Waƙar Yabon Manzon Allah(S.A.W).

0
989

Domin  shiga gasar mawaƙa wadda ƙungiyar gamayyar marubuta da yadda manazarta waƙoƙin Hausa ta ƙasa, ta saka a ƙarshen shekarar  2018 zuwa farkon  2019.

 

  • Allah na roƘa cikin ɗa’a,
  • A baitukan nan da babu ba’a,
  • Allah na ɗaro daɗin sa’a,
  • A baitukan nan da ba bidi’a,
  • Albarka sa min na ɗau ƙuri’a.
  • —————————–
  • Na yo salati ga Manzona,
  • Na Khadija, Hafsat, Uban Nana,
  • Na Sadiƙu, Umar, Usumana,
  • Na Aliyu zaki kisan arna,
  • Na Mu’awiyya sahihin ƙima
  • ————————–
  • Zuma farar gani farar saƙa,
  • Na ƙulla baiti cikin waƙa,
  • Na tsara ɗango cikin sarƙa,
  • Domin yabon Ɗaha kun ji haka,
  • In ka bi Manzonmu ka fi haka.
  • ——————————-
  • Kyawun ɗabi’unsa sun fi ɗari,
  • Kufurun, musulmanmu sun nazari,
  • Zama da Manzon fa ba haɗari,
  • Rayuwa a tsarinsa ba garari,
  • In ka bi Manzonmu ka ci gari.
  • ——————————–
  • An haifi Manzo a Makkiya,
  • Ran Litinin sha biyun ku jiya,
  • Auwal Rabiyun na ɗan juya,
  • Shekara ta giwa a Habshiyya,
  • Islam kalanda ta Hijriyya.
  • —————————-
  • Nasabar Mahaifinsa Abdallah,
  • Abdulmuɗallib cikin jumla,
  • Haashim fa Kaka ga Abdallah,
  • Abdulmanaf ɗan Ƙusai Allah,
  • Ya sa Kilab don cikar falala.
  • ——————————
  • Umminsa Babba Aminattu,
  • Yar Wahab, Manafi, Zuhuratu,
  • Sun haɗe a Kaka taƙaita batu,
  • Na biyar Kilab sai ku gane batu,
  • Sirarsa Manzon da bai shantu.
  • ———————————
  • Matansa sha ɗai na lobayya,
  • Khadija farkonsu kun ji ɗaya,
  • Assha da Hafsat suna baya,
  • Ummu Habiba da Salmayya,
  • Hindattu, Saudat ba sa ƙarya
  • —————————-
  • Sai Zai nabu bintu Jahshiyya,
  • Maimunatu bintu Harisiyya,
  • Zainab Khuzaima na jerayya,
  • Sai kam ta ƙarshe Juwairiyya,
  • Matansa cif-cif da sha ɗay
  • —————————-
  • ‘Ya’yanSa bakkwai cikar sunna,
  • Ibrahim a farko mai suna,
  • Abdallah, Ƙasim da ba su tsana,
  • Fatima, Kulsum cikar ƙauna,
  • Ruƙay da Zainab cikon juna.
  • ——————————
  • Manzo yana nan da mu’ujiziyya,
  • Ƙur’an da ba wasa ba ƙarya,
  • Tatsuniyar nan ta yan zolaya,
  • Ba shirme danniyar nan ku jiya,
  • Halinsa ne kun ji khairiyya.
  • ——————————
  • Halinsa Manzo cikar kunya,
  • Nutsuwarsa Manzo a taffiya,
  • Maganarsa ƙamshi yake zirya,
  • Dattijo ne mai halin manya,
  • Ƙur’an dalilinsa baki ɗaya
  • —————————
  • Dini na Manzo da ba ƙarya,
  • Ba yaudara ko kisan hanya,
  • Shi gaskiya ce zancensa ɗaya,
  • Dinin da Shaiɗan yake baya,
  • Ba ya kusantarsa don kariya.
  • ——————————-
  • Islam ya kawo a Makkiya,
  • Ya ƙira Ƙuraishi su bar ƙarya,
  • Sata da shirka da camfiyya,
  • Da kisa na juna da shirya tsiya,
  • Su riƙe ƙiran nan na kimtsiyya.
  • ——————————-
  • Rukunai shida ne na Addini,
  • Zan ambato su ku ɗan ji ni,
  • Kalma ta farko shahadataini,
  • Sallah, Azum, Zakka ba raini,
  • Hajji a ƙarshe ga mai sukuni.
  • ——————————-
  • Iman ku gane ajinsa shida,
  • Iman da Allah, Mala’iku da;
  • Littattafan nan na aƙida,
  • Manzanni, Lahira kui shaida,
  • Ƙaddar fa wajib cikon na shida.
  • ——————————-
  • Ya yaƙi arna cikin sa’a,
  • Ya rusa daular da ba ɗa’a,
  • Ya ce gumaka mu yo bara’a,
  • Kisa na juna mu bar bidi’a,
  • Kushe da juna mu bar ta ba’a.
  • ——————————
  • Yaƙi talatin na yo nazari,
  • Ya yo su ba ɗai Ya buɗe gari,
  • Islam ya zamto cikin fahari,
  • Kufurun suna can suna garari,
  • Aljanna ce duk cikar guzuri.
  • ——————————-
  • Daula ta zamto ta Islama,
  • Kowa ya zamto cikin hidima,
  • So, taimakon juna ba ƙyama,
  • Ba soke-soke da yin gulma,
  • Cab! Kun ji hanyar mutan ƙ
  • —————————–
  • Zan dakata zana sa birki,
  • Tamkar fa mota a kan tuƙi,
  • Nayaya ƙanin Bilki,
  • Yobe gari na da ba raki,
  • Tammat salamun na yo birki.

 

              domin samun karanta cikakkiyar waƙar danna koren rubutu

 

 

labarin da ya wuceWaƙar Hamdala .
Labarin na GabaWaƙar Yabon Farfesa Abdulƙadir Ɗangambo