Tag: yadda ake

  • Abin Da Ke Jawo Jarirai Suna Shan Ruwan Haihuwa (AMNIOTIC FLUID)

    Abin Da Ke Jawo Jarirai Suna Shan Ruwan Haihuwa (AMNIOTIC FLUID)

    Amniotic fluid ruwa ne dake zagaye da jariri a cikin mahaifa wanda ke taimakawa yaron ya sami balance ta yadda ko faɗuwa mai juna biyu ta yi ta ruf da ciki, cikin ikon Allah shi jariri ba zai san me yake faruwa ba ma ballantana abun ya shafe shi.

    Shi wannan fluid ɗin yakan haɗu da fitsarin da babies ɗin kan yi a cikin mahaifa lokacin da suka kai sati 25weeks sukan kuma fara shan wannan ruwan tun daga sati na 10-11 weeks na ciki, ko lokacin da fatar ƙwayar halittar kumatunsu cikin mahaifa ta fara rufe bakinsu. Dan haka dama sukan sha abinsu tun a ciki.

    Daga lokacin da ciki ya kai sati 20weeks duk wannan ruwan kusan yakan rikiɗe ya zamo fitsarin babies ɗin ya fi yawa. Yayin da ainisin ruwan amniotic ɗin da ke zuwa daga ƙodar baby ɗin ke kasancewa ɗan kaɗan kurum.

    ME YASA SUKE SHA WASU HAR HAKAN YASA SU MUTU?

    Kamar yadda na faɗa ainihin ruwan amniotic fluid dama suna shan abinsu tun a ciki kafin zuwan haihuwa domin shi ne ke ƙara ma huhun su (lungs) ƙwari. Abinda suke sha ya wahal da su yayin haihuwa koma su rasa ransu muna kiransa da (MECONIUM).

    Meconium wato na nufin kashin farko da suke fara yi a ciki yayin artabun naƙuda, idan ya haɗu da ruwan fluid ɗin suka haɗiya shi ke musu illa yake shiga ƙofofin numfashinsu.

    Wanda kamata ya yi sai bayan an haihu za su yi wannan kashin koma kada su yin kwata kwata sai bayan an fara ba su nono. Bisa larura amma idan aka samu doguwar naƙuda musamman haihuwar fari ko kuma matsatsi yayin haihuwa shi ke jawo su yi kashin kuma su sha abinsu musamman yayin da suka ja numfashin farko suka fara fitowa yayin haihuwa.

    Sannan hakan ya fi shafar yaran da suka jima suka ɗau sati 37 zuwa 41 a ciki ko sati 42. Wannan shi ne abinda ke faruwa, kun ga kenan ba abu ne da yake wajibi a a hana faruwarsa ba sai dai ana iya daƙilewa idan ka ba iyalin ƙwarin guiwa zuwa awo tare da kulawa yayin goyon ciki.

    Danna nan don karanta Hatsarin Amfani Da Mayukan Hasken Fata

    Edita@rumasau-kallamu

  • Daidaitacciyar Hausa (Standard Variety)

    Daidaitacciyar Hausa (Standard Variety)

    GABATARWA
    Ilimin kimiyyar harshe(Linguistics) ilimi ne da ke nazarin harsuna tun daga sautuka, ginin jimla, kirar kalma, da sauransu. An raba wannan ilimi zuwa babba (macro) da kuma ƙarami (Micro). Ƙarmin kason shi ne wanda ƙunsa waɗancan ilimai da aka ambata a baya, babban kuma ya ƙunsa ilimin walwalar harshe, ilimin karin harshe, haihuwar harshe da sauransu.

    MA’ANAR DAIDAITACCEN HARSHE

    Muhammad, D. (1990) Ya ce “standard variety” na nufin ‘Daidaitaccen Harshe’
    Daidaitaccen harshe, shi ne ɗaya daga cikin kare-karen harshe da aka zaɓo wanda aka mayar da shi a matsayin mafi girma da kuma karɓuwa a kan sauran karuruwan harshe.
    Misali; harshen Hausa da karuruwan harsuna da dama.

    Kamar karin harshen Zazzaganci da Basanci da Kananci, da sauransu daga cikin aka samar da daidaitacciyar Hausa wanda kuma da shi ne ake amfani a makarantu da sauran kafafen watsa labarai. Harshen Spanish da kuma Turancin Ingila wanda babban kotun Ingila ta yanke hukunci kan cewa Turancin Ingila shi ne karɓaɓɓe, kuma halastaccen harshen da aka aminta a yi amfani da shi a matsayin daidaitaccen harshe, don gujewa ɓarkaceceniya.

    KAMMALAWA

    A ƙarshe ana iya cewa daidaitaccen harshe wani harshe ne da ake samar da shi daga karuruwan harshe mabanbanta, wanda kuma aka amince da a yi amfani da shi a gidajen rediyo da makarantu wato dai da shi aka aminta a hukumance.

    MANAZARTA

    Muhammad,Ɗ (1990). “Hausa MetaLanguage”, University Press Limited.

    2) Cadelon, J.A (2013) “Literary Terms

    Danna nan don karanta Siyasa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Ayyukan Ta’addancin Matasa A Kano: Aure, Yawan Haihuwa Da Tarbiyya A Wata Mahanga

    Ayyukan Ta’addancin Matasa A Kano: Aure, Yawan Haihuwa Da Tarbiyya A Wata Mahanga

    Ku yi auren soyayya, sannan ku auri masu haihuwa, zan yi alfahari da yawanku ranar tashin kiyama”

    – Manzon Allah (SAW)

    SHIMFIƊA

    Tun da Allah ya tsara zamantakewar al`ummomi, ya ƙaddara samun masu bijirewa tsarin zamantakewa. An sami masu bijirewa Annabawa wajen bin dokokin Allah, ana kuma samun masu bijirewa tsarin rayuwar jama’a kamar ɓarayi da sauran masu aikata laifuka daban daban.

    Babban dalili a nan shi ne abinda Allah ya ba mu labari na ‘ya’yan Annabi Adam (Habila da Qabila). Wannan abin da Allah ya ƙaddara ba hujja ba ne game da ayyukan ɓarna a cikin al’umma, dan Allah da kansa ya zargi wanda ya yi kisan kai cikin ‘ya’yan annabi Adam da kuma irin uƙubar da aka tanadar masa.

    Thomas Hobes a cikin nazariyyarsa ta kasa- jama’a da ke rayuwa a wuri ɗaya- ya na ganin dole a samar da shugabanci mai ƙarfin iko ta yadda duk wani mutum –ɗan ƙasa- zai miƙa wuya kuma ya ba da duk wani haƙƙi nasa ga shugabancin da zai kare shi daga dukkan ta’addancin wani ɓata-gari.

    Hobes ya nuna cewa idan aka bar mutane kara zube, ba tare da wani shugabanci ba, toh kowa zai yaƙi kowa ta yadda rayuwa za ta zama, mummuna, gurɓataciyya, taƙaitacciya mai cike da tsoro da tashin hankali. Sai ya ce, don a kare mutane daga wannan yanayi dole ne sai an samar da shugabanci mai ƙarfin iko don tabbatar da doka da oda da kuma samar da zaman lafiya da kwanciyar hankalin jama’a.

    Duk da wannan nazariyya ta Hobes ta samu ƙalubale da ga wasu manazarta, amma dai tana da madogara mai ƙarfi. Idan muka dubi yanayin zamantakewar al’umma a yanzu, duk lokacin da aka ce ba idon hukuma a guri, toh sai ka ga ɓarna ta samu gindin zama, maɓarnata sun samu dama, jama’a kuma su shiga halin ɗar-ɗar, zullumi da tsoro.

    Karamin misali, a watan Oktoba, 2020 lokacin da aka yi zanga-zangar end sars, a jihar Legas akwai lokacin da aka janye jami`an tsaro na ɗan wani lokaci a wasu wurare don kare rayukansu, jama’a da yawa sun shiga halin zullumi saboda ƙaruwar ayyukan ta’addanci a waɗannan unguwanni, har sai da ta kai jama’a sun fara kira ga gwamnati da a taimaka a dawo da jami’an tsaro musamman `yansanda.

    Wannnan yana tabbatar da ce wa duk lokacin da aka rasa tasirin hukuma, toh lallai jama’a za su shiga cikin halin tsoro da barazar ayyukan ‘yan ta’adda da ɓata-gari. Wannan ba wai a irin ƙasashen mu na Afrika ba ne kaɗai, har da ƙasashen da suka ci gaba sosai. An ga irin abinda ya faru a Los Angeles na ƙasar Amurka a cikin wannan watan har sai da ta kai an sa dokar ta ɓaci a birnin, aka kuma tura sojoji masu yawa don kwantar da zanga-zanga da ta rikiɗe ta koma tarzoma.

