Author: wikiHausa

  • Yadda Ake Faten Shinkafa

    Abubuwan da ake buƙata:

    • Kaza ko Nama
    • Shinkafa
    • Kayan ƙamshi
    • Mai ɗanɗano
    • Masara
    • Tafarnuwa
    • Citta
    • Albasa
    • Cinammon
    • Persley
    • kayan miya
    • Koren tattasai

    Yadda ake haɗawa 

    1. Za a sami nama ko kifi, idan nama ne, yana buƙatar a dafa shi kamar awa ɗaya yadda zai yi laushi sosai.
    2. Idan kifi ne, za a wanke, a sa masa  sinadarai sai a sa shi a tukunya, a ba shi wuta kaɗan, dan su shiga jikinsa, amman kar a sa ruwa.
    3. Sai a zuba markaɗaɗɗen kayan miya, amman ba da yawa ba.
    4. A kawo ɗan mai kaɗan shima a zuba, a soya sama-sama, kar ya soyu sosai.
    5. Sannan a kawo ruwa da ɗan dama a zuba, da sinadaran ƙamshi, amman ba masu yawa ba.
    6. A wanke shinkafa a zuba, idan ya tafasa a zuba nama da ruwan naman, ana son aƙalla shinkafar ta yi awa ɗaya dan ta samu ta farfashe tunda romonta ake so. Idan anga ta yi kauri, sai a kawo kayan mai ɗanɗano da cinnamon a zuba, a rage wuta, idan kuma da kifi ake yi to sai a zuba.
    7. Sannan a yanka koren tattasai da parsley da albasa a zuba a bar shi ya yi kamar minti 2  sai ki sauke.

    Domin sanin yadda ake pancake danna nan

  • Yadda Ake Faten Shinkafa

    • Kaza ko Nama
    • Shinkafa
    • Kayan ƙamshi
    • Mai ɗanɗano
    • Tafarnuwa
    • Citta
    • Albasa
    • Cinammon
    • Persley
    • kayan miya
    • Koren tattasai

    Yadda ake haɗawa

    1. Za a sami nama ko kifi, idan nama ne yana buƙatar a dafa shi kamar awa ɗaya, yadda zai yi laushi sosai
    2. Idan kifi ne za a wanke a sa masa sinadarai da kayan ɗanɗano, sai a saka shi  a tukunya, a ba shi wuta kaɗan, don su shiga jikinsa, amman kar a sa ruwa.
    3. Sai a zuba markaɗaɗɗen kayan miya, amma ba da yawa ba
    4. A kawo ɗan mai kaɗan, shi ma a zuba, a soya sama-sama, kar ya soyu sosai
    5. Sannan a kawo ruwa da ɗan dama a zuba da sinadaran ƙamshi, amma ba masu yawa ba.
    6. A wanke shinkafa a zuba, idan ya tafasa a zuba nama da ruwan naman, ana son akalla shinkafar ta yi awa ɗaya, dalon ta samu ta farfashe tunda romonta ake so. idan an ga ta yi kauri, sai a kawo kayan ɗanɗano da cinnamon a zuba a rage wuta, idan kuma da kifi ake yi to sai a zuba.
    7. Sannan a yanka koren tattasai da parsley da albasa a zuba a bar shi yayi  kamar minti 2 sai ki sauke.

    Domin sanin yadda ake pancake  danna nan

  • Waɗanda Allah Ke Gaggauta Karɓar Addu’ar Su

    WAƊANDA ALLAH KE GAGGAUTA AMSA ADDU’ARSU

    1. Addu’ar Annabawan Allah.
    2. Addu’ar mala’ikun Allah
    3. Addu’ar wanda aka zalunta.
    4. Addu’ar mai ƙarfin imani da tsoron Allah.
    5. Addu’ar ɗa mai biyayya ga iyayensa.

    6. Addu’ar mai Azumi.

    7. Addu’ar shugaba adali.

    8. Addu’ar iyaye (nagartattu) ga ‘ya’yansu.
    9. Addu’a ga ɗan uwa a bayan idonsa.
    10. Addu’ar mai jihadi.
    11. Addu’ar mai Hajji ko Umrah.
    12. Addu’ar mai dauwama cikin zikirin Allah.
    13. Addu’a ga mai karatun AlQur’ani.

    14. Addu’ar matafiyi (tafiya ta halal).
    15. Addu’ar mai taka tsantsan wajen haram; abincinsa, abin shansa, tufafinsa da mazauninsa.

