Author: Usmannoor

  • Cizo Nawa Sauro Take A Kamu Da Malaria?

    Cizo Nawa Sauro Take A Kamu Da Malaria?

    Cizo ɗaya tak yakan iya saka Malaria, macen sauro da ake kira da Anopheles mosquito ce take wannan ta’asar. Tana ɗiban jinin mutum ne wanda yake ɗauke da microscopic malaria parasite.

    Alamomin malaria suna bayyana ne daga kwana na farko zuwa kwana 30 bayan mutum ya kamu da cutar duk da cewar ya danganta da yanayin kalar parasite ɗin, yayin da wasu ma ba sa rashin lafiyar har tsawon shekara guda, duk da cizon na sauron haka kuma cutar parasite ɗin ka iya zama shekara da shekaru ba tare da alamomi sun bayyana ga wanda sauron ya ciza ba.

    Komai yana da amfani da kuma rashin amfani

    Sauro yana da amfani ga al’umma domin kuwa idan har ka yi haƙuri da cizon sa to zai zama silar kankare maka zunubi da kuma samun lada.

    Kuma kamar “ƙudan zuma” da kuma “malam buɗa mana littafi” haka sauro yake saka pollen daga flower zuwa wata flower ɗin sakamakon samun abincinsu a nectar wanda hakan yake sa tsirrai su haɓaka. Daɗin daɗawa: ba wai jini ne abincin macen sauro ba, pollen flower ita ce abincinta, jinin kawai ana sarrafa shi ne wajen ƙwayaye.

    Yaɗa cutar Malaria shi ne babban rashin amfaninsu sakamakon cutar Malaria ita ce ta fi kowacce cuta saurin kisa a cututtukan duniya baki ɗaya Kamar yanda masana bincike suka faɗa. Amman mu a matsayinmu na musulmai sai dai mu ce komai da Allah SWT ya yi akwai hikima a ciki ko mun gane ko ba mu gane ba, domin kuwa zazzaɓin Malaria ko kuma waninsa zai zamo silar kankarewar zunubban musulmi ne kamar dai yanda cizon cinnaka zai zamo silar kankarar zunubi (Cikakken bayanin zai zo a littafin da zan wallafa mai suna: AMFANIN CIZON CINNAKA)

    Wannan dalilin ne yasa ma’aiki (Sallallahu alaihi wasallam) ya koyar da mu adduar da za mu dinga faɗawa mara lafiya yayin dubiya: “Laba’atha ɗahuran insha Allah” ma’ana “Tsarkakewa ne (daga zunubbai) da yardar Allah”

    (Sahihul Bukhari)

    YANDA ZA MU MAGANCE CIZON SAURO 

    Mu yawaita Istighfari a dukkanin al’amuran mu domin kuwa idan Allah Azzawajallah ya ga dama sai ya halakar da kai da cizon macen sauro ɗaya tak sakamakon zunubban da kake aikatawa musamman na ɓoye. 

    Akwai magungunan sauro kala-kala musamman waɗanda suke da alaƙa da hayaƙi. Dalilin da ya sa sauro ba ya son hayaƙi shi ne: akwai cikakkiyar iska (oxygen) wadda take shiga ramukan (cavities) da ke jikin sauro (spiracles) waɗanda su ne kamar hancinsa da suke a doron jikinsa. Hayaƙi yana ɗauke da wasu particles da idan sauro ya shaka suke fasa hunhunsa, hayaƙin kan hana sauro shaƙar tsaftatacciyar iska, shi yasa ba ya buƙatar kusantar inda aka saka maganin sauro (mosquito coils).

    Akwai magungunan sauro na shafawa a jiki kamar irinsu “Gardia mosquito repellent cream” wanda gaba ɗaya sauro baya son shi saboda yana ɗauke da diethyltoluamide kaso 13% wanda yana da matuƙar haɗari ga rayuwar sauro shi yasa ba ya iya sauka fatar mutum yayin da ya shafa maganin.

    A ƙarshe ina son in ja hankalin mu da mu yawaita tsaftace muhallin mu domin kuwa Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) yace: “Tsafta tana daga cikin cikin Imani” (Sahihul Bukhari)

    Danna nan don karanta cikakken littafin

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Sauro Yana Gani Ne Da Iskar Da Muke Fitarwa (Co2)

    Sauro Yana Gani Ne Da Iskar Da Muke Fitarwa (Co2)

    Kamar yanda ɗan Adam yake son launin kore domin ingantuwar lafiyar ganinsa, shi kuma sauro ya fi son duhu saboda baƙar kala ta fi karɓar yanayin zafi yayin da farar kala take mai da yanayin zafin. Misali: idan ka saka baƙaƙen kaya za ka ji gaba ɗaya jikinka yana gumi yayin da kuma idan ka saka fararen kaya za ka ga ko da rana ta doke ka ba za ka ji gumi sosai ba.

