Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Bilkisu Ahmad Funtuwa

0
78

Tarbiyyar Addini

Funtuwa tana jaddada muhimmancin bin koyarwar addinin Musulunci, musamman ga mata. Misalai:

Wa Ya San Gobe, ta nuna sakamakon barin ibada da zaluntar mata.

Wannan yana koyar da darasin tsoron Allah, gaskiya, da bin halal.

Tarbiyyar Aure da Iyali

Wannan batu yana da muhimmanci a yawancin littattafanta.

  • A Rabon Juna, ta bayyana yadda haƙuri, juriya da fahimta ke kawo zaman lafiya a cikin aure.
  • A Wa Ya San Jiki, ta nuna illolin rashin biyayya ga miji ko rashin adalci daga ɓangarorin biyu. Ta koyar da cewa aure ya kamata ya kasance bisa soyayya, tausayi, da girmama juna.

 Tarbiyyar Mata

Ayyukan Bilkisu Funtuwa suna mai da hankali sosai ga wayar da kai Ta koyar da cewa:

  • Mace ta zama mai mutunci da kunya.
  • Ta guji fitina, gulma, da zubar da mutunci.
  • Ta nemi ilimi da sana’a domin taimakon kanta da iyalinta.

Tarbiyyar Matasa

Hajiya Bilkisu Funtuwa tana amfani da jarumai matasa domin isar da saƙon tarbiyya.

  • Ta gargaɗi matasa su guji soyayya marar iyaka.
  • Ta jaddada muhimmancin karatu, ladabi, da bin iyaye.
  • Ta nuna illar bin abokai marasa tarbiyya.

Tarbiyyar Zamantakewa

Bilkisu Funtuwa tana amfani da labarai wajen:

  • Koyar da tausayawa da taimakon juna.
  • Nuna cewa zalunci da mugunta suna da sakamako mai muni.
  • Ingiza al’umma su kare martabar addini da al’adun Hausa.

Wanann bayanin an ciro shi ne daga maƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

Karanta Koyar Da Tarbiyya A Cikin Littattafan Yusuf M. Adamu

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceKoyar Da Tarbiyya A Cikin Littattafan Yusuf M. Adamu
Labarin na GabaKoyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Ado Ahmad Gidan Dabino
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.