Tag: hadisai

  • Ingantattun Hadisai Kan Falalar Ranar Ashura Da Azumin Ranar

    Ingantattun Hadisai Kan Falalar Ranar Ashura Da Azumin Ranar

    1- An karɓo daga Abdullahi ɗan Abbas (Radiyallahu Anhu) ya ce: Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya zo Madina; sai ya ga Yahudawa na azumi ranar Ashura. Sannan ya ce: mene ne wannan?

    Sai suka ce: wannan rana ce mai daraja, a wannan yini Allah ya kuɓutar da Banu Isra’ ila daga maliyansu; shi ne ya sa Annabi Musa yake yin azumin ranar. Sai ya Ce: “Ni na fi ku kusanci da Musa Sai ya yi azumin ranar; ya yi umarni da azumtar ranar (Bukhari Hadisi na 2004, azumtar ranar (Bukhari Hadisi na 2004, Muslim Hadisi na 1130).

    2- An karɓo daga Ibn Abbas (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Babu wata rana da Manzon Allah (Salallahu Alaihi Wasallam) yake kardadan azumi a cikinta; yake fifita ta a kan sauran ranaku, sai ranar Ashura. Sai kuma ranakun watan Ramadan. (Bukhari Hadisi mai lamba (2006) Muslim Hadisi mai lamba 1132).

    3- An karɓo daga A’isha (Radiyallahu Anha) ta ce: “Ƙuraishawa sun kasance suna yin azumin ranar Ashura a zamanin jahiliyya, sai Manzon Allah (Salallahu Alaihi Wasallam) ya yi umarni a rinƙa yin azumin ranar har zuwa umarni a rinƙa yin azumin zuwa lokacin da aka wajabta azumin Ramadan. Daga nan sai ya ce: “Wanda ya ga dama ya yi, wanda ya ga dama sai ya bari (Bukhari hadisi na 2001, Muslim hadisi na 1125).

    4- An karɓo daga Abu Ƙatada (Radiyallahu Anhu) ya ce: “Haƙiƙa an tambayi Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) game da azumin Ashura, sai ya ce: “yana kankare zunuban shekarar da ta wuce”. (Muslim hadisi na 1162). Shi kansa watan Muharram ana son yawaita azumi a cikinsa saboda:

    5. An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) ya ce Manzon Allah (Sallalahu Alaihi Wa Sallam) ya ce; “Mafificin azumi bayan azimin Ramadan, shi ne azumi a watan bayan azimin Ramadan; shi ne azumi a watan Allah Al-Muharram, mafificiyar salla bayan sallar farilla, ita ce sallar dare”. (Muslim hadisi na (1163). Shi azumin Ashura saboda muhimmancinsa ana iya ɗaukar niyyarsa bayan fitowar alfijir; ko da kuwa mutum ya ci wani abu, saboda:

    6- An karɓo daga Rubayyi’i Bint Mu’awwiz (Radiyallahu Anha) ta ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya aika unguwannin mutanen Madina a yi shela; “Wanda ya wayi gari ba ya ażumi ya kame bakinsa a ragowar yinin; wanda kuwa ya tashi da azumi, to ya cigaba da azuminsa. ” (Bukhari hadisi 1960, Muslim hadisi na 1137).

    Wannan hukunci har a yanzu mazhabar Malikiyya haka yake; kamar yadda Asshaikh Muhammad Ibn Ahmad Maiyara a cikin littafinsa Addurrus Samin Shafi na 454 yake cewa:

    “An keɓanci azumin ashura da cewa wanda ya wayi gari bai kwana da niyyar azumin ba; zai iya cigaba da niyyar azumin ko da kuwa ya ci abinci ana so a yi azumin ranar tara ga Muharram. Sannan kuma a yi na ranar goman wato Tasu’a da Ashura saboda:

    7- An karɓo daga Abdullahi Ibn Abbas (Radiyallahu Anhu) ya ce; “A lokacin da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya yi azumin ashura kuma ya yi umarni a yi sai aka ce da shi, wannan fa rana ce da yahudu da nasara suke gimamawa”. Sai ya ce; “In Allah ya yarda shekara mai zuwa sai mun fara azumtar ranar tara (tasu’a) kafin shekarar Allah ya karɓi “ransa (Sallallahu Alaihi Wa Sallam).

    (Muslim hadisi na 1134).

