Hadisai da yawa sun bayyana ɗimbin falala da darajar tasbihi kamar haka:
Ladan tasbihi da Alhamdulillahi yana cika tsakanin sama da ƙasa, Tasbihi yana kankare zunubai; tasbihi yana daidai da yin kalmomi, ladan tasbihi ya fi duniya da abinda yake cikinta; tasbihi kalmomi ne da Allah yake matuƙar ƙaunarsu, da sauran darajoji masu tarin yawa.
An karɓo daga juwairiyya Haris (Radiyallahu Anha) ta ce; “Wata rana Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya fita daga wurinta bayan sallar asuba; ya bar ta a zaune a wurin da ta yi salla, da ya dawo da hantsi ya tarar da ita tana nan dai a zaune; sai ya ce har yanzu kina nan a yadda na barki, ta ce na’am. Sai ya ce bayanki na faɗi waɗansu kalmomi huɗu da za a auna su da gaba ɗayan abinda kika faɗa yau sai su rinjaye su, su ne:
“Subhanallahi wa bi hamdihi, adada khalƙihi wa rida a nafsihi wa zinata arshihi wa midada kalimatihi” (Muslim 2726).
An karɓo daga Samarata Ibn Jundab (Radiyallahu Anhu) yace: “Abubuwa haɗu su ne zancen da Allah ya fi so, za ka iya farawa da kowanne daga cikinsu:
“Subhanallah, Walhamdu Lillah, Wa La Ilahaillallah, Allahu Akbar” (Ibn Majah 3811)
Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Istigfari Ya Ke danna nan.
Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Sujjadar Godiya Ga Allah danna nan.
Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.
Edita@rumasau-kallamu