Category: Ilimin Addini

Mun samar da wannan ɓangaren ne, domin samar da ilimin addini a sauƙaƙe. Za ku iya kai wa gare su ta hanyar amfani da kwamfutoci ko wayoyin hannu cikin sauƙi.

WikiHausa ta kowa ce. Kowa zai iya taimakawa da ilimi ko gyara. Bugu da ƙari, kowa na iya amfani da wannan kafa domin koyo ko koyarwa.

  • Ana Kiran Sallah Hailata Ta Zo

    Ana Kiran Sallah Hailata Ta Zo

    1. Tambaya

    As salamu alaykum wa rahmatul lahi wa barkatuhu. Malam barka da warhaka, Malam ina da tambaya, Ana kiran sallah Azahar sai mutum ya ga haila, in ya yi tsarki ya rama sallah ko baya rama sallah? Nagodé Allah ya saka da Alkhairi

    Amsa

    Wa’alaikumus Salam Warahmatullah. Irin wannan tambayar an yi wa SHEIKH SALEH UTHAIMEEN cewa, mace ce haila ta zo mata karfe 1:00 kafin ta yi sallar azahar, shin in jinin ya tsaya, za ta biya azahar ɗin ne⁉ Sai ya ce:
    “Akwai saɓanin malamai a kan haka zuwa gida biyu:
    1- suka ce, ba wajibi ba ne ta biya sallar, domin ba ta yi laifi ba, kuma ba ta yi sakaci ba, tunda ya halatta a jinkirta salla zuwa ƙarshen lokacinsa,
    2- suka ce wajibi ne ta biya wannan sallar, don umarnin faɗin Annabi (S.A.W)
    [عن أبي هريرة:] من أدرك ركعةً منَ الصلاةِ فقد أدركَ الصلاةَ
    أبو داود (٢٧٥ هـ)، سنن أبي داود ١١٢١ • سكت عنه [وقد قال في رسالته لأهل مكة كل ما سكت عنه فهو صالح] • أخرجه البخاري (٥٨٠)، ومسلم (٦٠٧)
    Wato, “Wanda ya riski raka’a guda a sallah, kafin fitar lokacinsa, to ya riski sallar,
    Sai UTHAIMEEN ya ce, “Abin da ya fi a gare ta, ta biya tun da sallah ce ɗaya kacal babu takura wajen biya,
    Dubi (MAJMU’U FATAWAL MAR’AH- tattarawan SHEIKH MUHD SALAH)
    ALLAHU A’ALAM.

    Amsawa : Sheikh Abubakar BN Mustafa Biu
    13/10/2019

  • Hukuncin Yin Aski Ga Sabon Jariri/Jaririya

    Hukuncin Yin Aski Ga Sabon Jariri/Jaririya

    Tambaya

    Assalamu alaikum. Mal ina da tambaya,
    Shin in an haifi ‘ya mace wajibi ne sai an mata aski⁉

    Amsa

    Wa’alaikumus Salam Warahmatullah, Game da aske kan jariri a ranar 7, Hadisai ne 2 suka zo
    NA FARKO: Lokacinda Fatima (R.A) ta haifi jaririnta Alhassan sai Annabi (S.A.W) ya ce da ita “Ki aske kansa” (MUSNAD-AHMAD)
    NA BIYU: Annabi (S.A.W) ya ce “Kowane yaro abin jinginawa ne da abin yankansa, a yanka masa yinin 7, kuma a raɗa masa suna, kuma a aske masa kansa” (AHMD, ABU DWD, NASA’IY, IBN MAJAH)
    Hadisin farkon yayin da aka haifi Alhassan ne shi kuma namiji ne,
    Hadisi na biyu kuma ya zo da lafazin (غلام) shi kalmar (GULAM) yana nufin yaro namiji,
    Don haka ba a shar’anta aske kan jaririya ta mace ba, sai in namiji ne, وبالله التوفيق
    (FATAWAL LUJNAH- no-17,998)
    ALLAHU A’ALAM.

