Tag: kano

  • Tunawa Da Yaƙin Santolo

    Tunawa Da Yaƙin Santolo

    (YAKI DON TABBATAR DA MUSULUNCI A ƘASAR HAUSA)

    9/12/2017

    DAGA SADIQ TUKUR GWARZO

    08060869978

    Haƙiƙa, idan har tarihin ƙasar Hausa ba zai cika ba har sai an kalli tarihin Kano, to haka ma tarihin Kano da zuwan musulunci ƙasar Kano ba zai taɓa kammaluwa ba har sai an sanya wani yanki daga yaƙin Santolo. Santolo tsohuwar daular Hausawa ce, tsohuwar masarauta ce wadda salsalar ta take tuƙewa da salsalar asalin Hausawa.

    A cikin zantuka masu yawa na maruwaitan tarihin Kano, an gamsu cewar wani mai suna ‘Dala’ shi ne wanda ya soma zama a kan dutsen da a yau ake kira da suna ‘Dala’, a wajajen shekarar 700 miladiyya, tun a wancan lokacin kuma wasu na ganin akwai mutane da ke rayuwa a kan wani dutse mai suna ‘santolo’, wanda shi ma da alama, sunan ya samo asali ne daga mutumin da ya soma rayuwa a saman dutsen.

    Zuwa yanzu, babu takamaimen tarihin asalin kafuwar Santolo, sannan kuma yana da wuya a iya lissafa tsawon zamanin da mutane suka soma rayuwa a kan dutsen santolo, to amma tarihi ya auna cewar mazauna Santolo da na Dala da ke Kano suna da alaƙa da juna.

    Alaƙar kuwa na iya zamowa ta jinsi, ko ta addini ko kuma ta duka gaba ɗaya, tunda har ma an samu cewa a can baya alakar kasuwanci na shiga tsakanin mazauna waɗannan duwatsu biyu. Wasu kuma na ganin Santolo ta yi shaharar da har daga Borno ake zuwa yin fatauci a koma, to amma daga baya sai Allah ya fifita yankin Dala sama da ita Santolon.

    Babban abin tunawa dangane da Santolo shi ne ‘Yaƙin Santolo’ wanda aka gwabza tsakanin Sarkin Kano Ali Yaji ɗan Tsamiya da kuma shugaban Santolo mai laƙabin ‘Magajin Santolo’ wanda ya karɓi baƙuncin takwaransa ‘Magajin Dala’ bayan sarkin Kano ma goma sha ɗaya Ali Yaji ɗan Tsamiya ya karya tsumburbura da ke saman dutsen Dala, sannan ya kori Magajin Dala da mutanen sa.

    Tarihi ya nuna cewa asalin garin Kano ya faro ne daga dutsen dala, inda ake bautar gunkin wata aljanna mai suna ‘tsumburbura’ da ke saman dutsen, amma daga baya maɗatai ta kafu, har Bagauda ya zo ya soma sarautar ɗaukacin yankunan maɗatai da na yankin Dala, waɗanda suka haɗe da sunan Kano.

    Haka kuma, tsawon zamani a Kano babu addinin musulunci, daga masu bautar tsunburbura ƙarƙashin ikon magajin Dala (wanda ya yi gadon Barbushe) sai kuma maguzawa waɗanda ba sa bautar komai irin su Bagauda da salsalarsa da ke sarautar Kano.

    A haka Kano ta taho har aka zo kan mulkin Sarki Ali yaji ɗan Tsamiya a wuraren shekara ta 1349-1385 miladiyya, wanda ya karɓi baƙuncin ƙabilar fulani Wangarawa daga ƙasar Mali, waɗanda suka kawo musulunci zuwa garin kamar yadda Marigayi Maje Ahmad Gwangwazo ya faɗa a littafinsa da ya yi magana akan tarihin Kano da tarihin zuwan wangarawa birnin.

    To, bayan sarki Ali Yaji ya karɓi addinin musulunci, sai kuma ya jagoranci karya gunkin tsunburbura tare da umartar masu bauta masa su dawo musulunci, amma sai wasun su suka ce sam-sam ba za su bar addinin kaka-da-kakannin su ba su yi addinin dungure, don haka sai suka gudu izuwa Santolo domin cigaba da bautar da suka saba.