    Tunda sauro yana da na’urar jin zafi nan take yake amfani da wannan damar wajen farmakar mutumin da yake sanye da baƙaƙen kaya, yana ɗaya daga cikin dalilan da yasa za ka ga sauro yana ta sunturi a saman gashin mutum saboda launin gashin baƙi ne.

    Duk da cewar sauro ba ya amfani da haske wajen ganin abu kamar mutane, amma launi yana taimaka masa bisa la’akari da launin baƙi yana janyo zafin yanayi wanda yake faruwa silar kaɗuwar iska wadda dama da iskar da muke fitarwa ta Carbon dioxide (CO2) yake ganin abu.

    Wani mai ilimin sanin ƙwari (entomologist) da ke jami’ar Florida a Vero Beach da ke ƙasar Amurka yace “Sauro yana dogara da gani ne wajen zaƙulo abin farautarsa, abubuwa masu duhu kamar irinsu: baƙaƙen kaya, blue ko ja kan saka ƙwari saurin gano abu”

    Ganin wannan hikima da Allah Azza wa jallah ya tsarawa wannan halitta ta sauro ne ya sa masu ilimin fasaha (technologist) suka kwaikwaya wajen fitar da na’urar gano abinda ya shamakance idon mutum, misali: ‘yan sanda suna iya gano adadin masu laifi yayin da suka shiga maɓoya ta hanyar amfani da hular kwano mai ɗauke da binoculars mai amfani da hasken ultraviolet light, wannan cigaba ne a tarihin ɗan Adam, dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allaah Azza wa jallah wanda ba ya kwaikwayon halitta a matsayinSa na gwanin iya halitta.

    Masana ilimi da suke a jami’ar Alaska ta Amurka sun ce halittar sauro ta zarce sama da shekaru miliyan 226. Amma mu a matsayinmu na musulmai sai dai mu ce “wallahu ta’ala a’alam” 

    Domin karanta adadin idanun sauro danna nan

    Danna nan don karanta cikakken littafin

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Shin Sauro Yana Yaɗa Cutar HIV/AIDS?

    Shin Sauro Yana Yaɗa Cutar HIV/AIDS?

    Mun san da cewar macen sauro tana da saliva wato miyau, sannan tana da allurai har guda 6 waɗanda da su take aikin zuƙar jinin mutum, guda 4 tana amfani da su ne wajen huda fatar mutum yayin da guda 2 ɗin kuma suke ɗauke da wani “pipe” da ake kira da “tube” wanda 1 magudanar miyau ne 1 kuma magudanar da jinin mutum yake bi ne yana komawa jikin sauron wannan ɗaya daga cikin dalilai ne da yasa ba sa iya yaɗa cutar HIV ko da sun ɗauko ta daga mai ƙanjamau ɗin, kamar yanda Professor Wayne Crans da ke jami’ar Rutgers ya sanar da manema labarai

    Dalili na 2 kuma shi ne: ƙwayar cutar HIV ba ta replicating ma’ana yaɗuwa a cikin hanjin sauro ko da ya yi ƙoƙarin yaɗa ta ga wanda ba shi da cutar, nan da nan Allah yake kiyaye bayinSa cutar take breaking down wato nan take take mutuwa. Ga mutane, cutar HIV tana nannaɗewa ne ga T-cells hakan yakan saka ta yaɗuwa amma a cikin sauro kuwa babu T-cells don haka cutar ba za ta iya tsallakawa zuwa miyau ɗin sauro ba.

    Wannan ikon Allah ne kam, domin kuwa ban manta da hadisin nan da ke cikin Sahihul Bukhari ba wanda Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) yace “Idan alfasha ta yi yawa a ban ƙasa to sababbin cututtuka da ba ku san su ba za su yawaita”, a nan Allah cikin ikonSa ya kiyaye wasu mutanen daga kamuwa da cutar ƙanjamau ta hanyar cizon sauro wanda suke zuƙowa daga masu ƙanjamau cutar da aka fi samu silar alfasha duk da dai ana samu ta ɓangaren amfani  da reza ko kuma allurar da take ɗauke da jinin mai cutar, wannan duk tsantsar lissafi ne na Allah Azza wajallah wanda dama shi ne “AL-HASIBU” mai lissafa kuma Mai ƙididdige abu. Allahu Akbar !