    Ƙarin Bayani

    Idan muka yi la’akari da hadisan da suka gabata za mu ga cewa; azumin ashura ya ƙetare matakai huɗu a sunnar Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) waɗànnan matakai su ne:

    Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya kasance yana yin azumin ashura; tun yana Makka kafin Hijira, amma bai umarci mutane da su yi ba.

    Lokacin da ya yi hijra zuwa Madina, ya ga yahudawa suna azumin ashura, kuma suna yahudawa suna azumin ashura. Kuma suna girmama ranar, shi kuma dama yana son ya dace da su akan abubuwan da ba a yi masa wani umarni a kai ba; sai ya ci gaba da azumtar ranar, ya kuma umarci mutane da yi, ya ƙarfafa umarnin, ya kwaɗaitar har ta kai Sahabbai suna sa ‘ya’yansu ƙanana su yi azumin.

    Lokacin da aka wajabta azumin watan Ramadan, sai ya daina yin umani da azumin ashura; wato sai ya tashi daga wajibi ya koma na sa kai (Mustahabbi).

    A ƙarshen rayuwarsa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya yi niyyar yin azumin Tasu’a tare da Ashura; sai ya koma ga Allah kafin lokacin, domin ya saɓawa yahudawa da Nasara.

    Domin karanta cikakken bayani akan Matsayin Azumin Ashura A Wurin Ahlil Baiti (Radiyallahu Anhuma) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Azumin Tasu’a Da Ashura danna nan

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gaskiyar Magana Akan Ashura wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Hidisai Goma Kan Hatsarin Shugabanci

    Hidisai Goma Kan Hatsarin Shugabanci

    Hatsarin Shugabanci: Shugabanci komai ƙanƙantarsa wani nauyi ne babba a kan wanda ya hau kansa, wanda in ba a ɗauke shi an sauke shi daidai ba; in ba a yi gaskiya da adalci ba, in ba a riƙe amana ba; tabbas zai zama nadama da takaici ga wanda ya yi wannan shugabanci.

    Da mun san hatsarin da yake cikin shugabanci koda an yi shi bisa gaskiya da riƙon amana; da babu wanda zai nemi a ba shi shugabanci; da sai an zo ana bin mutum ana haɗa shi da Allah don ya karɓi muƙami yana gudu yana a kai kasuwa. To amma rashin sanin hatsari da yake ciki; da kuma kallon da kwaɗayin ɗan roman da yake cikinsa, shi ne yasa ake ta yin kokawa; har ma ana kashe kuɗaɗe masu ciwo da ma roƙon Allah duk don a ɗare kan karagar mulki.

    Ga wasu daga hadisan da shugaban halitta ya faɗa a kan hatsarin shugabanci:

    Hadisi Na Ɗaya

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Umar (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Na ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa; “Kowane ɗaya daga cikinku makiyayi ne (shugaba ne) kuma za a tambaye shi a kan waɗanda aka ba shi kiwo; shugaba makiyayi ne kuma za a tambaye shi a kan waɗanda aka ba shi kiwo (mabiyansa), magidanci makiyayi ne a kan iyalansa kuma za a tambaye shi a kansu.

    Matar aure mai kiwo ce a gidan mijinta kuma za a tambaye ta a kan waɗanda aka ba ta kiwo. Yaron gida/kanti makiyayi ne a cikin dukiyar uban gidansa; kuma; kowa za a tambaye shi a kan abin da aka ba shi kiwo. Dukkanninku makiyaya ne, kuma za a yi masa tambaya a kan abin da aka ba shi kiwo.
    Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi.

    Karin Bayani

    Wannan hadisi ne mai girma da muhimmanci wanda ya ƙunshi abubuwa da dama kaɗan daga cikinsu su ne:

    1. shugabanci kalma ce mai faɗi bai taƙaita a kan masu riƙe da madafan mulki ba, a’a duk wani wanda waɗansu suke ƙarƙashinsa komai rashin yawansu to shi ma shugaba ne, kamar yadda hadisin ya faɗa:
    Mai mulki shugaba ne, mai gida shugaba ne a gidansa, matar aure shugaba ce a gidan mijinta, bara ko yaron gida ko angulun kanti, shugaba ne a kan dukiyar uban gidansa. Haka dai har shugaban aji da ɗalibai da na ƙungiyoyi da kwamitoci da sauransu.