    AURE, YAWAN HAIHUWA DA TARBIYYA

    Bazan faɗaɗa magana a wannan ɓangaren ba, amma zan yi tsokaci. A kwanakin nan, ayukan ɓata gari da ta’addanci na matasa ya yawaita a birnin Kano, musamman abinda ya shafi faɗan daba, kisan kai da ƙwacen waya. Mutane a shafukan sada zumunta musamman facebook- wanda shi na fi bibiya- suna ta rubuce-rubuce game da lamarin. Amma abinda na ga mutane sun raja’a a kansa shi ne yawaitar aure da haihuwa tsakanin al-unmmar mu da kuma rashin baiwa ‘ya’ya tarbiyya. Zan ɗauki kowanne cikin abubuwa ukun in yi magana a kai a taƙaice.

    Yawaitar aure, ni a fahimtata ba ita ce matsalar ba kai tsaye, domin yawaita auren shi ma yana da nasa matsalar wadda ta ke da alaƙa da ƙaruwar bata-garin matasa. `Yan mata sun yawaita, zaurawa ma haka, idan ba a yawaita aure ba, lallai zinace -zinace zai yawaita, ta hakan kuma za a yi ta haifar ‘ya’yan da ba su da iyayen da za su ɗauki nauyin su ko su ba su tarbiyya- an koma gidan jiya.

    Na biyu yawaitar haihuwa, shi ma ba laifi ba ne, saboda ai mun san gidaje a Kano waɗanda ‘ya’ya kawai sun kai talatin, arba’in ko ma sama da haka. Wasu ma dalilin ‘ya’yan suka sami ɗaukaka. Amma na tabbata idan da za a tambayi matasan nan masu aitaka ɓarna su nawa ne a gidan su, zai yi wahala a ce mafiya yawansu su kai ashirin, talatin ko arba’in, wasu ma su biyar ne ko uku ko ma shi kadai ne.

    Ba na goyon bayan haihuwa ba tsari, musamman a wannan yanayin da ake ciki na matsi, mutum ya san abinda ya kamata na yadda zai kula da haƙƙin da Allah ya ɗora masa, sannan ya sani Allah zai tambaye shi game da ‘ya’yansa. Idan bai kula da haƙƙin da Allah ya ɗora masa ba, ya san abinda zai biyo baya a gaban Allah.

    Tarbiyya, wacce ita ce muhimmi, kuma babban abin. Ko da ɗa ɗaya ne Allah ya baiwa mutum, idan bai tsaya da gaske ya ba shi tarbiyya ba, toh sai ya gagare shi kuma sai ya zamar wa jama`a fitina. Amma duk yawan ‘ya’yan mutum, da taimakon Allah idan ya tsaya da gaske ya ba su tarbiyya, toh sai ka ga sun zama masu mafani a cikin al`umma waɗanda ake alfahari da su.

    Tarbiyar nan fa, ba wai samar da abinci ne ko abin sha da tufafi ba kaɗai, ya haɗa har da ɗabi’u da halayyar uba da uwa su kansu, da kula da abokansa da waɗanda ya ke mu’amala da su, inda yake zuwa da sauransu. Babu yadda za a yi uba ya zama maƙaryaci, mai nuna rashin gaskiya mai zalintar iyalinsa kuma ya sa ran ɗansa ba zai zama haka ba.

    A yanzu iyaye sun ɗauka tarbiyya aikin su ne su kaɗai, ba ruwan kowa da ‘ya’yansu, kada wani ya yi katsalandan cikin aikinsu, ko yaya kusancin sa ya ke da su. Toh iyaye su sani, tarbiyyar ‘ya’ya ba aikin mutum ɗaya ba ne, aikin mutane ne da yawa, aikin iyaye ne su biyun, aikin malamai ne (malam makarantun ‘ya’ya), aikin maƙota ne, aikin ‘yan’uwa ne da abokan arziƙi.

    Duk lokacin da iyaye su ka kasa gane haka, toh su sani suna aikin banza ne kawai, suna yin abinda suke yi ne sauran mutanen kuma su na warwarewa. Saboda haka sai iyaye sun yarda cewa tarbiyar ‘ya’ya na kowa da kowa ne, kowa yana da gudumawar da zai bayar daga cikin waɗanda aka faɗa a baya.

    Wannan shi ne yanzu abin da ya ke cutar iyaye saboda son ‘ya’ya kuma shi yake kawowa taɓarɓarewar tarbiyyar ‘ya’ya don ba wanda zai taya ka abinda ba za ka iya yi kai kaɗai ba. Tarbiyya ba za ta samu ba idan masu taimakawa wajen tarbiyya suka zura wa iyaye ido game da ‘ya’ya ko da kuwa sun ga abinda zai cutar da ‘ya’yan ko zai cutar da iyaye.

    ZAMANTAKEWA DA TARBIYYA

    Yanayin zamantakewar mu a yanzu ya canza daga zamantakewa na Bahaushe da aka sani zu wa zamantakewa na ‘yan bariki. Rayuwa ta ba ruwa na da kai, ba ruwan ka da ni, ba ruwanka da gidana da ‘ya’yana ba ruwana da gidanka da ‘ya’yanka. Ya’yanka ‘ya’yanka ne, nawa nawa ne. Duk abinda na ga ‘ya’yanka suna yi ba abinda ya shafe ni ba ne, haka kai ma.

    Wannan ba zamantakewa ne ta al`adar Bahaushe ba. Addinin musulunci da tarbiyya duk ba su yi koyi da haka ba. Idan ana so a gyara tarbiyar ‘ya’ya dole sai an canza wannan zamantakewar ta bariki. A dawo duk abinda ya shafi ɗaya ya shafi kowa. Sannan a canza zaman munafunci zuwa zaman amana da mutunci, zaman amana shi ne a faɗa wa kowa gaskiya komai ɗacinta ta hanyar da ta dace, idan ta kama a tilasta masa game da wata maslaha na zamantakewa dole ne a yi masa haka don gyara.

    Babban abin yi kafin a sami wannan gyara na zamantakewa sai al`umma ta dawo da ga rakiyar gabatar da abin duniya a kan mutunci da dattaku. Ya zama masu dattaku da mutunci su ne iyaye, su ne jagorori su ne masu faɗa a ji a cikin unguwanni, girmama na gaba a cikin al`umma. Da dai sauran abin da ya kamata.

    Samun manyan mutane masu mutunci da dattaku a cikin al`umma ya na nuna cewa al’umma tana da na gaba waɗ anda za su iya hanawa a hanu ko su sa a yi ayi. Idan da waɗannan a cikin al`umma tarbiyya za ta gyaru daga sama har ƙasa. Duk al’umar da ta zama ba babba, ba dattijo mai faɗa a ji a cikin ta, toh ta kamar hanyar halaka, taɓewa da lalacewa.

    Waɗannan matasa sun zama haka ne saboda tun suna ƙanana ba wanda yake faɗa musu su ji har suka zama abinda suka zama yanzu ba wanda ya isa ya faɗa musu su ji. Tasirin mai faɗa a ji (dattawa) a cikin al`umma ya fi na jami’an tsaro, saboda dattawa za su iya daƙile faruwa duk wani abu kafin ya faru ta hanyar tsawatarwa tun daga layi zuwa unguwanni. Al’ummar mu yanzu muna fama da rashin manya dattawa a cikin mu, ba wai babu su ba ne, akwai su, sai dai mu ne ba ma girmama su, ba ma ganin kimarsu da darajarsu.

    RUFEWA DA SHAWARWARI

    Ayyukan daba da ƙwacen wayoyi ya fara zama ruwan dare a Kano, abin kullum yana ƙara tsamari, mutane kullum suna cikin zullumi da tsoro a lokutan da suke cikin harkokin su na yau da kullum. Sau da yawa ɓata-gari suna kashe mutane masu mutunci da kamala (masu aikin yi da iyali) wannan ba ƙaramin abin ta-da hankali ba ne, sannan yana ƙara yawan ɓata-gari da zaman banza a fakaice.

    Shawo kan mastalar faɗan daba da ƙwacen wayoyi a Kano ko ma kawo ƙarshen sa, dole ne sai gwamnatin jiha da jami’an tsaro sun tashi tsaye sosai don daƙile waɗannan ayyukan kafin abin ya kai wani yanayi, duk da akwai ‘yan matsaloli, amma za a iya shawo kansu.

    Abu na gaba, dole a samar da kwamitocin dattijai a unguwanni don tsawatarwa iyaye da ‘ya’ya kan duk abinda suka gani ba dai dai ba da ma ɗaukan mataki idan hakan ya kama. Masu hannu da shuni a unguwanni su samar da gidauniya na tallafa wa marasa galihu da sana’a ko karatu.

    A sami kyakkaywan haɗin kai daga mutanen unguwa, duk da ana samun waɗanda ba sa ba da haɗin kai, dole a taka musu birki don kar su yi zagon ƙasa ga tafiyar. Idan ta kama a ɗau mataki a kansu ma ba laifi ba ne don cimma abin da ake buƙata.