    A likitance ma ko da a ce sauro zai yaɗa cutar HIV to sai an samu cizon sauraye sama da miliyan 10 kafin a samu guda 1 da zai iya saka cutar, a kintace, masu cutar HIV ba sa ɗauke da unit 10 na cutar. A haɗarance kuma, ko da zaka hadiye sauro ko kuma make shi da hannu hakan ba zai sa ka kamu da cutar HIV ɗin a jikin sauron ba, hakan na nufin sauro ba shi da isasshen jinin mai ƙanjamau da har mutane suke tunanin zai iya yaɗa shi ga mara ƙanjamau ba.

    Suna ƙyanƙyashi ‘ya’yansu ne ta hanyoyi 4

    Na farko haihuwar ƙwayayen (eggs) daga nan kuma cikin ikon Allah da hikimarSa sai ƙwan ya koma abinda ake kira da larva (za su yi kama da caterpillar ko kuma ɗan mitsisin kifi) daga nan kuma sai pupa (kamar tsutsa) sai kuma su zama adult, sai Allah Azza wajallah ya ba su ikon buɗe fika-fikansu sai su fara tashi su zama sauro.

    Namijin sauro yana kai kwanaki 10 kafin ya mutu amma macen takan share kwanaki 42 zuwa 56 kafin mutuwarta. Bambancin adadin kwanakinsu kuwa yana da alaƙa da ɗawainiyar da macen take na ɗaukar nauyin ƙyanƙyashe ƙwayayenta.

    Ko da jininka ko babu Allah Azza wajallah yana ba wa sauro tsawon a ƙalla rayuwar sati 2 zuwa 3, ba wai dole sai da jini suka ta’allaƙa su rayu ba kamar yanda wasu suke tunani ba.

    A kowanne kwana 3 macen sauro take zuba ƙwayayenta akan ruwa, musamman ma ruwan kwata, ba abin mamaki ba ne kenan idan ya zamana sauro ya yawaita a kwatocin unguwanni da mutane marasa tsafta.

    Don karanta littafin sauro halittar Allah mai ban al’ajabi danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Ko Ka San Cewa Idanun Sauro Sun Fi 100?

    Ko Ka San Cewa Idanun Sauro Sun Fi 100?

    Allah (Subhanahu wata’ala) yace:

    ( إِنَّ اللَّهَ لَا يَسْتَحْيِي أَن يَضْرِبَ مَثَلًا مَّا بَعُوضَةً فَمَا فَوْقَهَا ۚ فَأَمَّا الَّذِينَ آمَنُوا فَيَعْلَمُونَ أَنَّهُ الْحَقُّ مِن رَّبِّهِمْ ۖ وَأَمَّا الَّذِينَ كَفَرُوا فَيَقُولُونَ مَاذَا أَرَادَ اللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلًا ۘ يُضِلُّ بِهِ كَثِيرًا وَيَهْدِي بِهِ كَثِيرًا ۚ وَمَا يُضِلُّ بِهِ إِلَّا الْفَاسِقِينَ )

    البقرة (26) Al-Baqara

    Lallai ne, Allah ba Ya jin kunyar Ya bayyana wani misãli, kowane iri ne, sauro da abin da yake bisa gare shi. To, amma waɗanda suka yi ĩmãni, sai su san cewa lallai shi ne gaskiya daga Ubangijin su, kuma amma waɗanda suka kãfirta, sai su ce: “Mẽne ne Allah Ya yi nufi da wannan ya zama misãli?” na ɓatar da wasu mãsu yawa da shi, kuma Yana shiryar da wasu mãsu yawa da shi, kuma bã Ya ɓatarwa da shi fãce fasiƙai.

    A cikin Tafsirin Ibn Khathir As-Suddi ya karɓo daga Ibn Abbas, Ibn Mas’ud da wasu daga cikin Sahabbai cewar: Da Allah ya buga misalai guda 2 na munafukai” ( مَثَلُهُمْ كَمَثَلِ الَّذِي اسْتَوْقَدَ نَارًا )  البقرة (17) Al-Baqara

    Misãlinsu shĩ ne kamar misãlin wanda ya hũra wuta, Da kuma: ( أَوْ كَصَيِّبٍ مِّنَ السَّمَاءِ ) البقرة (19)  Al-Baqara

    Ko kuwa kamar girgije mai zuba daga sama, Sai Munafukai suka ce: Allah ya fi ƙarfin ya buga misalai da waɗannan abubuwan Sai Allah (Subhanahu wata’ala) ya saukar da ita waccan ayar har zuwa:  أُولَٰئِكَ هُمُ الْخَاسِرُونَ ) البقرة (27) Al-Baqara waɗannan sũ ne mãsu hasãra.