    2. Kowa za a yi masa hisabi ranar lahira; za a bincike shi kan yadda ya gudanar da shugabanci da aka ba shi.

    3. Duk azabar da za a yi wa azzalumin shugaba; da kuma falala da rahamar da Allah yake yi wa adalin shugaba zai samu mai gida da uwargida, da yaron gida da sarki har zuwa shugaban ƙasa,babu bambanci, sai dai kuma kayan wani sun fi na wani yawa da nauyi.

    4. A duk lokacin da ake maganar shugabanci yabo ko zargi alhairi ko sharri kafin ka yi tunanin shugaban ƙasa ko gwamna ko sarki ko wani na can sama; ka fara duba kanka ka yi wa kanka hisabi. Shi shugabancin da aka ba ka, kana kula da shi yadda ya kamata? Shin kana ba da haƙƙoƙin da suke kanka?.

    Hadisi Na Biyu A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Anas ɗan Malik (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Haƙiƙa Allah zai tambayi kowane makiyayi a kan abin da aka ba shi kiwo, shin ya kiyaye shi ko ya tozarta shi? Har ma za a tambayi mutum a kan iyalansa”.
    Ibn Hibban ne ya rawaito shi a cikin sahihinsa.

    Karin Bayani
    Lallai ne magidanta masu tozarta haƙƙoƙin iyalansu su bar ‘ya’yansu kamar marayu, matansu kamar kuyangi ba tarbiyya ba cikakkiyar lafiya har dabbobin da suke kiwatawa ma sai su fi iyalansu jin daɗinsu, su ji tsoron Allah su riƙe iyalansu da gaskiya su sani cewa amana ce Allah ya damƙa musu kuma za su yi bayani ranar ƙiyama kan wannan amanar.

    Hadisi Na Uku A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Duk wanda ya zama alƙali haƙiƙa an yanka shi ba da wuƙa ba”.
    Abu Dawud da Tirmizi ne suka rawaito shi.

    Karin Bayani

    Duk alƙalin da ya yi rashin gaskiya a kan aikinsa, haƙiƙa ya yi babbar asara ya halaka; ba wai rayuwarsa kawai ya rasa ba, har ma da addininsa wato wanda aka yanka da wuƙa zai fi shi samun sauƙin mutuwa da halaka. Wannan hadisi yana bayanin hatsarin da yake cikin alƙalanci; saboda haka ya zama wajibi ga alƙalai su yi taka tsantsan su rinƙa kwatanta gaskiya da adalci su guji zalunci, da cin hanci da murɗe gaskiya.

    Hadisi Na Huɗu A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Auf ɗan Malik (Radiyallahu Anhu) haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “In kuna so zan ba ku bayani a kan shugabanci ko yaya yake? Sai na ɗaga muryata na ce, “Yaya yake ya Ma’aikin Allah? Sai ya ce: “Farkonsa zargi ne, na biyunsa nadama ce, na ukunsa azaba a ranar ƙiyama sai dai wanda ya yi adalci”.
    Bazzar da Ɗabarani ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisi ne mai ɗimbin fa’ida da bayanin ɗabi’ar mulki duk daga taƙaitattun kalmominsa

    • Mai mulki ba ya kuɓuta daga zargi da tuhuma da munana masa zato daga waɗanda yake mulka; da abokan hamayyarsa komai ƙoƙarinsa na kwatanta gaskiya. Haka zai ta shan suka da ƙalubale ta kowanne ɓangare, dukkanin idanu da kunnuwa suna kansa, komai ya faru shi ne ko bai sani ba, kuma ya fi ƙarfinsa.

    – Yayin da abubuwa suka dagule, matsaloli suka kunno kai ta ko’ina, magoya baya suka fara juya baya ga shugaba, barazana da fargaba ta yawaita a gida da waje, shugaba yakan tsinci kansa a halin da- na-sani, da nadamar karɓar wannan shugabanci.

    – Haka kuma bayan shugaba ya bar mulki musamman in an bi shi da jafa’i da bincike-binciken neman laifi da gazawa, wannan ma yana jefa masu mulki cikin kogin nadamar karɓar mulki.

    – Mafi munin yanayi kuma shi ne, matsananciyar azaba da take jiran azzaluman shugabanni a lahira da tozarta da wulaƙanta tun daga duniya.

