Yadda Ake Addu’ar Tafiyar Da Ƙuncin Zuciya

0
87

khairatu.shehu

لاَ إِلَهَ إلا اللهُ الْعَظِيمُ الْحَلِيمُ، لاَ إِلَهَ إلا الله رَبِّ الْعَرْشِ الْعَظِيمُ، لاَ إِلَهَ إِلَّا اللهُ رَبُّ السَّمَوَاتِ وَرَبُّ الأَرْضِ وَرَبُّ الْعَرْشِ الْكَرِيمُ .

La’ilaha illallahul azeemul haleem, la’ilaha illallahu rabbil arshil azeem, la’ilaha ilallahu rabbus samawati warabbul ardi wa rabbul arshil kareem.

Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Mai girma (wanda babu abin da yake girmama a gare Shi), Mai haƙuri (Mai jinkirin azaba tare da cikakken ikon aiwatar da ita). Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin Alarshi, Mai girma. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin sammai, Ubangijin ƙasa, Ubangijin Al’arshi, Mai yawan baiwa.

اللّهُمَّ رَحْمَتَكَ أَرْجُو فَلا تَكِلْنِي إِلَى نَفْسِيطَرْفَةَ عَيْنٍ وَأَصْلِحْ لي شأني كلهلا إله إلاأَنتَ.

Allahumma rahmataka arju fala takilni ila nafsee ɗarfata aini wa’aslih lee sha’ani kullah, la’ilaha illa anta.

Ya Allah! Rahamarka nake kauna, don haka Kar Ka kyale ni da kaina ko da kiftawar ido ne, kuma Ka kyautata mini sha’anina dukkansa; babu abin bautawa da gaskiya sai Kai.

لاَ إِلَهَ إلا أنتَ سُبْحَانَكَ إِنِّي كُنْتُ مِنَ الظالمين

La’ilaha illa’anta subhanaka inni kuntu minaz zalimeen

Babu abin bautawa da gaskiya sai Kai. Tsarki ya tabbata gare Ka, lalle ni na kasance daga cikin azzalumai.

الله الله رَبِّى لاَ أُشْركُ بِهِ شَيْئاً
Allah Allah rabbi la ushrika bihi shai’an

Allah! Allah ne Ubangijina, ba na yin tarayya da Shi da wani abu a cikin bauta.

Karanta Yadda Ake Addu’a A Kan Abokan Gaba

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceYadda Ake Addu’a A Kan Abokan Gaba
Labarin na GabaMatsayin Harshen Hausa A Ƙarni Na 21 Da Tagomashinsa