September 12, 2024
ƁANGARE NA II: HANYOYIN SADA ZUMUNTA
Musamman a wannan ƙasar Najeriya hanyoyin sada zumunta sun fara ɓulla ne daga shekara ta dubu biyu (2000) lokacin da aka fara amfani da wayar hannu mai amfani da layin waya.
Da farko wayoyin da ake amfani da su, wayoyi ne da ba sa ɗauke da manhajar hanyoyin sada zumunta, da yawan mutane a lokacin ba hanyoyin sada zumunta ne a gaban su ba, kawai abinda su ka fi yi shi ne buga waya da amsa kira.
Za a iya ce wa mafiya wayancin waɗannan hanyoyi ba a samar da su ba, balle ma a saka su a matsayin manhaja a wayar hannu. Misali, manhajar sada zumunta na 2go wasu ɗalibai na jami`ar Witwatersrand Johannesburge, suka ƙirƙire shi a 2007.
Brian Acton da Jan Koum su ne suka ƙirƙiri manhajar Whatsapp a shekara ta 2009, Facebook kuma Nick Clegg, Sheryl Sandberg, Sean Parker, Mark Zuckerberg suka ƙirƙira a 2004 a Massachuset ƙasar Amurka. Twitter kuma a shekarar 2006 aka ƙirƙire shi, amma sai 2012 aka ƙaddamar da shi wanda Jack Dorsey, Noah Glass, Biz Stone da Evan Williams su ka ƙirƙira.
Twitter (2006), Tiktok( 2016), Telegram (2012). Kafinsu akwai wasu hanyoyin na wasiƙu da sada zumunci kamar su hotmail, yahoomail (1997) da gmail (2004) da sauransu amma ba a samun su a manhajar wayar hannu. Waɗancan su ne aka fi sani a nan, amma akwai dubbansu suna nan ana ta amfani da su yau a faɗin duniya.
A nan kasar, musamman a yankin mu na Arewa, da yawa daga cikin masu amfani da waɗannan manhajoji na sada zumunta ba su san waɗannan manhajoji ba sai kusan shekarar 2010 yau shekara goma sha –biyar ke nan. Sannan da yawa da ga cikin mutane ba su san babban dalilin samar da waɗannan manhajojin ba, balle su yi amfani da su ta hanyar da ta dace.
Matasa na cikin `yan gaba dai gaba dai wurin amfani da waɗannan manhajojin. Ƙaramin misalin da zan bayar shi ne a cikin mutane miliyan hamsin (50M) da suka yi amfani da 2go a nahiyar Afrika miliyan 13 suna Najeriya kuma sama da kashi casa`in (90%) matasa ne.
Wannan hasashe haka yake har yau a ko ina, matasa su ne kan gaba wurin amfani da waɗannan hanyoyi musamman a ƙasashe masu tasowa. Wannan ya na faruwa ne sakamakon rashin aikin yi da zaman banza da matasa suke fama da shi a ƙasashe masu tasowa wanda ci bayan tattalin arziki ke sabbaba shi.
A yau ana ganin samari marasa aikin yi suna yin duk abinda za su yi dan su sami kuɗin da za su sayi data dan su sami damar amfani da waɗannan manhajoji na sada zumunta. Misali, Facebook idan mutum ba shi da data, idan kuma ba lite yake amfani da shi ba, toh a akwai abinda ake cewa “free mode” kwai za ka ga rubutu, amma hotuna ko bidiyo ba za su bayyana ba, sannan ba zai baka damar bin hanyar da za ka sami labari ba ko wani bayani ba wato “link”.
Sau da yawa wannan yana hana mutane fahimtar asalin abinda aka yaɗa ko aka wallafa, sannan ya kan sa mutum ya yi sharhi na goyon baya ko akasin haka, ko ma ya yaɗa abinda ba shi ne ba.
Abu mai mahimanci na gaba shi ne, mutane suna shiga abin da ba su da ilimi a kai. Wannan shi ne dalilin yin wannan rubutun. Sau da yawa babban malami zai yi bayani na ilimi mai zurfi a kan wani abu mai mahimmanci da ya shafi addini, a yaɗa shi ta hanyoyin sada zumunta, kwatsam sai ka ga wani matashi, ko wani ɗan tasha bai san dama ko hagu ba a kan abinda ya shafi ilimin addini, kawai sai ya ce wannan babban malamin nan “ƙarya” ya keyi, ko zai ci gyaran malamin.
Ba don komai ba, kawai wannan hanya ta ba shi dama ya ga ko ya ji abinda wannan babban malamin ya faɗa. Wani babban abin takaicin shi ne shi, wannan matashi ko ɗan tashan ba zai iya kawo wata hujja na ilimi ba, sai soki-burutsu, jahilci da hayaniya.
Misali ɗaya daga cikin misalai masu yawa shi ne mas`alar mutum ya ce ya saki matarsa da wasa ko da kuwa a shirin wasan kwaikwayo ne. Manyan malamai kamar Dr. Bashir Aliyu Umar, oon da Prof. Umar Sani Fagge sun yi fatawa a kan ce wa duk wanda ya aikata haka matarsa ta saku.
Suka kafa hujja da hadisin Manzon Allah SAW ingantacce. Amma aka samu wasu waɗanda ba su wani abu na ilimin addini, kai wasu ma `yan tasha ne, suka rinƙa surutai na jahilci da rashin ladabi ga malamai da malanta da ƙoƙarin ƙaryata hadisin Manzon Allah SAW da molon ka.
Ba abinda ya ba su wannan damar sai waɗannan hanyoyi na sada zumunta wanda suke ganin ilimi kamar abin banza da arhan malanta. Idan aka duba a baya za mu ga mas`aloli na addini, malamai da tsarekunsu su suke tattauna cikin girmamawa ta hanyar rubuce – rubucen ilimi.
Amma yanzu saboda waɗannan hanyoyin na zamani sai a ci mutuncin malami, a zage shi, a faɗi munanan maganganu game da shi, ba tare da an kawo wata hujja ko wata magana ta ilimi ba saboda ba abin da za a iya faɗa da rashin ilimi.
Sannan abu na biyu, wannan ya ba da dama kowa ya ga cewa zai iya zama malami saboda yawan yaɗuwar ilimin kayauta kuma cikin sauƙi. Kowa zai iya zama malami dare ɗaya. Wanda kuma ba haka ba ne, kuma ba ma zai yiwu ba.
Abu na uku, waɗannan hanyoyin sun bai wa wasu `yan dagajin mutane damar yin sojan gona, su mai da kansu malamai, su tsoma baki a cikin abinda ya shafi ilimi, da ma faɗin duk abinda suka ga dama. Jahilai kuma suna nan birjik followers, masu sharing da masu like.
Daga ƙarshe, waɗannan hanyoyin sun ba da gudumawa wurin yaɗuwar ilimi da wayar wa mutane kai game da addini, sannan a gefe ɗaya kuma sun ba da damar raina malamai da ilimi, rashin ganin girman ilimi da mahimmancinsa. Malamai sun zama ba komai ba, sannan malanta ta zama arha.
Duk wanda baya ganin wanɗanda suke riƙe da tushen addininsa, (ilimi) da girma ta yaya zai ga girman addininsa? Gimama malamai yana daga cikin abinda zai sa mutum ya san daraja da girman addininsa.
Whatsapp: 08039290267
Karanta Malamai, Malanta Da Hanyoyin Sada Zumunta A Yau (1)
Edita@rumasau-kallamu