    Sa’id yace: Ƙatada yace: “Allah ba ya jin kunyar faɗin gaskiya idan ya buga misali akan abu: babba ne ko ƙarami. Lokacin da Allah (Subhanahu wata’ala) ya buga misali da ƙwaro da gizo-gizo a littafin Sa, sai Munafukai suka ce: Me yasa Allah ya yi misali da waɗannan abubuwan. Sai Allaah ya saukar da:

    ( إِنَّ اللَّهَ لَا يَسْتَحْيِي أَن يَضْرِبَ مَثَلًا مَّا بَعُوضَةً فَمَا فَوْقَهَا ۚ  البقرة (26) Al-Baqara

    Lallai ne, Allah bã Ya jin kunyar Ya bayyana wani misãli, kõwane iri ne, sauro da abin da yake bisa gare shi. 

    Abu Jafar Ar-Razi ya karɓo daga Ar-Rabi bin Anas wanda ya yi sharhin wannan Ayar (2:26): “Wannan ne misalin da Allah ya bayar dangane da rayuwar wannan duniyar tamu”

    “Sauro yana rayuwa ne indai har zai ci abinci amman yayin da cikinsa ya cika sai ya mutu. Wannan shi ne misalin wasu mutanen waɗanda Allah ya faɗa a cikin Qur’ani:

    ( فَلَمَّا نَسُوا مَا ذُكِّرُوا بِهِ فَتَحْنَا عَلَيْهِمْ أَبْوَابَ كُلِّ شَيْءٍ حَتَّىٰ إِذَا فَرِحُوا بِمَا أُوتُوا أَخَذْنَاهُم بَغْتَةً فَإِذَا هُم مُّبْلِسُونَ )

    الأنعام (44) Al-An’aam

    Sa’an nan kuma a lõkacin da suka manta da abin da aka tunãtar da su da shi, sai Muka bũɗe, a kansu, ƙõfõfin dukkan kõmai, har a lõkacin da suka yi farin ciki da abin da aka ba su, Muka kãmã su, kwatsam, sai gã su sun yi tsuru-tsuru.

    A cikin waccan aya ta 26 (Da Allah ya yi misali da Sauro): فَمَا فَوْقَهَا ۚ (…da abin da yake bisa gare shi.) Wanda yana daga cikin halittun da ake ɗaukarsu da ƙasƙanci kuma mafi ƙanƙanta. Muslim ya rawaito Hadisin Aisha (Radiyallahu anha) tace: Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) yace: «مَا مِنْ مُسْلِمٍ يُشَاكُ شَوكَةً فَمَا فَوْقَهَا إِلَّا كُتِبَتْ لَهُ بِهَا دَرَجَةٌ، وَمُحِيَتْ عَنْهُ بِهَا خَطِيئَة»

    “Babu musulmin da zai cutu silar taka ƙaya (فَمَا فَوْقَهَا) ko abinda ya fi ta girma, face Allah yasa an rubuta masa lada cikakke sannan a kankare masa zunubinsa” (Sahih Muslim)

    Don haka Allah ya sanar da mu cewar babu wani abu ƙarami ko babba da ba za a iya misali da shi ba ko da kuwa ƙanƙantar sa ta kai Sauro ko gizo-gizo. Tun da har Allah (Subhanahu wata’ala) ya buga misali da sauro a cikin littafi Mai Tsarki, to tabbas sauro yana da abubuwan Al’ajabai. Ku gyara zama domin ilimantuwa da su.

    Sauro ! Tun muna yara muke ji da ganin illar wannan ƙaramar halitta ga lafiyarmu. To amma ya kamata mu ƙara zurfafa tunani akan wannan halitta mai ban mamaki. Yayin da ɗan Adam yake da idanu guda 2 domin gani, shin ko ka san da cewar sauro yana da idanu sama da guda 100 masu suna mini eyes kuma kowanne guda 1 a cikinsa shi ma akwai sama da guda 100 da ake kira da lenses, kuma kowanne da irin aikinsa.

    Dalilin hakan ne yasa ba za ka iya kashe shi farat ɗaya ba ko da kuwan ka biyo ta bayansa. Irin wannan dalilin ne yasa aka kwaikwayi idon sauron ta hanyar ƙirƙiro CCTV camera, drones, motoci masu tuƙa kansu da kansu da ake kira da “self driving cars”, da dai sauransu. Allahu Akbar !

