A ƙasar Zariya, neman ilimin Furu’a ya cuɗanya da neman ilimin Alƙur’ani. Wannan ya sa makarantun Alƙur’ani a Zariya da Sakkwato zama tamkar makarantun ilimi ne “Zaure”.
A wasu lokuta, ɗalibai masu neman ilimin lugga ko Fiƙhu kan rubuta baikutan karatunsu a jikin allunansu; kamar yadda ake rubuta Alƙur’ani a allo a Kano da Barno.
Tarihin yaɗuwar ilimin Alƙur’ani da ilimi a Zariya; kafin ma bayyanar Shehu Usmanu ba zai manta da zuriyar Juma do Kona ba. Waɗanda aka ce su ne na farko wajen kafa makarantun.
Don haka za mu ayyana wasu cibiyoyi da Malamai shahararru a Zariya da kewayenta; musamman ma daga ƙarni na ashirin zuwa na ashirin da ɗaya. Waɗannan Malamai sun haɗa da:
Malam Na’iya da Malam Inuwa Na Magajiya da Malam Muhammad Gali ƙofar Doka; da Malam Nuhu Ladan da Malam Auwal Kusfa; da Malam Usman Babajo Marmara da Muhammad Auwal Ƙaura da Malam Yakubu Kakaki da Alƙali Shu’aibu Kakaki; da Malam Alhassan Yawuri da Malam Haruna da Malam Junaidu Rimin Danza da Malam Umar Ƙwarbai.
Domin karanta cikakken bayani a kan Wasu Daga Malamai Allori danna nan.
Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Samun Nutsuwa Da Kwanciyar Hankali Da Wadatar Zuciya danna nan.
Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.