    Ga abinda ya zo a littafin Kano Chronicle game da wannan yaƙi:-

    Sarki ya umurci dukkan garururuwan Kanawa su yi salla, sai suka yi. Ya gina masallaci mai-kusurwa huɗu a ƙarƙashin itaciyar da muka ambata a baya, suna salla a cikinsa waƙati biyar, suna komawa gidajensu. Shi ko, Sarkin Gazarzawa yakan zo da jama’arsa, suna yin najasa suna shafe dukan masallaci da ita. Saboda wannan aka sa Ɗan-buje ya riƙa gewaya masallaci da dukan makamai iri iri tun daga lisha har hudowar alfijr, yana kururuwa.

    Kai duk da haka suka yaudare shi da mutanensa, waɗansu suka bi maganar arna, shi da sauran jama’a suka ƙi. Ba su daina najasa cikin masallaci ba, har Sheshe da Famore suka ce, “Babu maganin waɗannan kafirai sai roƙon Allah.” Sauran suka ce, “Hakanan ne.” Sa’an nan suka taru cikin masallaci daren Talata, tun daga magariba har hudowar rana suna addu’a a kan kafiran. Sa’an nan suka fito suka koma gidajensu suna masu rauni.

    A cikin wannan rana Allah ya karɓi roƙonsu, ya makantad da idanun babbansu, da kuma dukan wanda yake yin wannan aiki ya makance, duk da matansu. Daga nan sai sauran kafirai sukaji tsoro. Sa’an nan Yaji ya tuɓe babbansu daga sarautarsa, ya ce masa, “Kai ne Sarkin Makafi.”

    An ce a cikin zamanin Yaji ne Sarkin Dabi da Sarkin Daf da Sarkin Gano suka zo da dawaki cikin wannan gari, amma wannan zance ba shi da ƙarfi. Bayan haka sai Sarkin Kano Yaji ya ce da Wangarawa,”Ina so ku taimake ni da addu’a domin in rinjayi Santolo, idan na rinjaye ta dukan garuruwa za su bi ni, domin ita ce ƙusar ƙasashen Kudu. Suka ce, “To, ma taimake ka da addu’a amma ba za mu yi addu’ar ba sai a bakin ramin ganuwarta.

    Sa’an nan Sarki ya fita tare da Wangarawa zuwa Santolo, mayaƙan da ke tare da shi mutum ɗari da goma sha ɗaya, hamsin na fuskar Wangarawa, sittin na fuskar Sarki. Na farko daga cikin jarumawansa: Jarmai Gobara-daga-sama, da Jakada Kwalo, da Ragamar-giwa, da Makama Butaci, da Madawaki Kuamna, da Barde Shege, da Sarkin Zaura Gamaji, da Dan-buram Gantaroro, da Ɗan-makoyo Dagazau, da Galadima Tuntu, da Sarkin Sirdi Maguri, da Gauji, da Garuji da Tankarau, da Kargage, da Karfashi, da Kutunku, da Toro da Kamfashe, da Gwauron-giwa shine

    Galadima, da Zaki, da Bambauri, da waɗansu na Cikon sittin. Yayin da Suka kai Santolo, sarki ya zauna a Duji (Sunan mutum ne.) Da duhun dare ya tashi ya tafi tare da Wangarawa zuwa Santolo, suna kewaye ta suna yi mata addua har hudowar alfijir, sa’an nan suka komo sansani. Sa ad da rana ta hudo suka taso zuwa gare ta da niyyar yaƙi Mutanen Santolo suka fita suka tare su a sarari, suka soma yaƙi tun daga hudowar rana har faɗuwa ta ba wanda ya rinjayi wani.

    Kanawa suka koma Duji, mutanen Santolo suka koma gida. Sarkin Kano kuwa ya yi baƙin ciki. Famore ya ce, “kada ka yi bakin ciki, ma rinjaye Su in Allah ya so.” Sarkin Kano ya yi farin ciki saboda wannan magana. Daga nan Ƙosa bawan Sarkl, yace “Ya Ubangijina, ni na san asirinta. Akwai waɗansu mutum takwas cikinta, in ba a kashe su ba ba wanda zai iya shiga ramin ganuwarta”.

    Famore ya ce, Ka san sunan mutanen nan?”  Ƙosa Ya ce, “I na san sunan su”. Sai Famore yace, “Kaƙa sunayansu?” sai ya ce, “Sunan babbansu Hambari, da kuma Goshin-Ɓauna da Ka-fi-wuta, da Gugan-ƙarfe, da Gandar-giwa, da Hamburkin-toka da Zangada-kere, da Gumbar wake” Goje yace, “Idan na ga Hambare na kashe shi in Allah ya so”.

    Sa’ad da alfijir ya hudo Sarkin Kano ya fita tare da rundunarsa, zuwa dutsen Santolo da mashi a hannunsa, yana mai daurariyyar fuska, GoJe yana gaban sa, Zaite yana damar sa, Famore yana hagun sa, Sheshe yana bayansa, sauran Wangarawa da Kanawa suna binsa.

    Sa’ad da suka iso Santolo dukan kafirai suka fito. Da Goje ya ga Hambare sai ya zage dantsan sa ya zabura zuwa gareshi, dukan kafirai Suka zaburo wa Goje, sai ya yi musu tsawa suka watse. Sa’ad da ya kai wurin Hambare ya soke shi da mashi, Hambare kuma ya ribce wuyansa ya fizgo shi daga kan doki, sai Goje ya fid da ‘ƴar wuƙa ya soke shi da ita a ciki, ya mutu.

    Daga nan ya hau dokinsa ya shiga cikin ganuwar Santolo, Kanawa suka bi shi suka ci birnin dukkansa. Sarki ya yi umurni a yanka dukan wanda aka samu a cikinta, Sai mata da ƙananan yara. Goje kuma ya shiga cikin gunkinsu tare da Kosa da Gurgu, suka sami kuge da ƙaho biyu da barandami da mari.

    Goje ya ɗauki kugen da ƙahon nan biyu, Kosa ya ɗauki barandamı da mari, Gurgu ya ɗauki mari. Yaji ya zauna a cikinta kwana bakwai, ya rushe ta sarai, ta zama babu gini ko itace. Bayan wannan ya komo garinsa, ya ce da Goje, “Faɗi dukan abin da kake so, na ba ka. Goje yace “ba ni son kome sai ka naɗa mini sarautar Madawakin Kano”.

    Sarkin Kano ya ce. “Kai ne Madawakin Kano. Ya tube Madawaki Gasatoro, ya fita ya gina gida a gawo; saboda haka aka Kira shi da suna Madawakin Gawo, domin a rarrabe tsakaninsu. Dutsen Santolo gagarumi ne, faffaɗa da doro, tsayinsa ya tafi kamar hawan bene daga baya, daga gabansa kuwa goshi ya yi mai faɗi da santsi, tsakiyarsa yana da faɗi har ma akwai koguna da aka ce dabbobin daji misalin su kyarkeci, dila da macizai na rayuwa a ciki.

    Ko da yake, ba mu ji sunan gunki da aljanar da aka ce akwai a saman dutsen santolo ba, amma har yanzu mutanen da ke zagaye da wurin sun kiyaye cewar kakanninsu sun ba su labarin cewar a zamanin da, ana taruwa a hau kan wannan dutse don neman wata biyan buƙata. Sannan kuma akwai wata rijiya zuzzurfa da ke saman dutsen mai suna ‘Rijiyar Giɗaɗo’, wadda akan hana mutane zuwa kusa da ita saboda kuɓuta daga ƙwanƙwaman da ke wurin masu halaka mutane.

    Zuwa yanzu garin santolo ya kasu biyu, akwai sabon garin santolo wanda Kanawa (ƙabilar Hausawa) ke ciki, sai kuma santolon fulani, amma dukkan su suna ƙarƙashin ikon dagaci mai suna Santolo Da’u. Haka kuma dutsen yana nan a tsakiyar ƙauyukan sabon garin santolo, santolon fulani, Madawa, Koɗe, kyarmawa, da Tsakuwa waɗanda dukkanin su suke cikin gundumar Dawakin Kudu ta Jihar Kano.

    Danna nan don karanta Yadda Asalin Kishi Yake

    Edita@rumasau-kallamu

  • Nazarin Rayuwar Adabin Kasuwar Kano

    Nazarin Rayuwar Adabin Kasuwar Kano

    Balaga: 1990 zuwa 1995

    Nazarin rayuwar Adabin Kasuwar Kano a zamanin da muka kira na balaga ya fito mana da siffofi mabambanta. Da farko dai lokaci ne da littattafan da suka samu wanzuwa daga shekarar 1984 suka samu karɓuwa tsakanin makaranta da masu buga littatafan da kuma masu sayar da su.

    A daidai wannan zamani ne na shekarar 1990 zuwa 1995 za a ce Adabin Kasuwar Kano ya shiga tashen balaga, marubutan da suka yi suna da karɓuwa a tsawon shekaru, suka bayyana. Cikin irin waɗannan marubuta akwai Ɗan Azumi Baba Cheɗiyar ‘Yan Gurasa, wanda ya wallafa littatafai guda 9 a cikin wannan tsakani da kuma Aminu Abdu Na’inna da ya fitar da littatafai guda 6.

    Akwai kuma irin su Ado Ahmad Gidan Dabino da Bala Anas Babinlata da Badamasi S. Burji da suka wallafa littattafai 4 kowanensu, haka kuma akwai marubuta irin su Balaraba Ramat da Yusuf Lawan Gwazaye da Alkhamees Bature da suka fitar da littattafai bibiyu kowane. Saura kuwa, irin su Ibrahim Mandawari da Ibrahim Sheme da Bashir Sanda, kowane ya fitar da littafi guda.

    A ɓangaren mata kuwa, a wannan lokaci ne aka sami fitowar manyan marubuta mata da suka yi tashe a cikin wannan harka da daɗewa, marubuta irin su Bilkisu A. Funtua da Hadiza S. Aliyu da Hawwa Aminu da Atika S. Sidi da suka antayo daga shekarar 1994.

    Abin la’akari dangane da wannan zamani na balaga shi ne, yawancin littattafan da aka samar daga cikin sama da 110 da aka wallafa a wannan tsakani sun fito ne daga taskar ƙungiyar Raina Kama da muka yi bayani a baya, wadda ke ƙarƙashin jagorancin Ado Gidan Dabino.

    A daidai wannan lokaci za a fahimci cewa wanda ya fi tashe a cikin wannan ƙungiya shi ne Ɗan Azumi Baba, wanda ya fito da wani salo na labaran aljannu da dodanni da muridai, sai ko Ado Gidan Dabino da ya ɗauki fagen soyayy wanda kuma ya fi kowane daga cikin marubutan shahara saboda alaƙarsa da ‘yan jarida da suka yayata shi da kuma irin rawar da ya taka wajen tallata kansa da kuma ƙwazonsa wajen gina labari.

    Daga jadawalin marubutan da muka samu kai hannu kansu, mun fahimci nan ma maza suka fi shahara a fagen rubutun domin kuwa mata 12 ne suka tusgo, alhali maza 60 suka wallafa littattafai a wannan zango na Adabin Kasuwar Kanon (Dubi rataye na 8.0)

    Tsufa Da Hayayyafa: 1996 zuwa 2001

    Daga lokacin da kasuwar littatafan Adabin Kasuwar Kano ta yi tashin gwauron zabbi daga shekarar 1995  zuwa 1996 amon wannan sabon tsarin rubutu ba inda bai kai ba, wannan ne ya sa harkar ta koma irin ta wani babban kamfani. Ƙungiyoyin marubuta da suka ɓullo daga shekarar  1990  kamar su Kungiyar Matasa Marubuta da Kukan Kurciya da Raina Kama  da Jigon Hausa duk a cikin birnin Kano da Ruwan Dare a  Kaduna da kuma Kungiyar Matasa Marubuta ta Jihar Sakkwato a Sokoto (Adamu, 2006) su ma suka ƙara wa wannan harka martaba da ɗaukaka a idon mutane.

    Haka kuma ƙungiyoyin makaranta irin su Dakata Readers Association da Kabuga Readers Association da Tudun Wada Readers Association da Hotoro-South Readers Association duk a cikin Kano sun agaza wajen tabbatuwar wannan harka.

    Daga cikin kuma masu sayar da littattafan da suka agaza sosai a daidai wannan lokaci akwai irin su Alhaji Baba  na Jakara City Bookshop da Alhaji Musa Ɗanbala na Sauƙi Bookshop kuma Alhaji Garba Mohammed na Garba Mohammed Bookshop da ke Sabon Gari Kano.

    Wannan aure na marubuta da makaranta da masu sayar da littattafai da kuma ƙungiyoyi daban-daban, shi ne za a iya cewa ƙashin bayan wannan fasali na Adabin Kasuwar Kano, wanda ya sanya harkar ta hayayyafa, ta kuma bunƙasa fiye da yadda ake tsammani.

