Author: Prof. Sa’idu Muhammad Gusau

  • Iyalin Musa Ɗanƙwairo

    Iyalin Musa Ɗanƙwairo

    Iyali suturar mutum, iyali suturar gida. A bisa yanayin zamantakewar bil Adama da aljannu, cikar ɗa, mutum namiji ko ‘ya, mutum mace ita ce yadda Allah ya hore musu, ya ba su dama, suka assasa zuriya ta kankin kansu.

    Ta haka za su sami nutsuwa, da samun ayyukan yi a duniyarsu da lahirarsu, musamman ma idan suka yi aiki da hukunce-hukuncen addini da matakan zamantakewar rayuwa bisa kyakkyawan zaɓi da dacewa. Haka kuma aure yana a kan gaba wajen tsayar da usra ko iyali da za su iya zama ƙwarara, ina ma a ce an bi sharuɗɗa da kyawawan dangogi na yin sa.

    Alhaji Musa Ɗanƙwairo wanda aka fi sani kuma ake kira da Maradun, ya sami jagoranci na iyaye wajen yin matar farko 21. A yayin zaman Ɗanƙwairo a doron rayuwar duniya bayan matarsa ta fari, ya auri mata da yawa kuma wasu daga cikinsu ne suka haifa masa ‘ya’ya har goma sha bakwai (17).

    Matan Aure na Musa Ɗanƙwairo

    Mata waɗanda Alhaji Musa Ɗanƙwairo ya aure a rayuwarsa ta duniya su ne:

    i) Hauwa Taladan
    ii) Hajiya Hadiza (Ikka/Tashikka)
    iii) Amina
    iv) Tumba
    v) Rabi (‘Yar Zuma)
    vi) Maryam (Amarya)
    vii) Hauwa
    viii) Maimuna

    ‘Ya’yan Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maza da Mata

    Ga tsarin sunayen ‘ya’yan Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ta bin ɗakunan iyayensu mata da suka haɗa da:

    i) Ɗakin Hauwa (Taladan)

    ii) Ɗakin Hajiya Ikka (Tashikka)
    a) Muhammadu Ɗanmakaɗa, Dauda na ɗaya (1)
    b) Alhaji Garba, Zwacin Kiɗi, Marafa, Daudu (2)
    c) Audu Adodo, Wakilin Kiɗa
    d) Zulaihat
    e) Habiba

    iii) Ɗakin Amina
    f) Ummaru Ka-ji-Dama (Makaɗin Noma)
    g) Amina (Kassu): Tana aure a Maradun

    iv) Ɗakin Tumba
    h) Sanin Ɗanƙwairo, Zakin Murya

    v) Ɗakin Maryam (Amarya)
    i) Sa’adatu
    j) Muhammadu Balarabe
    k) Umaru

    vi) Ɗakin Rabi’a (‘Yarzuma)
    l) A’ishatu (Indo)
    m) Malam Musa Tunau (Malamin Makarantar Allo)

    vii) Ɗakin Hauwa
    n) Abubakar, Ciroman Kiɗa
    o) Amina, Ige
    p) Ibrahim Ɗan’auta22

    viii) Ɗakin Maimuna
    Ba ta Haihu ba.

    Bishiyar Iyalin Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun

    Kaka Maiganga
    Usman Ɗankwanagga = Yarnunu
    Musa Ɗanƙwairo23 Amina Binta (Maryam)

    = Hauwa = Haj. Hadiza =Amina = Tumba = Maryam =Rabi = Hauwa =Maimuna
    (Taladan) (Ikka Tashikka) (Amarya) (‘Yar Zuma)
    Malam Musa Ba ta
    Tunau haihu ba
    Umaru Amina (Kassu)
    (Ka-Ji-Dama) Tana Aure Sa’adatu Muh Umaru
    a Maradun (‘Yabbata) Balarabe
    Muhammadu Sani (Zaƙin Murya)
    Ciroma Amina Ibrahim Ɗan’auta
    Abubakar (Ige) (Harkokin
    Magaji na (2) Kasuwanci)
    Muhammadu Garban Audu Zainabu Habiba
    (Ɗanmakaɗa) Ɗanƙwairo (Adodo)
    Magaji na (1)

    = Salame = Baraka
    Muhammadu Muh Tamaikiɗi
    Ɗanjimma Basiru
    Magaji na (3)

    Domin karanta cikakken bayani a kan Kiɗa da Waƙoƙin Makaɗa Musa Ɗanƙwairo danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ma’anar Kiɗa da Makaɗi danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Wuraren Sadawar Waƙar Baka

    Wuraren Sadawar Waƙar Baka

    Makaɗan Hausa sukan sadar da waƙoƙin da suka yi bisa maƙasudai ne daban-daban gwargwadon waɗanda aka yi domin su. Waɗannan wurare da ake yin sadawar sababbin waƙoƙin baka sun haɗa da:

    i) Gidajen al’umma na ɗaiɗaikun mutane kamar gidajen sarakuna da gidajen malamai da gidajen attajirai; da gidajen masu jarumta da sauran gidajen masu sana’a da kuma sauran gidaje na ɗaiɗaikun al’umma.

    ii) Wurare na bukukuwa; kamar bikin aure da bikin suna da bikin kalankuwa da bukukuwan sarauta na al’adar Hausawa da bukukuwan masu sana’o’i da bukukuwan nunin amfanin gona da bukukuwan murna da bukukuwan da akan shirya na musamman da sauransu;

    iii) Dandali na shirya wasannin yara; tun a musamman lokacin kiɗan kalangu na ‘yan mata da na asauwara da kuma kiɗan duma da makamantansu.

    iv) Wuraren farauta; a fagagen da ake farauta a cikin dazuzzuka akan yi wa mafarauta sababbin waƙoƙi; kuma ana sadar da su da waƙoƙin ne a lokacin farautar a cikin dajin farauta, musamman a yayin da alalmisali, farauta ta rincime; ana buga in buga.

    Waƙoƙin da Kassu Zurmi ya yi sababbi; na farauta ya rera su ne kuma ya sadar da su kai tsaye a fagen farauta.

    v) Wurin noma, haka abin yake wurin manoma, musamman a yayi na gayyar noma a wata gona; kamar a Gandun Sarki, ko a gonar wasu Sarakai, ko a gonakin taimakon sauran talakawa. Nan ake sadar da sababbin waƙoƙi ga manoma, musamman waɗanda suke da sarautun noma kamar; Sarkin Noma da Madakin Noma da Gojen Noma da Kayayen Noma da sauran jaruman noma da makamantansu;

    vi) Wurin wasanni; Wurin wasannin al’ada a ƙasar Hausa wuri ne da ake rera sababbin waƙoƙi, a kuma sadar da su ga waɗanda aka yi wa su da sauran jama’a masu sauraro.

    Wurin wasannin al’ada sun haɗa da:

    – Wasan Asauwara wadda ake yi a kowace ranar kasuwa ta gari. Ana yin wasan Asauwara a ranar cin kasuwa ta wani gari da yammaci ne, gab da kamar la’asar sakaliya wato kasuwa za ta watse. A wasan Asauwara ana yin waƙoƙi ne tsakanin matasa-‘yan maza da ‘yan mata ko zabiyi da kuma zabiya. Kuma ana yin wasan Baura da kiɗan Baura, a wannan lokaci ma ana rera waƙoƙi sababbi da zimmar sadar da su.

    – Wasan kokawa

    – Wasan dambe

    – Wasan Sharu: wanda ake yi a lokacin da Hausawa suka shaƙu da Fulani

    – Da sauran wasanni.