    A taƙaice wannan hadisi yana ɗauke da tsoratarwa a kan shugabanci na zalunci da kwaɗaitarwa kan adalci saboda shi adalin shugaba babu ruwansa da wannan azabar.

    Hadisi Na Biyar A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Abu Zarr (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Na ce ya Ma’aikin Allah shin ba ka ba ni wani muƙami ba? Sai ya ɗora hannunsa a kan kafaɗata, sannan ya ce; “Ya kai Abu Zarrin haƙiƙa kai mutum ne mai rauni, shi kuma shugabanci amana ne, kuma yana jawo kunyata da nadama ranar ƙiyama; sai dai wanda ya kula da haƙƙoƙin shugabanci ya sauke nauyin da yake cikin shugabanci.

    Hadisi Na Shida A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga gare shi (Abu Zarr) Radiyallahu Anhu, haƙiƙa Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce da shi; “Ya kai Abu Zarr haƙiƙa na ga kai mutum ne mai rauni, kuma ina so gare ka abinda nake so ga kaina. Saboda haka, kada ka shugabanci koda mutum biyu, kuma kada ka karɓi riƙon dukiyar maraya.

    Muslim da Abu Dawud da Hakim ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) shugaba ne da yake lura da halin kowa kuma yake ba shi aikin da ya dace da shi.
    Duk tsoron Allah na mutum da yawan ibadarsa bai kamata a ba shi shugabanci ba, in dai ba shi da ƙarfi da gogewa kan al’amuran mulki. Wannan ne ya sa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ƙi ya ba wa Abu Zarr wani muƙami saboda ya san rauninsa da matsanancin sauƙin kansa da gudun duniya; har ma ya ba shi shawarar cewa ko da shugabancin mutum biyu aka ba shi kada ya karɓa.

    Haka kuma kada ya karɓi ajiyar dukiyar marayu ba don yana tsoron zai cinye ba, a’a sai don gudun kada tausayi ya sa ya yi sadaka da wannan dukiyar.

    Ɗan’uwa idan an faɗa wa Abu Zarr (Radiyallahu Anhu) duk da falalarsa; ina ga mutanen yanzu da za ka ga har kuɗi ake kashewa, ko a yi ta yin rigima a kan neman shugabanci, ba kuma tare da wata cikakkiyar cancanta ko manufa ko tsari ba.

    Hadisi Na Bakwai A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) haƙiƙa Manzo Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Haƙiƙa za ku rinƙa kwaɗayin shugabanci, kuma haƙiƙa zai zama sanadin nadama ranar alƙiyama. Madalla da mai shayarwa tir da mai yayewa”.
    Bukhari da Nasa’i ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan abu da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya faɗa na tsananin kwaɗayin shugabanci kamar a yanzu yake maganar. Sai ka ga ɗaruruwan mutane suna takarar kujera ɗaya; kuma a yanzu kowa so yake ya zama shugaba, sai ka ga komai da shugabansa; kuma har ana rigima a kan wannan shugabanci. Amma duka a ƙarshe nadama ce take biyo baya.
    Mai shayarwa da mai yayewa shugabancin ake nufi, wato kamar yadda yaro yake jin daɗi lokacin da ake shayar da shi, kuma yake shan wahala da fama da laulayi iri-iri lokacin yaye shi to haka daɗin shugabanci yake a farkon da kuma wahala da damuwa da ake shiga in an sauka.

    Hadisi Na Takwas A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Kaicon sarakuna, kaicon wakilai, kaicon amintattu. Wallahi waɗansu mutane (waɗanda suka karɓi shugabanci) a ranar ƙiyama za su yi burin ina ma da a ce a ɗaure gashinsu a jikin tauraron surayya; su yi ta reto tsakanin sama da ƙasa a maimaikon shugabancin da suka riƙe.

    Ibn Hibban da Hakim ne suka rawaito shi.

    Hadisi Na Tara A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Na ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa; “Zamani ya kusa zuwa da mutum zai yi burin gara a ce ina ma ya faɗo daga tauraron Surayya (zai fi masa sauƙi) a kan mulkin da ya yi komai ƙanƙantarsa”.

    Hakim ne ya rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Waɗannan hadisai guda biyu suna bayanin hatsarin shugabanci ta yadda mutum zai ji a ransa cewa gara a rataye shi da gashinsa a jikin tauraro ya yi ta reto; ko kuma a jefa shi daga can sama ya yi ƙasa ya ratattake a maimakon azabar da za a yi masa; saboda rashin adalci da gaskiya da ya gudanar a shugabancin.

