin ga ni da ke mun kusa haihuwa, ya kamata mu nemi wurin da za mu rinƙa  ɓoye ‘ya’yanmu.

    “Sai Kura tace: “E, gaskiya ne, to amma bari mu tona rami babba domin mu saka ‘ya’yanmu a ciki.” Da suka tona rami sai suka zauna tare, har lokacin haihuwarsu ya yi. Da suka haihu, sai suka tara ‘ya’yansu a rami ɗaya, kuma suka yi alƙawari cewa Kura za ta rinƙa samo musu abinci, ita kuma Zomanya za ta rinƙa renon ‘ya’yansu.

    Suka zauna, in Kura ta tafi neman abinci ta dawo, sai ta miƙa wa Zomanya ta ci, kuma ta raba wa ‘ya’yansu. Kullum haka. Amma ita kuwa Zomanya, in an kawo mata abinci sai ta ba ‘ya’yanta su ci, in sun ƙoshi sai ta cinye sauran, ta hana ‘ya’yan Kura. Kullum haka, kuma in Kura ta zo ta ce za ta duba lafiyar ‘ya’yanta sai Zomanya ta ce ai sun ci abinci sun ƙoshi, suna barci.

    Haka suka yi ta yi, har dai wata rana Kura ta ce sai ta ga ‘ya’yanta. Da ta leƙa ramin ta jawo ‘ya’yanta sai ta ga duk sun rame. Sai ta tambayi ‘ya’yanta abin da ya same su, suka rame haka. Sai ‘ya’yan suka ce ai ba a ba su abinci, in an kawo abinci sai Zomanya ta hana su, ta bai wa ‘ya’yanta, su kuwa sai ta sa su yi barcin dole kullum.

    Da jin haka sai ran Kura ya ɓaci, ta yi kuka, ta yi gumani da ƙaraji mai tsanani, ta ce tun da Zomanya ta ci amanarta, to ita da ‘ya’yanta za su cinye Zomanya da ‘ya’yanta gaba ɗaya. Ko da Zomanya ta ji abin da Kura ta faɗa, sai ta rasa abin da za ta yi, idanunta suka raina fata.

    Tsoro ya kama ta. Sai ta dubi Kura ta ce: “To shi ke nan, tunda kin ce ni da ‘ya’yana mun zama nama, to ki yi haƙuri mu fito daga rami tukunna.” Zomanya ta shiga rami ta gaya wa ‘ya’yanta idan ta fita Kura ta bi ta, to su fita da gudu su yi nasu wuri. Da Kura ta sake magana, sai Zomanya ta haɗa manyan kunnuwanta biyu, ta ɗan miƙo su waje ta ce da Kura: “Don Allah ki riƙe mini takalmana kafin in fito.

    “Jin haka sai ya sa ran Kura ya ɓaci, ita a tsummaninta yaya za a yi kamar Zomanya ta ce ta riƙe mata takalmanta, bayan ta zama nama a wurinta. Sai ta kama kunnuwan Zomanya da ƙarfi ta finciko su ta jefar, wai ita a nufinta takalma ne. Sai kunnuwa suka sulluɓe, Zomanya da ‘ya’yanta suka ranta a na kare.

    Kamar wasa, Kura ta kasa kama ko ɗaya daga cikinsu. Da ba domin Gizo ba da na shara muku ƙarya. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    •  Hannu ɗaya ba ya ɗaukar jinka.
    • Ƙarshen maci amana jin kunya.
    • Kowa ya ci zomo, ya ci gudu

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Mace Mai Ciki

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu