Category: Tarihi

Mun samar da wannan ɓangaren ne domin samar da dukkanin Tarihi a cikin harshen Hausa a sauƙaƙe.

wikiHausa ta kowa ce. Kowa zai iya taimakawa da ilimi ko gyara. Bugu da ƙari, kowa na iya amfani da wannan kafa wajan ɗora Tarihi ko saukewa

  • Tatsuniyar Dogarawa Uku

    Tatsuniyar Dogarawa Uku

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wasu dogarawa ne dai su uku masu suna Gi da Ɗa da kuma Ɗo. Aikinsu shi ne gadin gidan Sarki. To, akwai wani mutum kuma a garin sunansa Giɗaɗo. Shi ke nan, Sarki kuma yana da kaji da yawa a gidansa. Wadannan dogarai kuma su Gi da Ɗa da Ɗo kullum suna zuwa kamun fari.

    Idan sun zo da su sai su zuba wa kajin Sarki. In kajin sun ga farin, sai su zo suna ci. Su kuma dogaran sai su kama guda uku, kowa da tasa. Sai su je su gasa, su ci. To, kullum a ƙofar gidan Giɗaɗo suke gasawa. Shi ke nan, yau da gobe, sai Sarki ya ga kaji suna ƙarewa. Sai aka soma bincike; in aka tambayi wannan, sai ya kalli wancan.

    In aka tambayi wancan, sai ya kalli wannan. Sai Sarki ya ce in ba su faɗa ba, za a kashe su. To, akwai wani Bafulani da kan kai wa Sarki nono kullum. To, in ya tashi zuwa sai su haɗu da Gi, da Ɗa da Ɗo. To, ba ya iya bambanta sunayensu. In ya tashi kiran su, sai ya ce: “Giɗaɗo.” Kullum in sun haɗu, sai ya ce: “Giɗaɗo, ina za ka je?”

    Sai su ce ai Sarki ne ya aike su, su kai kaji wani gida. Kullum haka. Shi ke nan, ana cikin yi musu tambayoyi game da ɓacewar kajin Sarki, sai ga Bafulanin nan ya zo. Da ya ji zancen da ake yi, sai ya ce ai ya san waɗanda suka ci kajin. Sai aka ce to, ya faɗa. Sai ya ce: “Ai Giɗaɗo ne.” Sai Sarki ya ce: “Kai ɗan Fulani, ka faɗi gaskiya.

    Giɗaɗo ba zai zo ya kama kaji a gidana ya ci ba.”Jin haka ya sa Bafulani ya ce: “Wallahi Giɗaɗo ne yakan ci kaza kullum. Idan ina zuwa kawo nono mukan haɗu yana riƙe da kaza. Kuma idan na ce ina za shi da kaza, sai ya ce Sarki ya aike shi.” Sai Sarki ya ce a je gidan Giɗaɗo.

    Da aka isa ƙofar gidansa, sai aka tarar da gashin kaji ya cika ƙofar gidan, saboda kusa da gidansa dogarawan Sarki kan je su fige kajin da suka sato daga gidan Sarki. Sai aka ce to a shiga a kamo shi. Sai aka shiga gidansa, aka kamo shi. To, da aka tambaye shi bayani a kan kaji, sai ya ce shi bai sani ba, don shi bai isa cin kaza ba, balle ya je gidan Sarki da masu gadi, har ya kama kaza, ya gasa, ya ci.

    Sai Sarki ya ce: “To, in ba kai ba ne, sai ka gaya min wanda zai zo ƙofar gidanka da kaza, ya yanka, ya fige, kuma ya gasa, ba ka sani ba.” Giɗaɗo ya ce sam-sam, shi bai sani ba, kuma bai san wanda ya ci kaza ba. Sai Sarki ya kasa gane gaskiyar al’amari. Sai dogarawa suka ce tun da a ƙofar gidansa aka ga gashin kajin, ai sai a kashe shi.

    Sai Sarki ya ce to a kama shi a kashe. Sai Gi da Ɗa da Ɗo suka ingiza ƙeyarsa waje, suka je suka kashe shi. Da yake da man ba su da gidajen kawunansu, sai suka mamaye gidansa, watau sun ci nasara, har da gadonsa. Sarki bai san maciya kajinsa ba. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kuskure ne a zartar da hukunci ba tare da yin kyakkyawan bincike ba.
    • Maciyin amana komai daɗewa sai ya ga mummunan sakamako.
    • Ba a yin azzalimin sarki, sai bafade.
    • Wata shari’ar sai a lahira.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Ɗantsintuwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ɗantsintuwa

    Tatsuniyar Ɗantsintuwa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wata mata da mijinta, suna zaune a wani ɗan kauye. Sun daɗe tare, to amma Allah bai ba su haihuwa ba. Wata rana matar nan ta je gona, sai ta tarar da jinjiri a kan dutse, sai ta ɗauko. Ashe wannan yaro ba mutum ba ne, ɗan aljani ne, ba ta sani ba.

    Sai ta kawo yaron gida. Da mijin ya ga yaro, sai ya tambaye ta inda ta samo shi. Sai ta ce, ai ɗan tsintuwa ne, sai mijin ya ce, anya wannan mutum ne kuwa? Sai matar ta ce ai da ma ta san zai ƙi amincewa da yaron. Don gudun zuciyar matarsa, sai ya ce: “To, shi ke nan na yarda mutum ne, kuma ki riƙe shi.” Suka ci gaba da renon yaron.

    To, matar kullum tana zuwa gona da yaron. Daga ƙarshe dai ta samo yarinyar da za ta riƙa yi mata reno a gidan idan ta tafi gona. Kullum idan za ta tafi sai ta dafa musu abinci. To, da zarar ta tafi gona ta bar su da mai renon, sai ya rikiɗa ya zama babba ya kama yarinyar nan ya ɗaure, ya cinye abincin duka ya hana ta, ya yi ta wasanni iri-iri da rawa.

    Sai ya lura matar nan ta kusa dawowa daga gona, sai ya kunce mai renonsa ya koma yaro, ya yi ta birgima a ƙasa yana kuka. Idan iyayen sun dawo sai su hau kan mai reno da duka. Idan za ta yi magana ko bayani, sai su ce ta yi shiru, domin su a ganinsu yaron yana kuka ne saboda ta hana shi abinci, kuma tana dukan sa, har yana birgima.

    Kullum haka, sai wata rana wata tsohuwa maƙwabciyarsu ba ta je gona ba. Tana ɗaure dangarta, sai ta hango ɗan jariri ya miƙe, ya ɗauko igiya ya ɗaure mai renonsa, ya fara waƙa, yana rawa. Ya kuma cinye abinci duka, ya hana ta, tana ɗaure. Haka tsohuwa ta yi ta leƙen su, har yamma ta yi.

    Sai ta ga ya koma yaro, ya kama birgima, yana kuka, har iyayen suka dawo. Washe-gari sai tsohuwa ta yi kiran masu gidan, ta zana musu duk abin da ta gani. Ta ce idan sun shirya za su gona, su je gidanta su ɓuya, za su ga duk abin da yake yi. Sai suka amince. Washe-gari, suka shirya tafiya gona, amma sai suka shiga gidan tsohuwa suka ɓuya.

    Can sai yaron ya fara yin abin da ya saba, suna gani, abin ya fara ba su mamaki, har ya gama. Da suka dawo gida, sai suka ƙi dukan mai reno, shi kuma sai ya ƙi barin kuka. Sai matar ta shirya, ta tafi gidan boka, ta yi masa bayani.

    Sai boka ya ce, idan ta je gida washe-gari da safe ta sayo ɗan akuya ƙosasshe, ita da mijin su ja shi su yi ta tafiya, sai sun ga wata babbar bishiyar kuka. Ya ƙarasa da cewa: “Sai ku ajiye yaron, ku ce za ku huta. Sai ku ɗaure ɗan akuyan. Sai mijinki ya ce zai je ya yi fitsari, sai ya gudu. Ke kuma, sai ki ce za ki dubo shi, sai ki bi shi, kada ku juya”.

    Sai suka amince. Da gari ya waye, sai suka je suka samo ɗan akuya ƙosasshe, suka ɗaura igiya a wuyansa. Sai suka ce za su je wani ƙauye gaisuwa, sai matar ta ɗauki yaro ta goya, suka kama hanyar daji. Suna cikin tafiya, sai suka hango wannan babbar kuka, sai mijin ya ce su je su huta a gindinta.

    Da suka je, sai suka yi duk yadda bokan nan ya ce su yi, watau suka yi dabara, suka gudu. Da suka isa gida, sai tsohuwar ta sami matar ta ce to daga yau ta daina ƙwadayin sai ta sami ɗa ta kowace hanya, kuma ta rungumi ƙaddara sai abin da Allah ya yi da ita a rayuwarta.

    Da ɗan aljani ya gaji da jira, ya ga shiru, sai ya miƙe ya kunce ɗan akuya, ya riƙe, ya kama hanyarsa, ya shiga ƙungurmin daji, bai sake komawa gidan mutanen nan ba. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Zafin nema ba ya kawo samu.
    • Yi haƙuri da godiya ga abin da Allah ya ƙaddara a rayuwarka ta duniya.
    • Tsintacciyar mage ba ta yin kyanwa
    • Son zuciya, ɓacin zuciya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Ɓarayin Albagadadi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ɓarayin Albagadadi

    Tatsuniyar Ɓarayin Albagadadi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani attajiri a wani gari ana kiran sa Albagadadi. Ba abin da yake so kamar ya ji wani yana neman taimako, domin ya taimaka masa. Duk ranar Jumma’a mutane kan taru maƙil a ƙofar gidansa, suna karɓar sadaka.

    Ana nan, ana nan, wata rana sai wani saurayi ya je wajensa ya ce masa yana son masauki, ko ya sami aikin yi a garin. Sai Albagadadi ya sauke shi a gidansa. Sannu a hankali, sai yaron nan ya zama hadiminsa, watau ya riƙa yi masa aikace-aikacensa na gida. Yaron kuma makarancin Alkur’ani ne sosai.

    Kullum idan Albagadadi zai je unguwa, ko dai wani wuri, to tare za su. Sai mutane suka sa wa yaron suna Sheikh Ali Albagadadi. Tun da yaron nan ya shiga gidan Albagadadi, sai komai nasa ya sauya; arziƙin uban gidansa ya yi ta bunƙasa. Duk abin da ya saya, ko gonar da ya noma, sai riba ta riɓanya ta da.

    Wata rana Albagadadi ya zauna tare da abokansa, sai ya kira Sheikh Ali ya ce yana son duk wanda yake wurin ya ba shi wani labari da zai faranta masa rai, zuciyarsa ta kwanta. Sai Sheikh Ali ya ce: “Wanda duk ya yalwata wa wanda ke cikin matsi, to shi ma Allah zai yalwata masa duniya da lahira.

    Wanda ya rufa asirin wani a yayin da yake buƙatar rufin asiri, to shi ma Allah zai rufa masa asiri duniya da lahira. Kuma duk wanda ya ba da sadaka tamkar wanda ya yi shuka ne, domin idan aka shuka masara kwaya uku, za katarar ta tsiro fiye da dubu uku. Kamar haka ne Allah yake saka wa masukyauta.”

    Duk wurin aka yi tsit ana jin bayaninsa. Sai ya ci gaba da cewa: “Ita sadaka takan gusar da bala’i da masifa, ta karya maƙiyi da Shaiɗan, kamar yadda ruwa yake kashe wuta, kuma ta goge zunubin mutum.” Kafin Sheikh Ali ya gama zancensa mai amfani, sai ya ga hawaye na kwarara daga idanun Albagadadi.

    Ganin haka sai ya dakatar da maganarsa. Rannan suna gida da daddare, sai suka ji muryar mutane a cikin gida. Ashe ɓarayi ne riƙe da makamai suka dira gidan da nufin yin sata, to amma ba sa iya ganin komai a cikin gidan. Can dai Ali Albagadadi ya yi tari, kuma tarinsa sai ya fasa ɓarayin, suka runtuma da gudu.

    A garin gudu, ɗaya ɓarawon ya faɗa rijiya, wuyansa ya karye. Na biyun kuma ya faɗa wani gida a kan wani dutse mai kaifi, shi ma ya mutu. Na ukunsu da ya samu ya fita bayan gari yana gudun ’yan bin sawu, sai ya yi ƙundunbala ya faɗa a kan wani kwazazzabo da yake zato tafki ne.

    A nan take shi ma ya sheƙa lahira. Da gari ya ƙarasa wayewa, jama’a suka daɗa taruwa, sai aka ɗebi ɓarayin nan aka binne su a rami. Mutanen garin suka yi ta mamakin yadda ɓarayin nan ba su saci komai a gidan Albagadadi ba, kuma sai suka riƙa cewa Allah ne ya kare shi saboda taimakon da yake yi wa mutane.

    Wannan kariya da Allah ya ba Albagadadi daga muguwar aniyar ɓarayi ce sanadiyyar da mutanen garin idan za su nemi tsari daga maƙiyansu sukan ce: “Kamar mutuwar ɓarayin Albagadadi.” Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ladabi da biyayya kan jawo arziƙi.
    • Mai arziƙin da ke tallafa wa mabuƙata Allah ne zai kare shi ya daɗa bunƙasa arziƙinsa.
    • Kyauta sadaka ba sa tauye arziƙin kowa.
    • Aikata alheri ga kowa, sakayya na wurin Allah.
    • Sadaka maganin asara.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Ƙuda Mai Kwaɗayi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ƙuda Mai Kwaɗayi

    Tatsuniyar Ƙuda Mai Kwaɗayi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wata ƙuda da ’ya’yanta. Kullum sukan je mahauta a kasuwa neman abin da za su ci, idan sun ƙoshi su koma gida. Wata rana sai ƙudar ta ja ƙawarta suka je mahautar neman abinci tare.

    Bayan sun samo, sai suka kama hanyar gida domin ita mai ’ya’yan ta kai musu gida, ta yi wa ƙananan cikinsu ƙoto. A kan hanyar komawa sai suka gamu da wani mai zuma. Sai ƙudar ta ba ƙawarta ƙunshin abincin da ta samo wa ’ya’yan ta kai musu, saboda za ta bi mai zuma ko ta kalato musu zumar.

    Kawarta ta karɓi jaka ta nufo gida, ta ba yara; sai babbar cikin ’ya’yan ta tambayi inda mahaifiyarsu ta tafi. Kawar ta ce mata ta bar gyatumarsu a kasuwa, wurin mai zuma. Ko da ta ji haka, sai ta kama kuka ta ce ai kwanan uwarsu ya ƙare, tun da ta bi mai zuma.

    Sai yarinyar da ƙawar uwarta suka yanke shawarar gara su je kasuwar su gani ko za su taho da ita. Sai suka hangi mai zuma, suka leƙa jikin ƙwaryarsa, sai suka gan ta a manne cikin sakar zuma, ta mutu.

    A nan duk suka fashe da kuka, suka tashi fir, ba su tsaya ba sai gidansu. Da suka ba da labarin rasuwarta, sai aka shiga zaman juyayi. Duk inda kuka ga ƙudaje sun taru cunkus, to zaman juyayin suke yi. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabudin wahala.
    • Garin neman gira, an ya da ido.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Auta Da Dodanniya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Auta Da Dodanniya

    Tatsuniyar Auta Da Dodanniya

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani gari wai shi Shadafi. Mutanen wannan garin koyaushe suna zaune cikin tsoro, saboda wata dodanniya da takan cinye duk wanda ya fita waje daga faɗuwar rana har gari ya waye. Ana nan, ana nan, sai dodanniyar nan ta lura takan zagaye garin baki ɗaya ba tare da ta sami wanda za ta cinye ba.

    Sai ta dinga yi wa kanta kirari tana cewa:

    “Wa zai iya da ni,

    Ni dodanniya,

    Wa zai ja da ni,

    Ni dodanniya.”

    Kowa ya yi shiru, ba wanda ya taɓa tanka mata, ko da sau ɗaya. Kwanci tashi, sai kawai wata rana wani baƙon saurayi ana kiran sa Auta ya je garin yawo. Da ya nemi masauki, sai kowa ya ki saukar da shi a duk faɗin garin, sai can dai wani tsoho ya ce masa zai ba shi masauki a wani gidansa da ba kowa a ciki, idan ba ya jin tsoro.

    Sai saurayi ya ce wa tsoho shi ba ya fita hira. Sai tsoho ya ce da shi to kada ya fita da daddare, domin idan ya fita, to tasa ta kare, saboda ƙila dodanniyar nan da ta addabi garin ta cinye shi. Saurayi ya yi murmushi, ya dubi tsoho ya ce: “Ba abin da zai sami mutum wanda Allah bai nufa ba.”

    Tsoho ya raka shi masaukinsa. Suka yi sallama tsoho ya koma gida, ya bar shi. Ko da suka rabu sai Auta ya zaro wata doguwar wuƙarsa ta farauta ya wasa, ta yi kaifi. Daga nan ya ɗauko wata ƙatuwar fitila, ya ajiye. Can cikin tsakiyar dare, sai ga dodanniya ta fito tana cewa wa zai iya ja da ita a garin nan, “Wa zai iya bugawa da ni, ni dodanniya?”

    Da Auta ya ji, sai ya kunna fitila, ya ajiye a daf da bakin ƙofa, ya ɗauko wuƙa ya riƙe a hannu. Sai ya kare inda zai tsaya da wani tsumma don kar fitila ta haska shi. Sai ya buɗe kofa, ya dubi inda dodanniya take, ya ce mata: “Ga ni, ni ne Auta, ni zan iya ja da ke; kuma in tsiya ce, har ma na fi ki.”

    Kafin ka ce kwabo ta zo da gudu, buguzum-buguzum, wai kar ya gudu ta rasa nama. To da man ido ɗaya ne da ita, kuma sai ta karkata kai ta leƙa ɗakin da idon da ke gani. Ba ta ga Auta ba saboda yana cikin duhu, haske kuma ya kashe mata idonta mai rai. Tana sa kai, sai ya sa wuƙarsa mai kaifin gaske ya cake idon mai kyau.

    Zafin dafi da kaifin sihirtacciyar wuƙar farautar nan ya kama ta; ta kiɗime, ta yi wani namijin ƙarajin da ya cika gari. Iskar bakinta ta karya dangar karan gidan da ɗan Auta ke ciki. A nan take muguwar ta faɗi, ta shiga birgima. Can sai ta yi wani irin gwauron numfashi, na fitar rai. Haka dai ta mimmiƙe a mace.

    Da gogan naka ya ga ta mutu, ba ta sauran motsi, sai ya tuɓe takalminsa ɗaya, ya ɗora a kan mushen muguwar. Ya shiga ɗaki, ya garƙe ƙofa, ya kwanta ramuwar barci.Da gari ya waye, rana ta daga kowa ya fito a garin sai ya ga dodanniya shirim, ba su san ta mutu ba. Duk wanda ya gan ta kwance sai ya gudu gidan Sarki ya ba shi labari.

    Daga bisani Sarki ya fito, ya je ya ga dodanniya a mace, ga wuƙa an caka a idonta, ga kuma takalmi ƙafa ɗaya a kan ruwan cikinta. Sai Sarki ya ce duk mutumin da ya zo da irin wannan takalmin, to shi ya kashe ta. Aka nemi gano ko wane ne, amma aka rasa saboda Auta yana ɗaki yana biyan bashin barci.

    Can hayaniyar jama’a ta sa ya farka, kuma da ya gane abin da ake yi, sai ya fito da ɗaya takalmin; ya je kan mushen dodanniyar, ya zare wuƙar da ya caka mata a ido; ya goge jinin jikinta, ya zaro kuben wukar, ya sa ta a ciki. Daga nan sai ya shiga masaukinsa, ya ɗauko jakarsa zai tafi.

    Duk abubuwan nan da ya yi, har ya gama bai ce wa kowa komai ba. A nan ne fa Sarki ya kira shi, ya tambaye shi daga inda ya fito ya zo garin nan, domin sun jima suna wahala saboda dodanniyar nan, ba tare da sun san da jarumi kamarsa a garin ba. Auta ya ce wa Sarki da mutanen garin su gode wa Allah da tsohon da ya ba shi wurin kwana, domin da bai ba shi ba, da ya bar garin ya wuce.

    Sai Sarki ya ce su tafi gida. Da suka isa, Sarki ya yi masa kyauta mai yawa; ya raba garin biyu ya ba shi rabi, kuma ya naɗa shi Sarkin yaƙin ƙasarsa. Auta ya zama babban jarumi wanda, a dalilinsa aka sami zaman lafiya da walwala a garin.

    Yanzu haka ma duk da ya tsufa, masana kan ce ya fi Iliya Ɗan Maiƙarfi iya yaƙi. Wasu kuma suka ce da kaɗan Sarkin Yaƙi Ganɗoki ya fi Auta gwaninta da jiƙuwa da magunguna. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Alheri danƙo ne ba ya faɗuwa ƙasa banza.
    • Zaman duniya cuɗe ni in cuɗe ka ne.
    • Komai ya wuyato akwai maganinsa.
    • A karɓi baƙo da mutunci saboda gobe.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Samarin Ɓarayi Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Samarin Ɓarayi Uku

    Tatsuniyar Samarin Ɓarayi Uku

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can wani gari wai shi Komayya da ke kusa da Dajin Dila na yamma da ƙoramar Kada, akwai wasu samari su uku. Ɗaya ana kiran sa Ba-ka-son Asara; na biyunsu kuma Ɓarna; na uku Wayo.

    Kullum ba su da aiki sai su shiga gonakin mutane su tono rogo, ko su yi ta karya dawa ko gero ko masara, su je wani gari su sayar. Yau da gobe, abu ya ishi mutanen gari, har aka ɓullo da dabarar yadda za a kama ɓarayin nan.

    Da suka san an kafa doka a garin, sai Wayo ya ba su shawara a kan su je garin da ba a san su ba, su nemi abin yi. Suka yarda da wannan shawara, suka nufi wani gari. A wannan gari sai da suka yi shekara bakwai suna neman kuɗi, ba sa raba asusu.

    Sannu a hankali, suka tara kuɗin da suka cika asusunsu maƙil. Ganin sun sami kuɗi, sai suka yanke shawarar komawa gida. Da ranar tashinsu ta zo, sai suka kama hanya, har dai Allah ya kai su garinsu lafiya.

    Bayan sun isa gida, ba su ko shiga gari ba suka tarar da wata tsohuwa tana aikin sabulu. Sai suka ba ta ajiyar kuɗin a kan idan sun yi wanka, za su karɓa, tare da sharaɗin cewa kada ta ba kowa daga cikinsu kuɗin, sai su duka ukun sun haɗu.

    Tsohuwa ta ce: “To, ku da abin ku, ai yadda kuka ce za a yi.” Ta karɓi kuɗi, ta ajiye musu. Ko da suka shiga wurin wanka, har sun tuɓe kayansu, sai suka tuna ba su da sabulu. Sai suka sa Wayo ya je ya karɓo.

    Da Wayo yaje gun tsohuwa, sai ya ce mata: “Wai ki ba ni, ma’ana kuɗin.” Sai tsohuwa ta rantse, ta ce atafau, ba za ta ba shi ba. Sai Wayo ya koma ya sanar da ‘yan’uwansa, wai ta ce ba za ta bayar ba.

    Jin bayanin Wayo, sai suka je gaba ɗaya suka ce da ita: “Ai mu ne muka ce.” Da ta ji daga bakinsu, sai ta ɗauki kudi ta ba Wayo. Da kuɗi suka shiga hannunsa, sai ya kama hanya, ya gudu. Suka jira, kamar zai zo yanzu ne, ko sai an jima ne, shiru.

    Saboda sun gaji da jira, sai suka fito suka tambayi tsohuwa: “Ba ki ba shi sabulun ba ne?” Sai tsohuwa ta ce: “Wane irin zancen banza kuke yi, bayan kun ce in ba shi kuɗi, yanzu kuma ku ce sabulu?”