    Hadisi Na Goma A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Abdurrahman bin Samura (Radiyallahu Anhu) ya ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce da shi; “Ya kai Abdurrahman ɗan Samura kada ka nemi shugabanci, saboda in ya zo maka ba tare da ka nema ba, Allah zai taimake ka a kansa; in kuwa aka ba ka shugabanci saboda nema da ka yi sai Allah ya bar ka da dabararka”.

    Buhari da Muslim ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Duk wanda ya san hatsarin shugabanci da makomarsa; ba zai iya nacewa ya yi ta kokawar sai ya sami muƙami ba. To irin wannan idan aka ga cancantar su aka tilasta musu lallai sai sun karɓi muƙamin za su sami tallafi da agaji daga Allah.
    Wanda kuwa ya nace sai an ba shi muƙami musamman in bai cancanta ba ko kuma yana da wata muguwar manufa a ransa to ba zai yi wani abin kirki ba sai hauma-hauma da zalunci.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Hadisi Na Ɗaya A Kan Haramcin Goyon Bayan Azzaluman Shugabanni danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Shugabanci A Musulunci (Hadisai Tamanin Da Biyu A Kan Shugabanci); wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Falalar Adalci, Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    Falalar Adalci, Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    Hadisi Na Ɗaya A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Jarir ɗan Abdullahi (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Duk wanda ba ya tausayin mutane, Allah ba zai tausaya masa ba”.

    Bukhari da Muslim da Tirmizi ne suka rawaito shi. Ahmad ma ya rawaito shi ya ƙara da cewa: “Wanda ba ya afuwa, Allah ba zai yi masa afuwa ba”.

    Abu Dawud da Tirmizi ne suka rawaito shi.

    Hadisi Na Biyu A kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Amr ɗan Asi (Radiyallahu Anhuma) haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Masu tausayi Allah mai rahama zai tausaya musu. Ku tausayawa na ƙasa da ku, wanda yake sama da ku zai tausaya muku.

    Abu Dawud da Tirmizi ne suka rawaito shi.

    Hadisi Na Uku A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) ya ce: Na ji mai gaskiya abin gaskatawa mai wannan ɗakin baban Alƙasim (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa: “Ba a cire tausayi sai daga zuciyar mara rabo a lahira”.

    Abu Dawud da Tirmizi ne suka rawaito shi.

    Hadisi Na Huɗu A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Abbas (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Ba ya tare da mu wanda ba ya tausayawa ƙaraminmu, kuma ba ya girmama babbanmu, kuma ba ya umarni da kyakkyawan aiki, ba ya hani ga mummuna.

    Tirmizi ne ya rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Waɗannan hadisai guda biyar suna bayyana falalar tausayawa mabiya da jinƙan su da sauran masu rauni da haramcin gallaza musu, suna nuna cewa duk wanda yake da jinƙai da tausayi Allah zai tausaya masa, kuma rashin tausayi alama ce ta rashin imani da rashin rabo a lahira, har ma Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Ba ruwan sa da maƙetaci mugu maras imani da tausayi da kuma wanda ba ya girmama na gaba da shi” .

    Hadisi Na Biyar A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    Hadisi Na Biyar A kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Aliyyu (Radiyallahu Anhu) ya ce: “Maganar ƙarshe da Manzon (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi ita ce: “Ku kula da sallah, ku kula da sallah, ku ji tsoron Allah ku kula da haƙƙoƙin waɗanda suke a ƙarƙashinku”.

    Abu Dawud da Ibn Majah ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisi yana daga cikin wasiyyoyin da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya bar wa al’ummarsa dab da wafatinsa. Ya yi wasiyyar a kula da sallah kuma a kula da haƙƙoƙin bayi da barori; da kuma duk waɗanda suke ƙarƙashin mutum.

    Hadisi Na Bakwai A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Amr ɗan Asi (Radiyallahu Ahuma) ya ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Haƙiƙa masu adalci za su kasance a kan mimbarai na haske a daman Allah mai rahama; kuma duk hannayensa biyu dama ne. Su ne waɗanda suke yin adalci a cikin hukuncinsu da iyalansu da waɗanda suke jagoranta.