    Wannan ne ya sa aka sami yawancin tarin littattafan adabin Kasuwar Kanon masu yawan gaske da suka kai sama da 400, a tsakanin 1996 zuwa 2001. Daga wannan zango ne mata suka fara kunno kai sosai da sosai domin kuwa an sami marubuta mata sama da 50.

    ’Ya’ya Da Jikoki: 2002 zuwa 2008

    Littattafan da aka yi wa laƙabi da ‘ya’ya da jikoki su ne ƙagaggun labaran da aka samu daga shekarar 2002 zuwa shekarar 2008. Nazarin da aka yi wa waɗannan littatafai an fahimci cewa duk da sauye-sauyen da aka samu na litattafan Adabin Kasuwar Kano a wannan zango, ba a bar fasalin da aka saba ba, wato na yin rubutun bisa tsarin ni na rubuta, ni na gyara, ni na kai inda za a buga mini, ni kuma ke sayarwa da kaina.

    An dai samu wasu sababbin marubuta ne da irin nasu fasali, sun ɓullo domin taka rawa irin tasu. Sai dai kamar yadda muka fahimta, wannan ba ya rasa nasaba da ganin cewa tsofaffin marubutan da suka yi tashe a baya, wasu sun watsar da rubutun, ko dai saboda sun yi aure ko kuma yayinsu ya wuce, wasu kuma sun koma wata sana’ar, musamman shirya finafinai, ga shi kuma buƙatar litattafan ba ta kau baki ɗaya ba, wannan ya jaza fitowar sababbin marubuta domin nuna irin tasu fasahar. An dai ga cewa an samar da littattafai na wannan zangon kimanin 248.

    A wannan zangon kamar yadda muka nazarta, marubuta mata sun sami filin baje kolinsu. Daga cikin littattafan da muka samu kai hannu kansu marubuta mata sama da 76 ne suka yi tashe. Wannan shi ne karon da mata suka yi ambaliya sosai. Haka kuma daga hirar da na yi da makaranta littattafai a wannan zango sun nuna sha’awarsu kan rubuce-rubucen matan, ƙila wannan shi ya ƙara sa yawan marubuta matan.

    A cikin waɗannan jerin littattafan na wannan zango, wadda ta fi yawan littattafai ita ce marubuciya Sa’adatu Saminu Kankiya tana da 14 da suka yi fice sosai, wannan kuma alama ce da ke nuna littattafanta sun fi samun karɓuwa ga makaranta. Mai yiwuwa saboda suna ɗauke da labaran da suka shafi soyayya da aure waɗanda bisa ga nazarin da aka gudanar su ne suka fi tashe a wannan zango.

    Akwai kuma wasu marubutan mata da suka fi shahara a wannan zango da suka haɗa da Saliha Abubakar Zariya da Hadiza Salisu Sharif da Amina Abdullahi Sharaɗa da Zainab Birged da su Sa’adiya Kankiya da Rahmatu Hassan Sanda.

    Duk da cewa yawancin waɗannan sababbin marubuta ne, duk da haka akwai fitattu da suka yi tashe, wasu tun daga haihuwa da ƙuruciya, ba su kuma daina ba har zuwan ‘ya’yan da jikoki. Cikin irin wannan fasali akwai irin su Rahma A. Majid da kuma su Hafsat A. Sodangi da Zuwaira Isa da Bilkisu Ahmed Funtua, da dai sauransu da dama.

    Daga cikin maza kuwa, littattafan Nazir Adam Salihi su ne suka fi karɓuwa da tashe kuma ya rubuta littattafai guda 13. Shi kuma yanayin gabatar da jigon littattafansa ya sha bamban da na sauran marubutan wannan zamani, domin wani lokaci za ka ga labaran nasa na soyayya ne, amma cikin ban takaici, wata sa’a ma da ban tsoro. Sai dai irin yadda yake wasa da harshe a cikin littattafan nasa ya sa yawancin masu karatu ke biye da shi a kullum.

    Maje El-Hejeej Hotoro shi ma wani marubucin ne da litattafansa da kuma tauraruwarsa, musamman a wannan zango suka yi tashe. Shi ma ɗin yakan yi amfani da jigon soyayya ko kuma jigon ban tsoron da jan hankali.