    Da jin kalaminta sai suka tubure a kan cewa ba ta isa ba, sai ta nemo shi su amshi kuɗinsu. Daga nan sai suka tafi wurin alƙali. Alƙali ya tambayi tsohuwa yadda aka yi. Ta kwashe labarin abin da ya faru ta gaya masa.

    Sai alƙali ya ce ta je ta nemo musu kuɗinsu a cikin kwana uku. Tsohuwa ta fita da kuka, tana tafiya. Sai ta haɗu da wani mutum, ya tambaye ta abin da ya faru. Sai tsohuwa ta ce: “Gara mutuwa da abin da ya faru da ni.”

    Daga nan ta yi masa bayani daki-daki, ta gaya masa abin da ya faru sarai. Da ta gama, sai ya ce da ita: “Ai wannan abu mai sauƙi ne.” Ta ce: “Kamar yaya fa?” Sai mutumin ya ce: “Ki koma wurin alƙali ki ce masa kin samo kuɗin.

    Idan ya ce ina suke, ki ce suna nan, amma sai samarin nan sun haɗu su uku kafin ki ba su.” Tsohuwa ta yi godiya. Washe-gari ta koma wurin alƙali, ta gaya masa cewa kuɗi sun samu, kamar yadda mutumin ya gaya mata, tare da bayanin cewa amma ba za ta bayar ba sai samarin nan sun hadɗ su uku.

    Alƙali ya ce: “Kina da gaskiya. Ku kuma samari sai ku yi ƙoƙari ku samo ɗan’uwanku, ku zo gaba ɗaya, don ku karɓi kuɗinku.” Daga nan kowa ya watse, samari suka tafi cikin ɓacin rai, ita kuma tsohuwa ta tafi da murna.

    Shi kuma Wayo yana tafiya har rana ta fadi. Sai ya yanke shawarar zai bi ta wata gajeriyar hanya, wadda ta ratsa ta cikin ɗaya daga gonakin da sukan je sata a da. Bai san cewa masu gona suna fakonta ba don yawan rogonsu.

    Saboda haka yana shiga gonar zai wuce sai suka auka masa. Yana zaton abokansa ne suka gan shi, sai ya zura da gudu. A garin gudun tsira sai ya jefar da jakar kuɗi; ko garin ma bai shiga ba, ya wuce. Masu fako a gonar rogo suka ɗauki kuɗi.

    Ba tare da wata fargaba ba suka rabe kuɗin tsakaninsu. Da wani daga cikinsu ya yi lissafi, sai ya gano kuɗin sun yi daidai da masararsu da rogonsu da dawarsu da wakensu da dai sauran amfanin gonakin da aka sace musu aka sayar.

    Daga ƙarshe dai suka ce kuɗin nan sakamako ne daga Allah. Biyu daga cikinsu sai suka sayi shanun turka, ɗaya kuma ya ƙara gona. Yanzu haka suna can suna cin duniyarsu. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ba a cin amana a kwana lafiya.
    • Ba da umarni a duƙunƙune ba da cikakken bayani ba yakan janyo asara.
    • Duk wayonka akwai wanda ya fi ka wayo.
    • Wayo a kan rashin gaskiya wauta ne.
    • Kowa ya ɗauko da zafi, bakinsa.
    • Dubu ta cika.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Muwa Muwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Muwa Muwa

    Tatsuniyar Muwa Muwa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can wani daji an yi wata raƙumar dawa mai suna Muwa. Ba ta da ɗa ko ɗaya. Kullum in ta dawo daga kiwo, sai ta yi ta kuka saboda rashin haihuwar nan. Cikin ikon Allah rannan sai ta haifi ‘ya’ya huɗu. Saboda murna ta raɗa wa babban cikinsu suna Muwa Muwa, mai bi masa kuma Caccikarimba, na ukunsu kuma Malaladumba.

    Amma sai ta ƙi raɗa wa na huɗun suna, don ya fito a rame, ba ta son sa. Saboda yawan son ‘ya’yanta nata uku, sai ta gina musu ɗaki, ta saka su don kada ruwa da ƙura su taɓa su, amma sai ta bar ƙaramin a waje, ko ya mutu, ko ya yi rai, babu ruwanta.

    Kuma sai ta ce wa ‘ya’yanta ukun: “Idan kun ji muryata, ku buɗe ƙofa; idan ba muryata ba ce, to kada ku buɗe.” Kullum idan ta dawo daga kiwo sai ta ce: “Muwa, Muwa zo ka sha, Caccikarimba zo ka sha, Malaladumba zo ka sha.” Sai su fito su sha, su koma.

    Wata rana, Kura ta zo wucewa sai ta ji raƙumar nan tana cewa: “Muwa, Muwa zo ka sha, Caccikarimba zo ka sha, Malaladumba zo ka sha.” Sai suka fito suka sha, suka koma. Bayan uwarsu ta tafi, sai Kura ta zo bakin ƙofar da ƙatuwar murya mara daɗi ta ce:

    “Muwa, Muwa zo ka sha, Caccikarimba zo ka sha, Malaladumba zo ka sha.” Sai yaran suka yi ihu, suka ce: “Ba muryar mahaifiyarmu ba ce.” Sai wannan abu ya sa Kura ta ji haushi ta bar wurin, tun kafin raƙumar ta koma wajen ‘ya’yanta.

    Kura na tafiya sai ta haɗu da wani Biri mai ba da magani. Sai ta ce idan dai gaskiya ne yana ba da magani, to ya mayar da muryarta kamar ta raƙumar dawar nan. Sai Biri ya nuna mata yin haka abu ne mai sauƙi a gare shi, amma da sharaɗin ba za ta ci komai a hanya ba, domin idan ta ci, muryarta za ta koma kamar da.

    Kura ta ce ta yarda. Sai Biri ya ba ta magani, da ta yi magana sai ta ji muryar kamar ta Muwa. Kura ba ta doshi ko’ina ba, sai wurin ‘ya’yan Muwa. Daga zuwanta sai ta ce: “Muwa, Muwa zo ka sha, Caccikarimba zo ka sha, Malaladumba zo ka sha.”

