Fitattun Iyayen Gida Na Ɗanƙwairo A Kiɗan Fada

0
11

Bisa dukkan hasashe, ubangida a wajen Makaɗi yakan zama mutum wanda ya nuna damuwa a harkoki da al’amurran makaɗi; wataƙila kuma makaɗin nan ya fi daidaita tunaninsa da zubin waƙoƙin da yake yi masa.

Ubangida yakan zama murabbi ta fuskar kyautata ayyukan makaɗa don su zama na ƙwarai.

Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo tun a farko-farkon tsundumarsa a cikin waƙoƙin baka, Allahu ya hore masa irin waɗannan dattawan iyayengida.

Muhimmai daga cikinsu sun haɗa da:

a) Abubakar na Birnin Ƙaya a Gundumar Maradun
b) ‘Yandoton Tsahe, Alhaji Aliyu II (1960-1991)
c) Sardaunan Sakkwato, Firimiyar Jihar Arewa, Alhaji Sir Ahmadu Bello Sakkwato (1962-1966)
d) Sarkin Maradun Alhaji Abubakar (1939-1964)
e) Sarkin Maradun Muhammadu Tambari (1964-1981)

f) Sarkin Maradun Ibrahim II, Maigandi (1981-2003)
g) Sarkin Daura, Alhaji Muhammadu Bashar (1966-2007)
h) Sarkin Sudan, Alhaji Shehu Malami Wurno
i) Sarkin Das, Alhaji Bilyaminu Usman
j) Da sauransu

Domin karanta cikakken bayani a kan Ƙungiyar Makaɗa Musa Ɗanƙwairo Ta Kiɗa danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Waƙa A Matsayin Sana’a danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceSauran Waɗanda Suka Yi Shahada Tare Da Husaini (Radiyallahu Anhu)
Prof. Sa’idu Muhammad Gusau
FARFESA SA'IDU MUHAMMAD GUSAU, An haife shi a Gusau jihar Sakkwato, (Maris 24, 1952). Ya yi karatun firamare na Islamiyya daga 1965-1969, ya je kwalejin sarkin Musulmi Abubakar daga Junairu 1970 zuwa Yuni 1973. Ya yi Diploma, Digiri Na farko (B.A), na biyu (M.A) da Digiri na uku (Ph.D) duk a jami'ar Bayero, Kano.