An haifi Malam Isa Umaru a garin Ƙauranmata zamanin Sarkin Kano Usman. Mahaifinsa Malam Umar ya aika da shi garin Bunkure wajen Malam Adamu Gangaran a farko-farkon zamanin Sarki Abdullahi Bayero. Bayan Malam Isa ya data ne ya nemi a kai shi garin Rimi cikin yankin Sumaila wajen Malam Isuhu.
Gwanin Alƙur’ani, ma’abocin tawaru’u da yawan karamci, Malam Isa ya yi tafiye-tafiyen neman AIƙur’ani cikin ƙasar Gumel; wajen Malam AbdulHamid da garin Ciromawa a ƙasar Haɗeja.
Saboda irin baiwar da Ubangiji ya ba wa Malam Isa abokansa ne suka gabatar da shi a matsayin mai darasu bayan rasuwar Alaramma Malam AbdulHamid a katafariyar tsangayarsa da ke garin Ciromawa.
Dawowar Sa Kano Da Zama Bayan gwagwarmayar neman karatu daga wannan gari zuwa wancan; Malan Isa ya koma mahaifarsa a garin Ƙauranmata a inda ya cigaba da hidima ga mahaifinsa Malan Umar. Don haka kullum yana tsankanin cikin birni da ƙauyensu, sai dai ya yi ‘yan kwanaki ya koma gida.
Daga ƙarshe wasu daga cikin attajirai irin su Alhaji Hamidu Namudi da ke Unguwar Dala; suka nemi mahaifinsa da ya yi masa izinin dawowa Kano don koyar da Alƙur’ani.
Bayan samun izini mahaifinsa ne ya dawo Kano ya zauna a Unguwar Dala; daga bisani ya koma Gwale a farkon mulkin Sarki Ado Bayero Manyan abokan karatunsa su ne:-
- Malam Saleh Ɗangalinja Ƙarfi
- Malam Umar Magasawa
Malam Isa Ɗan Ƙauranmata bai gushe ba har zuwa yanzu yana karantarwa a tsangayarsa da ke gidansa a Gwale.
Yana da ‘ya’ya kamar haka:-
- Malam Umar Isa
- Malam Usman Isa
- Malam Abubakar
- Malam Abdulhamid
- Malam Garba
- Malam Sabi’u
- Malam Aminu
- Malam Jamilu
- Malam Kabiru
Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Alaramma Malam Salisu Ɗanruwantsa danna nan.
Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Magabata da Haihuwar Ɗanƙwairo danna nan.
Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.