    Sai suka buɗe ƙofa, sai Kura ta yi wuf ta cinye su, ta tafi abinta. Ashe ƙaramin da uwar ba ta so, watau ramammen nan, yana ganin ta. Can da raƙumar ta dawo ɗakin ‘ya’yanta sai ta yi kamar yadda ta saba: “Muwa, Muwa zo ka sha, Caccikarimba zo ka sha, Malaladumba zo ka sha.”

    Sai da ƙaramin ya bari ta gama kiran su baki ɗaya, sai ya dube ta ya ce:”Muwa, Muwa ba ya nan, Caccikarimba ba ya nan, Malaladumba ba ya nan.” Sai uwar ta ce: “To, kai ɗin ma zo ka sha.” Sai ya je ya sha nononta, kuma daga wannan rana ta shiga son sa, har ya zamana in za ta fita kiwo sai su fita tare. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Bai kamata a nuna bambanci tsakanin ‘ya’ya ba, domin Allah kaɗai ya san mai amfani cikinsu.
    • Wuya maficiya ce.
    • Mai rabon ganin baɗi ko ana ha maza ha mata sai ya gani.
    • Bora ya koma mowa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Abotar Biri Da Kifi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Abotar Biri Da Kifi

    Tatsuniyar Abotar Biri Da Kifi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani Biri da kullum yakan je rafi wanka, bayan ya gama yawon cin ‘ya’yan itatuwa da tsalle-tsallensa ya gaji. Wata rana ya je wanka rafin da ya saba zuwa, sai ya haɗu da wani Kifi a cikin ruwa. Sai Kifin ya nemi su ƙulla abota da Birin. Biri ya amince, kuma suka yi wa juna alƙawari ba za su ci amanar junansu ba.

    Suna nan, abotarsu ta yi ƙarfi. Wata rana sai Biri ya ce zai je ganin gida, watau a can wani daji da danginsa suke. Da Kifi ya ji haka, sai ya shirya wa Biri kayan tsaraba, ya ba shi; suka yi ban kwana, Biri ya kama hanya, ya tafi. Bayan ya tafi, sai sauran kifayen da suke cikin ruwa suka fara gunaguni wai su ba su son abokinsa Biri.

    Har ma dai sauran kifayen suka shirya taro a ɓoye. A wurin taron waɗansu kifaye suka ce a kashe Biri, ko a kashe Kifin da ke abota da Biri. Sai babban kifayen ya ce: “A a, ba maganar kisa, domin kisan kai zai jawo gaba mara amfani tsakaninmu kifaye, ko kuma tsakaninmu da Birai.”

    Haka dai suka ci gaba da shawarwari, har wani ya kawo shawarar cewa a kira Kifi a gaya masa za a ba shi sarauta a fadar Sarkin Kifaye, amma sai ya zo da zuciyar abokinsa Biri kafin a naɗa shi. Duk suka amince da wannan shawara. Aka kira Kifi abokin Biri, aka yi masa bayani.

    Da ya ji bayanin da kifaye suka yi masa, sai ya ce da su: “Amma fa ni da Biri mun yi alƙawari ba za mu ci amanar juna ba. Kuma ni ba zan iya cin mutuncinsa ba idan aka ba ni sarautar.” Sai Kifi abokin Biri ya ce da danginsa kifaye su bari Biri ya dawo daga ganin gida, ya san zai yi duk yadda ya nemi ya yi.

    Suna nan, sai Biri ya dawo daga tafiya, sai ya je wajen Kifi kamar yadda ya saba, ya kai masa tsarabar da ya zo da ita daga gida. Suka gaisa sosai, kuma suka shiga hira. Can sai Kifi ya sanar da Biri cewa bayan ya yi tafiya ‘yan’uwansa kifaye sun ce za su ba shi sarauta, ya zama Sarkin Kifaye.

    Da Biri ya ji haka sai ya ce: “Kai, amma wannan labari da daɗi yake.” Sai Kifi ya ce: “To amma fa za ka raka ni cikin ruwa don ka gaishe su.” Biri ya ce: “To, ai sai mu je.” Suka yi nutso, har wajen taron kifaye. Sai abokin Biri ya ce: “Amma fa abokina, an ce sai na kawo wani abu kafin su ba ni sarautar.”

    Da Biri ya ji haka, sai ya dubi Kifi ya tambaye shi: “To mene ne suke so? Ka ba su mana.” Kifi kuma ya ce da Biri: “Ai abin da suke so a jikinka yake.” Biri ya ce: “Mene ne, fadi zan ba ka.” Sai Kifi ya ce: “Sun ce in kai musu zuciyarka ne.” Sai Biri ya ce: “Ai don wannan babu komai, zan ba ka.

    Amma ka san ba na yawo da zuciyata; tana can a kan bishiya na rataye ta. Bari in je in ɗauko maka.” A cikin murna Kifi ya ce: “To.” Ya raka Biri har bakin ruwa domin ya je kan bishiya ya ɗauko zuciyarsa ya kawo wa Kifi a nada shi sarauta.

    Da Biri ya samu ya fita daga cikin ruwan, sai ya hau bishiya ya ceda Kifi: “Daga yau ba zan sake abokantaka da kai ba. Kuma ba zan sake shiga ruwa ba.” Da wannan dabara Biri ya gudu. Shi ya sa har yau din nan Birai ke tsoron shiga ruwa. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kowa ya ɗauki amana ya kamata ya riƙe ta da gaskiya.
    • Hassada ga mai rabo taki ce.
    • Kafin ka ga biri, biri ya ganka.
    • Dabara kashin kwance.
    • Iya ruwa, fidda kai.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Cin Amanar Ɗan’uwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Cin Amanar Ɗan’uwa

    Tatsuniyar Cin Amanar Ɗan’uwa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum da ‘ya’yansa guda biyu. Suna nan, suna nan, sai wata rana babansu ya tura su neman furannin ƙawa. An ɗauka cewa duk wanda nasa ya fi kyau, to mahaifinsu zai fi nuna masa soyayya a gidan, kuma za a yi masa aure. Shi ke nan, sai suka je. Da suka je, sai ƙaramin ya tsinki fure mai kyau.