    Shin ko kun san da cewar macen sauro ce take cijo ba wai namijin ba ?

    Shi aikin namijin shi ne: ya sadaukar da rayuwarsa ta hanyar jan hankalin mutum domin macen (wato matarsa) ta samu damar zuƙar jinin da za ta samar da isassun ƙwayayen da za ta ƙyanƙyashe ta yanda za a ƙara samun wasu ‘ya’yan sauron, kenan hakan yana nufin ta cikin jininmu suke samun ƙwayayensu, wanda a ƙalla macen sauro tana ƙyanƙyashe ƙwayaye guda 100 zuwa 200 a lokaci ɗaya, Allahu Akbar !

    Allah mai yanda ya so !

    Yayin da ya zamana Allah ya haliccemu da zuciya guda 1, shin ko kun san da cewar sauro yana da zuciya har guda 3 ?

    Akwai left ventricle  akwai right ventricle sannan kuma akwai central ventricle kuma cikin ikon Allah, kowacce da irin aikin da take yi a jikin sauron. Sauro ita ce halittar da ta fi kowacce halitta yawan kashe ɗan Adam ta hanyar saka masa cutar Malaria, Zika da kuma West Nile. A ƙalla da akwai ire-iren sauraye a duniya sama da 3,500 waɗanda suke satar jinin dabbobi kama daga micizai, kifaye da kuma mutane domin su samar da ƙwayayensu.

    Sauro na iya ganin mutum a cikin mosquito net ba tare da wani shamaki na bango ba, a maimakon mu da muke amfani da haske domin gani, shi kuma sauro yana amfani da iskar Carbon dioxide ne wadda yakan iya shaƙar numfashinka daga nisan ƙafa 150, hakan ke ba su damar gano blood group ɗinka, wanda indai bai yi dai-dai da nasu ba, ba za su sha jinin ba, Allahu Akbar !

    Allaah cikin iliminSa ya bawa Professor Jeffery Riffel (Malamin Biology a Jami’ar Washington ta Amurka) ikon gano dabi’un sauro dakuma yanda sauron yake tunani. Lokacinda ya bude qoqon kan sauron wanda ake kirada cuticle yaga qwaqwalwar sauron, kamar yanda ya zanatawa manema labarai. Sun gano hakanne bayan shafe shekaru samada 12 shi da abokan aikinsa (team)

    Shin ko kun san sauro yana kaɗa fika-fikansa sau 1000 a cikin second 1 ?

    Yayin da macen sauro take sokawa fatar mutum allurai 6 da suke a bakinta, a lokacin ne namijin sauro yake jan hankalin mutum don aikin macen ya kammala ba tare da mutum ya farga ba.

    Duk da cewar ma kafin ka ji zafin cizon sai an ɗauki ‘yan sakwanni saboda allurar sedative da take tsirawa fata domin kashe zafin cizon, yayin da aikin ya kammala ita kuma ta riga ta bar fatar a lokacin ne zafin cizon zai fara tasiri akan fatar mutum, yayin da ka kai duka kuma tuni ta daɗe da tsotsar adadin jinin da take buƙata. Allahu Akbar !

    Wannan duk ba abin mamaki ba ne domin kuwa idan muka koma cikin littafin Allah, Al-Qur’ani mai girma to za mu tabbatar da cewar ikon Allah ya wuce duk yanda ‘yar ƙaramar ƙwaƙwalwarmu take tunani. Tuni Allah ya faɗa a cikin Suratul Baqara aya ta 26. To a nan tunda ka ji misalin sauro ya fito a cikin Qurani kai ka san yana da abubuwan al’ajabi kam.

    Wannan kaɗan daga cikin bayani ne akan halittar sauro, daya daga cikin ziliyoyin halittun Allah, duk Allah ya ba wa masu ilimin kimiyya wannan damar ne domin su gane ayoyinsa da suke sararin sama’uddunya da kuma kan duniyarmu ta Ard da muke rayuwa.

    Domin karanta cikakken littafin danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

     

     

     

     

     

  • Sauro Halittar Allah Mai Ban Al’ajabi

    Sauro Halittar Allah Mai Ban Al’ajabi

    Yayin da ɗan Adam yake da idanu guda 2 domin gani, shin ko ka san da cewar sauro yana da idanu sama da guda 100 masu suna mini eyes kuma kowanne guda 1 a cikinsa shi ma akwai sama da guda 100 da ake kira da lenses, kuma kowanne da irin aikinsa ?

