An karɓo daga Jarir ɗan Abdullahi (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Duk wanda ba ya tausayin mutane Allah ba zai tausaya masa ba”.
Bukhari da Muslim da Tirmizi ne suka rawaito shi. Ahmad ma ya rawaito shi ya ƙara da cewa: “Wanda ba ya afuwa Allah ba zai yi masa afuwa ba”.
Domin karanta cikakken bayani a kan Hadisi Na Biyu Akan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu danna nan.
Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Shugabanci A Musulunci (Hadisai Tamanin Da Biyu Akan Shugabanci) wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.








