Tag: Aljanu

  • Guraren Da Aljanu Suka Fi Zama

    Guraren Da Aljanu Suka Fi Zama

    A wajen zama mun bambanta, sai dai da yawan mu muna rushe musu wurin zamansu sannan mu gina namu, kuma muna sare musu wajen zamansu mu dasa namu.

    Aljanu sun fi zama a cikin daji, saman dutse, saman ɗaki, cikin bola, cikin garken raƙuma, jikin shuri da dai sauransu. Da yawa akwai hatsari da mutum ya ga an share fili a daji ya tsugunna ya yi fitsari ko kashi.

    Akasarin irin wajejen nan aljanu ne suka yi jinya suka warke suka tashi a wajen don haka sai a kiyaye. Akwai waɗanda suke mu’amalantar mu a cikin gida, waɗanda su suke zama a cikin gida kamar yadda muke zama, haka kuma wasu daga cikinsu a hanya muke gamuwa da su, su rako mu har gida. Shi yasa musulunci ya koyar da mu addu’ar da za mu yi in za mu shiga gida da in za mu fita. Ya kamata in za ka bar gida sai ka ce;

    “Bismillahi tawakkaltu alallahi wala haula wala ƙuwwata illa billah, allahumma inni a’uzhu bika an adilla aw udilla, aw azilla aw uzalla, au azlima aw uzlama, aw ajhala aw yujhala alayya”

    Sannan in za ka shiga gida sai ka ce;

    “Bismillahi walajna, wa bismillahi kharajna wa’alal lahi rabbana tawakkalna”

    Amfanin addu’ar nan shi ne ko da aljanu sun biyo ka gida idan ka karanata wannan addu’ar za su ga babu ƙofa a gidanka, ba wurin zama sai su koma. Idan kuma ka yi sakaci wurin karanta ta, to za ka ga ka shiga gida cikin damuwa, da ƙunan rai da tashin hankali da jin haushin mutanen gidan. Daga lokacin shi kenan sun sami abinda suke so, ka yi ta faɗa da mutanen gida. Shi yasa musulunci ya koyar da mu hatta abinci in za ka ci ka ce bismillah, Allah ba zai ba su ikon su sa hannu su ci ba. In kuma ka gama cin abincin sai ka karanta wannan addu’ar;

    “Allahumma barik lana fi hi wa ta’amna khairan minhu”

    Idan ka yi wannan addu’ar Allah zai ba ka lada sannan kuma ya sa wa abincin da za ka ci albarka.

    Hatta kaya idan za ka cire, musulunci ya koyar da mu addu’a da ya kamata ka yi don ka samu kariya daga sharrin aljanu da sheɗanu. Don haka in za ka cire kayanka ka ce “bismillah” Allah zai rufe idanun aljanu ba za su ga tsiraicinka ba. Haka ɗakin da ya dade a rufe hatsari ne a shiga ba tare da an yi addu’a ba. Ko da shimfiɗa ce aka gyara ta domin a kwanta, musulunci ya koyar da mu ka karkadɗeta sau uku sannan ka yi addu’a ka kwanta. Kuma mu kiyaye zama a kofar ɗaki don wannan ma wurin zamansu ne.

    Sai a kiyayi zubar da ruwan zafi a makwarara, saboda nan ma wajen zamansu ne. Kuma a kiyayi zama a cikin ɗaki mai duhu da kuma yin surutu a bayi da zama kai ba ɗankwali da jiki a bude. Sai mu raba kanmu da yawan kalle-kalle marasa amfani ko jin kade-kade. Sannan uwar gida ki tattare kayanki da zarar magariba ta doso kai, ki killace yaranki, ki hana su zama ba riga, sannan a rufe kwanukan da aka ci abinci har dai za a bar su a waje. Wannan duk musulunci ya koyar da mu ne don kulawa da kanmu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Kalolin Aljanu Suke danna koren rubutun nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Samun Lafiya Ga Kowane Irin Ciwo danna koren rubutun nan.

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Matakan Da Za A Bi Domin Rabuwa Da Jinnu

    Matakan Da Za A Bi Domin Rabuwa Da Jinnu

    Akwai hanyoyi da yawa wajen rabuwa da irin waɗannan aljanu da ma wasu ba irin wannan ba. Ya zama duk inda aljani yake ajikin mutum sai ya gudu ya bar shi.

