Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; wanda ya yi salati ɗaya a gare ni, Allah zai yi salati goma a gare shi’.
Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘kada ku mai da ƙabarina idi; ku yi salati a gare ni ko ina kuka kasance’.
Kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Marowaci shi ne wanda aka ambace ni a wurinsa amma bai yi mini salati ba’.
Kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Allah yana da waɗansu mala’iku matafiya a bayan ƙasa; suna isar mini da sallama daga al’ummata’.
Sannan kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Babu wani wanda zai yi mini sallama face Allah ya dawo mini da raina na amsa sallamarsa’.
Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Yaɗa Sallama A Cikin Al’umma danna nan.
Domin karanta cikakken bayani a kan Wane Ne Ya Raɗa Wa Manzon Allah(S.A.W) Suna Muhammad? danna nan.