Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Ɗaya

0
108

Duk da bai ce mata zai zo yau ɗin ba amma dai haka kawai zuciyarta take gaya mata zai zo tunda an buɗe gari kuma tun wancan lokacin da aka buɗe gari ba su haɗu ba. Ta san dai yana jin haushinta daga yanda yake amsa wayarta amma ta nutsu a zuciyarta cewa zai zo ɗin.

Tun wuri ta tashi ta yi wanka ta shirya don ya same ta a shirye; sai dai ga mamakinta har azahar tana zaune a parlor tana ta faman duba waya, duk wanda ya buga gate da hanzari take tashi ta buɗe tana saka rai Mustapha ne amma har la’asar bai zo ba.

Dab da la’asar tana zaune a parlor tana ta faman latsa waya tana duba whatsapp ko ya buɗe saƙon da ta tura masa amma ga mamakinta har zuwa lokacin bai buɗe ba. Mommy ce ta fito daga ɗakinta; har ta kama hanyar kitchen sai kuma ta kula da Khadeeja a zaune a parlor ɗin.

Ta dawo ta tsaya tace ‘Ya na ganki a nan, ina Nabila PA ɗin taki?’ Ta yi dariya tace ‘Tana can tana abinda ta saba wato bacci. Ta wuce kitchen ta bar ta a nan, jimawa kaɗan ta fito ta dawo parlor ɗin ta zauna a kan three seater daga bangareb da yafi kusa da single seater din ta Khadeeja take zaune.

Ta ɗan yi gyaran murya tace ‘Uhm, ai na zata Mustapha zai zo yau ɗin, ko sai da yamma zai zo?’ Ta ɗan gyara zama tace ‘Umm! Ina jin dai sai da yamman, wataƙila gidansu ya wuce tunda shi da yara ne.’ ‘Um to bari mu gani. Amma dai kuna waya ko?’ ‘Eh, jiya da daddare ma mun yi magana.’

‘Ai shikenan bari mu gani. Suka yi shiru na ɗan lokaci; jimawa kaɗan tace ‘Mommy kina neman Mustaphan ne da naga kamar jiransa kike yi? Ta jijjiga kai tana murmushi ‘A a me zai yi min; kawai dai na san ya kamata a ce ya zo ya duba ki ko, ai ko gaisawa ne a yi duk da dai da an sallace za ki koma.’

Ita ma dariyar ta yi sannan tace ‘Zai zo Mommy in sha Allahu.’ Abu kamar wasa har aka sha ruwa babu Mustapha babu labarinsa’ haka dai ta lallaɓa ta ci abincin ba tare da tana jin daɗinsa ba. Tana kula da yanda Mommy ta saka mata ido sosai tana kula da duk wani motsinta tun ɗazu da suka yi magana.

Sai da aka tafi sallar isha’i lokacin ‘yan gidan duk sun tafi masallaci sannan Mommy ta kirawo ta; ta riga ta san kiran don haka cikin sanyi ta tashi ta wuce ɗakin Mommy ɗin. A zaune a kan dadduma ta same ta don haka ta zauna daga gefenta a kan kafet. Sai da Mommy ta ɗauki lokaci tana kallon fuskarta kamar mai karanta littafi sannan tace ‘Wai ya aka yi Mustaphan bai zo ba?

Gashi kin san ba za a sake buɗe gari ba sai satin sallah. Ko wani abu ne ya tare shi?’ ‘Umm! Kin san sai sun je office da zarar an buɗe gari. Sai da aka fara kiran magariba sannan ya kirawoni yake gaya min a lokacin yake barin office ga shi yana so ya isa gida kafin a fara tare hanya.’ Ta sharo ƙarya.

Ta sake kakkafe ta da ido na ɗan loakci sannan tace ‘Umm! Ko dai fushi yake don an ce ba za ki koma sai bayan sallah? Na ga fa bai sake zuwa ba tun wancan lokacin da ya zo ɗaukanki ba ki bi shi ba.’

Ta sunkuyar da kai tana ‘yar dariya tace ‘Umm, ya ma gama fushin ai. Da farko ne ya fara fushin ya zata zan fasa zama har bayan sallar amma daga baya da ya ga ba zai sami yanda yake so ba ya hakura.’ ‘Umm! To ko shi yasa bai zo ba?’

‘A a fa Mommy, na gaya miki ya je aiki ne shi yasa ya makara bai zo ba. Idan aka sake buɗe gari ko kuma ranar sallah zai zo.’ ‘To Allah ya kai mu. Idan dai da akwai wata matsala gara ki faɗa tun kafin ki koma a san matakin da za a ɗauka don na kula kamar akwai abinda kike ɓoyewa.’

Ta ɗan yi murmushi sannan tace ‘Babu wani abu fa Mommy, aiki ne kawai da raino; kin san harkar yara. Bana samun lokacin kaina kullum cikin hidimarsu nake. Shi yasa tunda Biba ta tafi ban sami natsuwa ba. Kin ga yanzu kin ce kafin sallah za a samo min yarinya sai mu koma tare, daga wannan babu wata matsalar.’