    Wurin wasannin al’adun Hausawa, wuri ne ma wanda ake sadar da waƙoƙin baka na Hausa.

    vii) Wuraren Tarukan Makarantu:

    A lokacin da Hausawa suka sadu da Turawa, musamman a zamanin mulkin mallaka; Turawa suka ƙagi makarantu ga Hausawa tun daga zamanin karatun manya har zuwa karatun yara; an kakkafa wa Hausawa makarantu na boko daban-daban.

    To a yanzu a waɗannan makarantu tun daga na boko da kuma na islamiyoyi da a masallatan addinin Musulunci; duka ana yin taruka mabambanta kamar:

    – Tarukan fitar ɗalibai.
    – Taruka na aikin makarantu, kamar tarukan gama makaranta wato Convocation a Jami’a.
    – Taruka na maulidi, kamar Maulidin Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) da na Shaihunai da na Mujahidai da na sauransu.
    – Tarukan ga-Fili-ga-mai-doki.
    – Taruka na Musamman.
    – Da sauransu.

    viii) Wurare na Musamman

    Akwai kuma wasu wurare da ake shirya taruka na musamman domin kawai a rera waƙoƙi sababbi; a sadar da su ga mutanen da aka yi wa su da sauran jama’a na musamman. A ire-iren wurare da muhallai na musamman waɗanda ake nema domin a sadar da waƙoƙi sababbi sukan ƙunshi;

    – Wuri wanda aka zagaye shi, kuma aka yi masa shuke-skuke na ciyayi da wasu hakukuwa masu ƙayatarwa; musamman masu ƙara ganin ido ko warware kwarkwatar ido;

    – Wuri da aka tanada a matsayi na Gadina;

    – Wurin da aka tanada a matsayi na utel-utel ko ɗakin taro na musamman a manyan garuruwa da birane;

    – Wurin da aka keɓe domin shaƙatawa, ko na masaukan baƙi;

    – da sauransu da yawa.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yin Waƙar Baka ko Sarrafa Waƙar Baka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Aiwatarwa Da Sadarwa A Waƙoƙin Baka Na Hausa wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Ƙungiyar Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ta Kiɗa

    Ƙungiyar Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ta Kiɗa

    Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya samar da ƙungiya ta aiwatar da kiɗa mai zurfin tunani wadda kuma ta amsa sunanta. A wannan ƙungiya Ɗanƙwairo shi ne Jagora, kuma yana ba ‘Y/Amshi nasa damar yin ƙari da ajewa da sauka da saukar sauka da takidi da rakiya ko karɓeɓeniya, wani bi ma da bayayyeniya, sannan da yin takidi na G/Waƙa.

    Haka kuma a rera wasu waƙoƙi Alhaji Musa Ɗanƙwairo yakan tafi da Sanƙirori da wasu hadiman waƙa duk a ƙungiyar kiɗa ta Musa Ɗanƙwairo.

    Da kansa Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya nuna yadda yake aiwatarwa da ƙullawa da rerawa da sadar da ɗiya a waƙoƙinsa a wannan ɗa na waƙarsa ta ‘Yandoton Tsahe Alhaji Aliyu II, mai G/Waƙa:

    Shirya kayan faɗa mai gida Tsahe:

    Jagora: Duk Makaɗan da at Tsahe nai jam’i,
    : Hab baƙi ha ‘yan gida su duka,
    ‘Y/Amshi: Babu mai shirya waƙa kamat tawa,
    Jagora: Ga makaɗi ya ƙulla wuƙatai,
    ‘Y/Amshi: Sai a amsa mashi ba a ƙara mai,
    : In nuk ƙulla waƙa a ƙara man,
    : Mu haɗu duk azanci gare mu,
    : Shin a a mutum guda za ya radde mu,
    : Shirya kayan faɗa mai gida Tsahe,
    : Ali ɗan Iro bai ɗauki raini ba.
    Jagora: Ga mu hwa! Ga mu hwa!!

    (Ɗan’ƙwairo, Waƙar Musa Ɗanƙwairo ta ‘Yandoton Tsahe Aliyu & Gusau, 2003: sh. ɗi)

    Domin haka, Musa Ɗanƙwairo yana ƙullawa da rera ɗiya na waƙoƙinsa a yayin sadarwa kamar haka:
    +Ƙungiya
    + Jagora (+Ƙulli)
    + ‘Y/Amshi (+Ƙari +ajewa +sauka +saukar sauka +takidi +rakiya +karɓeɓɓeniya +/-Bayayyeniya +ciko ko maimaita ko takidin G/Waƙa)
    + Sanƙira (Mai Kalato Ƙarin Bayanai)
    + Hadiman Waƙa

    Ƙungiyar Makaɗa Musa ƊanƘwairo Maradun ta Kiɗan Kotso ta haɗa da:

    i) Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun = Jagora

    ii) Muhammadu, Daudun Kiɗa na Farko, Ya rasu = Kiɗa da Amshi

    iii) Garba, Zawacin Kiɗa, Marafan Kiɗa,
    Daudun Kiɗa na Biyu (2), Ya rasu = Kiɗa da Amshi

    iv) Audu, Wakilin Kiɗa = Kiɗa da Amshi

    v) Ali, Sabon Kiɗa (ɗan Sa’idu Shayi, Wani Ƙanin Musa Ɗanƙwairo) = Kiɗa da Amshi

    vi) Sani, Zaƙin Murya, Marafan Kiɗa, Ya rasu = Kiɗa da Amshi

    vii) Abubakar (Garba), Ciroman Kiɗa (ɗa), Ya rasu = Kiɗa da Amshi

    viii) Ibrahim Sarkin Fada (Ƙane) = Kiɗa da Amshi

    ix) Muhammadu Jikka (Jikka, Halifa 3) = Kiɗa da Amshi

    x) Sani (Jika) = Kiɗa da Amshi

    xi) Muhammadu Gambo (Bara) = Kiɗa da Amshi

    xii) Malam (Bara) = Sanƙira, Kwandon Ɗanƙwairo

    xiii) Ƙanƙahu (Bara) = Tsaron Kaya

    xiv) Sada (Bara) = Sanƙira

    xv) Rabo (Bara) = Kiɗa da Amshi

    xvi) Nabuba (Bara) = Kiɗa da Amshi

    xvii) Bucaca ‘Yarkohji (Bara) = Kiɗa da Amshi

    xviii) Amadu Bakura (Bara) = Sanƙira

    xix) Sallah Kwana (Bara) = Hadimin Gidan Ɗanƙwairo

    xx) Daudu Ɗangaladima (Bara) = Kula da Doki da Gona

    Domin karanta cikakken bayani akan Tattali da Kulawar Ɗanƙwairo da Majiɓintansa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Dangantakar Harshe da Waƙa danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Yin Waƙar Baka ko Sarrafa Waƙar Baka

    Yin Waƙar Baka ko Sarrafa Waƙar Baka

    A lokacin da makaɗi ya zo yin waƙar baka tun a ƙwaƙwalwarsa da tunaninsa yake fara tsara ta. Wannan tsari shi ne na baɗini, wanda yake a rattaɓe a zuciyarsa kuma a cikin jumlolinsa.

    To, tun daga wannan lokaci ne ya riga ya yi waƙarsa ta baka ta bin waɗannan matakai:

    – Matakin Ƙullawa
    – Matakin Kiɗa
    – Matakin Rauji
    – Matakin Kalmomi
    – Gindin Waƙa
    – Layuka ko Saɗaru a Ɗiya 
    -Nuna Farin Ciki
    – Nuna Baƙin Ciki
    -Faɗakarwa
    -Gargaɗi
    -Ilmantarwa
    -Nasihantarwa
    – Isharantarwa
    -Yabawa
    -Yin Zambo
    -Yin Habaici

    Da Sauransu Kamar Kalmomin Azancin Magana

    Matakin Ƙullawa

    Makaɗan baka sukan ƙulla waƙoƙinsu ta azanci da fasahar da suke da su.
    Ma’anar ƙulli ta ƙamus:

    A ƙamus na Hausa-English (Awde, 1996: 102) ya nuna Ƙulli shi ne (1) to knot (2)to plan (3) to conspire; wato (1)ya ƙulla (2) ya shirya ko ya yi dabara (3) ya haɗa kai. Shi kuma Ƙamusun Hausa (CNHN, 2006: 285) cewa ya yi ƙulla, ita ce ɗaura ko ƙudura.