    ABUBUWAN DA SUKE KAWO JINKIRIN AMSA ADDU’A

    1. Shirka ƙarama da babba.
    2. Ta’amuli da haram ci, sha ko tufafi.
    3. Nauyin zunubai da ƙeƙashewar zuciya.
    4. Barin umarni da kyakkyawa da hani ga mummuna.
    5. Tafseel (Dalla-dalla) a cikin addu’a

    6. Wasa da wargi a cikin addu’a.
    7. Addu’a da zuciya gafalalliya mai shagala.

    8. Rashin ladabi a gaban Allah Jalla wa’ala.
    9. Ta’allaqa addu’a ga mashi’ah (In ka so)

    10. Gaggawa a cikin addu’a.
    11. Al-Istihsaar( Shi ne mutum ya bar addu’a saboda gajiya da ƙosawa)

    12. Rokon abin da hukuncin Allah ya gama da shi.
    13.Saja’i a cikin addu’a (shi ne mutum ya tilasta wa kansa daidaita harafin ƙarshen jumlolin addu’a )
    14. Bidi’o’I a cikin addu’a.

    15. Roƙon wani abu da ya shafi saɓon Allah ko yanke zumunta.

    Duba:
    1. TAS’HIHUD DU’A na Dr.BAKR
    2 ARRIYADUN NAZIRAH na Shk.Abdur Rahman Nasir Sa’adiy
  • Mece Ce Sana’ar Mahaifin Manzonmu?

    Mece Ce Sana’ar Mahaifin Manzonmu?

    Mece ce sana’ar Mahaifin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wassalama

    1.Kasuwanci

    Domin sannin wace ce mahaifiyar manzon Allah danna koren rubutun nan

  • Wace Sana’a Mahaifin Manzo (S.A.W) Yake Yi

    Wace Sana’a Mahaifin Manzo (S.A.W) Yake Yi

    Mece ce sana’ar Mahaifin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama

    1.kasuwanci

  • Wace Ce Mahaifiyar Manzon Allah(S.W.A)?

    Wace Ce Mahaifiyar Manzon Allah(S.W.A)?

    Wace ce mahaifiyar Manzomu Sallallahu Alaihi Wasallam

    1. Aminah ‘Yar Wahab Ɗan Abdulmanaf Ɗan zahrah ‘Yar Sayyid bani Zahra.

    domin sanin a ina aka haifi manzon Allah (S.W.A) danna koren rubutun nan

  • Mene Ne Amfanin Zumunci?

    Mene Ne Amfanin Zumunci?

    Sadar da zuminci,shi ne ziyarar ‘yan uwa da dangi da abokai na alkhairi da taimakon su da agaza musu.

    Annabi (S.A.W) ya bayyana mana sadar da zumunci da cewa hanya ce ta samun arziƙi da rayuwa mai daɗi a nan duniya da Lahira.

    Sai ya ce:
    (ﻣَﻦْ ﺳَﺮَّﻩُ ﺃَﻥْ ﻳُﺒْﺴَﻂَ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﺭِﺯْﻗُﻪُ، ﺃَﻭْ ﻳُﻨْﺴَﺄَ ﻓِﻲ ﺃَﺛَﺮِﻩِ ، ﻓَﻠْﻴَﺼِﻞْ ﺭَﺣِﻤَﻪُ)

    Duk wanda yake son Allah ya yalwata arziƙinsa kuma ya tsawaita rayuwarsa, to
    ya sadar da zumincinsa).
    @ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ‏) 2067 ‏( ،ﻭﻣﺴﻠﻢ ‏) 2557 ‏( ،ﻭﺃﺑﻮ ﺩﺍﻭﺩ ‏) 1693 )

    A wani Hadisin yana cewa:
    (ﺍﻟﺮَّﺣِﻢُ ﻣُﻌَﻠَّﻘَﺔٌ ﺑِﺎﻟْﻌَﺮْﺵِ ﺗَﻘُﻮﻝُ ﻣَﻦْ ﻭَﺻَﻠَﻨِﻲ ﻭَﺻَﻠَﻪُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻭَﻣَﻦْ ﻗَﻄَﻌَﻨِﻲ ﻗَﻄَﻌَﻪُ ﺍﻟﻠَّﻪ)

    (Zumunci yana rataye a jikin al’arshi, yana cewa, ya Allah ka sadar da wanda ya sadar da ni, ka yanke wanda ya yanke ni).
    @ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ‏) 5989 ‏( ﻣﺴﻠﻢ ‏)

    Mu haɗu a darasi na gaba insha Allah.

  • Yadda Za Mu Sabar Wa Kanmu Yawan Tuba

    Yadda Za Mu Sabar Wa Kanmu Yawan Tuba

    Tuba daga zunubi shi ne yin nadama, barin zunubin, da neman gafarar Allah.

    Ya zama dole ne mu tilasta wa kanmu yawan tuba. Domin samun yardar Allah maɗaukaki. Kuma Idan muna kwaɗayin samun amsawa ibadunmu, da addu’o’inmu , da arziƙi, da lafiya, da dukkanin biyan buƙatunmu.

