Abba Yusuf
Ni basimpe ne ku ganni
Ba taƙiyya zo ka ganni
Ba ni kunyar yin bayani
Tunda da ai ban faɗo hakan ba.
Babu mai sa in yi ridda
Daga Simphanci ku shaida
Na yi wasa kam a can da
Yanzu kam ba a kaini yin riƙo ba.
Sheik nake so ma a ba ni
A ɗariƙar Simp a kai ni
Matsayin Mufti na ƙarni
Ko kwa Ayatul-ilahi babba.
Ko na yo digirin digirgir
Har na farfeshe a koyar
Da mutane don a samar
Da tsayayyen Manhaji na babba.
Ga nasiha ta ga Simpis
Kar ka yarda ta ɗanji ko dis
A cikin rai nata ko ɗis
Wai da sunan ranta yai baƙi ba.
Lallaɓata a ko da yaushe
Kar ka ba ta kaɗan ta lashe
Ba ta duk malam Abashe
Haka ne ya fi ba fa hancini ba.
In ka ba ta ta ce ka ƙaro
Je ka deɓo du a baro
Ajiye a gabanta jero
Sai ta zaɓa yin hakan da riba.
In ka zo ka gida ka ganta
Ranta ɓace tsaya gabanta
Kai ta cewa shugaba ta
ISBIRI ban yo ina sani ba.
In ta bayyana ba ka lefi
Kar ka ƙyale ɗaukin lefin
Yi wa kanka hukunci ya fi
In ta sauko kai ne kacci riba.
Edita; Rumasa’u M. Kallamu
[…] Danna nan don karanata Iƙirarin Simpanci […]