Daga Salmanu Faris Kudan, Shugaban Ƙungiyar Marubutan Arewa ta Ƙasa Nijeriya
- A yau Arewa ta wayi gari da annuri,
An kunna fitilar da ta daɗe da alheri,
Gwarzon ilimi Mu’azu Sa’adu mai annuri,
Ya ɗaukaka harshe cikin nutsuwa bisa tsari.
2. Ranar nan ta zamo alfahari ga dukkanmu,
An ɗaga rawani a kan ƙashin kaifin basirarmu.
Ka hau kujerar Farfesa cikin ladabinmu,
A ɓangaren harshen Hausa mai cike da tarihinmu.
3. Ka zama jagoran harsunan Nigerian Languages,
A Jami’ar Sule Lamiɗo, Kafin Hausa mai darajas.
Ka ɗauki nauyin harshe da ƙarfin halis,
Kana koya wa duniya kima da martaban Hausas.
4. Ka reni ɗalibai da armashi da hikima,
Ka zuba ilimi kamar ruwan sama.
Darussanka sun zama turakun hawa sama,
Sun gina ƙarni masu zuwa tun kafin anjima.
5. A fagen nazari ka zama tamkar tauraro,
Kana haskakawa masana masu sauraro,
Littattafanka sun zama ginshiƙai abin dogaro,
Duk inda ake Hausa, za ku taho har ɗan goro .
6. Ka zama madoga ga marubutan Arewa,
Mai tsarkake harshen har da rera wa,
Ka zama ginshiƙi da ba ya dusashewa,
Wanda ya daidaita harshenmu cikin dubawa.
7. Ni Salmanu Faris Kudan, mai buƙata,
Na miƙa wannan waƙa a madadin marubuta,
Mu na yi maka barka da wannan babban kyauta,
Allah Ya ƙara maka lafiya ban da kunyata.
8. Rayuwarka ta zama izina ga matasa,
Ga waɗanda ke neman hasken don yai tasa,
Ka nuna musu cewa aiki ne jawur ga matasa,
Su ne hanyoyin da ake hawa don tasa.
9. Duniyar Hausa ta yi murna da annushuwa,
Ta ƙara jin ƙima da samun ɗaukakawa,
Nasara irin taka ta zamo abin dubawa,
Ga duk mai son zama abin koyi a rayuwa.
10. Malam Mu’azu, Allah Ya yi maka albarka,
Ya ƙara nisan kwana da nutsuwa a gare ka,
Ya zuba hikima wacce ba ta yankewa gare ka,
Ka ɗaukaka fiye da yadda kake yanzu da albarka.
Danna nan don karanta Tsokaci A Kan Littafin Salmanu Da Salma
Edita@rumasau-kallamu