    Ma’anar Ƙulli ko Ƙulla ko Ƙullawa ta isɗilahi wato ta fannin ilimin waƙar baka. Ita ce:

    Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ya faɗi yadda yake ƙulla waƙarsa a inda yake cewa:

    Jagora: Ga makaɗi ya ƙulla waƙatai,
    ‘Y/Amshi: Sai a amsa mashi ba a ƙara mai,
    Jagora: In naƙ ƙulla waƙa a ƙara man,
    ‘Y/Amshi: Mu haɗu duk azanci gare mu,
    : Shin a a mutum guda za ya radde mu,
    : Shirya kayan faɗa Maigida Tsahe,
    : Ali ɗan Iro bai ɗauki reni ba.

    (Ɗanƙwairo, Waƙar ‘Yandoton Tsahe Alhaji Aliyu II (1960-1991)

    Ƙullawa ta waƙoƙin makaɗan baka tana da matakai biyu. Akwai ƙullawa ta makaɗan ƙungiya, sannan akwai ƙullawa ta makaɗan kaɗaita. Ga su kamar haka:

    i) Ƙullawar Makaɗan Ƙungiya

    Waƙoƙin baka na Hausa waɗanda ake ƙullawa ta ƙungiya, waƙoƙi ne waɗanda ake tunaninsu ta tsakanin Jagora da kuma ‘yan amshinsa. Ita ƙungiya ita ce wadda ta ƙunshi Jagora da kuma yaransa masu yi masa amshi na waƙar baka da kuma yin kiɗa.

    Har wa yau, ƙungiya ta ƙunshi ‘yan ma’abba ko san-ƙirori ko masu kirarin baki. A wannan lokaci, za a haɗa ƙarfi da ƙarfe tsakanin Jagora da ‘yan amshinsa, a dinga tunanin yadda za a shirya waƙa, musamman ta kawo jumloli da yadda za a tsara saɗaru ko layuka, sannan ana yi ana dakatawa ko lumfasawa. Wannan shi ne ƙulla waƙa ta makaɗan ƙungiya.

    Su kuwa makaɗan kaɗaita, su ne waɗanda Jagororinsu kawai za su dinga ƙulla kalmomi da jumloli, amma yaransu, za a sami waɗanda suke yin amshi wato +ciko kawai, sai dai ba su yi musu kowane irin ƙari a waƙa. Akwai wasu jagororin da ba a ce musu ko ƙala, Jagora ne zai ƙulla waƙarsa kuma ya ƙare ta shi kaɗai. Irin wannan ƙulli jagora ne kawai zai yi tunanin waƙa a baɗininta idan ya gama ƙulla ta sai ya zo cikin yaransa ya rera ko ya je wani wuri ya sadar da ita. A irin wannan waƙa, Jagora ne kawai ake jin muryarsa yana rera waƙa, yana sadar da ita ga jama’a.

    A bisa waɗannan matakai ne ake bi, ake ƙuƙƙulla, waƙoƙi na gargajiya ko waƙoƙi na zamani na baka da Hausawa suke yin tunaninsu a baɗini, daga baya su rera su a yayin da suke sadar da su.

    Matakin Kiɗa

    A Ƙamusun Hausa an nuna kiɗa yana nufin bugun ganga ko kalangu ko abun bugawa ko bugun ƙwarya ko goge ko garaya ko taushi ko kotso da hannu ko da makaɗi ko da wani abu (CNHN, 2006: 243).

    A ilimin fannin waƙar baka, kiɗa yana nuni ne da wani amo ko sauti da ake samarwa ta gwama ko haɗa abubuwa biyu kamar dutsi + dutsi ko tafi + tafi ko baki + ƙahon dabbobi ko ganga + gula (makaɗi) ko wani abu + wani abu ko sauransu. Kiɗa kuma yakan zama wani amo ne wanda yakan shiga jikin mai sauraro, ya sa masa karsashi har ya dinga rausayawa, yana tattakawa ko jujjuyawa.

    Gusau (2008: 54) yana ganin kiɗa shi ne wanzar da amo mai shiga jiki wanda kuma ake aiwatarwa ta haɗa abubuwa biyu ta matakin busawa ko tafawa ko bugawa ko kaɗawa ko gogawa ko girgizawa ko kuma wasun waɗannan.

    Akwai kayayyakin kiɗa da dama. Wasu na gargajiyar Hausawa ne, wasu kuma na baƙin wasu al’ummu ne waɗanda Hausawan suka aro, suna amfani da su. A wajen Hausawa akwai kiɗa zallarsa kawai, ba tare da haɗawa da waƙa ba, ko kirari ko kaɗa take. Akwai kuma kiɗa ta amfani da kayan kiɗa wanda ake haɗawa da waƙa, wanda kuma ake yi wa waƙoƙin da makaɗan baka suke yi.

    Kiɗa a wajen Hausawa ya rarrabu zuwa: Kiɗa

    -waƙa +take -take +waƙa
    -Waƙoƙin Gaɗa
    -Waƙoƙin Samartaka
    -Waƙoƙin Manyan Mata
    -Waƙoƙin Manyan Maza
    -Waƙoƙin Makaɗa

    A wajen aiwatarwa ta waƙar baka akan gwama ta da amon kiɗa wanda za su dinga tafiya a tare tsakanin muryar makaɗi da sautin gangar da makaɗin yake amfani da ita. Bisa mahangar makaɗa, akwai wasu hanyoyi da ake ɗora kiɗa na waƙoƙinsu na baka domin su yi daidai da yadda ake sadar da su. Waɗannan hanyoyi sun haɗa da:

    – sadar da kiɗa daidai da nauyi na muryar makaɗi da kuma raujin da aka zaɓa wa matanin waƙa;
    – Dacewar amon kiɗa da gaɓoɓin murya bisa gurabunta na hawa da sauka da kuma faɗuwa;
    – Ƙarfafa madirar gaɓoɓi;
    – Wani bi a kaurara amon kiɗa;
    – Wani bi a sassauta amon kiɗa;
    – Wani bi a ja amon kiɗa;
    – Wani bi a matse ko a tauye amon kiɗa;
    – Wani bi a qwairanta amon kiɗa;

    Sannan kuma yanayin kiɗan yana iya zama:

     Mai diri
     Mai ƙarfi
     Mai kauri
     Mai zaƙi
     Mai kumbura
     Mai kaurara
     da sauransu

    Matakin Rauji

    Ƙamus na Hausa a ɓangaren Hausa-English (Awde, 1996: 131) ya bayyana kalmar rauji da clapping wato yin tafi ko ban tafi (Awde, 1996, 131 & 210). A kuma littafin Ƙamus na Keɓaɓɓun kalmomi wato Hausa Metalanguage ya fassara Rauji da Ingilishi da Rhythems wato Kari ko karin murya (Awde, 1996:361).

    A fannin ilimin waƙar baka kuwa, rauji wani sauti ko amo ne wanda yake tashi a sama ko ya sauka ko ya faɗi. Rauji yana iya zama murya ta wata halitta mai rai ko sautin wani abu maras rai kamar ƙara ko doka ƙafafu a bisa ƙasa ko wani tsando ko sauti daga kukan tsuntsaye. Har wa yau kuma akwai rauji mai ɗaɗi, mai zaƙi da kuma rauji maras daɗi, mai-ta-da-hankali, kamar kukan kanari (rauji mai zaƙi) da kuma kukan jaki (rauji maras zaƙi, mai ɗaukar hankali).