    Kiran waɗannan matasan da zama da su, jan hankalinsu, yi musu nasiha da nuna musu illar ayyukan su nan duniya da lahira. Jan su a jiki da nuna muhimmancin su a cikin al’umma, kwaɗaitar da su irin dammamakin da ke gaban su da irin abin da za su iya zama nan gaba.

    June, 15th 2025

    Don karanta Wasu Daga Dalilan Shaye-shayen Ƙwayoyi danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

     

     

     

     

     

     

     

     

     

  • Wasu Daga Dalilan Shaye-shayen Ƙwayoyi

    Wasu Daga Dalilan Shaye-shayen Ƙwayoyi

    Masu iya magana suna cewa, ruwa ba ya tsami a banza, kuma in ka ga zomo a kasuwa kai shi aka yi. Yadda iya bincike ya tabbatar daga majiya mai tushe shi ne, ‘yan mata masu shaye-shaye suna shan ƙwayoyi da wiwi da giya da hodar Iblis (cocaine) maganin mura ko na tari da sauran abubuwan sa maye don kawai su yi maye saboda wasu dalilai kamar haka:

    1. Don a yi nishaɗi kawai

    2. Saboda kawar da ɓacin rai, (wai don damuwarsu ta ragu)
    3. Yawan kwaɗayi da ƙwalamar cewa sai an sha duk wani abu da aka ga wata kawa ko wani saurayi ko kuma aboki yana sha.

    4. Idan suna so su yi wa wasu rashin albarka (wato rashin kunya ko tsageranci), domin in ba su sha ba kunya da tsoro suna iya hana su yin tsageranci.

    5. Kwaikwayon ƙawaye da samari ko abokai don sun ga suna sha.

    6. Wasu iyayensu suka gani suna sha, shi ya sa su ma suka shiga sha.

    7. In suna so su yi fasiƙanci sai su sha.

    8. Wasu don kawai su yi ta barci.

    9. Don su yi duk abin da suka ƙudiri aniyar yi a ransu;

    10. Kaɗaitaka da yawan tunane-tunane suna sa wasu su shiga shaye-shaye.

    11. Sha’awar yadda mawaƙan ƙasashen Turawa da na yammacin duniya suke tafiyar da rayuwarsu ta fuskar shaye-shaye.

    12. Saboda ba za su iya riƙe karatu ko haddace abin da aka koya musu a makaranta ba matuƙar ba su sha ba.
    13. Saurayi yana bai wa budurwa ba tare da ta sani ba, don ya samu ya yi lalata da ita.

    14. Akwai masu sha don su nuna cewa sun waye ko don su burge.

    15. Saboda nuna isa, cewa za su iya yin abin da suke so, don babu wanda ya isa ya hana su.

    16. Soyayya da mashayi ko ɗan maye ko ‘yar maye.
    17. Rashin aikin yi.

    18. Sakar wa yarinya budurwa kula da kanta da ɗaukar nauyin lamuran rayuwarta ta yau da kullum.

    19. Gwasalewa da rashin yabawa ga matashiya a bisa abubuwan da take yi ga iyayenta ko mijinta.

    20. Kariya daga tsoro ko fargaba.

    21. Tsayawa a kan ra’ayi domin cimma wani buri.
    22. Kora daga aiki ko makaranta.

    23. Ƙyashi da hassada da kushe.

    24. Zaman birni (ka zo na zo) babu ruwan kowa da kowa.

    25. Rashin adalcin shugabanni wajen rabon arzikin ƙasa.
    26. Cunkoso a gidaje musamman gidan haya.

    27. Wuraren ayyukan gayya da kalankuwa da bukukuwan noma.

    28. Bukukuwan salla da mauludi da kuma kirsimeti.
    29. Son yin hutu ko barci a ƙarshen mako.

    30. Gudun kada yarinya ta zama saniyar ware a cikin ƙawayenta masu sha.

    31. Don tallata sana’ar su ta sayar da kayan maye da sauransu.

    32. Don a sami ƙarfin ɗaukar kaya.

    33. Akwai waɗanda ba su ma san dalilin da ya sa suke sha ba.

    34. Bin ƙwaƙƙwafi (son a san yadda ake ji in an sha ƙwaya)

    35. Son tafiya da zamani.

    36. Rashin aikin yi.

    37. Rashin kusantuwar ‘ya’ya da iyayensu.

    38. Karance-karancen littattafai da mujallu da jaridu da ƙasidu da kallon finafinan baɗala.

    39. Mummunan tunani a rayuwa.

    40. Samun abubuwan maye barkatai a ckin al’umma, ba tare da wahala ba a cikin unguwanni da loko da sako da kan tituna da kuma kasuwanninmu, cikin farashi mai arha wanda kowa na iya sayensa.

    41. ‘Yan siyasa da ɓata gari a cikin al’umma, suna amfani da wasu daga cikin dalilan da muka bayyana halaye da ɗabi’un matasa (a sama) su samar musu da kayan maye.

    42, Rashin kwanciyar hankali a cikin iyali.

    43, Rashin tarbiyya ta addini.

    44. Sayarwa da tallatawa a kusa da makarantu da gidajen jama’a.

    Da yawansu in mayen ya sake su sai kuma su ji haushin abubuwan da suka yi a lokacin da ba su da cikakkiyar natsuwa ko hankali, musamman idan an gaya musu ire-iren abubuwan da suka yi a lokacin da suke cikin mayen.

    Kuma in ka ce wane daɗi suke ji in sun sha sai ka ji sun ce, ba wani daɗi illa dai kawai biya wa rai buƙata, kamar shan taba ne babu wani daɗi sai dai nishaɗi lokacin da kake busa hayaƙi sama.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga litttafin Mata Da Shaye-shayen Kayan Maye: Ina Mafita? Wanda Ado Ahmad Gidan Dabino MON ya wallafa.

    Don karanta Matakan Shiga Shaye-shayen Miyagun Ƙwayoyi danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Siyasa

    Siyasa

    GABATARWA

    Adabi sha kun dum ne cikin al’amuran rayuwar al’umma, kama daga abincinsu, abin sha, tufafi, kai har siyasa adabi bai bari ba, ya ratsa cikin rassan adabin nan uku, wato:Zube, Waƙa da kuma Wasan kwaikwayo.

    MA’ANAR SIYASA

    Siyasa hanya ce da mutane ke bi wajen rayuwa a haɗe, ko a tare, ko a ƙungiyance cikin manufa ɗaya. Siyasa na nufin haɗa yarjejeniya tsakanin mutane domin su zauna tare duk da maban-bantan ra’ayoyi, ƙabilu da addinai, a birane da ƙasashe.

    MA’ANAR SIYASA DAGA BAKIN MASANA

    Manzur (1978) Ya kawo asalin inda kalmar siyasa ta samo asali. Inda ya ce”Ta samo asali ne daga “sa’asa” sai ta koma “siyasa” wato ma’anarta tafiyar da shugabancin jama’a ko kuma july away kan wani al’amari ko yarda da wani abu ko jiɓintar al’umma tare da saninsu ko kuma ba su sani ba”

    Bargery (1934) Ya ce”Siyasa na nufin ko dai rangwame a farashin kowane abu, ko kuma tausayawa a cikin al’amura”

    Manzur (1978) Ya ce “Siyasa na nufin ilimi ne dake nuni da kuma gabatar da hanyoyi da manhajoji mabanbanta a cikin gida da kuma alaƙanta da al’umma a waje”.

    NAU’O’IN SIYASA

    Dangane da yadda zamani yake tafiya, haka nau’in siyasa ya dinga ratsuwa a tsakani har aka samu nau’i kamar haka:

    -Siyasar Gargajiya.

    -Siyasar Addini.

    -Siyasar Mata.

    -Siyasar Jami’a .

    -Siyasar Jam’iyya.

    Ga taƙaitataccen bayaninsu.

    * Siyasar Gargajiya: Idan aka ce “Gargajiya”wato abin da al’umma ta gada tun daga kaka da kakanni kafin wasu al’ummu su yi kutse cikinsu.

    Siyasar Gargajiya siyasa ce da aka samo ta daga addinin gargajiya, wanda wasu na ganin bauta ta gargajiya da imani da iskoki dodanni ita ce tsari na samar da shugabanci a tsakanin al’ummar Hausawa, wanda duk wani mai ƙarfi ko jarumi a wurin bauta da alaƙa da dodanni ko iskoki to shi ne jagorancin kuma shugaba, don kuwa babu wani mai iya taka shi ko mai musu da shi.

    *Siyasar Addini: Nau’in wannan siyasa ita ce wacce ta shafi addinin musulunci, wanda ake samun shugaban da hukunce-hukunce daga Alƙur’ani da Hadisi.