Ta kalle ta da alamomin tambayoyi domin jikinta yana ba ta kamar akwai abinda Khadeejan take ɓoye mata, amma babu wani abu da za ta iya yi a kai tunda ba ta ma san menene matsalar ba. Tace ‘To kuma shi Mustaphan ba ya baki wata matsala? Ta yi dariya ‘Mommy kema dai kin san da da matsala da tuni na gaya miki fa, babu komai.’

Dole Mommy ta haƙura ta ƙyale ta da tambayoyin nan ba don ta gamsu da amsoshin da ta bayar ba. Sai da ta yi da gaske sannan ta hana kanta kiran Mustapha a wannan daren; ta yi wa kanta alƙawarin daga yanzu ba za ta sake kiran shi ba har zuwa bayan sallah. Idan ya zo su koma, idan kuma bai zo ba ita dai to ba za ta neme shi ba. Haka ta kwana tana matse ƙwalla.

Duk yanda ya so ya daure zuciyarsa daga sharewar da Khadeeja ta yi masa zuwa yanzu ya gaza; ya riga ya saba tana kiransa tana lallaɓa shi da ba shi haƙuri amma shiru. Yana kallon kiranta ranar Asabar ya ƙi ɗauka don ya san za ta ce ya zo gidansu ne; shi kuma ba zai je ba in dai ba ɗaukanta zai je yi ba. Don haka ya ƙi ɗaukan kiran yana sa ran idan dare ya yi ma za ta sake kira, a lokacin sai ya ba ta uzurin dare ya yi.

Sai dai har ya kai yaran gidan Mama ya wuto gida ya gama duk abinda zai yi ba ta sake kira ba; lokacin da ya tashi sahur ma wayar ya fara dubawa ya ga ko ta kirawo yana bacci amma ga mamakinsa babu kiranta ko ɗaya. Haka ya yi sahur ya gama ibadarsa ya kwanta.

Sai da gari ya waye zuwa azahar sanna ya tuna akwai messages ɗinta na whatsapp da ta turo bai buɗe ba don haka ya je ya lalubo saƙonnin ya buɗe. Ya bi su ɗaya bayan ɗaya ya tura mata amsa, wanda tambayarsa take yi ko zai zo sannan tana gaya masa kayan da zai ɗauko mata a ɗakinta ya taho mata da su.

Har zuwa la’asar ba ta amsa saƙonninsa ba sai dai sun nuna alamar sun shiga; ya buɗa whatsapp sau babu iyaka amma har zuwa lokacin ba ta karanta saƙonninsa. Ba ta taɓa share shi haka ba; to ko dai ba ta da lafiya ne? kada fa ya je wani abu ne ya same ta don idan dai Khadeeja ce ya san za ta neme shi.

Zuciyarsa tana gaya masa wulaƙanci ne kawai take so ta yi masa don haka ya rabu da ita duk da yanda ya kasa cire tunaninta daga ransa. Haka suka zauna ba sa waya kuma ga saƙonninsa nan ta gani amma ta ƙi ta ba shi amsa. Ranar jajiberin sallah ya kasa jurewa shiru ɗin don haka ya kirawo ta; wayar tana dab da tsinkewa sannan ta amsa.

Murya ƙasa-ƙasa cikin halin ko in kula tace ‘Bana kusa da wayar ne. Kwana biyu na jiki shiru ne, kuna lafiya? Lafiya Alhamdulillahi. Ya yarana?’ Suna nan ƙalau, suna gidan Mama. Allah sarki, don Allah in ka je kace ina gaida su maman.’ Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan yace ‘Kin yi zamanki a gida gaba ɗaya kin manta da ni ko?’

Ta yi ‘yar dariya tace ‘Ka dai manta da ni. Ko kayan sallarki ma ba ki tambaya ba. Uhm, akwai wasu ma a nan da Mommy ta ɗinka min. To ya kike? Lafiya dai kike ko?’ ‘Lafiya ƙalau. Suka ɗan taɓa hirar haka wadda duk gaba ɗaya kusan shi ne yake ta daddagewa don ita ma ta ji haushin abinda ya yi mata, daga baya yace ‘Gobe fa Sallah, yaushe zan zo mu taho gida?’

‘Umm, in dai ka cire jibi duk lokacin da ka shirya za ka iya zuwa mu tafi, tunda an riga an samo min mai aiki ga ta har ta koyi duk wani aiki da nake so. Uhm, dole dai sai kin sani cin tuwon sallah a gidan hajia ko? To ina laifi, idan ka ci ni ma ka yi min take away.’ Haka suka cigaba da hirararsu a hankali suna sakewa, daga baya suka yi sallama a kan ranar sallah zai zo ya ci tuwo kafin ya wuce gidan Hajia.

Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceMijin Marigayiya Babi Na Goma
Labarin na GabaYadda Ake Addu’ar Gamuwa Da Abokan Gaba Ko Wani Mai Iko 
Sakina Muhammad Yazid
Ni ma'abociyar son rubuce-rubuce ce, malama kuma mai gudanar da sana'o'i. Ina ƙarfafawa matasa gwuiwa ta hanyar jagorantarsu da koyar da su. Ina rubuta labarai masu jan hankali kuma masu ƙunshe da tsari da al'adun Bahaushe.