    Wata ma’anar isɗilahi kuma, rauji na iya zama masaukar murya a gaba.

    A yayin da aka gwama rauji a waƙar baka ta Hausa ana ɗora shi bisa muryoyi na gaɓoɓi na kalmomi ne waɗanda akan sarƙa su a tayar da saɗara a ɗa na waƙa. Rauji wanda aka zaɓa, aka ɗora wa saɗara ko layi a ɗa na farkon waƙa, shi ne zai dinga daidaita rauji a dukkan layuka da ake ƙullawa a ɗiya na waƙar.

    Nauyin rauji a waƙar baka ta Hausa gajere ne, shi ya sa yake tafiya bisa gaɓoɓi na kalma gwargwadon hawansu da saukarsu da faɗuwansu. Matakai waɗanda ake bi a wajen samar da rauji a waƙar baka ta Hausa sun haɗa da:

    – Rauji mai dogon zango
    – Rauji mai gajeren zango
    – Rauji mai matsakaicin zango

    Sannan gaɓa ta rauji za ta iya zama mai nauyi wadda za ta ƙunshi [bww] ko [bwb], ko kuma ta zama mai sauƙi wadda za ta iya zama gaɓa mai [bw] kawai.

    A wajen furta rauji na waƙar baka ana yi masa waɗannan abubuwa kamar haka:

    – Kaurara gaɓa mai nauyi;
    – Jan gaɓa mai nauyi ko mai sauƙi;
    – Daidaita amsa-amon kari (hawa ko sauka ko faɗuwa) a ƙarshen kowace saɗara ko layi.

    Haka kuma ana yin rauji ne na waƙar baka daga karin murya (na hawa da sauka da faɗuwa) da kuma amon kiɗa tun daga tunanin makaɗi a zuciyarsa. Domin haka, ana samar wa waƙoƙin baka rauji ne ta waɗannan hanyoyi:

     Karin murya daga makaɗin waƙar;
     Amon kiɗa daga kayan kiɗan da makaɗi yake amfani da su, ta la’akari da madiransu na hawa da saukar amo ko kuma faɗuwarsa.
     Daga nan sai a fitar mata da raujinta;
     Rauji zai samar wa waƙar baka wani amo wanda zai fitar da ita kaɗai daga sauran waƙoƙin baka na makaɗin.

    Matakin Kalmomi

    Kamar yadda aka nuna a baya, idan makaɗin baka ya tashi aiwatar da wata waƙa ta baka, yakan fara aiwatar da waƙar ne a cikin zuciyarsa da kuma ƙwaƙwalwarsa tun kafin ya furta waƙar a waje. Haka kuma tunanin makaɗi na kalmomi da yadda zai sarrafa su cikin azanci da hikima shi ne wani abu da zai biyo biyo baya a aiwatar da waƙar baka.

    Sannan kuma dukkan makaɗi na ƙungiya da kuma makaɗi na ƙire duk suna yin aiwatarwa a wajen daidaita waƙoƙinsu da tsawaita su. Matakin kalmomi yakan bambanta dangane da kalmomi da makaɗi ya yi tunaninsu ko kuma ya zaɓo su wajen tsawaita waƙar da zai yi. Wasu daga cikin kalmomi da ake zaɓa a shirya waƙar baka sun haɗa da:

    Kalmomin Shirya Gindin Waƙa

    Gindin waƙa furuci ne na wasu kalmomi masu ma’ana masu nauyin saƙo, masu hikima da balaga da azanci waɗanda ake shiryawa don a gabatar da waƙar baka. Ta gindin waƙa ne ake rarrabe ɗa da ɗa a waƙar baka. Waƙoƙin baka sun kasu kashi biyu. Akwai waɗanda ake yi wa Gindin Waƙa kamar waƙoƙin Alhaji Abdu Karen Gusau. Sannan kuma akwai waƙoƙin da ba a yi wa Gindin Waƙa kamar waƙoƙin Alhaji Babangida Kakadawa.

    Ga Misali na Gindin Waƙa:

    G/Waƙa: A lula ɗan haya,
    : Mai gyaran kekuna.
    (Abdu Karen Gusau; Waƙar Alhaji Alula Ɗanhayar Kekuna, Fagge, Kano)
    Har wa yau kuma, Gindin waƙa yakan bayyana abin da waƙa take nufi tun kafin a shiga cikinta. Gindin waƙa wani ginshiƙi ne ko babban matangali na ginin waƙar baka. Wani kuma harsashe ne ko majingini na farko a waƙar baka, inda duk bai zauna ba, waƙa ba za ta ba da sha’awa ba, balantana har ta yi wani armashi.

    Idan makaɗi ya sami zaunuwar Gindin waƙa, to, zai sami haske ya buɗu a gare shi, ya sami walwala ta zaɓo kalmomi waɗanda suka dace ya saka a waƙa waɗanda za su ba shi damar samun sauran ɗiyan waƙar. Makaɗin baka yakan yi tunani a zuciyarsa idan kuma wanda suke a ƙungiya ne sukan haɗa ƙarfi da azama su samo kalmomi zaunannu kuma mafi girkuwa a waƙar da suke shiryawa ta baka su samar da Gindinta.

    A wajen shirya Gindin waƙa makaɗa sukan yi amfani da waɗannan matakai:

    Yawanci Gindin waƙa bai shige layuka biyu (2) zuwa huɗu (4) ba;
    – Yakan ƙunshi kalmomi masu nauyi da ake sarrafa su cikin azanci da hikima;
    – Gindin waƙa yakan ƙunshi sunan mai waƙa ko laƙabinsa ko alkunyarsa ko wata ƙarina da ke nuna Mai waƙa;
    – Sannan ana wakiltar Gindin waƙa da harafin [X] na ABCD;
    – Ana kuma wakiltar adadin saɗaru ko layuka a Gindin waƙa da alkalumma na [1,2,3,4] kamar haka: [X1] ko [X2] ko [X3] ko [X4] da sauransu;

    – Ga misalai:

    i) Gindin Waƙa; (mai layuka huɗu (4)
    X1: Ka bawai maza,
    X2: Na Magajin Gari Bubakar,
    X3: Kai ad da yanzu,
    X4: Allah ya ba ka Sarkin Kabi.
    (Mamman Inyaga Argungu; Wakar S/Kabi Muhammadu Mera. Wato kalmomin nuna farin ciki).

    ii) Gindin Waƙa; (mai layuka biyu (2)
    X1: Tankwafau namijin zaki,
    X2: Sa’idu bai taɓa tsoro ba.
    (Idi Ɗangiwa Zuru: Waƙar Sarkin Sudan Sa’idu, Kwantagora. Wato kalmomin nuna farin ciki)
    – Yawancin kalmomi masu nauyin ma’ana da hikimar zance da makaɗa suke tsarawa a Gindin waƙa sun ƙunshi na nuna farin ciki ko na nuna baƙin ciki. Misalin Gindin waƙa na kalmomin nuna baƙin ciki:
    G/Waƙa: X1: Gagarabadon namiji tsayayyen ɗan kasuwa
    (Shata: waƙar ‘Gagarabadau, Mp3)

    – Kuma wani Gindin waƙar yakan ƙunshi kalmomin yabawa ko na zambo ko na habaici da na zugugutawa da makamantansu. Misali:

    G/Waƙa: X1: Ya ci maza ya kwan yana shirye,
    X2: Gamda’aren Sarki Tudu Alu.
    (Narambaɗa, Waƙar Tudu Alu; Kalmomin zuga da kururantawa da yabawa).
    Akwai kuma a wani G/Waƙa:
    X1: Madogara na Malam,
    X2: Iro Uban Bawa,
    X3: Maigida Shinkahi.
    (Narambaɗa, Waƙar Magajin Garin Shinkahi, Ibrahim; Kalmomin zuga da yabawa).