    Allah Ya fada cikin suratu Nuh: 10-11.
    :Ku nemi gafarar Ubangijinku, lallai shi mai gafartawa ne. Sai ya aiko muku da ruwa mai kwarara daga Sama .

    Kuma mu sani, saɓon Allah yana zama masifa a kan kowane abu. Yakan shafi rayuwar mutum, iyalansa har ma da dabbobinsa.

    HANYOYIN DA ZA MU BI, DOMIN SABAR WA KANMU YAWAN TUBA

    1 – Yawan karantawa da yin nazari wannan hadisin da Annabi ( S.AW) ya ce: Ya ku Mutane, ku tuba zuwa ga Allah, cewa ni ina tuba a cikin yini sau ɗari”. ( Muslim)

    2 – Duk lokacin da muka aikata laifi. To mu yi amfani da damar da muka samu. Duba abin da Annabi (S.A.W) ya faɗa a wannan hadisi :

    Babu wani musulmi da zai aikata laifi, sai mala’ika ya tsayar da shi har sa’a uku, wato ko zai tuba. In har ya tuba to..kuma ba za a yi masa azaba ba, a ranar alkiyama…

    3 – Kwaɗayin rahamar Allah, a koda yaushe. Domin mu kasance cikin waɗanda Allah Yake farin ciki da mu. Duba wannan hadisi: Allah yana tsananin farin ciki da tubar bawansa, ..fiye da ɗayanku da yake kan dabbarsa sararin daji sai ta tsere masa, alhali abincinsa da
    ruwan shansa yana tare da ita. Har ma ya fidda rai da ita. Sai ya zo jikin bishiya ya kwanta a inuwarta yana fidda rai da ita…sai kawai ya gan ta a gabansa tsaye. sai ya kama
    ragamarta, sannan ya ce saboda tsananin farin ciki Ya Ubangiji Kai ne bawana,  ni kuma ubangijinka. YA YI KUSKURE SABODA TSANANIN FARIN CIKI (Mslm)

    4 – A Koda yaushe muka yi azkaar ɗin safiya ko na maraice ka da mu manta da yin waɗannan:

    Sayyidil Istighfar

    5 – Sanya wa kanmu adadin yi a kullum. Kamar yadda Annabi (S.A.W) yai 100 / 70.

    6 – Yin ayyuka na alkhairi , wanda Allah zai yafe mana da su. Misali. Kamar yadda karuwa ta shayar da kare ruwa, kuma Allah ya yafe mata, ya ba ta aljanna.

    7 – Kauracewa saɓo domin gudun mummunar shaida daga mutane. Saboda tasirin shaida bayan mutuwar mutum. Ya tabbata cewa: Muminai su ne shaidun Allah a ƙasa.

    tuba daga zunubai
    Acikin wannan hadisin

    An wuce da gawa, sai sahabbai suka yaba ta, sai Annabi (S.A.W) ya ce:” Aljanna ta tabbata a gare shi. Sannan aka sake wucewa da wata gawar, sai suka faɗi sharrinta, sai ya ce:” Wuta ta tabbata a gare shi. Sai Umar (R.A) ya ce me ya tabbata a gare su? Sai ya ce: Wannan kun yi masa kyakkyawan yabo, sai aljanna ta tabbata a gare shi. Wannan kuwa kun ambaci sharrinsa, sai wuta ta tabbata a gare shi. Domin ku ne shaidun Allah a doron ƙasa.

    A ƙarshe jama’a mu duba mu gani. Idan har wanda Allah Yai masa gafara duk abin da yai a baya, da wanda zai a gaba. Annabinmu dan gatan Allah. Shugaban Manzanni. Wanda yake mafi kyawun halaye. Mai yawan ibada har kafafunsa na kumbura. A kullum yana yawaita Istighfari. To yaya mu za mu dinga sakaci? Allah Ya sa mu cikin bayinsa masu yawan tuba.

    Litattafai da aka duba
    Qur’an
    Riyadu Salihin

  • Na Sha Ruwa Bayan Tayar Da Iƙama A Kan Kuskure, Ya Hukuncin Azumina?

    Na Sha Ruwa Bayan Tayar Da Iƙama A Kan Kuskure, Ya Hukuncin Azumina?