    Ansawa : Sheikh Abubakar BN Mustafa Biu
    13/10/2019

  • SHAN RUBUTU DA NUFIN SAMUN MIJIN AURE

    SHAN RUBUTU DA NUFIN SAMUN MIJIN AURE

    Tambaya

    Assalamu Alaikum warahmatullah. Malam don Allah ina neman fatawa ce.

    Wata ce take neman miji kasancewar duk masu zuwar mata ba da gaske suke yi ba, to shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure, yake ba ta tana shan rubutu da niyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya a nan shi ne, shin mece ce makomar abin da ta aikata, shin Malam ta yi shirka ne ko kuwa ta yi ba daidai ba? nagode.

    Amsa

    Da farko game da shan rubutu, muddin ayar QUR’ANI ce tsantsa, babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta,  IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU’UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbatar da hakan a SARIMUL BATTAR,
    Amma in akasin haka ne haramun ne, don yakan zama shirka ce da surkulle,
    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya, to galibi irin na shirkan suke yi, don haka ki tuba tsakaninki da Allah da alkawarin ba za ki sake zuwa wurin su ba, don kare addininki da mutuncinki.
    Don samun biyan bukatunki sai ki zage da addu’a da kiyamul laili da azumi da istigfari, kuma kina iya lazimtar wannan adu’ar domin ita  Annabi Musa ya yi, ya sami aikin yi da matar aure a ranar, ga adu’ar👉🏼
    رب إني لما أنزلت إلي من خير فقير
    Allah ya yafe mana kuma ya ba ki miji nagari,
    ALLAHU A’ALAM.

    Amsawa Sheikh Abubakar BN Mustafa Biu
    05/10/2019

    Daga : ZAUREN ISLAMIC SUNNAH

  • Ina Cikin Sallah Sai Na Tuna Akwai Najasa A Zanina. Yaya Zan yi?

    Ina Cikin Sallah Sai Na Tuna Akwai Najasa A Zanina. Yaya Zan yi?

    Tambaya

    Asslamu alaikum Malam. Lokacin sallah ne ya yi, na je na yi alwala na tayar da sallah, to, ina cikin sallah sai na tuna akwai najasa a zanina, don Allah yaya zan yi, zan sake sallar ne ko yaya?

    Amsa:

    Wa’alaikumus salam Warahmatullah, irin wannan tambayar an yi wa SHEIKH ABDLH IBN ABDIRRAHMAN AL-JIBRIN ga amsar da ya bayar.

    Wanda ya yi salla da najasa kuma da saninsa, sallarsa ta ɓaci, in kuma bai sani ba, sai bayan ya sallame to sallarsa ta yi, ba a lazimta masa biya ba.

    Amma in yana kan sallar, sai ya san akwai najasa a tufarsa, in zai yiwu ya cire ta da wuri, ya ci gaba da sallarsa, to ya halatta, domin ya tabbata ANNABI (S.A.W) yana salla watarana da takalmi sai Mala’ika JIBRIL ya sanar da shi akwai najasa a takalman.

    Nan take ya cire takalman, ya ci gaba da sallarsa, ba tare da cewa farkon sallar da yayin da takalmin ya lalace ba, haka ma in ya tuna najasar yana jikin rawaninsa sai ya cire rawanin ya ci gaba da sallar.

    Amma idan cire abin da yake ɗauke da najasar, yana buƙatar dogon aiki, kamar kwaɓe riga ko wando ko makamancin haka, to bayan ya kwaɓe ya fara salla daga farko.

    Don haka, baiwar ALLAH kin ga cire zani da sauya wani zanin a daura dogon aiki ne, sai ki canza ki fara salla daga farko,
    BARAKALLAHU FEEK.

    Domin sanin Nasabar Manzon Allah danna koren rubutun nan

  • Yadda Ake Taimama

    Yadda Ake Taimama

    Taimama hanyar da ake yin tsarki ce idan an rasa ruwa, ta hanyar amfani da ƙasa; ana shafar fuska da hannaye biyu da ƙasa mai tsarki, da niyyar ɗahara.

    Ga bayani dalla-dalla yadda ake taimama:

    1 – A doki ƙasa da hannayensa biyu, bugu ɗaya.