    A daidai kuma cikin wannan zango ne aka soma ganin ɓullar sabon tsarin rubutun Adabin Kasuwar Kanon. Da farko dai an sami marubutan da suka canza akalar rubutun nasu domin ya dace da zamani musamman ganin cewa an sha suka da taƙaddama kan yawaitar rubuce-rubuce kan soyayya da aure. Ire-iren waɗannan marubuta sun haɗa da Bala Anas Babinlata da Ibrahim Sheme da Sakina A. Aminu da Rahma A. Majid da Saliha Abubakar Abdullahi da sauransu da dama.

    Daga nazarin da aka yi, an fahimci cewa yawancin waɗannan marubuta ko dai ilminsu na zamani ne da suka yi nisa a ciki ya sa littattafan nasu suka yi armashi; wato kamar Ibrahim Sheme da Rahma Majid da suka nazarci adabin duniya daban-daban, da yake sun yi digiri, Ibrahim Sheme har digiri na biyu ya yi, ko kuma sun dai tsara littattafan ne domin su ɗan sha bamban da waɗanda aka saba ji da gani a wannan zango bisa sani, domin sun ga yadda aka daɗe ana ta kai-kawo game da neman sauyi, wato kamar su Babinlata da Rahma da Saliha da Abdullahi da Mukhtar Yaron Malam.

    Duka dai alamu ne da ke nuni da cewa sabon yanka rake na Adabin Kasuwar Kano ya shigo kasuwa. Baya ga wannan kuma ga gasar ƙaga littattafai da ta kunno kai, musamman ta Bashir ƙaraye da aka fara a shekarar 2007, wadda ta ba da dama aka sake ɗaga martabar rubutun da kuma marubutan wannan zango. A nan ana maganar irin su Ibrahim Sheme da Lawan Barista da Maje El-Hajeej da suka cinye gasar rubutun a cikin wannan zango. 

    Wannan bayani an ciro shi ne daga rubutaccen kundi mai taken: ADABIN KASUWAR KANO: Nazari da Sharhi Game da Ƙagaggun Labaran Hausa (1984-2008) wanda Bashir Abu Sabe 07/211111002 (M.A Hausa Studies) USMANU ƊANFODIYO UNIVERSITY, SOKOTO, NIGERIA ya wallafa.

    Karanta Adabin Kasuwa A Ƙasar Hausa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tarihin Kano

    Idan ana so a nakalci Tarihin Kano sosai, dole ne sai an tabo tarihin kasar Hausa. Shi kuma tarihin kasar Hausa sai an leka cikin tarihin Sudan. Shi kuma tarihin kasar Sudan sai an lelleka cikin tarihin daular Larabawa ta Banu Ummayyata da ta Banu Abbasi. Har ila yau kuma da binciken labarin wani tunzuri da ya sa jama’a suka rika kauratowa daga tsakiyar kasar Asiya suka yi wo yamma.

    Kasar Sudan itace yankin kasar Afrika na wajen tsakiya, daga gabas ta iyaka da kasar Habasha (watau Ethiopia), daga arewa ta yi iyaka da Sahara daga kudu ta yi iya da yankin gabar Tekun Atlantic da ake kira ‘Gulf of Guniea’ — da kuma kasashen sunkurun kurmin nan na tsakiyar Afrika. Kalmar nan ‘Sudan’ ma’anarta baki, saboda galibin al’ummar da ke zaune a cikin yankin Sudan masu bakar fata ne. An ce zafin rana shi ke sa su baki (kunne ya girmi kaka), gama dukkan kasar Sudan tana daf da wurin da ake kira ‘Haddul Etidali’ watau ‘Equator’. Kasar Hausa ita ce yankin nan na kasar Sudan wanda ke wajen tsakiya-tsakiya. Daga gabas da ita ga kasar Borno; daga Yamma ga kasar Dahomey (wacce yanzu ake kira Jamhuriyar Benin); daga arewa ga Hamadar Sahara; daga kudu kuma ga kasashen Nupe da kasahen da ake kira ‘Middle Belt’. Kasar Kano tana daga yankin tsakiya na arewacin kasar Hausa. Daga gabas ta iyaka da kasashen Borno da Bauchi; daga yamma ta yi iyaka da Katsina; daga kudu ta yi iyaka da Zariya; daga arewa kuma tayi iyaka da kasar Neja. Tun daga yanzu za a fara fahimtar lalle Kano wajibi ne ta zama babbar alkarya saboda ita ce kamar tsakiyar kasar Sudan duka.