    Dalilin hakan ne yasa ba za ka iya kashe shi farat ɗaya ba ko da kuwan ka biyo ta bayansa. Irin wannan dalilinne yasa aka kwaikwayi idon sauron ta hanyar qirqiro CCTV camera, drones, motoci masu tuqa kansu da kansu da ake kirada self driving cars, dadai sauransu. Allahu Akbar !

    Shin ko kun san da cewar macen sauro ce take cijo ba wai namijin ba ?

    Shi aikin namijin shi ne: ya sadaukar da rayuwarsa ta hanyar jan hankalin mutum domin macen (wato matarsa) ta samu damar zuƙar jinin da za ta samar da isassun ƙwayayen da za ta ƙyanƙyashe ta yanda za a ƙara samun wasu ‘ya’yan sauron, kenan hakan yana nufin ta cikin jininmu suke samun ƙwayayensu, wanda a ƙalla macen sauro tana ƙyanƙyashe ƙwayaye guda 100 zuwa 200 a lokaci ɗaya, Allahu Akbar !

    Allah mai yanda ya so !

    Yayin da ya zamana Allah SWT ya halicce mu da zuciya guda 1, shin ko kun san da cewar sauro yana da zuciya har guda 3 ?

    Akwai left ventricle akwai right ventricle sannan kuma akwai central ventricle kuma cikin ikon Allah, kowacce da irin aikin da take yi a jikin sauron.

    Sauro ita ce halittar da ta fi kowacce halitta yawan kashe ɗan Adam ta hanyar saka masa cutar Malaria, Zika da kuma West Nile. A ƙalla da akwai ire-iren sauraye a duniya sama da 3,500 waɗanda suke satar jinin dabbobi kama daga mijizai, kifaye da kuma mutane domin su samar da ƙwayayensu.

    Sauro na iya ganin mutum a cikin mosquito net ba tare da wani shamaki na bango ba, a maimakon mu da muke amfani da haske domin gani, shi kuma sauro yana amfani da iskar Carbon dioxide ne wadda yakan iya shaƙar numfashinka daga nisan ƙafa 150, hakan ke ba su damar gano blood group ɗinka, wanda in dai bai yi daidai da nasu ba, ba za su sha jinin ba, Allahu Akbar !

    To ya akai muka san wannan ilimin ?

    Allah cikin ikonSa ya ba wa Professor Jeffery Riffel (Malamin Biology a Jami’ar Washington ta Amurka) ikon gano ɗabi’un sauro da kuma yanda sauron yake tunani. Lokacin da ya buɗe ƙoƙon kan sauron wanda ake kira da cuticle ya ga ƙwaƙwalwar sauron, kamar yanda ya zanatawa manema labarai. Sun gano hakan ne bayan shafe shekaru sama da 12 shi da abokan aikinsa (team).

    Shin ko kun san sauro yana kaɗa fika-fikansa sau 1000 a cikin second 1?

    Yayin da macen sauro take sokawa fatar mutum allurai 6 da suke a bakinta, a lokacin ne namijin sauro yake jan hankalin mutum don aikin macen ya kammala ba tare da mutum ya farga ba. Duk da cewar ma kafin ka ji zafin cizon sai an ɗauki ‘yan sakwanni saboda allurar sedative da take tsirawa fata domin kashe zafin cizon, yayin da aikin ya kammala ita kuma ta riga ta bar fatar a lokacin ne zafin cizon zai fara tasiri akan fatar mutum, yayin da ka kai duka kuma tuni ta daɗe da tsotsar adadin jinin da take buƙata. Allahu Akbar !

    Wannan duk ba abin mamaki ba ne domin kuwa idan muka koma cikin littafin Allah SWT, Al-Qur’ani mai girma to zamu tabbatarda cewar ikon Allah ya wuce duk yanda ‘yar ƙaramar ƙwaƙwalwarmu take tunani. Allah SWT yace a cikin Suratul Baqara ayata 26 “Innallaha layastahyi anydriba, masalamma ba’udatan fama fauƙaha” ma’ana “Lalle ne, Allah ba ya jin kunyar ya buga misali kowanne iri ne, SAURO, da binda yake bisa gare shi”. To a nan tunda ka ji misalin sauro ya fito a cikin Qurani kai ka san yana da abubuwan al’ajabi kam.

    Wannan kaɗan daga cikin bayani ne akan halittar sauro, ɗaya daga cikin ziliyoyin halittun Allah SWT, duk Allah ya ba wa masu ilimin kimiyya wannan damar ne domin su gane ayoyinsa da suke sararin sama’uddunya da kuma kan duniyarmu ta Ard da muke rayuwa

    Muna roƙon Allah ya ƙara mana imani da kuma jin tsoronsa, ya tabbatar da mu akan bin sunnar ma’aiki ya raba mu da bidi’a ya nesanta mu daga azabar wuta sannan kuma ya saka mu a AljannarSa don RahamarSa ba don halinmu ba.

