Waƙa Mai Taken Nagartaccen Jagora

0
19

1. Da sunan Rabbana Karimi sarki guda,
Da ke bayar da ɗaukaka daji ko gida,
Da ya aiko wa duniya Ɗaha Muhammada,
Da ya ɗora mu kan tafarki mara gargada.

2. Baitoci ne nake nufin yi don shugaba,
Babban masani kama tai ba a yi shi ba,
Bai yarda a bar talakka halin ni-‘yasu ba,
Bai mallaki duniya da ya bar bayansa ba.

3. Shi ne ya zamo mujahidi rai ya ba da shi,
Shi yat tari duk aradu ta faɗa kai nashi,
Shi yai tsayuwar talakka komai a yiwo da shi,
Shi yaj ja rundunar adalci a tsayar da shi.

4. Ya samu amintatar dukan ‘yan Nijeriya
Ya zam sane duk ƙasa Kudunta da Shimaliya,
Ya zam jigo ƙasa da shi ne aka fariya,
Ya rungumi duk talakka bai yarda da wariya.

5. Na san wasu sun zaƙu shin waye a faɗa mana,
Nagartaccen mutum nufina ba tsokana,
Najeriya shi yake da siffar da na bayyana,
Nasara garai suna da shayi har razana.

6. Aminu Kano nake nufi ya san shari’a,
Aikin da ya yi kawar da zaluntar jama’a,
A neman ‘yantuwar ƙasa ya yi mubaya’a,
A mulkin mallakar da Turai suka ɗabba’a.

7. Mulkin mulaka’u sunka yaƙa da akai mamu,
Mulkin kai sunka tabbatar ya samu ga mu,
Mulki ya zamo ga ‘yan ƙasa don hidima wa mu,
Mulki na Nasara ya tafi sai murna ga mu.

8. Malam burinsa adalanci ba taƙama,
Mai son a kawar da ɓangaranci ba haɗɗama,
Mai son talaka ya tsira cuta bisa haƙƙuna,
Maza mata lallai mu waye ba riggima.

9. Ba za a yiwo batun siyasa ba a sa shi ba,
Batun ‘yancin talakka malam na kan gaba,
Ba za a faɗi gwagwarmayar haƙƙu a bar shi ba,
Bangon talaka na jingina ban ga kamar sa ba.

10. Bisa haka NEPU sun kafa haƙƙi don a bi,
Biɗar talaka ya walwala babu tararrabi,
Bisa haka sun wahaltu ɗauri kuwa bi da bi,
Bi hamdillahi sun nasartu bisa martabi.

11. Jamhuriya fari sun tsayu an ja sunka ja,
Jan aiki ne sukai na sai da rayi ba amaja,
Jari nasu lafiya da kutsen dukkan luja,
Jama’a sun samu horuwa daga duk a ja.

12. Karo na biyun jamhuriya an san ɗaukaka,
Kafon P.R.P. jam’iya an tsayuwar daka,
Karantarwar Aminu ta ratsa dawa ɗaka,
Kano da Kaduna sun shiga tutar talaka.

13. Haraji anka soke karɓar sa a nan jiha,
Hakan nan jangali ka soke shi ba raha,
Haƙiƙa talakanmu ya ‘yantu ya farraha,
Harkoki sun yi kyautuwa don an sarraha.

14. Malam ya kutsa takara an yi arangama,
Matakin shugaban ƙasa yab biɗi yaz zama,
Mai ba da abin Ilahu bai so bisa hikkima,
Masoya nasa ya kafa manya sun zama.

15, Fa mulkin lokacin Gawan soja da an kafa,
Fahimtar daraja ta Malam mai falsafa,
Fa an zaɓar Minista aiki ya yi kaifafa,
Farar aniyarsa ta fito ta shiga duk kafa.

16. Sanin haƙƙin nisa’u mata ɗan “ب” ya sa,
Sahun farko biɗa ga haƙƙinsu shi ka sa,
Samun ‘yanci na walwalarsu Malam ya sa,
Saka su a gwamnati da saurran aikin ƙasa.

17. Gogaggen malamin siyasa bai zam rago,
Goran ƙarfe fagen sani maliya bai shigo,
Goni a kitabu har da sunna kan ɓuɓɓugo,
Goman fanni dubunsa Malam ba ya tago.

18. Sun ɗaukaka ɗaliban da ya zam koyar da su,
Sukul fannin siyasa sun zamto ba ya su,
Su ne hulafa’u nasa har gobe muna da su,
Sunansu ba zan kira al’umma ta san da su.

19. Aminu Kano mutum da bai ƙyamar jama’a,
Abin hannunsa bai bari sai ya wazza’a,
Abin koyi tawali’u ga shi da ƙanna’a,
Allahu Gwani ka tausasa mar mun addu’a.

20. Lamarin harkar siyasa yau an sa ƙin kula,
Lallai shiriyar Aminu in mun bi a hankala,
Lagon matsalar da ke ciki har duka mushkila,
Labari zai zamo gaba sai yin hamdala.

21. Allahu ka kyautata makwancin mai jama’a,
Aminu Kano garai rahama taka wassa’a,
Aljanna ka sa ta zam gare shi ran Waƙi’a,
Albarkar  Musɗafa ka tashe shi da fara’a.

22. Nasir Ahmad ya yi ba a san ni ba ko’ina,
Na dai zam mai biɗar sani ilmu na shinshina,
Na gaishe da dukka kowa nai jinjina,
Nai roƙo ga Rabbana ba mu yawan shina.

Alhamdu lillahi.

Danna nan don karanta Waƙa Mai Taken Kowa Ya Bar Gida…
Edita@rumasau-kallamu

 

 

labarin da ya wuceWaƙa Mai Taken Kowa Ya Bar Gida…
Labarin na GabaWaƙa Mai Taken Masha-Jini
Nasiru G. Ahmad
Haifaffen jihar Kano ne a unguwar 'Yan awaki. Ya yi digiri na ɗaya da na biyu a kan harshe da adabin Hausa. Yana cikin ƙungiyoyi da dama na marubuta a ciki da wajen jihar Kano. Malami ne kuma mawallafin littattfai da waƙoƙi.