Waƙa A kan Dangina

0
882

Salam alai dangina, Ku amsa domin ƙauna, Allah daɗo tsiran na, ga Shugaba Manzona, Mai son sa ba ya gaba.

  • Tsira, aminci ƙara,
  • Ga sahiban nan jera,
  • Mai son su ba ya ƙyara,
  • Sai so da ƙauna jera,
  • Daɗo aminci Rabba.
  • ———————————
  • A yau akwai wani zance,
  • Ku bi ni, kar da na mance,
  • Batu na murna kunce,
  • Na bayyano ba ƙifce,
  • A zaurukan nan babba.
  • ——————————–
  • Lasan na yo tattaki,
  • Cikin aminci ɗoki,
  • Domin halartar fa biki,
  • Na tsara baitin baki,
  • Na jera murna babba.
  • ———————————
  • Abokanai sun zo wa,
  • Ta ko’ina ba ƙiwa,
  • Domin su nuno sowa,
  • Cikar mutunta da yawa,
  • Su shaidi ƙauna babba.
  • —————————–
  • Da safe in yai wanka,
  • Ran Juma’a ba shakka,
  • Da yamma yai tattaka,
  • Gare ki sai sam-barka,
  • Domin ku zazzaga hira.
  • —————————–
  • ƙarshen ta cuta mutuwa,
  • haka ƙarshen gani soyewa,
  • kuma ƙarshen fa so aurewa,
  • A dabdale bidirewa,
  • A so a kore gaba.
  • —————————–
  • Nura abokin kaina,
  • Aurenka nai wa murna,
  • Na tsara baitin ƙauna,
  • Domin gabatarwana,
  • Aure zumunci babba.
  • —————————-
  • Fa Nura kare haƙƙi,
  • Ka bi su kar ka yi raki,
  • Tuwo, tufafi ɗauki,
  • Ka ba ta har fa a baki,
  • Da rangwaɗar nan duba.
  • ———————————
  • Auren ga sunnar Manzo,
  • Ku raya domin ƙwazo,
  • haka Ku yi shi har ku yi tozo,
  • Dan Ku amsa kiran Manzo,
  • Don Ku zazzago so babba.
  • ————————–
  • Amarya zan yo kanki,
  • Ki tsara kanki da kanki,
  • Biyayya ba yin birki,
  • Mijinki shi ne angwanki,
  • Gare ki tamkar Baba.
  • —————————
  • Ki lallaɓa shi a komai,
  • Danginsa so su da sosai,
  • Ki tausaya mai ji nai,
  • Ki toshe kunnen son rai,
  • Allah ya kawo riba.
  • —————————-
  • Nayaya na tsara,
  • Baiti fa sha uku jera,
  • Hanyar zuwa nat tsara.
  • NWAN uwa mai gyara.

domin samun karanta waƙoƙi danna koren rubutun nan

labarin da ya wuceSaƙo Ga Masoyiyata
Labarin na GabaYadda Ake Kwalakca