    Da yayansa ya gani, sai ya ƙwace, sannan kuma ya kashe shi. Sai ya kai furen nan gida. Sai babansa ya yi masa aure. Daga baya sai babansa ya tambaye shi inda ƙanensa yake, sai ya yi wa uban ƙarya, ya ce masa ya bar shi a baya, kuma zai ƙaraso gida ba da jimawa ba. Ana nan, ana nan, har wuni biyu, yaro bai dawo ba, Mahaifinsu ya jure ya kau da kai.

    Wata rana wani boka ya zo wucewa, sai ya ci karo da ƙashin yaron da aka kashe, ya ɗauka yana hurawa. Sai ƙashin ya fara rera wa bokan nan wannan waƙa: “

    Kai bokan nan kai bokan nan;

    Ƙashina ne kake hurawa.

    Baba ya aike mu daji, Mu samo furannin ƙawa,

    Nawa sun fi na ɗan’uwana kyau,

    Sai ya ƙwace nawan, Ya kashe ni.”

    Da boka ya ji haka, sai ya kai wa Sarki wannan ƙashi. Da Sarki ya hura sai ya ce:“Kai Sarkin nan, kai Sarkin nan, Ƙashina ne kake hurawa. Baba ya aike mu daji, Mu samo furanni, ni da yayana, Nawa sun fi na wana kyau, Sai ya ƙwace nawan, Ya kashe ni.”

    Sai Sarki ya sa a yi shela a sanar da mutanen garin cewa washegari gaba ɗayansu su zo ƙofar fadarsa, domin a tambaye su wanda ya yi wannan ɗanyen aiki. Da suka taru washe-garin, sai kowa ya ce ba shi ba ne. Sai Sarki ya ce, to za a sa duk wanda ke garin ya hura wuta, domin ƙashin zai faɗi wanda ya yi kisan kan.

    Sai aka fara ta kan mahaifin yaron da aka kashe. Da ya hura, sai ƙashi ya ce: “Kai babana, kai babana, Ƙashina ne kake hurawa, Kai ka aike mu daji, Ni da wana, mu samo furanni, Nawa sun fi nasa kyau, Sai ya ɗauke nawan, Ya kashe ni.” Sai Sarki ya ce to ya kira yaron, watau yayan wanda aka kashe.

    Ya zo, aka ba shi ƙashin ƙanensa, da ya fara hurawa, sai ƙashi ya ce: “Kai yayana, kai yayana, Ƙashina ne kake hurawa, Baba ya aike mu daji, Mu samo furanni, Nawa sun fi naka kyau, Sai ka ɗauke nawan, Ka kashe ni.” Sai Sarki ya ce to a kama yaron shi ma a kashe shi. Aka kama shi, aka kashe. Shi ke nan, an yi maganin wanda ya ci amana. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Cin amana kan jawo wulaƙanci.
    • Zafin nema ba shi ke kawo samu ba.
    • Idan Allah ya nufi mutum da arziki ba wanda ya isa ya hana.
    • Alhaki kare ne, mai shi yake bi.
    • Abin da ka shuka, shi za ka girba.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Ya Tsinci Dami A Kala

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ya Tsinci Dami A Kala

    Tatsuniyar Ya Tsinci Dami A Kala

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wasu yara su uku abokan juna. Wata rana sun je farauta sai suka kama maciji, suka aiki ƙaramin cikinsu ya nemo wuta domin su babbaka macijin, su ci; ya ce da su ba zai iya ba. Suka ba shi riƙon macijin, suka tafi neman wutar da kansu. Kafin su dawo ya saki macijin.

    Da suka dawo suka ce ina macijin, ya ce maciji ya fi ƙarfinsa, wai sun yi kokawa ya ka da shi a cikin toka, kuma ya gudu. Sai suka ce ba su yarda ba, sai ya biya su. Baki ɗaya suka shiga gari, ba su tsaya ko’ina ba sai a gidan su wannan yaron. Bayan sun yi wa iyayensa bayani, sai mahaifansa suka kori yaron daga gidansu domin a hore shi.

    Ya rasa inda zai zauna, sai ya shiga dajin da sukan je farauta da abokan nan nasa. Yaro ya gina gida a dajin nan, kuma ya faɗa a ransa cewa gara da bai kashe macijin nan ba. Can sai ga macijin nan ya fito, yaro ya gaya masa abin da ya faru. Sai ya ce da yaron ya bi shi gidansu domin su ci abinci.

    Yaro bai yi musu ba; suka kama hanya. To, ashe macijin nan ba maciji ba ne, wani ɗan sarki ne da yakan rikida ya zama maciji idan ya yi nishaɗi. Suna zuwa gidan aka kawo musu tuwo a kwanon tagulla, irin na gidajen manyan tajirai da sarakuna. Yaro bai saba ba, ya ce ba zai ci tuwo a kwanon tagulla ba, sai a cikin ƙwarya.

    Sai aka kawo masa abinci a ƙwaryar, ya kuma cinye shi duka; bai saba da rage abinci ba, kamar yadda akan yi a gidajen sarauta. Da zai kwanta sai aka yi masa shimfiɗa da buzun Sarki, sai ya yi fitsarin kwance a kai. Aka ce masa ya je ya wanke buzun. Yaro ya kama hanyar rafi domin wanke buzun Sarki.

    Amma sai ya faɗa wani gida haka kwatsam, ba tare da ya sani ba. Sai masu gidan suka ce masa in yana jin yunwa tun da sun ga shi baƙo ne, kuma ba su san irin nisan tafiyar da ya yi ba, ya ɗauki shinkafa ƙwaya ɗaya ya dafa; sai ya ɗauka, ya wanke, ya jefa a tukunya, ya ɗora sanwar shinkafa; sai ya ga ta cika tukunya; ya ci, har ya ƙoshi, kuma ya bar saura.

    Bayan ya yi wa masu gidan godiya, sai ya ce da su zai tafi gida. Sai suka ce ya ɗebi ƙwaiƙwaye guda uku, idan ya kama hanya ya fasa ɗaya. Da ya kama hanya ya ɗan yi nisa da gidan nan, sai ya fasa ƙwai ɗaya. Yana fasawa sai ya ga fatu masu yawa masu launi iri daban-daban.