    2 – Sannan ya bushe su, don ya rage ƙurar da take kansu

    3 – Sannan sai ya shafi fuskarsa da hannayensa sau ɗaya

    4 – Sannan sai ya shafi bayan tafin hannunsa, ya shafi bayan tafin hannun dama da cikin hannun hagu, sannan bayan hagu, da cikin hannun dama.

    Dalilin wannan siffar ta taimama shi ne, hadisin Ammar Allah ya ƙara yarda da shi ya ce; “Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya doki ƙasa da tafin hannayensa biyu, ya busa a cikinsu; sannan ya shafi fuskarsa da hannayensa da su” [Bukhari Da Muslim ne suka rawaito shi].

    Ga bidiyon yadda ake taimama domin ƙara fahimta sosai:

    Domin ƙarin bayani a kan duk wani abin da ya shafi taimama danna nan

    Domin ƙarin bayani a kan Sallar Alwala Da Falalarta danna nan

  • Yadda Ilimi Zai Zama Hasken Rayuwarka

    Yadda Ilimi Zai Zama Hasken Rayuwarka

    Ma’anar Ilimi Da Matakansa

    1. Ma’anar Ilimi

    A wannan gaɓar za mu yi magana a kan ma’anar Ilimi a madarar lughah (a harshe Larabci) da kuma Isdilahi (mahangar yaren shari’ar musulunci) a taƙaice.

    2. Ma’anar Ilimi A Lughah

    Kalmar Ilm a lughah tana nufin duk abin da yake warware jahilci ya kawar da shi.

    2.1. Ma’anar Ilimi Isdilahan

    Ilimi a mahangar shari’ah shi ne, duk abin da za a riska a haƙiƙanin yadda yake ta fuskar karatu ko binciken nazari ko gwaji ko ƙwarewa da taimakon wahayi ko hankali ta ɗayan hanyoyin riska guda biyar na ɗan Adam.

    2.2. Matakan Ilimi

    Wasu ma’abota ilimi suna kallon ilimi ta nahiyar yadda ake riskar shi, sai su raba shi gida biyu Ilmud Daruriy ad-dabi’iy da Ilmun Nazariy al-Muktasab. Wasu kuma suna kallon shi ta fuskar addini da rayuwa, su ce akwai Ilmus Shar’iy da Ilmul Kauniy, wasu kuma ta nahiyar addini kaɗai su ce.

    Akwai Ilmul Ghayah (Aqeedah, Qur’an, Hadith) da kuma Ulumul Wasa’il (Ulumul Qur’an, Usulul Fiqh, Musdalahul Hadeeth, Usulut Tareekh, Lughawiyyat d.s).

    Ibnu AbdulBarr (Allah ya masa rahma) yana cewa: “Matakan ilimi a wajen dukkanin masu addini Uku ne; (a) Ilimi mafi ɗaukaka shi ne na addini da babu wanda ya halatta ya yi Magana a cikin sa ba tare da abin da Allah ya saukar ba a littafinsa ko  harsunan manzanninsa -Tsira da amincin Allah su tabbata a gare su- (b) Ilimi na tsakiya wanda ya ƙunshi sanin ilimin duniya ta hanyar nazari da bincike kamar Ilmud Dibb da Handasah da makamantan su (c) Ilimi na ƙasa wanda yake da alaƙa da koyan kyautata wata ƙwarewa ta iya zaman duniya kamar koyan zane, tsalle-tsalle, motsa jiki, iya ruwa da sauransu.

    Ibnu Hajar (Allah ya kara masa rahma) ya ce: “Abin da ake nufi da Ilimi shi ne na shari’ah da mukallafi zai san abin da ya wajaba a kansa na al’amuran ibadah, mu’amalah da sanin Allah (Tauhidi).

    ____________

    1. Atthaqafah al-Islamiyyah na Prof. Shaukat Muhd Ulayyan sh108.
    2. Al-Fawa’id na Ibnu Qayyim sh137.
    3. Lisanul arab na Ibnu Manzur al-Ifrikiy 6/145.

    Domin karanta cikakken bayani akan Islamiya Daɗi danna nan.