    Muslim da Nasa’i ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Haƙiƙa masu yin adalci da gaskiya a shugabancin da yake kansu da iyalansu suke kaucewa zalunci da nuna bambancin a tsakanin waɗanda suke jagoranta, za su samu babban matsayi a wurin Allah ranar lahira.
    Hannun dama da ya zo a wannan hadisin sifa ce daga siffofin Allah Ta’ala waɗanda ake yin imani da su kamar yadda suka zo, ba tare da an yi musu tawali ko canja su, ko kore su ba, ko kuma kamanta su da sifofin halittu ba.

    Hadisi Na Takwas Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Iyad bin Himar (Radiyallahu Anhu) ya ce: Na ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa; “Yan Aljanna guda uku ne: Mai mulki mai adalci mai dacewa da gaskiya; da mutum mai tausayi mai taushin zuciya ga dukkanin ‘yan uwansa da dukkan musulmi da kuma mutum mai iyali, mai kame kai da wadatar zuci.

    Muslim ne ya rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Falalar da darajar waɗannan mutane uku ta sanya Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya taƙaice ‘yan Aljanna a kansu. Saboda duk wani wanda yake riƙe da wani jagoranci tun daga mai gida da uwargida har zuwa kan shugaban ƙasa ya yi ƙoƙari ya yi adalci ya nemi gaskiya kuma ya yi aiki da ita.

    Kowa ya fitar da mugunta da ƙeta da gaba da ganin ƙyashi daga zuciyarsa, mu kasance masu tausayi da taimako da ƙauna ga dukkan ‘yan uwanmu da gabaki ɗayan musulmi.

    Kowa ya zage damtse ya nemi halal ya kula da iyalansa kuma ya wadatu da abin da Allah ya ba shi ya kasance mai godiya ga Allah ya rinƙa hangen na ƙasa da shi, kada ya rinƙa hangen na sama da shi.
    Waɗannan halaye za su sa mu cancanci shiga Aljannah, kishiyoyinsu kuwa, babu abin da za su jawo mana sai shiga wuta tun daga duniya kafin ta lahira.

    Hadisi Na Tara A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) ya ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: Allah Ta’ala yana ƙin mutane huɗu: Ɗan kasuwa mai yawan rantsuwa, da talaka mai girman kai, da tsoho mazinaci da kuma azzalumin shugaba.

    Nasa’i da Ibn Hibban ne suka rawaito shi; Muslim ma ya rawaito makamancinsa, sai dai a ruwayarsa ya ce; “Da talaka mai girman kai da shugaba maƙaryaci”.

    Hadisi Na Goma A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Mu’awiyya (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Ba za a tsarkake al’ummar da ba hukuncin gaskiya a cikinta ba, kuma mai rauni ba ya iya karɓar haƙƙinsa daga mai ƙarfi cikin daɗin rai”.
    Ɗabarani ne ya ruwaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisin Ibn Majah ma ya rawaito shi tare da wata ƙissa mai ban sha’awa kamar haka:

    “Wani baƙauye ya zo wurin Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) domin karɓar bashin da yake bin sa. Ya matsa masa har ya ce: “Ba makawa sai ka biya ni bashina”. Sannan sahabbai suka daka masa tsawa suka ce: “Kasan da wa kake magana kuwa? Sannan ya kada baki ya ce: “To ba haƙƙi nake nema ba? Sai Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce da su: “Don me ba za ku goyi bayansa ba?

    Sannan ya aika wajen Khaulatu ‘yar Ƙaisu ya ce da ita: “Idan kina da dabino ki ba ni rance, kafin a kawo mana dabino mu biya ki”. Sannan ta ce: “An gama ya Ma’aikin Allah, uwata da ubana su zama fansa a gare ka”. Sai ta ba shi ya biya baƙauyen, har ya ba shi wani ya ci, ya ji daɗi, ya ce ka cika min Allah ya cika maka.

    Sai ya ce: “Ai waɗannan (masu cika wa mutane haƙƙoƙinsu) su ne zaɓaɓɓun mutane, haƙiƙa ba a tsarkake al’ummar da mai rauni ba ya samun haƙƙinsa cikin sauƙi daga mai ƙarfi”.

    Allahu Akbar! Ɗan’ uwa yi nazari kan wannan ƙissa dubi matsayin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) dubi kuma wane ne wannan Baƙauyen? Sannan ka dubi abin da ya faru tsakaninsu da kuma abin da ma’aikin Allah ya faɗa, lallai za ka fahimci darussa masu yawa.