    – Haka kuma wani Gindin waƙar yakan ɗauki kalmomin faɗakarwa ko gargaɗi ko ilimtarwa ko isharantarwa ko nasihantarwa da sauransu. Misali:
    G/Waƙa: X1 “Yan Nijeriya sai Hausa
    (Abdu Karen Gusau; waƙar Harshen Hausa-kalmomin kishin Hausa da na gargaɗi da na ilimantarwa. Gusau, 2015: 64-75).

    G/Waƙa: X1 Mu kama sana’a ‘yan Nigeriya,
    X2 Zaman banza ba namu ne ba.
    (Abdu Karen Gusau, Waƙar Gargaɗi kan riƙo da sana’a – kalmomin gargaɗi da na faɗakarwa da na isharantarwa, Gusau, 2015: 75-78).
    G/Waƙa: X1 Shegiyar ƙafa ke kika saba da gulando,
    X2 Ki tallafe ni, ɗaukar ni ƙafa kar ki gaza ni.
    (Abdu Karan Gusau, Waƙar Shegiyar ƙafa – Kalmomin faɗakarwa da na gargaɗi da na isharantyarwa. Gusau, 2015: 96-97).

    Layuka ko Saɗaru a Ɗiya

    Layuka jam’i ne na layi (tilo). A Ƙamusun Hausa (CNHN, 2016 206-304) an faɗi ma’anarsa kamar haka: (i) Miƙaƙƙen zane (ii) miƙaƙƙiyar hanya ta cikin gari, ko jerin rumfunan kasuwa ko wani abu (iii)majalisar alƙalai ko kotu ko ɗakin shari’a. Amma kuma a ƙamus (Hausa-English) na Awde (1996:106) ya bayyana Layi (p/layuka) da harshen Inglishi da Line. A kuma ɓangaren ƙamus ɗin na English-Hausa, Awde

    (1996: 295) ya fassara line da noun=n=: (1) layi (2) Baiti (3) Telephone line wato waya. Ta Fuskar Saxaru (Jam’i); saɗara (tilo) kuwa – Ƙamusun Hausa (CNHN, 2006: 381) ya fassara ta da layi cikakke na rubutu.

    A cikin layuka ne ko saɗaru waƙar baka take shirya saƙonni tun a ƙwaƙwalwa, sannan ta rera su, ta sadar da su ga al’umma; ta amfani da mataki na kalmomi waɗanda suka haɗa da nau’o’i daban-daban.

    Kuma har gami da kalmomi na maganganun habaici da isharantarwa da gargaɗi da ilimantarwa da tunasarwa da faɗakarwa da makamantansu da yawa.

    A waƙoƙin baka na Hausa akan shirya layuka ko saɗaru masu sauƙi a ƙagi ɗa na waƙar baka wanda zai ƙunshi saƙo ɗaya kawai. Akwai kuma layuka ko saɗaru da ake shiryawa masu tsauri, waɗanda za su haɗu su tayar da ɗa ɗaya na waƙar baka. Shi ɗa ɗaya mai tsauri yakan ƙunshi saƙonni da yawan gaske kamar guɗa huɗu (4) ko ma fiye da haka waɗanda ake wakiltarsu kamar haka:

    Ɗa ɗaya mai tsauri:
    A1:
    A2:
    B1:
    B2:
    B3:
    C1:
    C2:
    C3:
    C4:

    Da sauransu. Za a ba da misali na ɗan waƙa mai sauƙi (Mai saƙo guda ɗaya kawai) kamar haka:
    A1: Ni kam lafiya nit taho salla,
    A2: Lafiya ni ishe Sarki,
    X1: Amadun Bubakar gwarzon Yari,
    X2: Dodo na Alƙali.
    (Narambaɗa, waƙar Sarkin Gobir Ahmadu Bawa (1935-1975).

    Shi kuma ɗan waƙa ɗaya mai tsauri (mai Saƙonni da yawa fiye da ɗaya), ga wani misali kamar haka:

    A1 Na Magaji mai Martaba ɗan Mu’azu,
    A2 Irin assabad Bubakar baba yay yo,
    A1.1 Na Magaji mai Martaba ɗan Mu’azu,
    A2 Irin assabad Bubakar baba yay yo,
    B1 Tsarin gaskiya Bello kai Shehu yac ce,
    B2 Bari masu son duk su maishe ka yaro,
    B 1.1 Tsarin gaskiya Bello kai Shehu yac ce,
    B2 Bari masu son duk su maishe ka yaro,
    B3 Da kyauta da ilimi da neman dalili,
    B4 Da gode ma Allah da istingfari,
    B5 Da su Bello ɗan Shehu yat tsarmo kowa,
    B6 Ka kai kamar Bello ka gadi Moyi,
    B7 Saura ka kai inda mai Hausa yak kai,
    B6.1 Ka kai ka mar Bello ka gadi Moyi,
    B7 Saura ka kai inda mai Hausa ya kai,
    X1: Bajinin gidan Bello Mamman na Yari,
    X2: Sarki Kudu Macciɗo ci maraya.

    (Sa’idu Faru, waƙar Muhammadu Macciɗo lokacin yana a matsayin Sarkin Kudun Sakkwato, ya rasu a 1995 yana Sarkin Musulmi).

    A layi na ɗan waƙa ana wakiltar sa da alƙalumma na [1-0], da haruffa na ABCD ban da [X] kamar yadda aka gani a misalan da suka gabata. Har wa yau kuma ana iya wakiltar ɗan waƙa ta jan layuka kawai. Misali:

    Ɗanwaƙa mai layuka biyu ko uku
    Xa: 1 ____________________
    2 _______________________
    3 _______________________
    X1 ______________________
    X2 ______________________

    Ko ɗa mai layuka biyu
    Xa: 1 ____________________
    2 _______________________
    X1 ______________________
    X2 ______________________

    Saƙonni a ɗa na waƙa, bisa yawanci ba su shige layuka guda biyar (5). Misali: A1, B1, C1, D1, E1, wato saɗo na ɗaya (1) zuwa na biyar (5).

    A layuka ne kuma ko saɗaru ake tunani a zuciya a gina saƙo na farin ciki ko na baƙin ciki ko na faɗakarwa ko na tunasarwa ko na gargaɗi ko na ilimantarwa ko na isharantarwa ko na yabawa ko na zambo ko na habaici ko na wani saƙo da makaɗi yake son ya gaya wa al’ummarsa a harshen waƙar baka.

    Alalmisali:

    Jarora: Yara farau-farau farar tabarma,
    : Farin cikin mai baƙunta,
    Y/Amshi: Gagarabadon namiji tsayayyen ɗan kasuwa.
    (Shata, Gagarabadau; Gusau, 2018:20)
    Akwai kuma
    Jarora: Ga wani ya yi ilimi babu hankali,
    : Ga dai ilimi babu nutsuwa,
    : An kira shi Dabtan ya amsa,
    : Da ganin ƙurji sai ya yaɓa wuƙa,
    Y/Amshi: Na gode wa Amadun Gaya.

    (Shata, Waƙar Amadun gaya; Gusau, 2018: 23)

    A lokacin da makaɗa suke yin tunanin baɗini na wata waƙa da za su shirya sukan bambarta a wajen yin wannan tunani da kuma samo kalmomi na waƙa.

    i) Wasu makaɗan sukan zauna a ƙarƙashin wata inuwa kamar ta wata bishiya, su kwanta su lulluɓe kansu, suna tunanin wata waƙa. Alalmisali, Alhaji Ibrahim Narambaɗa, idan yana tunanin waƙa har zana tunanin nasa yake yi a ƙasa, ya dinga shata wani zani ko zane-zane kamar zai zana wani hoto na musamman. Zai dinga zanawa a ƙasa a cikin layuka, ya dinga yin zane-zane, yana tsara saɗaru na waƙa.

    ii) Wasu kuma makaɗan sukan dinga jefo wasu kalmomin suna sarƙawa suna kuma zubar da wasu, suna warwarewa, har su haɗa kalmomin da suke buƙata na waƙar. Wasu makaɗan, kamar Salihu Jankiɗi, har tattaka ‘yan amshinsa yake yi, suna zazzaune, idan sun jefo wasu kalmomi da ba su dace ba.

