Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Daya)

0
1

Ga ta nan, ga ta nanku.

Wata rana Kurege da Kura suna yawo, sai suka tsinci ƙyallen fatari. Sai Kurege ya ce, bari ya je ya ɗinka musu riguna da shi. Ya je ya ɗinko riguna biyu, amma girmansu ɗaya. Ya bai wa Kura ɗaya. Da Kura ta saka sai rigar ta matse ta, ta shaƙe mata wuya saboda ta yi mata kaɗan.

Sai Kurege ya ce da Kura tun da rigar nan ta yi mata kaɗan, sai ta bar masa ita. Da Kura ta ji haka sai ta ce masa: “Daman ka cuce ni ne tun da ka ɗinka rigata daidai da taka, sai ka ɗauka.” Kurege ya haɗa duka biyun, suka shiga jeji don su farauto abinda za su ci. Da suka kamo namun daji da yawa sai suka dawo gindin wata bishiya, suna hutawa.

Kurege yana so ya cinye namanshi kaɗai, amma ya rasa yadda zai yi. Can sai ya hango wasu ‘yanmata a bakin rafi, sai ya dubi Kura ya ce: “Ga ‘yan mata can, mu je mu yi musu magana. “Sai Kura ta yarda, suka je suka tarar da ‘yan matan suna hira. Suka zauna suna sauraron hirar.

Da Kurege ya ga hira ta fara yin daɗi sai ya ce da Kura su je su dafa naman nasu. Sai Kura tace ita tana nan a wurin hira, ba za ta je ba. Shi kuwa Kurege sai ya je domin ya dafa musu naman. Ashe ya sami abin da yake so, wato sai ya zaɓi nama mai kyau ya zuba a jakarsa, ya ɓoye. Sai ya samo naman mushe ya dafa, ya ajiye wa Kura. Bayan ta dawo sai ya miƙa mata nama.

Kura ta hau ci ba ta san mushe ya dafa mata ba. Ta ci nama, irin cin haɗama, amma ta ɗan rage ta ɓoye a jakarta. Kura ba ta da masaniyar cewa Kurege ya ɓoye nama mai kyau, ya ba ta mushe. Saboda wayo irin na Kurege, sai ya dubi Kura ya ce: “Kura ki rage mini naman mana. Saboda haɗama irin ta Kura ita ma sai ta harari Kurege tace:
Ni ba zan ba ka ba tun da kai ne ka dafa, na san sai da ka zaɓi inda ya fi ko ina daɗi ka ci ka ƙoshi, ba zan ƙara maka ba.

Da rana ta faɗi, kuma dare ya yi sai suka samu wata bukka suka kwanta, can cikin dare sai zawayi ya kama Kura. Ta nemi Kurege ya raka ta, sai da rana ta faɗi, kuma dare ya yi sai suka sami wata bukka suka kwanta ki, ya ce in zawayin yana damunta, to ta fita waje. Ya ƙara da cewa: “Idan ma abin ya dame ki ai sai ki yi shi a kwance ba sai kin tashi ba.

Amma idan na ji ihu to babu lafiya, idan kuma abin ya yi tsanani, idan kuma kin yi shiru to lafiya kenan. Sai Kura ta fita waje ta yi kwanciyarta. Jim kaɗan sai kunama ta harbe ta. Kura da raki sai ta ƙwala ƙara, haka dai ta kwana tana zawo. Wayewar gari ke da wuya, sai ta je ta faɗa wa Kurege cewa jiya da daddare kunama ta harbe ta.

Sai Kurege ya ce: “Ai dama mun yi da ke idan na ji shiru lafiya ta samu, idan kuma na Ji ihu to ta yi tsanani sai in fita in taimaka miki. “Bayan Kura ta ji bayanin Kurege, sai ta ce: “To shi ke nan.” Da suka gama maganganunsu, sai Kurege ya rasa yadda zai yi ya ɗauki naman da ya ɓoye ya kai gida, domin ya sani idan Kura ta gani za ta ƙwace. Sai ya yi dabara ya ba Kura shawara ta je ta sha ruwa, ta wanke jikinta kafin su tafi gida.

Ba tare da zaton wani abu ba, sai ta kama hanyar rafi. Da Kurege ya ga ta tafi rafi, sai ya ɗauko namansa a inda ya ɓoye, ya saka shi a jakar Kura, shi ma ya shiga cikin jakar. Da ta dawo daga wanka, sai ta ɗauki jakarta ta rataya. Ba ta san Kurege yana cikin jakar ba, sai ta kama hanya. Daɗin waƙa ya sa ta kama hanyar gida ta fara tafiya, ta manta da Kurege.

Tana cikin tafiya sai ta fara yi wa Jakarta waƙa tana cewa. “Sai ni Kura durungu, Na yi farauta, Na cika jakata da nama, Nama sai mun ture, Ga shi a cikin jakata.” Haka ta rinƙa yi wa jakar waƙa. Sai da ta isa gida ta tuna ta bar cikin jakar Kura, riƙe da namansa ya gudu zuwa gidansa. Shi ya sa duk wanda ya je daji zai ga Kura tana ta yawon nema nai. Shi kuma da za ku je gidansa, za ku tarar da gidan cike yake da nama mai kyau, wanda yake ci ya more. Da babu Gizo da na yi muku ƙarya. Ƙurunƙus.

Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

  • Karamin mai hankali ya fi babba mai wauta.
  • Wauta mai janyo wuya.

Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

Danna nan don karanta Tatsuniyar Kishiyoyi Biyu

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceTatsuniyar Kishiyoyi Biyu
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.