    *Siyasar Mata: Ƙwarai su ma mata ba a bar su a baya ba, don tun lokacin da aka haɗa kudancin Nijeriya da Arewa a shekarar 1914 mata suke taka rawar gani a siyasar jam’iyya. Ko a yanzu za mu ga a Jihar Kaduna Dr. Hajiya Hadiza Balarabe ita ce mataimakiyar Gwamnan Jihar a 2019 zuwa 2023. Haka kuma ita ce za ta yi wa zaɓaɓɓen Gwamnan wato Sanata Uba Sani a shekarar 2023 zuwa 2027.

    Haka Hajiya Aisha Binani, ita ce Waƙiliyar Majalisar Dattawa a yankin garin Adamawa, haka kuma ta fito takarar Gwamna, wanda ita ake tsammanin cin ta, sai dai abin akwai ruɗani, sai an sake fafata zaɓen Jihar.

    *Siyasar Jami’a:Irin wannan siyasar ita ce wacce ake gudanar wa a farfajiyar Jami’o’i, kuma ana gudanar da ita ne irin tsarin siyasar Damukuraɗiyya, akwai tsarin Kwansutushon da komai.

    Babban misali kuwa idan muka kalli wannan Jami’ar da muke ciki ta Jihar Kaduna (KASU) za mu ga ita kanta ana fafata siyasar a cikinta. Shugaban ɗalibai na shekarar 2021/2021 shi Abdulhamid Umar, bayan shi kuwa Abubakar Abdullahi ne ya hau a shekarar 2021/2022.

    *Mashi (1986) ya bayyana siyasar jam’iyya da cewa “Jam’iyya tana nufin wata ƙungiya mai wakiltar wani ra’ayi na neman mulkin al’umma, irin wannan ƙungiya akan same ta a ƙasa ɗaya ne, kuma sukan yawaita yadda manufofinsu suka kasance, wannan shi ne ya jawo samun hanyoyin siyasa iri-iri, wato akan sami salon siyasa na Damukuraɗiyya, wato mulkin al’umma ta hanyar abin suke buƙata, kuma suke da ikon tarfe ra’ayinsu cikin lamarin tafiyar da mulki” Wannan ke nuna siyasar jam’iyya tana nufin irin gwagwarmayar da jam’iyyan suke yi don neman kafa gwamnati da saman mulkin al’ummar ƙasa.

    A taƙaice ma iya cewa siyasar Jam’iyya dai wata ƙungiya ce da take gudanar da siyasarta a jam’iyya ɗaya da samun haɗin kai don su kayar da wata jam’iyya daban wato ta abokan hamayya.

    A ƙarƙashin wannan siyasar ta jam’iyya akwai Jamhuriyya har huɗu, inda kowacce Jamhuriyya akwai rawar Jam’iyyu da dama da suka taka rawa a ƙarƙashinta.

    *Jamhuriyyar Najeriya ta farko (1963 – 1966)

    Akwai jam’iyyu kamar su :

    AG, BYM, DP, KPP. Da sauransu

    *Jamhuriyya ta Biyu (1979 – 1983)

    Akwai jam’iyyu kamar su:

    PRP, NPP, NAP, NPN, Da sauransu.

    *Jamhuriyya ta uku (1993)

    Akwai jam’iyyu kamar su:

    SDP, NRC.

    *Jamhuriyyar Najeriya ta Hudu (1999 – yanzu)

    Akwai jam’iyyu kamar su:

    CND, JP, CNC, APC, CPC, PDP, Da sauransu.

    Yanzu za mu ɗauki ɗauki waƙa ta Jamhuriya ta farko don fito da hoton siyasa a ciki.

    WAKAR ‘YAN SAWABA GAMBO HAWAJA JOS.

    Wannan waƙa ta ƙunshi hotunan siyasa da dama kamar su: son yunƙurin canja jam’iyya yayin da aka gane zaluncinta, kamar yadda ya faɗi a baiti na 10 zuwa na 17.

    AMSHI: Allahu Taimaki NEPU Kan Azzalumai

    10. Albarkacin Manzonka zan yabi jam’iya,

    Mai son ta tunɓuke zaluman Nijeriya.

    11. Mu ne mutanan nan da munka fito biɗar,

    ‘Yanci ya samu a tsarkake Nijeriya.

    12. Ita jam’iyar NEPU ta ɗau aniya,

    Sai ta ga bayan zalumanga masha giya.

    13. Ta ɗau makamai sun fi bom har bindiga,

    Kun san su ko in faɗe su su ne gaskiya.

    14. Iggwa da bom bai magani in sun zaka,

    Wa ke da ikon dankwafe wa gaskiya.

    15. Kai fankashali shazumami ka dakata,

    Koron da ba shi da nasa sai ƙwalamar tsiya.

    16. Kai baka noma ba fatauchi ko kaɗan,

    Kuma ba sana’a sai yawan faharin tsiya.

    17. Na tabbata ɗan NEPU ba zai so ka ba,

    Tamkar ƙudan shadda ya sauka a kan miya.

    Haka daga baiti na 18 ya yabi jam’iyyar,kuma ya nuna da su za su samu nasara gami da kirari ga jam’iyyar ta NEPU har zuwa 20.

    18. Mu NEPU mu ne kainuwa bisa kan ruwa,

    Wawan da zai taka mu shi zai dulmiya.

    19. Ga NEPU dutse ba a far maka nan da nan,

    In munka far wa zalumi zai sha wuya.

    20. Mu ne tsakin tsakuwa a gun azzalumai,

    Kafin a ci mu aradu sai an sha wuya.

    Haka tun daga na 21 zuwa na 40 Ya fito da nuna addinanci ne a siyasa, don kuwa ya bayyana yadda za a tsani wanda ba musulmi ba kwata-kwata da shugabanci, don kuwa munanan halayensu da ɗabi’unsu marasa kyau.

    21. Kai turdimi jaki daƙiƙin duniya,

    Ƙaton cikin wofi na cinye haramiya.

    22. Ni zan gaya maka gaskiya in za ka ji,

    Bar sa Wali a cikin a batun dab a shi da gaskiya.

    23. Don Shehu bai ja kafiri a jikinsa ba,

    Shi sai musulmi wanda ke riƙe gaskiya.

    24. Bai je cikin hotel ba Shehu Mujaddidi,

    Kuma ba shi ƙarya bai zama da masha giya.

    25. Har yai wafati Shehu bai cuce mu ba,

    Allah Ya gafarce shi Shehu mazan biya.

    26. Ku jakunan Sheɗan ba za ku ga Shehu ba,

    Bar sanya Shehu cikin batunku na jam’iya.

    27. Kaka, uba bai fidda dan sa ga hallaka,

    In dan yace bai kama hanyar gaskiya.

    28. Kuma ga misali jalla Ya saukar mana,

    Aya a kan Kan’ana inda ya dulmiya.

    29. Kai mai kirarin martabar kaka tsaya,

    Ka tuna Hassan da Hussaini sun riƙe gaskiya.

    30. Bar taƙamar kakanka ban ga fitar ka ba,

    Kakanka baya yin hannu da baturiya.

    31. Kuma bashi cewa goro ai masa jangali,

    Shi bai kawa da Nasara ba ya shan giya.

    32. Gemunka har sajenka ba shi da martaba,

    In dai ya zam aikinka babu na gaskiya.

    33. Ɗan wane jikan wane ba ta isar maka,

    Allahu Ya ce sai kana bin gaskiya.

    34. Mai ɗaura bante in ya bayyana gaskiya,

    Ya zarce mai rawanin da ke son dulmiya.

    35. Da martabar kaka ka mulkin duniya,

    Awolowo shi kuma wa ya ba shi Firimiya?

    36. Kai gafara sa ya ishe ni ku dakata,

    Ba na gudu sai na ga goshin saniya.

    37. Sun raina hanyar Shehu sun bijire masa,

    Ba sa buƙatar lahira sai duniya.

    38. Su dai su hau mota su sauka a hil tasha,

    Ran Jumu’a ran nan suke shagalin giya.

    39. Da ya yi imani ya dubi mazan gaba,

    Da sukai sarautar duniya baki ɗaya.

    40. Ba su shuka sharran don su cuci waninsu ba,

    Su sai shirin da sukai a taimaki gaskiya.

    Haka daga 40 zuwa 58 ya suka jam’iyyar hamayya wato NPC da kuma waɗanda suke cikinta.

    46. Ba na cikin NPC ba na son shiga,

    Manyansu ba sa taimakon Nijeriya.

    47. Na raina jam’iyarsu masu abin faɗa,

    Ni na tsaya kan NEPU tutar gaskiya.

    48. Tutar da ba ta da jahili ko zalumi,

    Da baƙi da ja kore farar taurariya.

    49. In ban da wawa jahili da rashin shina,

    Wai zai bi jam’iyar da ba ta da gaskiya.

    50. Wallahi Allah zan faɗa muku ‘yan uwa,

    Talakan da ke NPC ba shi da zuciya.

    51. Daga dai kawali sai maroƙi ke shiga,

    Sai wanda zai ƙi ubansa don kwaɗayin miya.