    Ta haka dole ɗan amshi ya yi taka-tsantsan da abubuwan da yake ba da tasa gudummawa.

    iii) Wasu makaɗan, musamman makaɗan ƙire (kaɗaita) sukan sami saulin yin tunani ne a yayin da ‘yan amshinsa suke maimaita kiɗa, su kuma makaɗan sukan yi shuru, suna numfasawa. A lokacin da kuma sanƙirorinsu suke ba da tasu gudunmawa, su kuwa makaɗan (Jagororin) suna yin shuru, suna saurarensu. Da sauran halayen makaɗan kaɗaita. A duk lokacin da makaɗan suka yi shuru suna tunani ne a kan abubuwan da za su ƙara ƙulla waƙoƙinsu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Sadarwa a Waƙar Baka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Aiwatarwa Da Sadarwa A Waƙƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita, RMK

  • Waƙar Ban Mutu Ba (Fati Nijar)

    Waƙar Ban Mutu Ba (Fati Nijar)

     Mawaƙiya : Fati Nijar 

    G/Waƙa: Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

     Ba ta mutu ba. 

    Jagora : Ya jama’a ga ni da rai, 

    Fati Nijar ban mutu ba, X2 

    ‘Y/Amshi: Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

     Ba ta mutu ba. X2 

    Jagora : Nai sallama gare ku dukkan al’umma,  

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba

    Jagora: Waƙa nake sai ku saurara kuma, 

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba, 

    Jagora: Na sanar da ku kan ƙorafin, 

    : Da ake ta yi na yi gaba, 

    ‘Y/Amshi: Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

    : Ba ta mutu ba. 

    Jagora : Rannan da safe na ji ana tai min waya,                                 

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba, 

    Jagora: Wajen sau biyar duk jama’a na tambaya, 

     ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba, 

    Jagora: Wai gaske ne Fati Nijar, 

    : Ta mutu ko ba ta mutu ba, 

    ‘Y/Amshi: Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

    : Ba ta mutu ba. 

    Jagora: Sai na ce musu Fati ne ke maggana,

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba, 

    Jagora: Ban san irin wannan kalamai ƙanƙana, 

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba, 

    Jagora: Kui haƙƙuri Allahu in dai yai niyya, 

    : Ba zai bar ni ba, 

    ‘Y/Amshi: Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

    : Ba ta mutu ba. 

    Jagora: Masu faɗin haka, 

    : Wai shin me ta tsare muku? 

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba. 

    Jagora: Ku faɗa mana ko kuma laifi tai muku, 

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba. 

    Jagora: Kui wa Allah zancenku ya zama alheri, : Ba sharri ba, 

    ‘Y/Amshi: Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

    : Ba ta mutu ba. 

    Jagora: Ya jama’a ga ni da rai, 

    : Fati Nijar ban mutu ba, 

    ‘Y/Amshi: Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

    : Ba ta mutu ba.

    Jagora : Wani maƙaryacin gari, 

    : Ya je yana ta faɗin haka, 

    ‘Y/Amshi : Ba ta mutu ba, 

    Jagora : Wai yana faɗin kabarina shi ma yai haƙa, 

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba, 

    Jagora: Ƙarya kake ga ni da rai, 

    : Fati Nijar ban mutu ba, 

    ‘Y/Amshi: Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

    : Ba ta mutu ba. 

    Jagora : Ya jama’a ku dinga zancen alheri, 

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba, 

    Jagora: Ko kui shiru, 

    : Don kar ma kui sharri, 

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba, 

    Jagora: Wannan magana Annabi ne ya faɗa, 

    : Jama’a ba Binta ba, 

    ‘Y/Amshi: Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

    : Ba ta mutu ba. 

    Jagora : Roƙo nake Allah don Almusɗafa, 

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba, 

    Jagora: Dukkan sharri, 

    : Kadda ka bar shi ya ƙarfafa, 

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba, 

    Jagora: Ka ije mini kai min abin da mutum, 

    : Ba zai cuce ni ba, 

    ‘Y/Amshi: Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

    : Ba ta mutu ba. 

    Jagora: Nai gaisuwa dukkan masoya bai ɗaya,

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba, 

    Jagora: An mun sharri har ƙasarmu gaba ɗaya, 

    ‘Y/Amshi: Ba ta mutu ba, 

    Jagora: Ku yi haƙuri ga ni da rai, 

    : Fati Nijar ban mutu ba, 

    ‘Y/Amshi: Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

    : Ba ta mutu ba. 

    Jagora: Ya jama’a ga ni da rai, 

    : Fati Nijar ban mutu ba, 

    ‘Y/Amshi: Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

    : Ba ta mutu ba, 

    : Ayyaraye ga ta da rai Fati Nijar, 

    : Ba ta mutu ba.

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Taƙaitaccen Tarihin Hajiya Fati Nijar 

    Taƙaitaccen Tarihin Hajiya Fati Nijar 

    Sunan Fati Nijar na yanka shi ne Fatima, Mahaifinta kuma Abdurrahman wanda ake yi wa sunan rana Labaran, mahaifiyarta kuma A’ishatu ‘yar Hassan Ɗan Tanko. 

    Fatima (Binta) ta sami sunan fati Nijar daga Sadi Sidi Sharifai a lokacin da take yi masa amshi na waƙoƙin finafinai. 

    Labaran bisa asali mutumin Madawa ne cikin Jihar Tawa, kuma ɗan kasuwa ne mai zagayen garuruwa da ƙauyuka a ranakun cin kasuwanni a Jamhuriyyar Nijar. 

     Haihuwar Fati Nijar 

    Haihuwar Fatima (Binta) ta auku ne a ranar Alhamis 26/10/1984 a birnin Maraɗi, Jamhuriyar Nijar. 

    Bishiyar Nasabar Binta Labaran (Fati Nijar): 

    Ibrahim Tanko 

    Hassan 

    Abdurrahman ==== A’ishatu

    Saudatu Usman Fatima Ibrahim Isa Musa (Fati NIjar) (Binta) 

     Yanayin Karatun Fati Nijar 

    Fatima (Binta) ta yi karatun Alqur’ani, mai tsarki. Haka kuma Fatima ta kori jahilci ta fuskar ilimin boko. 

    Fara Waƙar Fati Nijar 

     Binta Labaran mutum ce mai sha’awar waƙoƙin gaɗa na ‘yan mata, musamman waƙoƙin dandali masu tafiya da wasannin al’ada. Fati (Binta) ta zama zabiya, mai zaƙin murya, wadda ake son a ji amon muryarta a tsakanin ƙawayenta. 

    A wata ziyara da Binta ta kawo wa ‘yar’uwarta wadda take aure a Nijeriya cikin 2003, ta sami damar haɗuwa da wasu daga cikin makaɗa da mawaƙan sitidiyo, tun ma ba Ali Baba Yakasai da Sadi Sidi Sharifai ba. 

    Daga nan ne ta shiga hidima ta yin waƙoƙin fina-finai har ta kai lokacin da take shirya waƙoƙi nata na kanta daga 2006, kuma tana yaɗa su ta albam -albam. Fati Nijar tana da kyakkyawar dangantaka da makaɗan sitidiyo na lokacinta a Nijeriya da Jamhuriyyar Nijar. 