    Domin karanta cikakken littafin danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

     

     

  • Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Iyaye Mata A kan ‘Ya’yansu Mata

    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Iyaye Mata A kan ‘Ya’yansu Mata

    Ina farawa da sunan Allah mai rahma, kuma mai jinƙai, Wanda yake ara min iko da har dubun nan bayinsa suke karanta rubuce-rubucena a kafar sadarwa ta zamani.

    Yakan ba ni iko ne ba wai don na isa ba, ko kuma na kai ba, sai domin ya nunawa al’umma ayarsa ta halittar ƙwaƙwalwa a kaina, mai fitar da abin da ake mamakin fitar sa, sarki ɗaya tilo wanda bashi da kishiya.

    A karon farko wannan ne rubutuna da harshen Hausa a maimakon da can da nake yi da harshen Bature wato Ingilishi, na yi hakan ne domin iyayenmu mata su samu sauƙin fahimtar saƙon da nake son isarwa a kan ‘ya’yansu mata

    Ina mai amfani da wannan dama, domin nusar da iyaye mata da su ƙara zage damtse a kan yadda suke, su saka ido a kan rayuwar ‘ya’yansu ta yau da gobe, abubuwa suna faruwa sosai wanda kuma wani lokacin ƙawayen ‘ya’yan ne sanadi.

    Ciwon ‘ya mace na ‘ya mace ne, Kai a waye ya kamata ki kira ‘yarki, ku zauna daga ke sai ita, ki ci gaba da ba ta shawarwari a kan ta kiyaye mutuncinta da kuma mutuncin gidan da ta fito, saboda tarwatsewar tarbiyyarta daidai yake da taɓarɓarewar al’umma baki ɗaya, kamar yanda Annabi S.A.W ya faɗa a cikin hadisi “…Idan mace ɗaya ta lalace, to al’umma ce gaba ɗaya ta lalace”.
    A matsayina na ɗalibi a Jami’ar Bayero ta Kano, a da can na ga yadda kowa yake tafiyar da rayuwarsa a kan tafarkin da iyayensa suka ɗora shi, kenan ya zamo babban nauyi ne, da Allah ya ɗora wa iyaye mata wanda ya kamata su jajirce domin ganin sun sauke wannan nauyi wanda ya rataya a wuyansu.
    Akwai wani lokaci ba zan taɓa mantawa ba, ina zaune a makaranta wani bawan Allah wanda ba zan kama sunansa ba, ya zo ya same ni, ya ce, “Shi fa babu abin da ya tsana sama da ya ga ina rubutun fadakarwa a kan abubuwan dake faruwa a Jami’a”. Na kawo wannan magana ce ba wai don na ci masa mutunci ba sai dai domin na kafa hujja da cewar abubuwan dake faruwa a Jami’a sai an sa ido sosai kuma an dage da addu’a domin gudun da-na-sani)

    Za ka ga yarinya ta taso daga gidan mutunci da kamala, amman a sanadin haɗuwa da ƙawa mai son abin duniya, za ka ga ta zubar da mutuncinta, wannan abin kunya ne kam, a maimakon kiyaye mutuncinta, saboda kunnen ƙashi sai kawai ta siyar da shi a kan farashi mai rahusa, sun manta da Suratul Maryam aya ta 86

    Inda Allah (S.W.T) yake cewa “Kuma muna kora masu laifi zuwa jahannama, gargadawa {Wanasuqul majrimina ila jahannama wirda}”…Bayan wannan kuma akwai inda Allah S.W.T yake faɗa wa Annabi (S.A.W) a cikin Suratul Maryam Aya ta 83 cewar “Shin ba ka gani ba cewa mun saki shaiɗanu a kan kafirai suna susuta su ga masu zunubi, susutawa?
    Ma’ana idan shaiɗanu sun ga mai wa’azin gaskiya, sai su dinga susuta mabiyansu domin su yi faɗa da mai wa’azin, domin kada su saurare shi, har su gane ɓatan su, Shaiɗan shi ne mai ɓatar da wani mutum ne ko aljan.
    Shekara ɗaya da ta gabata, wani bawan Allah wanda ba zan kama sunan shi ba, ya zo har inda nake, ya zazzage ni, na tambaye shi ko mene ne dalilin zagina da ya yi? Kun san me yace min kuwa? Wai akwai wata yarinya wadda suka yi da ita cewar za su haɗu, su je yawon ashararanci tare, sai kawai ya ji ta kirasa a waya, ta ce masa “Ya hau WhatsApp”. Hawansa ke da wuya, sai kawai ta tura masa wani rubutuna da nake magana a kan hukuncin aikata zina, nan take ya kira ta a waya ya ce mata, “Na gani, sai akai yaya?” sai ta ce masa, “Sai mu daina aikata aikin haram”.
    Ya ji haushin abin matuƙa a lokacin, amman cikin ikon Allah sai ban neme shi da rigima ba, na ba shi shawarwari a nutse, to yanzun haka dai bawan Allan nan shima, ya tuba ya daina abin da yake yi, Allah gafurur Raheem ne, ya kamata iyaye su zaunar da ‘ya’yansu mata, su tuba kafin su koma gare shi.

