Ƙungiyar Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ta Kiɗa

0
57

Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya samar da ƙungiya ta aiwatar da kiɗa mai zurfin tunani wadda kuma ta amsa sunanta. A wannan ƙungiya Ɗanƙwairo shi ne Jagora, kuma yana ba ‘Y/Amshi nasa damar yin ƙari da ajewa da sauka da saukar sauka da takidi da rakiya ko karɓeɓeniya, wani bi ma da bayayyeniya, sannan da yin takidi na G/Waƙa.

Haka kuma a rera wasu waƙoƙi Alhaji Musa Ɗanƙwairo yakan tafi da Sanƙirori da wasu hadiman waƙa duk a ƙungiyar kiɗa ta Musa Ɗanƙwairo.

Da kansa Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya nuna yadda yake aiwatarwa da ƙullawa da rerawa da sadar da ɗiya a waƙoƙinsa a wannan ɗa na waƙarsa ta ‘Yandoton Tsahe Alhaji Aliyu II, mai G/Waƙa:

Shirya kayan faɗa mai gida Tsahe:

Jagora: Duk Makaɗan da at Tsahe nai jam’i,
: Hab baƙi ha ‘yan gida su duka,
‘Y/Amshi: Babu mai shirya waƙa kamat tawa,
Jagora: Ga makaɗi ya ƙulla wuƙatai,
‘Y/Amshi: Sai a amsa mashi ba a ƙara mai,
: In nuk ƙulla waƙa a ƙara man,
: Mu haɗu duk azanci gare mu,
: Shin a a mutum guda za ya radde mu,
: Shirya kayan faɗa mai gida Tsahe,
: Ali ɗan Iro bai ɗauki raini ba.
Jagora: Ga mu hwa! Ga mu hwa!!

(Ɗan’ƙwairo, Waƙar Musa Ɗanƙwairo ta ‘Yandoton Tsahe Aliyu & Gusau, 2003: sh. ɗi)

Domin haka, Musa Ɗanƙwairo yana ƙullawa da rera ɗiya na waƙoƙinsa a yayin sadarwa kamar haka:
+Ƙungiya
+ Jagora (+Ƙulli)
+ ‘Y/Amshi (+Ƙari +ajewa +sauka +saukar sauka +takidi +rakiya +karɓeɓɓeniya +/-Bayayyeniya +ciko ko maimaita ko takidin G/Waƙa)
+ Sanƙira (Mai Kalato Ƙarin Bayanai)
+ Hadiman Waƙa

Ƙungiyar Makaɗa Musa ƊanƘwairo Maradun ta Kiɗan Kotso ta haɗa da:

i) Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun = Jagora

ii) Muhammadu, Daudun Kiɗa na Farko, Ya rasu = Kiɗa da Amshi

iii) Garba, Zawacin Kiɗa, Marafan Kiɗa,
Daudun Kiɗa na Biyu (2), Ya rasu = Kiɗa da Amshi

iv) Audu, Wakilin Kiɗa = Kiɗa da Amshi

v) Ali, Sabon Kiɗa (ɗan Sa’idu Shayi, Wani Ƙanin Musa Ɗanƙwairo) = Kiɗa da Amshi

vi) Sani, Zaƙin Murya, Marafan Kiɗa, Ya rasu = Kiɗa da Amshi

vii) Abubakar (Garba), Ciroman Kiɗa (ɗa), Ya rasu = Kiɗa da Amshi

viii) Ibrahim Sarkin Fada (Ƙane) = Kiɗa da Amshi

ix) Muhammadu Jikka (Jikka, Halifa 3) = Kiɗa da Amshi

x) Sani (Jika) = Kiɗa da Amshi

xi) Muhammadu Gambo (Bara) = Kiɗa da Amshi

xii) Malam (Bara) = Sanƙira, Kwandon Ɗanƙwairo

xiii) Ƙanƙahu (Bara) = Tsaron Kaya

xiv) Sada (Bara) = Sanƙira

xv) Rabo (Bara) = Kiɗa da Amshi

xvi) Nabuba (Bara) = Kiɗa da Amshi

xvii) Bucaca ‘Yarkohji (Bara) = Kiɗa da Amshi

xviii) Amadu Bakura (Bara) = Sanƙira

xix) Sallah Kwana (Bara) = Hadimin Gidan Ɗanƙwairo

xx) Daudu Ɗangaladima (Bara) = Kula da Doki da Gona

Domin karanta cikakken bayani akan Tattali da Kulawar Ɗanƙwairo da Majiɓintansa danna nan.

Domin karanta cikakken bayani akan Dangantakar Harshe da Waƙa danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceYin Waƙar Baka ko Sarrafa Waƙar Baka
Labarin na GabaWaƙar Neman Zaman Lafiya
Prof. Sa’idu Muhammad Gusau
FARFESA SA'IDU MUHAMMAD GUSAU, An haife shi a Gusau jihar Sakkwato, (Maris 24, 1952). Ya yi karatun firamare na Islamiyya daga 1965-1969, ya je kwalejin sarkin Musulmi Abubakar daga Junairu 1970 zuwa Yuni 1973. Ya yi Diploma, Digiri Na farko (B.A), na biyu (M.A) da Digiri na uku (Ph.D) duk a jami'ar Bayero, Kano.