    Tambaya

    Assalam MALAM ni ne lokacin azumi, sai na farka zan yi sahur, sai na ji ana kiran sallah, sai aka ce mun ai kiran assalatu ne, ni kuma sai nace bari ko ruwa na sha, sai aka ce kar ka sha, to ashe su suna nufin har an shiga sallah, sai da na fara shan ruwan, sannan na ji ai har an shiga sallah, sai na tsaya da shan ruwan, to yaya azumina na wannan ranar⁉

    Amsa

    Wa’alaikumus Salam Warahmatullah, Azuminka ya yi, babu biya a kanka, Hujja kuwa shi ne: A tsarorinda IBN JAREER ATDABARY ya kawo su a tafsirinsa cikin Tafsirin SURATUL BAQARA- ƙarƙashin aya ta (187)👉🏼

    👉🏼(2873) ABU UMAMAH ya ce:
    أقيمت الصلاة والإناء في يد عمر، قال أشربها يا رسول الله؟ قال “نعم” فشربها.
    Wato= An tada iƙamar asuba, alhali akushi yana hannun UMAR (R.A), sai ya ce “In sha ne YA RASULALLAH? Sai ANNABI SAW ya ce “Ka sha” sai UMAR ya sha,”

    👉🏼(2874)&(2875) BILAL (R.A) ya ce:
    أتيت النبي (صلى) أذنه بالصلاة وهو يريد الصوم، فدعا بإناء فشرب، ثم ناولني فشربت، ثم خرج إلى الصلاة.
    Wato= Bayan kiran sallah na shigo wurin ANNABI SAW na sanar da shi, yana da niyyan azumi, sai ya sa aka kawo abin sha, ya sha ya ba ni ni ma na sha,

    👉🏼(2858)BARRA’U IBN AZIB ya ce:
    تسحرت في شهر رمضان ثم خرجت فأتيت ابن مسعود فقال: اشرب،فقلت: إني قد تسحرت، فقال: اشرب! فشربنا ثم خرجنا والناس في الصلاة.
    Wato= na kammala sahur a RAMADAN, na zo wurin Sahabi ABDLH BN MAS’UD R/A sai ya ba ni abin sha, na ce masa na kammala sahurfa! Sai ya ce= ka sha na ce, BARRA’U ya ce “Sai na sha, muna mutane na cikin sallar asuba,

    👉🏼(2864) HIBBAN ya ce:
    تسحرنا مع علي ثم خرجنا وقد أقيمت الصلاة فصلينا.
    Wato= mun yi sahur tare da ALIY BN ABI DALIB (R.A) mun fito an riga an tayar da iƙamar sallah, sai muka yi sallah,
    ALLAHU A’ALAM.

    Domain sanin hukuncin yi wa mata kaciya danna kuren rubutu

    Amsawa : Sheikh Abubakar BN Mustafa Biu
    22/10/2019

    Daga : ZAUREN ISLAMIC SUNNAH

  • Ana Kiran Sallah Hailata Ta Zo

    Ana Kiran Sallah Hailata Ta Zo

    1. Tambaya

    As salamu alaykum wa rahmatul lahi wa barkatuhu. Malam barka da warhaka, Malam ina da tambaya, Ana kiran sallah Azahar sai mutum ya ga haila, in ya yi tsarki ya rama sallah ko baya rama sallah? Nagodé Allah ya saka da Alkhairi

    Amsa

    Wa’alaikumus Salam Warahmatullah. Irin wannan tambayar an yi wa SHEIKH SALEH UTHAIMEEN cewa, mace ce haila ta zo mata karfe 1:00 kafin ta yi sallar azahar, shin in jinin ya tsaya, za ta biya azahar ɗin ne⁉ Sai ya ce:
    “Akwai saɓanin malamai a kan haka zuwa gida biyu:
    1- suka ce, ba wajibi ba ne ta biya sallar, domin ba ta yi laifi ba, kuma ba ta yi sakaci ba, tunda ya halatta a jinkirta salla zuwa ƙarshen lokacinsa,
    2- suka ce wajibi ne ta biya wannan sallar, don umarnin faɗin Annabi (S.A.W)
    [عن أبي هريرة:] من أدرك ركعةً منَ الصلاةِ فقد أدركَ الصلاةَ
    أبو داود (٢٧٥ هـ)، سنن أبي داود ١١٢١ • سكت عنه [وقد قال في رسالته لأهل مكة كل ما سكت عنه فهو صالح] • أخرجه البخاري (٥٨٠)، ومسلم (٦٠٧)
    Wato, “Wanda ya riski raka’a guda a sallah, kafin fitar lokacinsa, to ya riski sallar,
    Sai UTHAIMEEN ya ce, “Abin da ya fi a gare ta, ta biya tun da sallah ce ɗaya kacal babu takura wajen biya,
    Dubi (MAJMU’U FATAWAL MAR’AH- tattarawan SHEIKH MUHD SALAH)
    ALLAHU A’ALAM.

    Amsawa : Sheikh Abubakar BN Mustafa Biu
    13/10/2019