    Matakan Rabuwa Da Jinnu: Matakin farko akan so mara lafiya ta cire duk wani hoto a ɗakin da take kwana sannan ta kiyayi yawan kalle-kalle. Sannan ta sabarwa kanta kwanciya da alwala, idan za ta iya yi wa kanta ta yi da kanta, in kuma za ta sa ne a yi mata shi kenan, abinda dai ake so a yi shi yadda ya kamata. Duk lokacin da za ta kwanta bacci bayan ta yi alwala sai ta karanta waɗannan ayoyin kamar haka; 1. Aya ta ɗaya zuwa goma cikin suratul Kahf 2. Sai kuma ƙarshen suratul Mu’minun 3. Aya ta 54 zuwa ta 56 a cikin suratul A’araf Sannan ta karanta wannan addu’ar kamar haka;

    “Allahumma inni auzhubika min su’i ahlami, wa’astajiruka min talaubish shaidan fil yaƙzati wal manami”

    In kika karantata shi kenan sai ki yi baccinki. In Sha Allah muddin za ki kikayi wannan shawarar ba ki da matsala.

    Haɗin Turare

    Wannan turare aljani ba ya sonsa, duk inda ka turara aljani ba zai so wajenba In Sha Allah. Hannit Lubazzakar Habbatussaud Tafarnuwa Kajiji

    Waɗannan su ne za a haɗa su guri ɗaya sai a rinƙa turarawa. In kika yi haka ba ke ba aljanu In Sha Allah.

    Daddawar batso Habbatus sauda Kajiji Kustul hindi Al-mum Su ma turarawa za ayi da yardar Allah aljani zai bar jikin mutum da kuma gida. Sannan za a samu ruwa mai kyau, an fi son na zam-zam in ba a samu ba sai a yi amfani da ruwan rijiya ko kuma ruwan sama, ya zamo dai ruwan mai tsafta ne. Sai a yi alwala a nemi za’afaran mansa ko kuma garinsa sannan a samu ma’ul wardi sai kuma jan muski kaɗan sai kuma a samu ganyen magarya a niƙa shi a zuba kaɗan a ciki sannan a karanta wannan ayoyin kamar haka kowacce ƙafa bakwai ana yi ana tofawa cikin ruwa ko kuma numfashin na sauka cikin ruwan.

    Ga ayoyin kamar haka;

    Suratul Fatiha Suratul Baƙarah aya ta 1-5 Suratul Baƙarah aya ta 101-102 Suratul Baƙarah aya ta 255-256 Ƙarshen Suratul Baƙarah aya ta 273-277 Suratul A’araf aya ta 54-56 Suratul Yunus aya ta 90-92 Suratul Isra’i aya ta 109-111 Suratul Mu’minun aya ta 113-118 Suratul Kahfi aya ta 1-10 Suratul Saffat aya ta 1-11 Suratul Mulk Suratul Jinn Suratul buruj aya ta 1-3 Suratul Kafirun Suratul Ikhlas Suratul Falaƙ Suratul Nas Waɗannan ayoyin su za a karanta a tofa a cikin ruwan sai a ba wa mara lafiya tasha da safe kafin ta ce komai, ta shafe kanta da ruwan kaɗan, sai kuma da daddare kafin ta kwanta bacci ya zama shi ne ƙarshen abin da za ta sha ta kuma shafe jikinta gaba ɗaya.

    Sannan waɗannan ayoyin za a karanta su kamar yadda suke, a samo mayuka kamar haka;

    Man habba Man kwakwa Man alayyadi Man zaitun Jan Muski (ɗan kaɗan) Man ridi A haɗe su wuri guda a karanta waɗannan ayoyin a tofa a ciki ta rinƙa shafawa a jikinta musamman in za ta kwanta bacci. Duk irin taurin kai da aljani yake da shi to zai bar jikinsa da yardar Allah. Domin karanta cikakken bayani akan Hanyar Ƙona Aljani Ajikin Mutum danna koren rubutu. Domin karanta bayani akan Addu’a A Lokacin Da Mutum Ya Fitinu Da Wasuwasi A Cikin Sallah danna koren rubutu. Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu
  • Guraren Da Aljanu Sukafi Zama

    Guraren Da Aljanu Sukafi Zama

    A wajen zama mun bambanta, sai dai da yawan mu muna rushe musu wurin zamansu sannan mu gina namu, kuma muna sare musu wajen zamansu mu dasa namu.

    Aljanu sun fi zama a cikin daji, saman dutse, saman ɗaki, cikin bola, cikin garken raƙuma, jikin shuri da dai sauransu. Da yawa akwai hatsari da mutum ya ga an share fili a daji ya tsugunna ya yi fitsari ko kashi.

