Azumin Watan Ramadan 2

0
26

SALMANU FARISS ADAMU

Idan kuma mutum ya kusa haɗiye abinci ko abin shan, sannan kuma sai ya ji ana kiran sallah, idan lokaci ne, ma`ana shi ne wanda ya fara kiran sallah a lokacin ko kuma mutumin yana da saurin yin kiran sallah, saboda shi mutumin ya tashi da wuri ya yi sahur ɗinsa, to mutum zai iya yin sauri ya haɗiye wancan lomar ko abincin ko abin shan.

Saboda haka yana da matuƙar mahimmanci ko amfani ga mai azumi haɗi da mai kiran sallah su san lokacin da alfijir yake fitowa ko alamar fitowar alfijir a kowace rana, saboda wasu ladanan suna kiran sallar asubah ko kiran sallah na biyu kafin alfijir ya fito, wasu kuma ladanan suna kiran sallah ne bayan alfijir ya fito da jimawa, wasu kuma masu yin azumi da su suke yin la`akari.

Haka kuma ya kamata ladanai da masu yin azumi mu san hukunce-hukuncen na yin azumi haɗi da yadda alfijir yake fitowa da yadda rana take faɗuwa, saboda a nan ma ana samun wasu matsaloli da yawa ga wasu ladanan, saboda suna kiran sallah magariba kafin rana ta gama faɗuwa ko lokacin kiran sallah magariba ya yi, su kuma wasu mutane da su ke la`akari da zarar sun ji kiran sallah sai su ɗauki abin shan su ko abin cin su, sai su kama ci ko sha ba tare da yin la`akari da duba lokacin shan ruwa ba.

Saboda haka yana da matuƙar mahimmanci ga mai yin azumi, idan zai sha ruwa ya tabbatar lokacin shan ruwan ya yi, saboda da mutum ya yi gagggawar shan ruwa, kuma bai tabbatar lokacin shan ruwan ya yi ba, to gara ya jinkirta shan ruwa bayan an yi sallah, sai mutum ya sha ruwan, saboda idan ya sha ruwa kafin lokacinn shan ruwan ya yi, to ba shi da azumin wannan ranar, haka kuma idan mutum da gangan ko alfahari ko taƙama ya sha ruwan, to ya karya azuminsa, sannan kuma akwai kaffaran azimi a kansa guda sittin a jere haɗi da guda ɗayan can da ya karya.

Saboda waɗannan misalan ya kamata ‘yan uwana musulmai mu tashi tsaye wajen ilimi addini da na zamani, saboda malam mai ” ahlari ” yace “bai kamata ba ga wani mutum ya aikata wani abu a cikin addinin musulunci, har sai ya san hukuncinsa ko abin da Allah (da manzom Allah) yace a kan abin da zai aikata a cikinsa”.

Haka kuma wannan ƙa`idar take a cikin addinin musukunci, babu wani abu da wani mutum ya isa ya aikata har sai ya san hukuncinsa a addinin musulunci, saboda haka yana da matuƙar mahimmanci ga ladanai su koyi yadda ya kamata su dinga kiran sallah, saboda kaucewa wasu kura-kurai na kiran sallah.

Bugu da ƙari kuma, idan mutum ya yi mafarki suna ganawa da rana da wani mutum (mace ko namiji), sannan kuma a cikin watan azumin Ramadan, yaya azuminsa yake ?, amsa, azuminsa yana nan matuƙar a wannan yanayin hakan ta faru.

Amma kuma idan mutum tunanin wani abu ne ko kuma ya kalli wasu abubuwa ne, sai ya fitar da wani abu daga gabansa mai kauri-kauri, sannan kuma fari-fari kamar ruwan kwakwamba ko ƙurji, to hukuncinsa shi ne, hukuncin wanda ya karya azumi da gangan, zai rama azumi guda sittin a jere na kaffara, sai kuma guda ɗaya wanda ya karya.

Danna nan don karanta Guzirin Ramada Daga Rayuwar Sahabbai Da Magabata Na Gari

Edita:@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceTambayoyin Azumi Da Amsoshi
Labarin na GabaHatsarin Yin Wasa-rere Da Hawan Jini