Amfanin Haƙuri

0
13

SALMANU FARISS ADAMU

Haƙuri: Shi ne danne zuciya a kan wani abu mara kyau, wanda ya baƙantawa mutum zuciya.

Haƙuri yana da matuƙar amfani ga mutane, kamar yadda ya zo a cikin littafin Sheikh Abdulrahim bin Ahmad Alkadhi mai suna “Daƙa’ikul khabar” shafi na 17 babi na goma sha biyu yace, labari ya gangaro cewa wanda aka jarabce shi da wata masifa, sai ya yaga tufafin sa ko ya bugi ƙirjin sa (to hukuncin wanda ya aikata haka) kamar (wanda) ya riƙi makami ne zai yi yaƙi da Allah (Subhanahu wata’ala).

Sannan kuma an ruwaito daga Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) yace wanda ya ɓalle ƙofa ko ya yaga tufafin sa ya yi da wata masifa ta same shi ko ya bugu wajan zaman sa ko ya sare bishiya ko ya yanke gashin kan sa (saboda tsanani masifar da ta same shi), to za a gina masa gida na wuta a kan kowane gashi (wanda ya cire), sa’annan kuma Allah ba zai karɓi aikin sa na farilla ba ko na nafila matuƙar yana kan wannan hali.

Har ila yau, Allah zai ƙuntata ƙabarinsa, kuma zai tsananta yi masa hisabi, sannan kuma dukkanin mala’ikun da suke sama da ƙasa za su dunga tsine masa, haka kuma za a rubutawa laifuffuka guda dubu a gare shi, sannan zai tashi a cikin ƙabarin sa tsirara.

Haka kuma, wanda ya karya gefan jikin sa, saboda wata masifa, to Allah zai karya addinin sa, idan kuma ya bugi ko ya mari kumatun sa ko ya azabtar da fuskar sa, to Allah (Subhanahu wata’ala) ba zai kalle shi ba da rahmar sa ba ranar alƙiyama.

Bugu da ƙari, kuma ya zo a cikin shafi na 18, babi na goma sha huɗu a cikin wannan littafin yace Sayyadina Aliyu bin Abu-ɗalib (karramallahu wajhahu) yace “haƙuri ana yin sa ne ta hanyoyin guda uku; na farko yin haƙuri a kan yi wa Allah biyayya, na biyu yin haƙuri a kan saɓawa Allah, na uku haƙuri a kan wata masifa wacce ta samu mutum.

Saboda haka, duk wanda ya yi haƙuri a kan yi wa Allah biyayya, to Allah zai ba shi daraja guda ɗari, sa’annan kuma ko wace daraja yawanta ta kai tsakanin sama da ƙasa.

Wanda kuma ya yi haƙuri a kan saɓawa Allah, to Allah zai ba shi daraja guda ɗari shida ranar lahira, haka kuma kowace dajara yawan ta ta kai faɗin sama da ƙasa, wanda kuma ya yi haƙuri a kan wata masifa wacce ta same shi, to Allah zai ba shi lada ba tare yi masa hisabi ba (ranar lahira).

Karanta Tarihin Farfesa Abdallah Uba Adamu

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceMijin Marigayiya Babi Na Biyar