    52. Kuma mai kuɗin da ka ganshi ya shiga tabbata,

    Ya raina nasa yana biɗar na haramiya.

    53. Ku ne talakka uba talakka uwa haka,

    Wai har da ɗan sarki kuke gama jam’iya.

    54. Kurdinku ya ruɗe ku kunyi abin faɗa,

    Don kun ki bin asalinku kun bi masha giya.

    55. Ko mai kuɗi ko malami da ya karkata,

    Allahu shawo kan sa mui masa fatiya.

    56. Asirin cikin riga jama’a na tuna,

    Zan bar uba domin ɗiyansa na gaskiya.

    57. Na ‘yanta rand don ruwan da yake ciki,

    Ba don wadansu ba wane da ya sha wuya.

    Tun daga na 89 zuwa na 117 duk yana shimfiɗa habaici da zage-zage da zambo kan ‘yan jam’iyyar adawa.

    89. Babban abin kunyar da sunka yi zan faɗa,

    Wasu tajirai suka je su gai da Firimiya.

    90. Police ya ce babban su, Alhaji dakata,

    Koma, idan kuwa ka ƙi yanzu ka sha wuya.

    91. Wani turdumi dunan amale kututtuɓi,

    Kun san shi ko in faɗe shi, gara mu sakaya.

    92. Ya tattare cuna ya gangare hel tasha,

    Ya dafe kansa yana gudu ba waiwaya.

    93. Ya manta rancen dukiyar da ya tambaya,

    Ya tuna da kwanan yari, gara ya sakaya.

    94. Im ban da jahilcinka ba ka da hankali,

    In anka cinye kuɗinka sui maka dariya.

    95. Bayan watanni ‘yan kaɗan suka tabbata,

    Kurɗinka sun kare su sa ka a jam’iya.

    96. ‘Yan NEPU don ba su ce a cinye kuɗinka ba,

    NPC ba ta biyanka wannan dukiya.

    97. Na tabbata ɗan NEPU bai ci kuɗinka ba,

    Ɗan NPC ne ya ci dukiyarka ta dulmiya.

    98. Mai son yana da sule biyar a yi mai jaka,

    Ba na saka shi cikin mutanen gaskiya.

    99. Koma Kaduna ka nemi mai maka tsibbu can,

    Kuma na ji ba shi Kaduna ya tafi Zariya.

    100. Jama’a takarda na gaba ta mantuwa,

    Na gan ta na tuna jahilin tsohon tsiya.

    101. Duk fasiƙin tsohon da bai tsare kansa ba,

    Wallahi in muka gauraya zai sha wuya.

    102. Wani ɗan farin tsoho cikinsa baƙinƙirin,

    Ya manta Allah ya ji ruɗin dukiya.

    103. Mai shekara saba’in ka gan shi da daduro,

    Me zan kira shi ku ce da shi tsohon tsiya.

    104. Tsohon da bai san Fatiha ba munafiki,

    Bakinsa na kumfa ya bakin saniya.

    105. Duka fasikin tsohon da ba zai tuba ba,

    Wallahi zai tozarta tun daga duniya.

    106. Kai danƙaro mai danne tsaba, ka ɓata,

    Sha talla doki ba ido wa zai saya.

    107. Ɗaukar macuci ban ga amfaninta ba,

    Noman kisan gero a kewaye harkiya.

    108. Yau duk mutan NPC in na ƙididdige,

    Maciya amana sai ɓarayin tunkiya.

    109. Sai wanda zai baki ya kai su cikin tasha,

    Ya gama da ‘yan sane su ɗauke dukiya.

    110. Wa ke shiga NPC ban da munafiki,

    Sai Alhajin da ya kasa ƙarasa Fatiya.

    111. Ko yai karatu in ka bi shi a hankali,

    Ka tadda imaninsa babu a zuciya.

    112. Jama’a masoya NEPU kar ku yi fargaba,

    Wallahi ƙinsu da sonsu ma faɗi gaskiya.

    113. Duk mai abin kunya ba zai shiga NEPU ba,

    Wallahi ko da ya shigo ta da sakiya.

    114. Kai kyankyaso kwaɗayinka bai fishshe ka ba,

    Koma cikin shadda, fito daga tsariya.

    115. Wani sakarai maganarsa in muka bincika,

    Muka buɗa tarihinsa sai a yi dariya.

    116. Don sai da tsohon yai shiri yai gangara,

    Sannan ya nemi shiri da shi don dukiya.

    117. Jama’ar garin muka taru dai aka lallaɓa,

    Mutuwarsa ke da wuya ya kwashe dukiya.

    Idan muka dauba, za mu ga cewa lallai a wannan waƙa an fito da wasu ƙaɗan daga cikin hoton siyasa dangane da adabi, kamar yadda muke shantalo wasu baitika mu tsatso ma’anonisu a dunƙule.

    Ga wasu halayyan ‘yan siyasa ko abin da ya shafi siyasa a wannan waƙa kamar haka:

    -Yabon jam’iyya, wato ta NEPU.

    -Kirari wa jam’iyya don janyo ra’ayin mutane.

    -Nuna Addinanci don a samu damar sukar jam’iyyar adawa.

    -Sukar jam’iyyar Adawa wato NPC

    -Zambo da zagi da habaici wa jam’iyyar adawa.

    KAMMALAWA

    Duba da yadda muka tsatso hoton siyasa a wannan waƙa ta NEPU, za a ga cewa lallai ana tsintan abubuwa da dama da suka shafi siyasa a rubutaccen adabi ko kuma adabin baka.

    MANAZARTA

    -TARIHIN SIYASARNIJERIYA,FACEBOOK GROUP.

    -Bawa S 2021


    ,Siyasa da adabi ;nazari daga wasu rubutattun labaran Hausa.Sashen harsunan Nijeriya da kimiyyar harshe Jami’ar Jahar Kaduna.

    -C.N.H.N(2006) Ƙamusun Bayero.Jami’ar Bayero Kano.

    -Waƙa a bakin mai ita1,center for nigerian languages,Bayero University,Kano.

    Danna nan don karanta Haɗuwar Harshe

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Adana Harshe (LANGUAGE PRESERVATION)

    Adana Harshe (LANGUAGE PRESERVATION)

    GABATARWA
    Harshe ya kasance muhimmin al’amari ko ginshiƙin tubalin da ya haifar da nazarin kimiyyar harshe, wato Linguistics a Turance, wanda kuma kimiyyar harshe yana da rassa guda biyu su ne: manyan rassa (macro linguistics) da kuma ƙananan rassa (micro linguistics). Idan aka waiwayo ɓangaren ilimin walwalar harshe (sociolinguistics) za a ga cewa yana ɗaya daga cikin ƙananun rassa kimiyyar harshe ne. Saboda haka wannan harshe zai yi magana ne a kan adana harshe, wato (Language Preservation) a Turance.

    MA’ANAR HARSHE

    Masana da dama sun yi ƙoƙarin bayyana ma’anar harshe da cewa ;
    Brown (1976); “Tamkar jerin ma’ana ne cikin tsarin sauti”.
    Yakasai (2012); “Wata hanya ce ta bayyana kai da kuma hulɗa tsakanin juna wadda dabbobi ba su da irin ta.

    Ilimin Walwalar Harshe (Sociolinguistics)

    Ilimin walwalar harshe wanda da Turanci ake kira da “Sociolinguistics”;
    Holmes (1971) ya bayyana ma’anar da cewa; “Fage ne nazari da kan nazarci hanyoyin da ake sarrafa harshe domin tantance kima da matsayin mutane cikin zamantakewa”.
    Yakasai (2012) cewa ya yi; “Wani ɓangare ne daga fannin nazarin harshe da kuma yadda ake sarrafa shi” (Yakasai, 2012: 24).

    Adana Harshe (Language Preservation)

    Kafin mu shiga cikin aikin yana da kyau mu san abin da ake nufi da abin da ake kira da adana harshe. Hornby A.S, (2015) ya bayyana ma’anar language preservation da cewa:
    “The act of keeping language in it original state.”
    “The degree of which language has not been changed.”

    Ma’ana:
    Wato adana harshen a nufin kula da harshe ta yadda yake tun usuli. Sannan ya ƙara cewa adana harshe wani yanayi ne na adana harshe ta yadda yake ba tare da sauyawa ba. A wannan yanayin idan ana maganar adana harshe, to ana magana ne a kan yadda ake adana wasu zantuka ko hikima ko kuma kalmomi na harshe. Wannan ɓangare ya shafi kowane irin harshe da ake da shi a duniya, to amma mu a nan za mu ɗakko batun harshen Hausa wanda shi ne harshenmu na kusa wanda muke tare da shi a kodayaushe kuma a kan shi za mu ba da misali.