    Sai ya kwasa, bai zame ko’ina ba sai gaban Sarki, da nufin Sarki ya zaɓi wadda yake so, Sarki ya zaɓa. Bayan yaron ya ƙara hutawa, sai ya ce da abokinsa ɗan Sarki, zai tafi. Sai abokin ya ce in babansa, watau Sarki, ya ba yaron kyauta, to kar ya karɓa, kuma ya ce masa ba ya son komai sai zoben da ke hannun Sarkin na hagu.

    Yaro ya matsa kusa da Sarki ya sanar da shi zai tafi. Da Sarki ya ji bayanin yaro, sai ya ce da shi ya faɗi duk abin da yake so zai ba shi. Sai yaro ya dubi Sarki ya ce ba ya son komai sai zoben da ke hannun Sarki na hagun. Sai ko Sarki ya ba shi; ya yi godiya, ya fita waje suka haɗu da abokinsa ɗan Sarki.

    Sai ɗan Sarki ya ce wa yaron nan abokinsa: “A duk sanda ka ji yunwa, sai ka ce zobe-zobe, mai shekara tamanin da takwas, zai ba ka duk abin da kake so.” Shi ke nan, yaro ya yi ban kwana da abokinsa, ya kama hanya.Yana cikin tafiya sai ya fara jin yunwa, kuma ba abin da zai ci. Sai ya zauna a gindin wata bishiya.

    Sai abokinsa ɗan Sarki ya zama maciji, ya same shi ya ce da shi: “Ka manta abin da na gaya maka ka faɗa wa zoben idan kana jin yunwa?” Sai ya tuna masa. Sai yaron ya ce: “Zobe, zoben shekara tamanin da takwas”. Zoben ya ce: “Me kake so?” Ya ce: “Ina son tuwo.” Sai ko ya ga tuwo; ya zauna ya ci har ya ƙoshi.

    Da ya tafi gidansa na ciyawa, sai ya ce: “Zobe, zobe mai shekara tamanin da takwas.” Sai zoben ya ce: “Me kake so?” Sai ya ce: “Ina so gidana ya zama mai kyau kamar na samarin da ke tashe a gari.” Sai ya ga gidansa da ɗakinsa sun yi kyau. Sai ya je gidan babansa ya ce ya zo ya kai su su ga gidansa.

    Sai suka bi shi, suka gano gidan. A gaban iyayensa ya kirawo sunan zobe mai shekara tamanin da takwas, ya sa zoben nan ya mayar da shi saurayi kyakkyawa. Daga bisani a wannan hali na kyau ya je neman aure gidan Sarki. Sarki ya sa masa sharuɗa, watau lallai sai ya kawo shanu masu yawan da ba a taɓa ganin yawansu ba a garin, tare da zannuwan da kamar ba za su ƙare ba saboda yawa.

    Nan da nan yaron nan ya sa zobe mai shekara tamanin da takwas ya kawo duk abin da aka nema. Sarki ya aura masa ‘yarsa. Suna nan, suna nan, sai wata rana yana wurin wanka, sai matar ta sace zoben, ta kai wa babanta. Sai aka kama yaron aka ɗaure. Sai yaron ya aiki kare da kyanwa da ɓera su je gidan Sarki su ɗauko masa zoben nan.

    Da suka je, kare ya ja Sarki da taɗi, kyanwa tana yi wa Sarki wasa, ɓera kuma ya shiga wajen da Sarki ya ajiye zoben, ya sato shi. Daga bisani suka yi sallama da Sarki, suka kama hanya domin su kai wa yaron nan zobe. Suna cikin tafiya, sai suka tarar da wani kogi, wanda dole sai sun haye shi kafin su kai gidan yaro.

    Sai kare ya goya ɓera da kyanwa domin su ƙetare ruwan. A garin tsallaka ruwan, sai zoben ya sulluɓe, ya faɗa cikin ruwa. Bayan sun isa gidan yaro sun gaya masa, sai ya ce su je bakin ruwa su ce da masu kamun kifi suna son hanjin kifayen da suka kama, suka feda. Aka yi ta kawo musu hanjin kifi, har aka ba su wanda zoben ke ciki.

    Sai suka kai wa yaron nan zoben. Da ya kira zobe mai shekara tamanin da takwas ya amsa masa, sai ya tambaye shi abin da yake so. Yaro ya ce ya na so zoben nan ya fitar da shi daga gidan maza, watau kurkukun da aka ɗaure shi a ciki. Nan take ko sai ya gan shi a gidansa. Can kuma sai ya lura da ɓera da kyanwa da kare ma suna nan.

    Sai ya tambayi ɓera abin da yake so. Ɓera ya ce daddawa yake so. Yaro ya tambayi kare abin da yake so ya ci. Kare ya ce yana so ya ci ɗanyen nama. Daga nan kuma yaro ya tambayi kyanwa abin da take son ci; ta ce ƙadangare take muradi. Sai yaron ya ce: “Zobe, zobe.” Kafin ma ya kai ga cewa mai shekara tamanin da takwas a duniya, tuni zoben ya tambaye shi abin da yake so.

    Sai ya ce yana son ɗanyen nama da daddawa da ƙadangare. Kafinya gama rufe baki har ya kawo masa su. Ba tare da jinkiri ba kowa ya ɗauki nasa, ya tafi. Sai yaron ya ce wa zoben yana son ya ga Sarki da matarsa ‘yar Sarki a gabansa suna rawa. Sai ko ya gan su suna rawa. Sai ya ce yana so ya ga sun mutu. Sai suka faɗa wuta, suka mutu. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Alheri ɗanƙo ne ba ya faɗuwa ƙasa banza.
    • In za ka haƙa ramin mugunta, haƙa shi gajere.
    • Kowa ya yi da kyau, zai ga da kyau.
    • Kowa ya tausayawa wani, shi ma sai Allah ya tausaya masa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Ɗan Agwai Da Kura

    Edita@rumasau-kallamu