Waƙa Mai Taken Masha-Jini

0
15

1. Allah ba ni buɗi in yi tsari na baituka,
A kan ƙwaro wanda bai da tausai a duniya.

2. Ƙwaron da yakan cutar da manya da ƙanƙana,
Mai shanye jini na ɗan Adam ba shi tausaya.

3. Gwanin zilliya yake da ɓoyo jikin tufa,
Ko gashi na kai ya zam shi birni ya wataya.

4. Gudun kar ku ƙosa Kwarkata ce nake nufi,
Bai ƙyale baƙar fata fara ko ko rawaya.

5. Abin da kan samar ta ƙazanta ce Lamba Wan,
Haɗewar zufar jiki da dauɗa annakiya.

6. Da wannan haɗi Allah kan samar da kwarkwata,
Ta rayu tufar mutum gashin kansa kulliya.

7. Tana sanya ƙwai ta ƙyanƙyashe shi da hanzari,
Su zamto yawaita ɓamɓare ta akwai wuya.

8. Abinci nasu jinin mutum za su yi ta sha,
Ya kasa sukuni a dare ko ko safiya.

9. Hanyar yaɗuwa tata kusantar jikin mutum,
Da ya zam yana ɗauke da ta ko da sau ɗaya.

10. Ko ko sanya rigarsa hula ko ko fattala,
Hakan nan kwana da mai ita gun ɗaki ɗaya..

11. Idan har ta samu sai a wanke dukan jiki,
Da ruwa na kogi “Ma’ul Khalli” a gauraya.

12. Mutum kan yi kwarkwata ba don ba shi tsaftace,
Jikinsa sai Ibtila cire ta akwai wuya.

13. Misali mutum Biyu cikin wanda anka wa,
Busharar shiga Aljanna tun nan a duniya.

14. Abdurrahamani Auf Sahabi attajiri,
Zubairu ɗan Awwamu Sahabi abin biya.

15. Allah ya jarabce su da ƙwaron ga kwarkwata,
Tufarsu da gashin kai dare har da safiya.

16. Har Manzo ya sauƙaƙa gare su halal yake,
Rigar Alharini sunka sanya ta duniya.

17. Hakan nan a Hajji ya halatta su aske kai,
Su bayar da fiddiya ga nassin Ƙur’aniya.

18. Dalili na Ukku nan ga samo na kwarkwata,
Azaba ga kafirai su komo ga shiriya.

19. Misali Fir’auna lokacin da ya kangare,
Da shi da mutanensa ɓarna sun yi dulmiya.

20. Aazabobin gargaɗi da anka saukar musu,
Ciki har da kwarkwata jikinsu tufafiya.

21. Har sai da sukai roƙon a janye ta za su bi,
Musa Annabi ya roƙi Allah ta zam tsaya.

22. Akwai wanda kwarkwata ba sa yin ta ko kaɗan,
Luɗufi na Allah ne gare shi a duniya.

23. Shi ne mai kuturta wanda ta ci yatsu nasa,
Da ba yatsan kama ta gare shi ko da ɗaya.

24. Ba a cin ta kwarkwata ƙwaro ne masha jini,
Jini ko haramun ne umarnin kitabiya.

25. Hakan nan abinci in ta faɗa ciki nasa,
Ita da Kuɗin cizo barin cin sa lafiya.

26. Jininta jikin tufar mai salla an sahhale,
Ba ya ɓata salla ta dare ko ta safiya.

27. Haka ma kashe ta nan a salla abin bari,
Sai dai binne ta ka so ko ƙyale ta bai ɗaya.

28. Ba a son a kamo ta a jefar abin ƙiya,
Domin kar jikin wani ta hau tai ta wataya.

29. Muna roƙon Allahu ya ƙare mu lafiya,
Ya ije dukkan cuta gare mu baki ɗaya.

30. Alfarmar Alƙur’ani da Sidi Muhammadu,
Da an ba wa cetonmu a rana ta tambaya.

31. A nan zan taƙaita ɗan bayanin da na shira,
A kan kwarkwata masha jini babu tausaya.

32. Sunana Muhammad Nasiru Garba Ahmadu,
Almajir da ke biɗar sani kar ya sulmiya.

33. Baitoci Talatin ne da Ukku ran Litinin,
Alfaini da Isshirin Agusta yai gomiya.

Alhamdu lillahi

Karanta  Waƙa Mai Taken Nagartaccen Jagora

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceWaƙa Mai Taken Nagartaccen Jagora
Labarin na GabaWaƙa Mai Taken Gudumar Dukan Rashawa
Nasiru G. Ahmad
Haifaffen jihar Kano ne a unguwar 'Yan awaki. Ya yi digiri na ɗaya da na biyu a kan harshe da adabin Hausa. Yana cikin ƙungiyoyi da dama na marubuta a ciki da wajen jihar Kano. Malami ne kuma mawallafin littattfai da waƙoƙi.