    Fati Nijar tana yin waƙoƙi na sitidiyo a ƙungiya da kuma a kaɗaita. vii) Wasu waƙoƙin Fati Nijar sun haɗa da: 

    – Waƙar ‘Ɗan Amina’ 

    – Waƙar ‘Girma-Girma’ 

    – Waƙar ‘Nijar-Nijeriya’ 

    – Waƙar ‘Ala Gidigo’ 

    – Wakar ‘Na yi Ritayar So’ 

    – Waƙar ‘Duniya’ 

    – Waƙar ‘Uwa mai Gyara ɗanta’ 

    – Waƙar ‘Dawo Aliyu Dawo’ 

    – Waƙar ‘Gamji Jijjige’ 

    – Waƙar ‘Manguno’ 

    – Waƙar ‘Gidan Sauro’ 

    – Waƙar ‘Musa Ango’ 

    – Waƙar ‘Al’amarin Hassan yana ban Mamaki’1 

    – Waƙar ‘G Cell’ 

    – Waƙar ‘Fati Nijar ba ta Mutu ba’ 

    – da sauransu 

    Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau 

    Alhamis 26/4/2018 

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Lokaci Da Yanayin Sadarwa A Waƙar Baka

    Lokaci Da Yanayin Sadarwa A Waƙar Baka

    Bisa yawancin lokuta na sadar da waƙoƙin baka na Hausa, kamar yadda aka yi bayani a baya; akan sadar da waƙar baka ne a lokaci na safiya ko na hantsi ko na rana ko na yammaci ko na daddare da dai sauran lokuta.

    Haka kuma Hausawa sukan sadar da waƙoƙin baka a kowane yanayi na damina ko na kaka; ko na rani ko na bazara ko na hunturu ko na ɗari. Alal misali waƙoƙin noma an fi yin su a yanayi na damina, wato lokacin da ruwan sama yake sauka.

    Haka kuma waƙoƙin ɓullowar kaka akan yi su ne da zarar damina ta shige ko tana gab da wucewa; wato an cimma amfanin gona ka’in da na’in, da dai sauransu.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wuraren Sadawar Waƙar Baka danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yabon Gusau A Waƙoƙin Baka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Aiwatarwa Da Sadarwa A Waƙoƙin Baka Na Hausa. wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Sadarwa A Waƙar Baka

    Sadarwa A Waƙar Baka

    Bayan makaɗan baka sun gama tunanin waƙar da za su yi; sai kuma su zo, su sadar da ita ga al’umma.

    Ana sadar da waƙar baka ga Hausawa a ɗaiɗaikun gidajensu da wani wuri da suka shirya wanda ake kira dandali; wato wurin yin wasannin jama’a da a yayin farauta ko noma, musamman a lokacin gayyar noma a fadojin sarakuna, da lokacin bukukuwan al’umma da kuma taruka na makarantu da sauransu.

    A ma’ana ta lugga ko ta ƙamus, Ƙamusun Hausa (2006:380) ya bayyana kalmar sada tana nufin (i)gama (ii) isar da (iii)sulhunta. Shi kuma littafin Ƙamus na Keɓaɓɓun Kalmomi wato Hausa Metalanguage (Muhammad, 1990 UPL Ibadan:104) cewa ya yi, kalmar Sadarwa da Ingilishi tana nufin Communication.

    Shi ma Awde (1996:135) yana ganin kalmar Sadarwa tana nuni ne Communications da Ingilishi.

    Sadarwa a ilmin waƙar baka tana yin nuni ne game da wasu dabaru; waɗanda ake amfani da su wajen isar da waƙoƙin baka ga waɗanda ake yiwa su. Ana isar da waƙoƙin baka ta hanyar rera wa mutane a wasu wurare da lokuta da yanayi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Lokaci da Yanayin Sadarwa a Waƙar Baka danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yabo A Waƙoƙin Baka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Aiwatarwa Da Sadarwa A Waƙoƙin Baka Na Hausa wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Magabata da Haihuwar Ɗanƙwairo

    Tarihin Magabata da Haihuwar Ɗanƙwairo

    Magabatan Musa Ɗanwaƙiro Maradun su ne; kakanninsa da mahaifinsa da mahaifiyarsa da yayansa da ‘ya’yansa da kuma sauran ‘yan’uwa na jininsa.

    Musa Ɗanƙwairo da magabatansa sun fito ne daga garin Ɗankadu ta cikin Gundumar Bakura ta jihar Zamfara ta yanzu.

    2.1 Usman Ɗankwanagga: Mahaifin Ɗanƙwairo

    Usman Ɗankwanagga shi ne ɗan Kaka Maiganga, kuma shi ne ya haifi Musa Ɗanƙwairo. Usman Ɗankwanagga da zuriyyarsa mutanen Ɗankadu ne da ke cikin Gundumar Bakura, kamar yadda bayanai suka gabata.

    Usmaan Ɗankwanagga manoni ne, mai jajircewa a ayyukan gona. Haka kuma makaɗi na noma ne wanda ya shahara sosai. Sannan ya gaji kiɗan noma daga mahaifinsa, Makaɗa Kaka Maiganga. Har wa yau kuma Usman Ɗankwanagga ya gwama kiɗan fada da kiɗan noma. A kiɗan fada ya kaɗa abin kiɗa na kotso ne.

    A wani ƙauli an nun a wajejen 1914 Usman Ɗankwanagga ya bar garinsa na asali; ya fita neman wani wuri da zai yi noma shi da iyalinsa. A wannan tafiya ce ya haɗu da Sarkin Maradun, Alhaji Ibrahim I (1903-1923) a wata gonarsa ta Bazamawa. A wannan haɗuwa ce Sarkin Maradun ya amince ya ɗauki nauyin Usman Ɗankwanagga da dukkan jama’arsa; shi kuma ya zama makaɗinsa. Daga nan ne Usman Ɗankwanagga ya zaɓi ya zauna Birnin Ƙaya gari mai dausayi da ƙasar noma mai albarka. Iyalin Usman Ɗankwanagga sun zauna a ƙasar Ƙaya a wani wuri da ake kira Tunga, mai yalwar ƙasar noma7.

    Bayan da Usman Ɗankwanagga ya tsufa, sai ya yi murabus; aka naɗa babban ɗansa Abdu Kurna Sarkin Kiɗan Sarkin Maradun, mai amfani da kotso.

    2.2 ‘Yarnunu: Mahaifiyar Ɗanƙwairo

    ‘Yarnunu ita ce mahaifiyar Alhaji Musa Ɗanƙwairo. Ita kuma ‘yar asalin Goran Namaye ce, Bazamfariya ce gaba da baya.

    2.3 Makaɗa Abdu kurna

    Shi makaɗa Abdu Kurna an haife shi ne a garin Ɗankadu, a cikin Gundumar Bakura; Ƙaramar Hukumar Bakura, Jihar Zamfara a yau a daidai shekara ta 1899 bisa ƙiyasi. Tare da Abdu Kurna ne Usman Ɗankwanagga ya baro Ɗankadu zuwa Tunga ta Birnin Ƙaya, Maradun. Makaɗa Abdu Kurna ya yi kiɗan noma da na masu Sarauta . Makaɗa Abdu Kurna ne ya gaji Halifar Mahaifinsa Usman Ɗankwanagga ta Sarkin Kiɗan Sarkin Muradun. An naɗa Abdu Kurna a matsayin makaɗa na Sarkin Maradun a yayin da mahaifin nasu Usman Ɗankwanagga ya tsufa; kuma ya roƙi a maye gurbinsa na sarautar kiɗa da babban ɗansa Abdu Kurna.

