Akasari akan sami:
a. Koyar da Darussa na Rayuwa
Littattafan ƙagaggun labaran sukan koyar da ɗabi’u irin su gaskiya, haƙuri, da tsoron Allah. Galibi sukan nuna yadda mugunta ke kai mutum ga halaka, abin da ke zama darasi ga masu karatu.
b. Ƙarfafa Tunani da Basira (Tarbiyya ta musulunci)
Suna motsa tunanin matasa su zama masu hangen nesa da ƙirƙire-ƙirƙire wajen magance matsalolin rayuwa. Inda ake gane tarbiyya
c. Ƙarfafa Soyayya da Haɗin Kai
Labaran na nuna muhimmancin taimakon juna da zaman lafiya a cikin al’umma.
d. Hana Mugunta da Laifi
Ta hanyar nuna sakamakon laifuffuka kamar sata, ƙarya da cin hanci, matasa suna fahimtar illar yin haka.
e. Ƙarfafa Sha’awar Ilimi
Jarumai masu ilimi a cikin labarai sukan zama abin koyi ga matasa wajen neman ilimi.
f. Adana Al’adu da Harshe
Kagaggun labaran suna adana harshen Hausa da al’adunta ta hanyar karin magana da hikima.
Bilkisu Ahmad Funtuwa
Bilkisu Ahmad Funtuwa tana daga cikin fitattun marubatan Hausa mata da suka taka rawar gani wajen gina tunani da tarbiyya ta hanyar adabi. Rubuce-rubucenta suna ɗauke da darussa na addini, zamantakewa, aure, da rayuwar mata. Ta yi amfani da labarai domin koyar da ɗabi’a, adalci, da darajar mace a cikin al’umma.
Takaitaccen Tarihin Bilkisu Ahmad Funtuwa
An haifi Bilkisu Ahmad Funtuwa a Funtua, jihar Katsina, kuma ta shahara a fagen rubutun littattafan soyayya, zamantakewa da ilimi. Marubuciya ce mai kishin addini da al’adun Hausa, wacce ke amfani da rubuce-rubucenta wajen gyaran halayen matasa da mata.
Daga cikin shahararrun littattafanta akwai:
– Wa Ya San Gobe
– Allura Cikin Ruwa
– Wa Ya San Jiki
– Rabon Juna
Wanann bayanin an ciro shi ne daga muƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.
Danna nan don karanta Adabin Kasuwa A Ƙasar Hausa
Edita@rumasau-kallamu










