An haifi Malam Buhari, Sarkin Malaman Sakkwato a Unguwar Siriddawa da ke Sakkwato a shekara ta 1934. Ya yi karatu wurin mahaifinsa Malam lbrahim da Malam Na Ta’ala Gidan Kanawa Sakkwato da Malam Mujeli Garge da Malam Shehu NaLiman (Limamin Masallacin Shehu).
A halin yanzu tsangayarsa cike ta ke da almajirai da makaranta sama da ɗari biyar, baya ga ɗumbin masu karatun littatafai kowace rana a wurinsa. Babbar baiwar Malam Buhari ita ce ƙwarewar da Ubangiji Maɗaukaki Ya ba shi a fagen ilmin Fiƙhu.
A yanzu shi ne ya ke riƙe da ragamar Jagorancin malaman Sakkwato a fadar Sarkin Musulmi. Makarantarsa na gudana ne tare da taimakon ɗansa Malam Sambo da wasu daga almajiransa.
Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Malam Muhammadu Na Ta’ala danna nan.
Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Sahabbai Suka Yi Koyi Da Annabi Muhammad (S.A.W) danna nan.
Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.