-
Da sunan Rabbi mai baiwa gare mu,
Da nau’o’in ni’imta ba musawa.
2. Salati da sallama ga Rasulu Ɗaha,
Da ya ceto mu bin hanyar ɓacewa.
3. Cikin ni’imar da Rabbi ka yi gare mu,
Fitar najasa ga mu don tsarkakewa.
4. In ban da haka jiki za tai zamanta,
Guba ce wallah za tai illatarwa.
5. A don haka gode Allah ya wajabta,
Bisa ni’imar ga kullum mui ta yowa.
6. Musulmi an buqƙaci ya yo ladubba,
Ya bambanta da gayyar kafirawa.
7. Idan ya buƙatu banɗaki ya zaga,
Da Bismillah ake son yai shigewa.
8. Ya sanya ƙafar hagu yayin shigarsa,
Ya zam addu’ar tsari daga jinnatawa.
9. Idan ba ka ambaci Allah shigarka,
Al’aurarka sukan riƙa kallatawa.
10. Hijabi naka Basmala du’a’i,
Idan ka yi ba su duba ko tsayawa.
11. Kada ka shiga da sunan Rabbi Allah,
Jikin zobe waninsa an hanawa.
12. Idan sarari ka je don tsuggunawa,
Cikin dajin Ilahu ka zam kulawa.
13. Ba a tsuguno a kan hanyar mutane,
Da inwoyi na amfani ga kowa.
14. Ƙasan bishiya da ‘ya’ya ta yi ban da,
Da gefanni na gulbi mai wucewa.
15. Da ramukka tana yiwuwa da jinnu,
Da yin bawali ruwa mai dawwamewa.
16. Ka nesaci duk idanu kar su gan ka,
Ko sauti mai fita wari jiyowa.
17. A nemi wuri da babu ruwa bisansa,
Bai zam shi faƙo ƙasa mai taurarewa.
18. A zancen Hausa ma an ce Mugunta,
Fitsari kan faƙo zai fallatsowa.
19. Ba a cire riguna ko janye wando,
Sai an yi kusan isa ƙasa za a yowa.
20. Ba a fuskantuwar Qibla a yayin,
Da an tsuguna a fili mui kulawa.
21. Hakan nan ba ta baya an hana shi,
In ba sutura ko banɗaki ginewa.
22. A yayin ko fitar najasa ana so,
Qafar hagu za a ƙarfafa dogarewa.
23. Ba a magana a yayin tsuggunawa,
Abin karhantuwa an tsawatarwa.
24. Tsarkin bawali akan fara gabanin,
Muhallin gayaɗi sai mui kulawa.
25. Idan najasar ta ƙare fita a tashi,
Kada a jima yawan nishi anaiwa.
26. Ba a tsarki da hannun dama yayin,
Wanke najasa hagun za ai sakawa.
27. Ko da da Tishu ya zamto za a goge,
A yo da hagu kafin da ruwa biyewa.
28. Hakan ne ma bin so in ya samu,
Gudun hannu taɓar najasa ya yowa.
29. Ba a sanya ƙashi don goge najsa,
Ko ko tutu na dabba an hanawa.
30. Kaza da dukansa dangogin abinci,
Da duk abu mai darajja ba a yowa.
31. Shi ma bawali a yo Istinjimari,
Kafin tsarkin ruwa ya zamo biyewa.
32. A zam addu’a idan za ai fitowa,
Da banɗaki a bayan tsuggunawa.
33. Mu zam gode wa Allah don raba mu,
Da duk najasa da mun zam kasayewa.
34. Kaza najasar ruwa da mukai bawalta,
Aminta don gare mu yai daɗowa.
35. A nan zan dakata ya ‘yan uwana,
Kurenmu Tabaraka yai garafawa.
36. Ya Rabbi daɗo salati babu haddi,
Ga Manzo naka jikan Hashimawa.
37. Idan an tambayi mai tsara waƙar,
Nasir Ahmad iri na Bukar ya yowa.
38. Baitoci Arba’in Biyu babu waƙar,
Dubu Biyu sha Tara Maris na yowa.
Alhamdu lillahi
Wannan waƙa an ciro ta ne daga littafi mai suna TASKIRA wanda Nasiru G. Ahmad ya wallafa.
Karanta Tarihin Marubuci Nasiru Garba Ahmad
Edita@rumasau-kallamu