    Hanyoyin Adana Harshe

    Akwai wasu hanyoyi daban-daban da ake bi don adana harshe waɗanda za su taimaka wajen ƙara fahimtar wannan batun da ake son tattaunawa. Daga cikin waɗannan hanyoyin akwai:

    • Hanyar Rubutaccen Labari
    • Hanyar waƙa ko waƙe-waƙe
    • Kafofin Sadarwa
    • Hanyar Rubutaccen Labari

    A wannan ɓangaren ana kallon yadda wasu marubuta littattafai suke amfani da wasu kalmomi ko zantuka waɗanda suke tsofaffin kalmomi ne na Hausa waɗanda suka kasance za a iya cewa sun ɓace a yanzu, amma a sanadiyyar rubuce-rubuce da aka yi suna nan ba su ɓata ba. Misali:

    “… can zuwa La’asar ya farfaɗo aka kai shi gidan mahaukata aka sa shi turu aka banƙare,” (Ruwan Bagaja shafi na 19)

    “… Sai ya ɗakko buzu ya fito bakin dabi ya kishingiɗa.” (Magana Jari Ce shafi na 49)

    “Ya tashi tsaye ya yi kirari ya ce: “Sai ni gyauro mai gani baɗi.” (Ganɗoki shafi na 1)

    Turu: Wani irin mari (mai kama da ankwa) da ake huda gungumen itace a kafa masa ƙarfe inda ake sa ƙafafuwan mahaukacin da yake neman ya gagara. (Ƙamusun Hausa 2006).
    Dabi; Rumfar da ake yi da itace da ciyawa mai kama da rufin kwano. Ko kuma farfajiya ko fafaranda. (Qamusun Hausa 2006).
    Gyauro: Amfanin gonar da ya fito ba tare da an shuka shi ba. (Ƙamusun Hausa 2006).

    Hanyar waƙa ko waƙe-waƙe

    A wannan ɓangaren ma akwai misalai da za a kawo don tabbatar da hakan:
    Jagora: Da zarar sun san kai as sarki,
    Ba su ɗegiya. (Makaɗa Ibrahim Narambaɗa)

    Jagora: Allah mun yi zaman dirshan,
    Tamkar fitila a lokon alkuki. (Aminu Ladan Abubakar Alan Waƙa)
    Ɗegiya: Bayeyeniyar abinci tsakanin maƙwabta. (Qamusun Hausa 2006).
    Alkuki: Wani ɗan rami mai kusurwa uku a jikin bangon ɗaki don ajiye fitila ko littattafai.

    Kafofin Sadarwa

    Kamar yadda aka ga misalai a baya, a nan ma za a yi ƙoƙarin kawo wasu misalai na adana harshe a kafofin sadarwa. Misalan da za su biyo a nan, za a kalli yadda tashar sadarwan nan ta Arewa24 wanda suke gudanar da shirin nan nasu mai suna Daga Titi. Misali:

    Kawalwalniya: Haske mai ƙyalli-ƙyalli kamar ruwa da mutum yake hange daga nesa wanda tsananin zafin rana yake haddasa shi.
    Holoƙo: Hadarin da ya taso da ƙarfi kuma da iska, amma kuma sai ba a yi ruwan ba.
    Safarago: Tsani (lada).
    Ƙarfanfana: Kuɗin wuri mafi ƙanƙanta. Ko kuma dauɗar aljihu.

    Dukkan waɗannan misalan idan aka lura za a ga cewa kalmomi ne da suke nema su ɓace ko kuma ma a ce sun ɓace, amma a sanadiyyar waɗannan dalilai an ga cewa suna nan a adane a cikin labarun Hausa da waƙoƙin baka na Hausa da kuma wasu daga cikin kafofin sadarwa na zamani.

    Kammalawa

    Duba da bayanan da suka gabata kama tun daga ma’anar harshe da bayani game da ma’anar ilimin walwalar harshe da kuma language preservation wato (Adana Harshe) da kuma misalan da suka bayyana a cikin aikin, an fahimci cewa lallai wannan fanni da adana harshe ba ƙashin yarwa ba ne.

    MANAZARTA

    Brown, P. (1976) : Language Society. Cambridge Unversity press.
    Holmes J. And Pride J.B (1971) : Sociolinguistics, Penguim Book Ltd.
    Hornby A.S, (2015) Oxford Advanced Learner’s Dictionary Of Current English 9th Edition. Oxford University Press. OUP.
    Qamusun Hausa, (2006), Na Jami’ar Bayero Kano. Cibiyar Nazarin Harsunan Nigeria da kiniyar Harshe Kano.
    Yakasai (2012), Jagoran Ilimin Walwalar Harshe. Garkuwa Media Services LTD Sokoto Nigeria.

    07065994177,

    2025.

    Don karanta Mai Jin Harshe Ɗaya danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Hukunci A Kan Sallar Juma’a Idan Ta Yi Karo Da Ranar Idi

    Hukunci A Kan Sallar Juma’a Idan Ta Yi Karo Da Ranar Idi

    GABATARWA:
    Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jinƙai. Malamai na fiƙihu suna da saɓani a kan wannan mas’ ala kuma suna da ra’ ayi guda huɗu a kai wanda bayanin su zai zo kamar haka. Allah ya ba mu ikon faɗin gaskiya da kuma ikon aiki da ita.

    RA’AYI NA FARKO:

    Ra’ayi na farko a kan wannan mas’alar suna cewa idan ranar idi ta faɗo daidai da ranar Juma’a dole ne a yi Sallar Juma’ a kuma wajibi ne a yi ta a kan lokacin ta ko da kuwa mutum ya yi sallar idi ko bai yi ba. Kuma ba a ɗaukewa limami da masu salla ba. Wannan shi ne matsayar makarantar Hannafiyya, Malikiyya da Zahiriyya. Sannan ibni Kudama a littafinsa wato “Almughni” ya danganta wannan ra’ayi ga mafi yawan malaman fiƙihu.

    Har Wala yau, ibni Rushd ya ambata a cikin littafin sa Bidayatul Mujtahidâ
    cewa hujjar su a kan wannan ra’ayi ita ce faɗin Allah (SWT) a cikin suratul
    Jumu’a:

    Ya ku waɗanda suka yi imani idan an yi kira zuwa ga salla a ranar Juma’a to ku yi hanzari kuma ku bar harkar cinikayya, yin hakan shi ne mafi alkhairi a gare ku in kun kasance kun sani.

    Haka kuma al’amarin wajibcin sallar Juma’ a yake a cikin littafin hadisin Bukhari da Muslim da ma wasu littattafan hadisai na sunnah. Suka ƙara da cewa sallar Juma’a wajibi ce saboda haka sallar idi kaɗai ba ta ɗauke ta kamar yadda ita ma Juma’ a ba ta ɗauke IDI. Malam Ibni Hazm acikin littaffinsa mai suna “al-Muhallaa” yana cewa idan ranar IDI ta yi karo da ranar Juma’ a to mutum zai fara yin sallar IDI ne farko sannan Juma’a.

    Ya ƙara da cewa yin wannan dole ne kuma babu ƙwaƙƙwarar hujja na rashin aikata hakan. Ibni Hazm ya ƙara da cewa ita Sallar Juma’a wajibi ce amma ita kuma sallar IDI nafila ce saboda haka ba a barin wajibci don nafila. Daɗin daɗawa, ibni Hazm ya ƙara da cewa al’amarin Juma’a da IDI tamkar al’amarin IDI da sallar azahar ce a kowace rana bayan ranar Juma’a. Akan haka, idan dai har za a buƙaci yin sallar Azahar a ranar IDI, to haka ma sallar Juma’a wanda ta zama (sallar) farillar ranar Juma’a za a buƙaci
    gudanar da ita.

    RA’AYI NA BIYU:

    Masu ra’ayi na biyu suna ganin cewa sallar Juma’a a wannan yanayi tana wajabta ne ga mazauna gari da kuma waɗanda ba su da nisa sosai da masallaci. Amma ga masu wucewa ko waɗanda ke nesa da masallaci(waɗanda suke tafiya mai yawa kafin su zo masallaci), idan suka sallaci IDI ya wadartar da su ba sai sun dawo sallar Juma’ a ba. Sai dai shi limami wajibi ne ya dawo ya yi sallar Juma’a. Wannan shi ne ra’ayin Imam ash-Shafi’ee.

    Haka Imam An-Nawawi ya danganta wannan ga mafi yawan malaman musulunci a cikin littafin sa mai suna “AlMajmou”. Hujjar sa ita ce faɗin Sahabi Abu-Ubaid kamar yadda aka ruwaito a cikin Muwatta na Imam Malik (Allah ya ƙara masa yarda) cewa (Abu-Ubaid) na yi sallah a bayan Usman bin Affan wani lokaci a inda ya fara da gabatar da Salla sannan ya yi huɗuba a ciki yake cewa: “a wannan rana kuna da IDI guda biyu a rana ɗaya, saboda haka mutanen da suka zo daga yankin al-Awaali (wani ƙauye a cikin yankin Madina) duk mai so ya tsaya sallar Juma’a zai iya tsayawa. Wanda kuma yake so ya koma gida zai iya tafiya. Wannan umarni na ne”.

