Waƙa Mai Taken Alƙawari Kaya

0
26
  1. Sunanka farko ya Allah,

Tsira amincinka Allah,

Ƙara su gun Manzon Allah,

Shi munka burin mui kalla,

Ko da cikinsa mafarkinmu.

 

  1. Yau damuwa ce ke raina,

Bisa batu da muke raina,

Cikin darenmu ko rana,

Son rai gare mu abin ƙauna,

Kan dukkanin harkokinmu.

  1. Cika shi alƙawari sunna,

Ga dukka manya da ƙanana,

Saɓa shi ko aikin ɓarna,

Da Rabbi sarki ya yi hana,

Ga duk maza har matanmu.

  1. Muna barin sa umarnin nan,

Na Rabbana da ya yo ɗin nan,

Ayar cikin Qur’anin nan,

“Ku zam cika alƙawarin nan,

Don za a tambayi shi” gun mu.

 

  1. “Ya muminai shin mis sa ne,

Kuke batu” a tsaye zaune,

“Da ba ku yin sa a aiki ne?”

Faɗin Ta’ala sarki ne,

Gare mu kan hali namu.

 

  1. Abin takaici mun ƙyale,

Wannan umarni sai hole,

Ran tambaya ba ma kalle,

Halinmu ba kyawu walle,

Don babu alƙawari gunmu.

 

  1. Alƙawari in mun ɗauka,

Na lokaci kan duk harka,

Ko yin wani aiki gun ka,

Ni kam gaske nake ɗauka,

Amma cikawa bai samu.

 

  1. Murna muke in mun saɓa,

Muna ganin ai mun caɓa,

Har jinjina muka zam karɓa,

Kuka ya dace mui sharɓa,

Don ya  ƙazanta aikinmu.

 

  1. Ga ‘yan siyasa ko ado ne,

Suna ganin mai sauƙi ne,

Hanyar zuwa ga muradi ne,

Bayan guba mai halaka ne,

Gare su har umma tamu.

 

  1. Babu dalilin saɓawa,

Sai don mugunta aikawa,

Nuna isa ko burgewa,

Ko sakaci ga mutuntawa,

Da munka yi bisa zatinmu.

 

  1. Ƙarfe goma ka ce zan zo,

Ko ko ka ce wa wane ya zo,

Ba kai shiri goman ta zo,

Sai uzuri ba yin ƙwazo,

Ba ka nadama ko damu.

 

  1. Ka ce wa yaro bar kuka,

Abu kaza ne zan ba ka,

Alƙawari ne ka ɗauka,

Amma ka saɓa wa ɗanka,

Ka muna tarbiyyar ɗanmu.

 

  1. Wannan fa mugun hali ne,

Amma gare mu abin so ne,

Da takamar mun burge ne,

Bayan ko laifi babba ne,

Za ai hisabin sa kanmu.

 

  1. Bai zam cikar addini ba,

Bai zam shi halin kirki ba,

Bai zam abin tunƙaho ba,

Bai zam cika ga kamala ba,

Saba wa alkawari namu.

 

  1. In ka tsananta ga cikawa,

Ka ƙyamaci a yi saɓawa,

Wai ka yi halin Turawa,

Halinka na da tsanantawa,

Don ka ƙi mugun halinmu.

 

  1. Faɗa a cika dattaku ne,

Ko da ko mai yin yaro ne,

Ko a ina mai ƙima ne,

Abin a ba wa aminci ne,

Mai martaba gun sarkinmu.

 

  1. Da mu ya dace ai koyi.

Ya zam gare mu abin ya yi,

A zahiri da cikin rayi,

Mun bar Nasara kaɗai ke yi,

Mun zaɓi ɗaukar son ranmu.

 

  1. Wannan abin jin kunya ne,

Gare mu babban aibu ne,

Abin ragewar ƙima ne,

Da za mu taru mu gaggane,

Da sun yi kyau harkokinmu.

 

  1. Tsari rashin sa ka damun mu,

Na lokutan harkokinmu,

Loto abin banza gunmu,

Shi ne ko ai rayo tamu,

In ya wuce bai komen mu.

 

  1. Faɗa a saɓa laifi ne,

Loto a sauya aibu ne,

Warware zance nakasa ne,

Kin cika kawari sabo ne,

Mu zam cire shi a halinmu.

 

  1. Shi alƙawar ai kaya ne,

Bisa ga kai nannauya ne,

Kula da shi imani ne,

Cika shi aikin lada ne,

Mai nauyaya mizaninmu.

 

  1. Allah ya ba mu dukan dace,

Mu’amalarmu ta zam tsafce,

Ta zam gudana dinance,

Yara su koya su gwanance,

Su zam du’a’i bayanmu.

 

  1. Nan zan tsaya na ciyo burki,

Tabara ba mu yawan ɗauki,

Mu tabbata a halin kirki,

Kullum bisa dukka mataki,

Na rayuwa har ƙarshenmu.

 

  1. Mai tsara waƙar Nasir ne

Ahmad rarrauna ne,

Gare mu mai yin addu’a ne,

Bisa ga kyautata hali ne,

A dukka alƙawarorinmu.

Danna nan don karanta Waƙa Mai Taken Haƙƙin Dabbobi

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceWaƙar Neman Mafita Da Riba Babba
Labarin na GabaWaƙa Mai Taken Ɗan Achaɓa
Nasiru G. Ahmad
Haifaffen jihar Kano ne a unguwar 'Yan awaki. Ya yi digiri na ɗaya da na biyu a kan harshe da adabin Hausa. Yana cikin ƙungiyoyi da dama na marubuta a ciki da wajen jihar Kano. Malami ne kuma mawallafin littattfai da waƙoƙi.