    A game da rubuce-rubucen faɗakarwa, an sha zuwa har inda nake, an ci mun mutunci kawai, saboda faɗin gaskiya, amman ba na damuwa samsam idan na tuno da aya ta 84 a cikin dai Suratul Maryam:

    Allah ya cewa Annabi S.A.W “Saboda haka kada ka yi gaggawa a kansu, muna yi musu ƙidayar ajali ne kawai, ƙidayawa {Fala ta’ajal alaihim innama na’uddu lahum addaa}”
    Kowa da yanayin ƙarfin gidansu, wasu sun kasance masu kuɗi ne, wasu kuma talakawa wasu kuma akwai dai ɗan rufin asiri, rashin godiyar Allah ke saka wasu ƙawayen su ji suna sha’awar mallakar abin da ya fi ƙarfin aljihun iyayensu, ballanatana su da kansu, kin ga ƙawarki da babbar waya mai tsada, ki ce ke ma dole sai kin siya, shi kuma saurayi idan ya duba wannan, sai ya ce miki ya yi miki alƙawarin zai yi amfani da kuɗinsa ya biya miki buƙatarki, amman fa shi ma yana da sharaɗi wanda ba saina fada ba.
    Ya ku iyayenmu mata, Ku ja musu kunne sosai, a kan su dinga kiyayewa, su yi taka tsantsan, su san da waɗanda za su dinga mu’amula musamman ma ƙawayensu na jami’a, nasan wasu ba za su ji daɗin karanta wannan saƙo nawa ba, saboda za su yi tunanin da su nake, masu kunnen ƙashi kenan, to amman idan ma mutum ya ji haushi to ya gyara, an ce dai gyara kayanka, ba ya zama sauke mu raba.
    Wasu suna mantawa da rayuwar lahira, abin da ka shuka, shi za ka girba, ku tuba kafin ku mutu, kuna masu laifi, idan kuka tuba za ku zamo baƙin girma a Aljannah, saboda Allah (S.W.T) ya ce a cikin Suratul Maryam aya ta 85 “A ranar da muka tara masu taƙawa zuwa ga mai rahama suna baƙin girma {Yauma nahshuru almuttaqina ilalrahman wafda}”
    Wasu matan suna jazawa wasu, ba duka ba ne aka taru aka zamo ɗaya ba, akwai nagari da yawa, tsiraru ne na banza. A matsayina na tsohon shugaban department ɗin Microbiology, Jami’ar Bayero wanda yake da masaniya a kan halayyar al’umma, na yi binciken mene ne silar gurɓacewar halin mata, ɗaya daga cikin sakamakon da na samu shi ne zuwa Club (Gidan Wasa) yana taka muhimmiyar rawa wajen kassara tarbiyyar mata
    Mene ne fa’idar zuwa Club, wajen da zuwan sa ba zai amfana miki komai ba a duniya, ballantana a lahira. Allah ka sa mu fi ƙarfin zuciyarmu ka shiryar da zuri’armu ka sada mu da dukkan hanyoyin alkhairi, ka raba mu da na sharri, sannan ka haɗa mu da mutanen kirki a duk inda suke, ka nesanta mu da bara gurbi
    A nan zan dasa aya, ba wai don abubuwan da zan faɗa sun ƙare ba, sai don kada na cinyewa masu karatu lokaci, a ƙarshe ina ƙara jan hankalin Iyayenmu mata da su yi hattara sosai a kan ‘ya’yansu, musamman a game da harkokin su na makarantar jami’a
    Ku tura wannan muhimmin saƙon ga iyaye mata, Allah ne kaɗai ya san ladan da za ku samu idan kuka zamo silar shiriyar bayinsa.