    Taswirar birnin Kano

    Tun da dadewa kasar Hausa da kuma sauran kasashen Sudan sun sami adabunsu na zaman duniya daga fuska biyu mabambanta —- watau Gabas da Yamma. Sa’adda sabawa ta sa jama’ar kasar Mangoliya ta Asiya suka rika fuskantowa yamma-yamma, a hankali sai masarauta ta rika kafuwa, in wannan ta fadi, wata kuma ta tashi a can gabas. Shi ne daga bisani mulkin Farisa, (watau persia), ya kafu, ya mallake kasashen gaba duka.

    Mazaunan Farko

    A kasashen Karni na Tara (9th Century) na Masihiyya wadansu maharba, wadanda babu hakikar daga inda suka zo suka zauna kan duwatsun da ke kewaye da sararin da ake kira Kano yanzu. Irin duwatsun nan sune irinsu Dala. Gwauran Dutse, Magwan da Dutsen Fanisau.
    Su maharban nan suka rika yin farauta a wani kurmi wanda ya ke shine tushen rafin Jakara, inda kasuwar Kurmi ta Kano ta samo suna. dan wadannan maharba suka jarraba dan koma suka ga wurin yana da albarka, sai suka ci gaba suna kara saran dajin suna yin gonaki. Albarkar wurin nan mai ban mamaki sai ta jawo wadansu mutane daga wadansu wurare suna zuwa. Da taron mutanen wannan lokaci mai nisa, ya kan zama mutum ne da ke da fifikon karni game da tsafi.

    Babu tahakikanin akan irin tsarin mulkin da wadannan al’umma su ka gina shugabacinsu, amma duk da haka ana iya cewa aikin shugaba a wannan lokaci bai wuce tsare dokokin farauta da kuma kusaci da tsafin da mutanen ke bautawa

    An bayar da bayanan nan a karkashin littafin ‘Kano Ta Dabo Cigari’ wallafar Alhaji Abubakar Wazirin Kano.
    ISBN: 978-140-501-2218

  • Jerin Gwamnonin Kano Daga (1967 zuwa yau)

    Jerin Gwamnonin Kano Daga (1967 zuwa yau)

    Jerin sunayen mutanen da suka taɓa rike muƙamin Gwamna a Jihar Kano.

    Jihar Kano gari ne da aka samar da shi a shekara ta 1967-05-27. A lokacin da ake raba yankin Arewa. Benue-Plateau, Kano Arewa ta tsakiya.

    Sunaye Matsayi Kama aiki Barin aiki Jam’iyya
    Kwamishinan ‘yan sanda, Audu Bako Gwamna Mayu 1967 Juli 1975 Soja
    Kanel Sani Bello Gwamnan soja Juli 1975 Satumba 1978 Soja
    Group Captain Ishaya Shekari Military Governor Satumba 1978 Oktoba 1979 soja
    Alhaji Muhammad Abubakar Rimi Gwamna Oktoba 1979 May 1983 PRP
    Alhaji Abdu Dawakin Tofa Gwamna May 1983 Oktoba 1983 PRP
    Alhaji Sabo Bakin Zuwo Gwamna Oct 1983 Disamba 1983 PRP
    Air Commodore Hamza Abdullahi Gwamna Janairu 1984 Agusta 1985 Gwamnan soji
    Kanel. Ahmad Muhammad Daku Gwamnan soji Agusta 1985 1987 Soji
    Group Captain Muhammad Ndatsu Umaru Gwamnan soji December 1987 27 Juli 1988 Soji
    Kanel Idris Garba Gwamnan soji Agusta 1988 Janairu 1992 Soji
    Architect Kabiru Ibrahim Gaya Governor Janairu 1992 Nuwanba 1993 NRC
    Kanel Muhammad Abdullahi Wase Kwamandan soji Desemba 1993 Juni 1996 Soji
    Kanel Dominic Oneya Kwamandan soji Agusta 1996 Satumba 1998 Soji
    Kanel Aminu Isa Kwantagora Kwamandan soji Satumba 1998 Mayu 1999 Soji
    Engineer (Dr.) Rabiu Musa Kwankwaso Gwamna Mayu 1999 Mayu 2003 PDP
    Malam Ibrahim Shekarau Gwamna Mayu 2003 Mayu 2011 ANPP
    Engineer (Dr.) Rabiu Musa Kwankwaso Gwamna Mayu 2011 Mayu 2015 PDP
    Abdullahi Umar Ganduje Gwamna Mayu 2015 Har izuwa yau APC