    Duk al’ummar da ake rayuwar kashin dankali a cikinta, ake rayuwa irin ta rabon kura; rayuwar da uwa ba kwaɓa, uba ba harara, sai dai kowa ƙarfinsa ya ƙwace shi; maras ƙarfi kuwa sai dai ya yi Allah ya isa, to haƙiƙa wannan al’umma ko ƙasa ko gwamnati ba za ta yi wata daraja da mutunci da kwarjini ba, ballantana ta samu wani tsarki da yabo a wurin Allah da kuma mutane. Wannan zai gaggauta rushewar wannan al’umma da ci bayanta. Auna rayuwarmu a yau da wannan hadisi anya ba mu shiga cikinsa ba kuwa?

    Hadisi Na Goma Sha Ɗaya A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abu Buraida daga mahaifinsa haƙiƙa Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Alƙalai iri uku ne: alƙalai biyu ‘yan wuta ne, alƙali ɗaya ɗan Aljanna ne. Alƙalin da ya yi hukunci ba na gaskiya ba, yana sane wannan ɗan wuta ne. Kuma Alƙalin da ba shi da ilmi ya yi hukunci ya halaka haƙƙoƙin mutane shi ma ɗan wuta ne. Alƙalin da ya yi hukunci na gaskiya wannan ɗan Aljanna ne.
    Abu Dawud da Tirmiz da Ibn Majah ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisin yana bayanin matsayin alƙalai a lahira. Duk alƙalin da ya yi zalunci saboda son rai ko wata buƙata ko rashawa da aka ba shi, da kuma alƙalin da bai nuna ba, ba shi da ilmin cancantar alƙalanci aka yi abin da aka yi aka ba shi alƙalanci ya zo yana taɓargaza, waɗannan biyun ‘yan wuta ne.
    Shi kuma alƙalin da ya cancanta kuma yana adalci da gaskiya wannan ɗan Aljanna ne.
    Saboda haka alƙalai su ji tsoron Allah, su yi gaskiya da adalci, su kasance cikin karatu da bincike a kowane lokaci. Su ma masa na da alƙalai su ji tsoron Allah su rinƙa naɗa waɗanda suka cancanta su guji naɗa jiƙaƙƙun mutane don kawai sanayya ko rashawa da sauransu.

    Hadisi Na Goma Sha Biyu Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Ibn Abi Aufa (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Haƙiƙa Allah yana tare da alƙali matuƙar bai yi zalunci ba, idan kuwa ya yi zalunci sai Allah ya rabu da shi sai shaiɗan ya naniƙe masa.
    Tirmizi da Ibn Majah da Ibn Hibban da Hakim ne suka rawaito shi. Sai dai a ruwayar Hakim ya ce: “idan ya yi zalunci sai Allah ya yi watsi da shi”.

    Ahmad da Bazzar da Tabarani ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Allah Ta’ala yana taimaka wa shugabanni da alƙalai masu adalci yana ba su kariya; yana rufa musu asiri ya ɗaukaka su matuƙar sun kama hanyar zalunci da rashin gaskiya; sai Allah ya yi watsi da su ya bar su da dabararsu, su yi ta ɗimuwa da shirme, ga rashin ƙima a idon mutane; sannan in suka tafi a haka, a lahira su haɗu da matsananciyar azaba.

    Hadisi Na Goma Sha Uku Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) daga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Duk wanda ya shugabanci mutane goma za a kawo shi ranar ƙiyama a ƙuƙume (ɗaure) kodai adalcinsa ya kwance shi ko kuma zalunci ya halakar da shi.

    Ahmad da Bazzar da Tabarani ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Lallai wannan hadisin tsoratarwa ne mai girma ga shugabanni da masu neman shugabanci. Babban abin tsoron shi ne; hadisin bai taƙaita a kan shugaban ƙasa ko gwamna ko sarki ba, a’a duk wanda ya yi shugabanci daga mutane goma zuwa sama, to za a zo da shi a ɗaɗɗaure ranar ƙiyama cikin kukumi wato za a haɗe hannayensa a kan wuyansa a ɗaure. A haka za a yi masa hisabi in ya yi adalci a kwance shi; in bai yi adalci ba a hakan za a nutsa shi a wuta. Allah ya kiyaye mu Ameen.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Shugabanci A Musulunci (Hadisai Tamanin Da Biyu A kan Shugabanci); wanda Shehu Mansur Dala ya waallafa shi. Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mazajen Da Nana Khadija Ta Aura Kafin Manzon Allah (S.A.W) danna nan.