    Haka Imam Annawawi ya dangata wannan ga Bukhari. Imam As-Shirazi yake cewa “ ana karɓar uzurin mutanen da zuwa sallar Juma’a ta tsananta a garesu, saboda haka buƙatar mutane su dawo zuwa sallar Juma’a daga ƙauyuka bayan sun halarci sallar IDI zai tsananta matuƙar tsanantawa a garesu.

    RA’AYI NA UKU:

    Masu ra’ayi na uku suna cewa duk wanda ya halarci sallar IDI to an yi masa afuwa daga halartar sallar Juma’a ba tare da la’akari da wurin zaman sa ba, haka yake ga limami da masu halarta. Amma duk da haka, shi limami zai gabatar da sallar Juma’ a ga waɗanda suke da buƙatar halarta da kuma waɗanda ba su sami halartar sallar IDI ba.
    Karin bayani: A nan ba ana nufin an ɗauke sallar AZAHAR ba a saboda sallar Juma’a.
    Wannan ra’ayi, saboda bayyana hujjoji a buɗe ya zama mafi ƙarfi a dukkanin ra’ayoyi a kan wannan mas’ala.

    Haka kuma wannan shi ne ra’ayin Imam Ahmad ɗan Hambal kuma haka shaykhul Islam Ibn Taymiyyah yake danganta wannan ra’ayi ga wasu sahabbai irin su Umar ɗan khattab, Usman ɗan Affan, Abudllahi ɗan Mas’ud, Abdullahi ɗan Abbas da sauransu. Kuma ya ƙara da cewa babu wani ilimi na saɓani da suka yi a kan wannan mas’ala. Haka kuma wannan
    shi ne ra’ayi na mafi akasarin malaman hadisi.

    Hujja a kan wannan shi ne hadisin Zaid ɗan Arƙam wanda yace: Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya yi sallar IDI a ranar Juma’a sai ya ba da dama ga halartar sallar Juma’a inda yace: “ duk mai son ya yi salla (ma’ana halartar sallar Juma’a) to ya yi”. Wannan hadisin an rawaito shi daga Imam Ahmad ɗan Hambal da kuma litattafan Sunani Dawud da Tirmizi kuma Ibn Khuzaima ya inganta shi.

    Haka kuma, a cikin Sunan Abu Dawud, Abu Huraira ya rawaito cewa Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce: “ a wannan rana kuna da IDI guda biyu saboda haka ga duk wanda ya so, sallar IDI ta wadatar masa amma mu kam za mu yi sallar Juma’a”.
    Shaykhul Islam Ibn Taymiyyah (rahimahullah) ya ƙara da cewa “ idan mutum ya sami halartar sallar IDI to ya riga ya samu manufar da ake so a samu ta jam’i a sallar Juma’a, saboda haka sallar Azahar kaɗai zai yi idan bai halarci sallar Juma’a ba. Sallar Azahar zai gabatar akan lokacin ta.

    Sallar IDIn sa ta wadatar masa cimma manufar sallar Juma’a. Masu wannan ra’ayi suka ƙara da cewa farlanta sallar Juma’a a wannan yanayi zai sanya tsanani da takura ga mutane kuma zai rusa manufar IDI wanda dalilin yin sa shi ne don nuna farin ciki da nishaɗi. Haka, idan mutane aka tirke su daga jin daɗin lokutan su (domin halartar sallar
    Juma’a) a nan IDI zai janyo ƙunci kuma ma’anar sa za ta kau.

    RA’AYI NA HUƊU:

    A wannan ra’ayi wanda shi ne fahimtar Ata’ ibn Abi Rabah da kuma ɗaya daga cikin sahabbai wato Ibn Zubair suna ganin cewa duk wanda ya hallarci sallar IDI to an yi masa rangwame ba ya buƙatar ya sallaci kowace salla har sai sallar La’asar, ma’ana ba zai yi sallar Juma’a da sallar Azahar ba. An ruwaito wannan cewa shi ne ra’ayin Imam Ahmad Ibn Hanbal.

    An ruwaito Abdullah ibn az-Zubair radiyallahu anhu yana cewa “ IDI guda biyu (IDIn Sallar da IDIn Juma’a) sun zo a rana ɗaya, sai (Abdullah ibn Azzubair ) ya yi salla raka’a biyu da safe da wuri kuma bai ƙara yin salla ba har sai La’asar. Dangane da kore wannan ra’ayi na huɗu, Imam al-Khattabi rahimahullah ya ce: “irin wancanenka aiki na Ibn Zubair ba za a iya fahimtar sa ba sai dai ta hanyar fahimtar masu ra’ayin yin sallar Juma’a gabanin zawali (Zawali shi ne farkon lokacin Azahar yayin da rana ke fara matsawa daga tsakiya). Don haka Ibn az-Zubair sallar Juma’a kawai zai yi a maimakon IDI da Azahar”

    Daɗin dadawa, shi Ata Ibn abi Raba wanda shi ne ya ruwaito aikin Ibn azzubair yace: a lokacin Juma’a mun taru domin salla amma shi (wato Ibn Azzubair) ya ƙi ya fito domin ya limance mu saboda haka sai muka yi salla daban-daban” wannan yana nuna cewa sallar Azahar suka yi kuma akwai yiyuwar Ibn az-zubair shi ma ya yi sallar Azahar a gidan sa. Allah shi ne masani

    TAƘAITACCEN NAZARI MAI GAMSARWA NA MALAMAN FIƘIHU DA
    MAZAHABOBI A KAN MAS’ALAR SALLAR JUMA’A DA SALLAR IDI IDAN
    SUKA HAƊU A RANA GUDA WATO RANAR JUMA’A.
    DAGA ALKALAMIN HUSAIN INUWA MAITAKARI
    USAINISKIMA@GMAIL.COM
    +2349042152353

    Danna nan don karanta Yaushe Ne Kwanakin Layya Suke Ƙarewa?

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yaushe Ne Kwanakin Layya Suke Ƙarewa?

    Yaushe Ne Kwanakin Layya Suke Ƙarewa?

    Haƙiƙa kwanakin Layya suna ƙarewa ne bayan kwana Uku (3) waɗanda ake kira Ayyamul Tashriq (Kwanakin kekketa nama) su waɗannan kwanaki Uku (3) na sallah, kwanaki ne na ci da sha da kuma ambaton Allah SWT (yawan ambaton Allah). Wasa ya halatta a cikin waɗannan kwanaki, amma banda nau’in wasan da ya ƙunshi saɓawa Allah.

    Sannan ana yawaita kai ziyara ga ‘yan Uwa da abokan arziki da kuma marasa lafiya na gida da na asibiti. Sannan yana wajaba ga lyaye su lura da ‘ya’yansu (Musamman Mata) yayin Hidimar Sallah, Yaran sukan sa matsattsun sutura da zai fitar da surar jikinsu gaba ɗaya, ko kuma sutura shara-shara da zai nuna duk wani abinda ake ɓoyewa da makamantansu, wannan duk bai halatta ba.

    Kada ‘ya’yanmu su kasance irin waɗanda Manzon Allah SAW yake siffanta su da cewa: “wasu Mata ne da za su zo a ƙarshen zamani, wanda ban gansu ba, amma ga siffarsu: Mata ne suna tafiya a jikinsu akwai tufafi amma tsirara suke, Karkatattu masu karkatarwa; Kan su ya yi kama da tozon raƙumi, Ku tsine musu domin su daman tsinannu ne”. Don haka ya kamata lyaye su kula sosai don sauke amanar Allah da yake kansu na tarbiyyar ‘ya’yansu. Allah ya ba mu ikon kulawa.
    Alhamdulillah.

    WAƊANDA BA SU SAMI DAMAR LAYYA BA

    Lallai Manzon Allah SAW ya yi layya da raguna biyu. Ragon farko ya yanka da niyyar shi da lyalansa, rago na biyu kuma saboda tsabar soyayyar da yake mana mu Aľummarsa yace: wannan ya yanka da niyyan layya ga duk wani daga cikin Aľummarsa da ya yi ƙoƙarin neman Abin Layya amma ya gagara.

    To jama’a duk wanda bai samu damar yin layya ba fiyayyen Halitta, farin jakada Annabi Muhammad SAW ya yi masa, don haka kada ya tada hankali kuma kada ya yi baƙin ciki.
    Da fatan Allah ya karɓawa waɗanda suka samu damar Layya waɗanda ba su samu ba Allah ya hore musu. Daga ƙarshe muna roƙon Allah gafarta mana zunuban mu baki ɗaya.

    Don karanta Abubuwan Da Suka Shafi Idi danna nan 

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mai Jin Harshe Ɗaya

    Mai Jin Harshe Ɗaya

    GABATARWA
    A duk lokacin da aka ce an sami wasu al’umma kuma mazauna yanki ɗaya, sannan kuma masu magana da harshe ɗaya, dole ne a samu cewa lallai akwai wani harshe guda da zai zamo zakaran da yake cara a tsakanin wannan rukuni na al’umma, wato harshe guda ɗaya da ake amfani da shi a wannan yanki.

