Saƙo Maƙoƙo

0
49

Abba Yusuf

Sallama farko na miƙo
Ɗan ƙasa ne ko kwa baƙo
Wanda ke sama to ya sauƙo
Ya ji saƙon umma kuma ya karɓa.

Magana zan yo a kanta
Tsohuwar nan ta wahalta
Ni fa tinda na zo cikinta
Na fahimci akwai abin da bai ba.

Nai mafarki ne da umma
Ta faɗan magana da dama
Dan akwai maganar da ai ma
Ba buƙatar bayyana ta nan ba.

Wata ƙila wanin ku zai ce
Wacce umma hala mutum ce
Ko kwa aljan to wace ce
Ɗan uwa ƙasarmu nai nufi ba.

Ƙorafinta da tai na farko
Kan ɗiyanta na farko-farko
Sai ta yo ƙasa can ta sakko
Sai ta yo maganar da zan faɗi ba.

Tunda nai aure na farko
Ga sadaki har da baiko
Har na haifi wasunku aiko
Aka auran wanda ban nufi ba.

Ku kuke nemo mazajen
Da kuke so sai ku auren
Sai su zo ƙarshe su cucen
Su sakeni su bar ni da ciki ba.

Kansu sau ni su illata ni
Kalli duk sun raunata ni
Ga jikina ya yi rauni
Ni fa ko, ba zan ƙi in mace ba.

Da abin a iya garen ne
Kan tsaya to da sumul ne
To fa kuma duk a jone
Kuke kan wahalar da ke zuwa ba.

Sai nace mata ya uwarmu
Yanzu menene kalamu
Wa kike so ne ki samu
Ki yi wuff da abinki ne nufi ba.

A a na ga kuna ta naci
Za ku je tonan muruci
So kuke ku daɗe ni ƙunci
Ni da ku ai duk muna ta karɓa.

Nifa dimukradiyar ce
Bam biɗa in dai wannan ce
Tinda an yi gwaji shiru ce
Babu canji ko da na sile ba.

Abba Marke ka cewa sauran
Su ji tsoran rabbu sarkin
Da ya yi ni ya yi ku haƙƙun
Su fitar ni hannun birirrika ba.

Don karanta Duka A Murɗe danna nan

Edita; Rumasa’u M. kallamu

 

labarin da ya wuceYin Amfani Da Maganin Sauro Na Ƙonawa
Labarin na GabaNasiha A Kan Mata