Tatsuniyar Wata Mata Mai ’Ya’ya Biyu

0
4

Ga ta nan, gata nanku.

Akwai wata mata tana da ’ya’ya biyu, ɗaya mace, ɗaya kuma namiji. Macen ce babba, namijin kuma shi ne ƙarami. Tana nan, tana nan sai wata rana ta kamu da rashin lafiya. Tana cikin rashin lafiyar ta kira ’ya’yanta, tana yi wa macen wasiyya cewa, ko da bayan ranta yaron ya ce zai yi wani abu to kada ta hana shi, ta bar shi.

Bayan uwar ta rasu sai suka bar gidan, suka kama hanya suka nufi wani gari daban. Suna tafiya a cikin daji kwana da kwanaki, rannan sai wata babbar tsuntsuwa ta ɗauke su ta tashi sama da su, ta yi ta tafiya har suka isa daidai wani babban gari. Sai yaron ya ɗauki tsinke ya ce da yayarsa zai tsokale zumɓutun tsuntsuwar, amma sai ta ce idan ya tsokale tsuntsuwar ai za ta yar da su.

Da ya ji haka sai ya ce mata ba uwarsu ta ce ta bar shi ya yi duk abinda yake so ya yi ba? Da yarsa ta ji haka sai ta yi shiru. Ya samo tsinke ya tsokali zumɓutun tsuntsuwar nan. Ita kuwa sai ta zubar da su a wannan gari.Can sai suka ga wani gida suka shiga, to ashe na wata tsohuwa ne. Da ta gan su sai ta yi maraba da su, ta ba su ruwa suka sha, ta tambaye su daga inda suke, sai suka kwashe labari suka ba ta.

Sai ta ce da su za ta riƙe su, amma kuma akwai wani dodo da yakan zo da dare yana cinye mutane kullum a garin. Da dare ya yi aka kulle gida, sai yaron nan ya ce a ba shi ƙarafa guda uku, waɗanda zai yi amfani da su ya soke dodon, kowa ya huta a garin. Da tsohuwa ta ji abin da yaro ya faɗa, sai ta ce da shi ba zai iya ba, amma sai ya dage a kan shi dai a ba shi.

Tsohuwa ta yi masa yadda ya nema amma ba da son ranta ba. Yaro ya hura wuta, ya zuba ƙarafan a ciki. Da suka yi ja, sai ya ji waƙar dodon yana cewa:

“Wane ne ya isa ya ja da ni, a garin nan?

Wane ne ya isa ya ja da ni, ni dodo?

”Sai can yaron nan ya ce: “Ni ne na isa na ja da kai a garin nan. Ni ne na isa na ja da kai, Ni Auta, har ma na fi ka.” Da dodo ya ji haka sai ya buɗe bakinsa ya yi wani irin ƙaraji. Sai Ɗan auta ya yi wuf, ya jefa masa ƙarfe ɗaya da ya yi jajir a cikin bakin. Sai dodon ya cafe ya haɗiye ƙarfen, yaron ya jefa masa ƙarfe na biyu, dodo ya cafe ya ƙara haɗiyewa.

Da yaron ya jefa masa na uku ya haɗiye, sai dodon nan ya faɗi rigija. Nan take ya mutu a ƙofar masallaci, ko shurawa bai yi ba. Ganin haka sai Ɗan auta ya bar takalminsa a wajen mushen dodo. Da asuba ladan ya je ƙofar masallaci domin ya shirya ya kira salla, amma sai ya ga mushen dodon nan shim. Sai ya je ya gayawa Sarki abin da ya gani.

A cikin murna Sarki ya je ya ga mushen dodo, kuma ya tambaya ko wane ne ya kashe shi, domin an ga takalmin wanda ya kashe dodo, amma ba a san ko na wane ne ba. Abu kamar wasa, sai Sarki ya ce duk wanda ya sa takalmin nan ya yi masa daidai, to shi ne ya kashe dodon, kuma Sarki ya yi alkawari zai ba wanda ya kashe dodon ladan rabin garin nan.

Masu kwaɗayin wannan kyauta suka ta zuwa suna gwada takalmi, amma bai zauna musu daidai ba. Can sai aka ba Sarki labarin wata tsohuwa da ta yi baƙi, sai Sarki ya sa aka kira ta ta sa takalmi bai yi mata daidai ba. Daga ƙarshe dai Ɗan’auta ya sa takalami, kuma ya yi masa daidai. Da dai aka tabbatar shi Ɗan’auta ne ya kashe dodo, sai Sarki ya cika alƙawarin da ya yi, watau na ba shi rabin garin.

Yaron kuwa ya karɓi rabin gari ya ci gaba da mulki cikin nasara, shi da yayarsa. Ƙurunƙus.

Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

  • Mai biyayya lamarinsa ba ya ɓaci.
  • Kowa da irin baiwar da Allah ya yi masa a wannan duniya.
  • Duk mai mugunta sai ya gamu da wanda ya fi shi.

Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

Danna nan don karanta Tatsuniyar ’Yan Mata Masu Kamun Kifi

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceTatsuniyar ’Yan Mata Masu Kamun Kifi
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.