    MA’ANAR HARSHE (LANGUAGE)

    A taƙaice dangane da ma’ana, an bayyana harshe da cewa ;
    “Wata hanya ce ta bayyana kai da kuma hulɗa a tsakanin mutane wadda dabbobi ba su da irinta”. Hickey; (1956).

    “Hanya ce ta amfani da ƙwayoyin sauti a tsai da kalmomi, su kuma kalmomin su bayar da jimla”.Yakasai (2012) ;

    MA’ANAR MONOLINGUALISM

    Ita wannan kalma haɗaka ce ta wasu kalmomi mabambanta, wato;
    Mono- abu guda ɗaya.
    Lingua- harshe (language).
    Idan kuma aka ce monolingual ana nufin mutum mai jin magana da harshe guda ɗaya.
    Monolingualism kuwa; Oxford :
    “Damar yin amfani da harshe guda ɗaya”.
    “Yin magana ko kuma rubutu da harshe guda ɗaya”.
    Kenan a taƙaice za a iya cewa “monolingualism” yana nufin yin hulɗa ko mu’amala da wani harshe guda ɗaya a cikin al’umma.

    Haƙiƙa an fi samun irin wannan al’amari na magana ko hulɗa da harshe ɗaya ne a cikin ƙauyuka ko karkara, wanda hakan ba ya rasa nasaba da rashin samun cunkoson harsuna mabambanta a wannan yankin. Ba lallai sai harshen Hausa ne kaɗai za a iya samun “monolingualism” ba.

    Alal misali Fillanci da Yarbanci da Inyamuranci da Kanuri da Itiyap da Nupe da dai sauran harsuna da muke da su, za a samu mutum mai jin wannan harshen guda ɗaya daga cikin jerin waɗannan harsunan, idan ba da harshen ba to babu wani harshe da yake ji kuma yake iya mu’amala da shi, in ba da harshensa ba sai dai a haƙura da mu’amala.

    IRE-IREN MONOLINGUALISM

    Spender (1980) ya kawo ire-iren monolingualism kamar haka ;
    Mai rinjaye (majority).
    Mara rinjaye (minority).

    MAI RINJAYE (MAJORITY)

    Wannan yana nufin dukkan wani yanki ko ƙasa go gari da mafiya al’ummar wannan gari ke amfani da shi. A wannan jawabin, za mu iya kallon ƙasarmu Nijeriya a matsayin majority (masu rinjaye), ta la’akari da zarrar da harshen Hausa ya yi a ƙasar. Sahihin zance ya nuna cewa hatta waɗanda ba harshensu ba ne, su ma sun saje harshen ya zama tamkar nasu a sanadiyyar amfani da shi da suke yi a dukkan al’amuransu.

    A wani ɓangaren ma, za a ga cewa mutane da yawa suna da nasu harshen da suka gada, amma kuma ba sa jin wannan harshen nasu na asali, a dalillin haka ne ma sai su koma suna magana da harshen Hausa kaɗai a matsayin harshensu. Imo da Enugu da kuma Ribas, dukkansu garuruwa ne ko yankuna ne na Inyamurai, za mu ga cewa a wannan yankunan ba su da wani harshe da ya fi Inyamuranci tasiri a yankin.

    A garuruwa kuwa kamar irin su Osun da Lagos da kuma Ogun, su ma suna da nasu harshen na Yarbanci da suke gudanar da al’amuransu, kuma da wannan harshe suke magana suke kuma fahimtar juna, domin babu wani harshe da y wuce Yarbanci a gare su.

    Haka kuma idan muka zo garuruwa kamar su Katsina da Kano Zamfara da Zariya, za mu ga cewa ba su da wani harshe da ya wuce harshen Hausa. Da wannan ne ake ganin cewa waɗannan jihohi za a iya kiran su da masu rinjaye a sanadiyyar yawan masu amfani da harshen da ke wannan yankuna ko garuruwa.

    MARA RINJAYE (MINORITY)

    Wannan shi ne ake samun wasu al’umma da adadinsu bai taka kara ya karya ba idan aka kalli yanayin harshen da kuma yawan adadin masu magana mu’amala da shi.

    ILLAR AMFANI DA HARSHE ƊAYA

    Amfani da harshe guda ɗaya yana da wasu illoli da yake haifarwa a tsakanin al’umma;
    Tattalin Arziki/cinikayya: Ana samun koma-baya idan aka ce za a yi ciniki tsakanin ƙasa da ƙasa ko gari da gari a tsakanin al’umma.
    Ilimi: Ana samun nuƙusani sosai idan aka ce ana amfani da harshe guda ɗaya a fagen ilimi, domin kuwa akan sami rashin fahimta.

    ALFANUN AMFANI DA HARSHE ƊAYA

    • Samar da haɗin kai da jituwa a tsakanin al’umma.
    • Samun daidaito a al’amuran rayuwa.

    KAMMALAWA

    Bayanai sun gabata tun daga ma’anar harshe da kuma ma’anar kalmar monolingualism, da kuma bayani game da ire-iren monolingualism da bayani game da alfanunsa da illarsa ga al’umma, mun fahimci cewa lallai ilimin walwalar harshe abu ne mai muhimmanci a fagen harshe.

    MANAZARTA

    Spender, D. (1980) ; Man Made Language, London Rutledge Kegan Paul.

    Raymond Hickey(1956), English Linguistics Language Meaning and Use.

    Hornby A.S, (2015) Oxford Advanced Learner’s Dictionary Of Current English 9th Edition. Oxford University Press. OUP.

    MUHAMMAD SAHAL ALIYU

    07065994177

    2025.

    Don karanta Haɗuwar Harshe (Language Contact) danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Abubuwan Da Suka Shafi Idi

    Abubuwan Da Suka Shafi Idi

    Da farko dai ana son mutanen da za su je Idi su zamto sun tsabtace jikinsu sannan su sanya sababbin tufafi ko kuma mafi kyau daga cikin kaya, sannan su tafi a ƙasa (ba a kan abin hawa ba). Domin sayyidina Aliyu (R.A) yace: “Yana daga cikin sunnah tafiya idi a ƙasa”. Tirmizi

    Game da mata kuma an halarta musu zuwa idi saboda Hadisin Ummu adiyya (R.A) tace: Manzon Allah SAW ya kasance yana umurtar mu da zuwa Idi mu da bayinmu da masu haila a cikin mu domin mu halarci wannan alheri da kuma addu’ar Musulmai, amma masu haila an umurce su da su nisanci wurin da ake yin sallah. Bukhari da Muslim.

    Saboda haka ya halatta mata su je idi, amma fa su ji tsoron Allah domin neman dacewa.
    sannan ana buƙatar mai zuwa idi ya rinƙa yin kabarbari da hailala tare da Hamdala Kamar haka:

    ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR, LA ILAHA ILLALLAHU, ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR WA LILLAHIL HAMDU.

    Ba a son ana tafiya Idi ana Surutu. An tambayi Anas Bn Malik (R.A) yaya kuke aikatawa lokacin Manzon Allah (SAW)? Sai yace: “Mai ambaton Allah ba a hana shi; sannan mai kabbara na kabbara ba mai hana shi”. Bukhari.

    Bayan haka, ana son idan an idar da Sallah mutum ya saurari Huɗuba (ba wai daga idar da sallah mutum ya tafi gida ba). Sannan kuma ana so a cigaba da wannan zikiri da kabarbari har tsawon kwana Uku (3) saboda faɗin Manzon Allah SAW: “Kwanaki uku na sallah kwanaki ne na ci, da sha, da kuma ambaton Allah (SWT)” Wanda ya je filin Idi ba zai yi nafila ba saboda faɗin Abdullahi Ɗan Umar yace Manzon Allah SAW da Sayyidina Abubakar, da Sayyidina Umar suna yin sallar Idi kafin Huɗuba. Bukhari da Muslim.

    Sannan kuma ya tabbata a Hadisi Manzon Allah SAW yana yin Sallar Idi raka’a biyu (2). Sannan ba ya yin wata sallah kafin ko bayan Sallar idi. A nan za mu fahimci cewa; ba a sallar Nafila kafin idi ko kuma bayanta.

    HANI GA YANKE FARCE KO CIRE GASHI GA WANDA ZAI Yl LAYYA

    Ana son wanda zai yi layya kada ya gyara gashinsa da kuma yanke farcensa yayin da watan sallah (Dhul-Hajj) ya kama domin an samu Hadisi daga Manzon Allah SAW yace: “Idan kuka ga watan sallah ya kama (Dhul-Hajj) sannan ɗayanku zai yi layya to kada ya cire gashin kansa” Wannan Umurni ne shi ma yana daga cikin nau’in ibada.

    Domin karanta Abin Da Ya Shafi Yanka danna nan

    Edita@rumasau-kallamu