Haramun Ne Mata Su Halarci Husainiyya

0
16

A baya kaɗan mun kawo wasiyyar da Imamu Husaini ya yi wa mata a gab da shahadarsa har ila yau a cikin wasiyyar ya ce:

“Yake ‘yar uwata, ya ke Ummu Kulsum, ya ke Fatima; ya ke Rabab ku nutsu idan na mutu kada ku yaga tufafinku, kada ku ya ƙushe fuskokinku.

Sannan kuma Abul Hasan da Abu Ja’afar (Alaihis Salam) sun faɗa akan fassarar faɗin Allah Ta’ala; “Kuma kada Su (mata) su saɓa maka a kan wani abin aihair? ya ce: “Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya gayawa Fatima (Alaihis Salam) cewa; “Idan na mutu kada ki yakushe fuskarki, kada ki cizge gashinki, kada ki yi min kururuwa, kada ki yi makoki. Sai ya ce wannan shi ne ma’anar “abin da Allah ya ke faɗa”.

Abu Abdullah (Alaihis Salam) ya ce; “Ma’anar wannan ayar ita ce kada su yaga tufafinsu; kada su yakushe fiskokinsu, kada su yi ihu da kururuwa, kada su tsaya a kan ƙabari.

An karɓo daga Abu Sa’id Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya ce; “ya la’anci mace mai rera-kuka da mai sauraro”

To ‘yan uwa mata (sisters) kun ji abinda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam); da Imamai (Alaihis Salam) suka faɗa a kan matan da suke halartar Husainiyya. Shin ko za ku bi maganar Manzo (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) da ta Imamai ku hutar da kawunanku daga zarya da kuke ba dare ba rana; domin ku kaucewa fushin Allah ta’ala da Manzo (Sallallahu Alaihi Wa Sallam). ‘Yar uwa ki bi gaskiya ki bi Allah da Manzo (Sallallahu Alaihi Wa Sallam); ba jagorori ba waɗanda su suna huce cikin raɓa suna kwasar girki ku kuma kullum kuna kan hanya.

Ni dai nasiha nake yi miki. Kuma gyara kayanka…

Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihi Da Falalar Husaini (Radiyallahu Anhu) A Taƙaice danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kanFalalar Ba wa Ɗan Uwa Sadaƙa danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gaskiyar Magana Akan Ashura wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceYadda Ake Mandi Rice
Labarin na GabaTarihin Alaramma Malam Salisu Ɗanruwantsa