  • Hadisai A Kan Kada A Goyi Bayan Mai Laifi

    Hadisai A Kan Kada A Goyi Bayan Mai Laifi

    Hadisi Na Ɗaya A Kan Kada A Goyi Bayan Mai Laifi

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Umar (Radiyallahu Anhu) ya ce: Na ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa: “Duk wanda alfarmarsa ta hana a yi wani hukunci na Allah, haƙiƙa ya kishiyanci Allah Ta’ala, kuma duk wanda ya yi husuma a kan ƙarya yana sane, zai kasance cikin fushin Allah Ta’ala, kuma duk wanda ya yi wa wani mumini ƙage, Allah zai zaunar da shi a dagwalon Khabalu (Tafkin da surƙamin ‘yan wuta yake taruwa) har sai ya janye abinda ya faɗa.
    Abu Dawud da Hakim ne suka ruwaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisi ya ƙunshi abubuwa uku muhimmai:

    1- Duk mutumin da ya hana a hukunta mai laifi; saboda matsayinsa to haƙiƙa ya yi daidai da mai ƙalubalantar Allah da kishiyantar sa. Wato ya mayar da kansa kamar wani kishiya ga Allah.

    2- Wanda yake ba da kariya ga mai laifi alhali ya san ba shi da gaskiya; Allah zai ta yin fushi da shi har sai ya janye jikinsa ya bar shari’a ta yi aikinta. Wannan ya haɗa da iyaye da ‘yan uwa da lauyoyi; da sukan kafe su yi ta jayayya a kan kare wanda su da kansu sun san ba shi da gaskiya.

    3- Masu yi wa mutane ƙage da sharri suna cikin babban hatsari; za a jefa su cikin dagwalon da ake tara da tafasa ruwan ciwo da ƙuraje na ‘yan wuta a ranar lahira; har sai sun daina yaɗa shi wanda tun daga nan duniya za a yi hakan in kuwa aka yi sake aka je lahira to fa sai yadda ta yiwu.

    Hadisi Na Biyu A Kan Kada A Goyi Bayan Mai Laifi

    Wani abu da yake kawo cikas ga ci gaba da nagartar kowace gwamnati da al’umma; shi ne neman alfarma da masu faɗa a ji sukan yi, domin a ƙyale masu laifi; ko kuma a sassauta hukuncin da ya dace a yi musu, ta yadda koda an yi hukuncin, sai ya zama kamar wasa. Wannan sai ya ƙarfafa guiwar ‘yan gata su yi ta tafka ta’asa son ransu; har ma aikata laifi ya zama wata burga da nuna isa, wato iya matsayinka ko gatanka, iya damarka ta aikata laifi, ka kwana lafiya. To shi me Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya faɗa kan nemawa masu laifi alfarma a ƙyale su?

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Shugabanci A Musulunci (Hadisai Tamanin Da Biyu A kan Shugabanci); wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi. Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Hadisi Na Ɗaya A Kan Haramcin Goyon Bayan Azzaluman Shugabanni danna nan

  • Sahabban Da Suka Fi Kowa Rawaito Hadisai

    Sahabban Da Suka Fi Kowa Rawaito Hadisai

    Waɗannan sahabban su suka fi kowa rawaito hadisan Manzon Allah Sallahau Alaihi wasallam. Allah ya ƙara yarda da su.

    1. ABU HURAIRA (R.A) ya rawaito
    hadisai guda 537
    2. ABDULLAHI ƊAN UMAR (R.A) ya
    rawaito hadisai guda 2630
    3. ANAS ƊAN MALIK (R.A) ya
    rawaito hadisai guda 2286
    4. AISHA ‘YAR ABUABKAR (R.A) ta
    rawaito hadisai guda 2210
    5. ABDULLAHI ƊAN ABBAS (R.A) ya
    rawaito hadisai guda 1660
    6. JABIR ƊAN ABDULLAHI (R.A) ya
    rawaito hadisai guda 1540
    7.ABU SA’ID A KHUDRI (R.A) ya
    rawaito hadisai guda 1170

    Bayan waɗannan, babu wanda ya rawaito hadisai sama da dubu.