    Akasarin irin wajejen nan aljanu ne suka yi jinya suka warke suka tashi a wajen don haka sai a kiyaye. Akwai waɗanda suke mu’amalantar mu a cikin gida, waɗanda su suke zama a cikin gida kamar yadda muke zama, haka kuma wasu daga cikinsu a hanya muke gamuwa da su, su rako mu har gida. Shi yasa musulunci ya koyar da mu addu’ar da za mu yi in za mu shiga gida da in za mu fita. Ya kamata in za ka bar gida sai ka ce;

    “Bismillahi tawakkaltu alallahi wala haula wala ƙuwwata illa billah, allahumma inni a’uzhu bika an adilla aw udilla, aw azilla aw uzalla, au azlima aw uzlama, aw ajhala aw yujhala alayya”

    Sannan in za ka shiga gida sai ka ce;

    “Bismillahi walajna, wa bismillahi kharajna wa’alal lahi rabbana tawakkalna”

    Amfanin addu’ar nan shi ne ko da aljanu sun biyo ka gida idan ka karanata wannan addu’ar za su ga babu ƙofa a gidanka, ba wurin zama sai su koma. Idan kuma ka yi sakaci wurin karanta ta, to za ka ga ka shiga gida cikin damuwa, da ƙunan rai da tashin hankali da jin haushin mutanen gidan.

    Daga lokacin shi kenan sun sami abinda suke so, ka yi ta faɗa da mutanen gida. Shi yasa musulunci ya koyar da mu hatta abinci in za ka ci ka ce bismillah, Allah ba zai ba su ikon su sa hannu su ci ba. In kuma ka gama cin abincin sai ka karanta wannan addu’ar;

    “Allahumma barik lana fi hi wa ta’amna khairan minhu”

    Idan ka yi wannan addu’ar Allah zai ba ka lada sannan kuma ya sa wa abincin da za ka ci albarka.

    Hatta kaya idan za ka cire, musulunci ya koyar da mu addu’a da ya kamata ka yi don ka samu kariya daga sharrin aljanu da sheɗanu. Don haka in za ka cire kayanka ka ce “bismillah” Allah zai rufe idanun aljanu ba za su ga tsiraicinka ba.

    Haka ɗakin da ya dade a rufe hatsari ne a shiga ba tare da an yi addu’a ba. Ko da shimfiɗa ce aka gyara ta domin a kwanta, musulunci ya koyar da mu ka karkadɗeta sau uku sannan ka yi addu’a ka kwanta. Kuma mu kiyaye zama a kofar ɗaki don wannan ma wurin zamansu ne.

    Sai a kiyayi zubar da ruwan zafi a makwarara, saboda nan ma wajen zamansu ne. Kuma a kiyayi zama a cikin ɗaki mai duhu da kuma yin surutu a bayi da zama kai ba ɗankwali da jiki a bude. Sai mu raba kanmu da yawan kalle-kalle marasa amfani ko jin kade-kade.

    Sannan uwar gida ki tattare kayanki da zarar magariba ta doso kai, ki killace yaranki, ki hana su zama ba riga, sannan a rufe kwanukan da aka ci abinci har dai za a bar su a waje. Wannan duk musulunci ya koyar da mu ne don kulawa da kanmu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Kalolin Aljanu Suke danna koren rubutun nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Samun Lafiya Ga Kowane Irin Ciwo danna koren rubutun nan.

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Yadda Kalolin Aljanu Suke

    Yadda Kalolin Aljanu Suke

    Aljanu kala-kala ne kamar yadda muke nau’in mu kala-kala:

    Ga kalolin Aljanu kamar haka:

    • Jinnul gawas
    • Jinnul ɗayyar
    • Jinnul bait
    • Jinnul jalab wal tahdir
    • Jinnul majus
    • Jinnul yahudi
    • Jinnul nasari
    • Jinnul muslim
    • Jinnul ashiƙ
    • Jinnul kamil
    • Jinnul tabdil
    • Ifritu minal jinn

    Waɗannan su ne kaɗan daga cikin kalolin aljanu, kuma kowanne aljani akwai alamominsa sannan akwai irin nau’in magungunansa. Akwai jinnu da yake kama da mutane sannan akwai jinnu da ake tura shi ya shiga mutum.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Alamomin Jinnu Yake danna koren rubutu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mutane Biyar Da Suka Yi kama Da Manzon Allah (S.A.W)

  • Yadda Nau’ikan Aljanu Suke

    Yadda Nau’ikan Aljanu Suke

    Kamar yadda muke da mata da maza, haka ma aljanu suke da mata da maza, yara da manya, tsoho da tsohuwa, sarakuna da talakawa, masu arziki da kuma matsiyata kuma musulmai da kafirai.

    Kamar yadda Allah (Subahanahu Wata’ala) ya faɗa acikin Al Ƙur’ani mai girma a cikin suratul jin;

    “Wa’anna minnas salihuna waminna du na zalika kunna ɗara’iƙa ƙidada”

    Domin karanta cikakken bayani akan Guraren Da Aljanu Sukafi Zama danna nan.

    Domin karanta bayani akan Addu’ar Da Ba ta Dawowa In An Yi Ta danna nan