    2.4 Yanayin Haihuwar Musa Ɗanƙwairo (1909)

    Yanayin haihuwar Musa Ɗanƙwairo ya riski wani hali na ɓurɓushin tasirin da zai zo wa Hausawa da al’ummar Arewa na shigowar Turawan Mulkin Mallaka a ƙarƙashin jagorancin Sarauniyar Ingila. Duk da saɓanin tarihin haihuwa; an ɗauka an haifi Musa Ɗanƙwairo a 1909, jim kaɗan da tsayar da mulkin mallaka na Turawa a 1902.

    Haihuwar Musa Ɗanƙwairo ta wakana a garin Ɗankadu na gundumar Bakura a yau ta Jihar Zamfara; kafin iyayensa su koma Tunga, Birnin Ƙaya ta gundumar Maradun. An raɗa wa Ɗanƙwairo sunan yanka na Musa.

    Shi kuwa Ɗanƙwairo wata alkunya ce ake gaya wa Musa bayan da ya kai shekaru bakwai da haihuwa; kuma ya fara sa hannu a harka ta kiɗa da waƙa a ƙarƙashin mahaifinsa Makaɗa Usman Ɗankwanagga. A cikin mataimakan kiɗa na Usman Ɗankwanagga akwai wani baransa, wani mutum mai murya wasai; mai zaƙi da shiga jiki wanda ake yi wa laƙabi da Ƙwairo. To sai Musa ya gaji irin wannan murya, shi ne mahaifinsa Usman Ɗankwanagga yake faɗin; ‘Ga Ɗanƙwairo an mayas (Gusau, 1996: sh. 104). Bishiyar Nasabar Kaka da Iyayen Musa Ɗankwairo.

    Makaɗa Kaka Maiganga

    Binta Amina Usman na Ɗankwanagga
    Sa’idu Shayi
    Mairana Naruwa Ɗantomi16
    Ali Sabon Kiɗi
    Abubakar Muh Maigayya Amadu Zuwaira Lawali Umaru17
    Lawali Shamsiyya Aliyu Musa Ibrahim Nasfatu
    (a) (b) (c)

    = Karima = Yarnunu = Ba’u (Mora)
    Abdullahi
    (Yawale) Ya Rasu a Ilorin
    Abdu Kurna Hauwa Musa Ɗanƙwairo Binta (Maryam)
    Galadima Maituwo Amina “Yardaudu Ƙauna
    (Indo A’isha)
    Ambaye Amina ‘Yaddaudu (Dosara)
    Garba Sambo Mani Ige Ibrahim
    (Ɗandarali) (Zuma) Usman (Kahiyo)
    Tamaidaji20 Umaru Karɓa Iro Abdu
    (Tsahara) ɗankutuɓe Maikano
    Tashayi (Inno) Safiya (‘Yarkwando)

    15 Makaɗa Usman Ɗankwanagga ya koma sabon mazauninsa na Tunga, Birnin Ƙaya; a Gundumar Maradun tare da dukkan wannan zuriyya ta mahaifinsa Makaɗa Kaka Maiganga.

    16 Sauran ‘ya’yan Amina su ne: Mustafa da Ibrahim da Mukhtari da Talatu da Rabi da kuma Saratu.

    17 Saruan ‘ya’yan Ali Sabon Kiɗi su ne: Abubakar da Zuwaira da Rumasa’u da Lawali.

    18 Sauran ‘ya’yan Muhammadu Maigayya su ne: Amadu da Ladidi da Hamida da Nomau Libiris (Namagarya).

    19 A dubi ‘ya’yan Musa Ɗanƙwairo a 3.3.2.

    20 ‘Ya’yan Tamaidaji (Tsahara) su ne: Ta’inna (A’isha) da Muhammadu Magaji (Sarkin Gida) da Sale da Hassi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Iyalin Musa Ɗanƙwairo danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Yanayin Harshen Waƙar Baka

    Yanayin Harshen Waƙar Baka

    Mazubi na harshen waƙar baka yana ɗauke da ƙwayoyin sauti da gaɓoɓi da kalmomi da kuma jumloli; waɗanda suke ba makaɗa damar su iya aiwatarwa da sadarwa cikin rerawa a sauƙaƙe.

    A zubi na waƙoƙin baka, daɗa a wajen makaɗa masu shiri na baka ko masu shiri na ƙire ko haye ko masu shiri na rubuce; suna shirya kalmomi ne da kansu ko wasu su shirya musu, sannan su saka amo na murya da na kiɗa, su kuma rera.

    Waƙar Baka

    Shirya Kalmomi

    Shiri na Baka Shiri na Ƙire/Haye Shiri na Rubuce

    Kalmomi Kalmomi Kalmomi na kai
    na kai na kai
    Satar waƙar Kalmomi na wani
    Satar Waƙa

    Idan aka lura, dangane da harshe a zubin waƙar baka, makaɗa da mawaƙa suna tasirantuwa bisa wasu matakai na ginawa da shirya waƙa da suka haɗa da:

    3.1 Shirya Kalmomi

    Kamar yadda aka nuna a baya, waƙoƙin baka ana shirya su ta gaɓoɓin kalmomi bisa zaɓi na makaɗi. Kalmomi a harshe su suke yi wa makaɗi tsani ya saƙa saƙonni, manya da ƙanana, a waƙa.

    3.2 Daidaita Murya da Amon Kiɗa

    Makaɗi ko mawaƙi yana daidaitawa ne a tsakanin amon muryarsa, wadda take tafiya a saje da gaɓoɓi da kalmomi na zubinsa; da kuma amon kiɗa wanda yake wanzuwa daga kayan kiɗa waɗanda yake amfani da su. A lokacin da wannan yanayi ya daidaitu, sai rauji na waƙa ya wanzu; wanda yakan zama gajere ko dogo ko matsakaici, gwargwadon yanayin kalmoni da kuma amon kiɗan da aka ɗauka.

    3.3 Daidaita Tunani a Saɗaru

    A waƙar baka akan daidaita tunani da ma’ana, babba ko ƙarama ta waƙa ta gurabun kalmomin waƙa waɗanda ake rerawa ta hanyar tsayin rauji a saɗaru. Dole ne tunanin waƙa ya dinga tafiya tare da zubin kalmomi a saɗaru na waƙa.

    3.4 Kaucewa Dokokin Nahawu

    Harshen waƙa, musamman yadda wani bi yakan ƙunshi tarin kalmomi, sannan da yanayin rauji da rerawa; yakan wadatu da tsarinsa ne har ya dinga bauɗe wa wasu dokokin nahawu.

    Shi harshen waƙa yakan sanya masana nahawun harshe da jujjuyawar kalmomi da karin harshe da sauransu; su yi ta ƙoƙarin gwada ɗora kalmomi da jumloli na waƙa a kan daidaitaccen tsarin nahawu. A wajen waƙar baka ƙirƙirowa da baddala kalmomi ko tsarin jumla da sauransu wata hanya ce ta kamalar harshen waƙa.

    3.5 Jefa Dabarun jan Hankali

    Wasu daga cikin hikimomi na harshe wanda ake shirya waƙa da shi, sukan yi naso a waƙa. Makaɗi yakan yi amfani da dabaru na yi wa zubin waƙarsa kwalliya ya daɗa armasa waƙar; ya ƙara mata nagarta cikin dausayin harshe. Dabarun nan na jan hankali sukan iya sanya harshen waƙa ya ƙara tsada; ya zama mai nauyin fahimta, mai jefa sarƙadodo a wajen warware ma’ana.

    Akwai dabarun jan hankali da yawa waɗanda makaɗa da mawaƙa suke jejjefawa a waƙoƙinsu da suke bambanta a daraja da nauyi na kowace waƙa; ko kuwa a mabambantan waƙoƙi na makaɗi ko mawaƙi ɗaya.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Makaɗi a Sarrafa Harshen Waƙa danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Waiwaye Kan Harshen Makaɗi A Zubin Waƙar Baka wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.