Falalar Salati Ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam)

0
38

Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; wanda ya yi salati ɗaya a gare ni, Allah zai yi salati goma a gare shi’.

Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘kada ku mai da ƙabarina idi; ku yi salati a gare ni ko ina kuka kasance’.

Kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Marowaci shi ne wanda aka ambace ni a wurinsa amma bai yi mini salati ba’.

Kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Allah yana da waɗansu mala’iku matafiya a bayan ƙasa; suna isar mini da sallama daga al’ummata’.

Sannan kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Babu wani wanda zai yi mini sallama face Allah ya dawo mini da raina na amsa sallamarsa’.

Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Yaɗa Sallama A Cikin Al’umma danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Wane Ne Ya Raɗa Wa Manzon Allah(S.A.W) Suna Muhammad? danna nan.

 

labarin da ya wuceGarin Kunun Aya
Labarin na GabaMatasa
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.