An haifi Gwani Sharif Bala ɗan Sharif Musɗafa ɗan Sharif Muhammad a shekarar 1345; wadda ta yi dai-dai da shekarar 1934 a Unguwar Gabari cikin garin Kano.
Mahiru Sharif Bala ya taso a gidan ilimi da wadata da karamci a inda ya yi karatu a wurin mahaifinsa tare da ɗan uwansa Sharif Ahmad. Mahiru Sharif Bala ya rubuta Alƙur’ani sau uku tun yana ɗan shekara goma sha takwas; kuma a dai-dai wan nan lokaci ne aka yi masa auren fari. Mahiru Sharif Bala ya kutsa fannonin ilmi inda ya karanci tafsiri da Hadisi da Fiƙhu a Unguwar Makwarari.
Wani abin mamaki game da rayuwar Mahiru Sharif Bala ya yin neman Alƙur’ani shi ne: bai taɓa zuwa ko’ina ba kamar yadda abin yake wajen mafi yawan makaranta. Babbar baiwar da Mahiru Sharif ya shahara da ita baya ga ƙarfin tilawar Alƙur’ani, shi ne gwanintar rubutunmu na Magribi.
Kwanciyar baƙaƙen AIƙur’ani irinsu “Kaulasan” da Lam’ara da tsaiwar Bayala shaida ce ga ficen da Mahiru Sharif Bala ya yi a wannan fage. Saboda irin baiwar rubutunsa da irin karɓuwar da yake da ita tsakanin makaranta Alƙur’ani ba a ƙasar Kano ba kawai; har ma da wasu sassa na Afrika ta Yamma; ta sa Mahiru Sharif Bala ya juyi littattafai a sassan ilman Musulunci da hannunsa irinsu:-
– Asshifa
– Dala’ilul Khairati
– Ishriniyya
– Alburda
– Hamziyya
– Risatul Anwar
– Igasatul ibad
– Risala
– Iziyya da sauransu
Babu shakka wannan ya sauƙaƙawa makaranta tsangaya waɗanda ba su saba da rubutun sharƙiyya ba, damar kutsawa fannoni ilmi.
A taƙaice za mu iya cewa hannun Mahiru Sharif Bala da tasirinsa a tsarin tsangaya ya zama “hantsi leƙa gidan kowa”; domin kuwa ya ratsa kowane loko da saƙo na makaranta.
Ma’ana dai, in almajiri bai je gabansa ya yi karatu ba to kuwa ya kwaikwayi irin salon rubutun hannunsa; tun daga kan Juzi’i biyar ko goma har zuwa ashirin.
Yaɗuwar da Alƙur’anin Mahiru Sharif Bala ya yi ya zarta yaɗuwar mafi yawan Alƙur’anan da aka rubuta da hannu; domin kuwa ya rubuta Alƙur’ani hamsin da hannunsa. An buga bakwai daga cikinsu, kuma an ɗabba’a su fiye da sau dubu ɗari biyu: waɗanda duk sun yi fice da fitar da harji da meram da falalar kowace sura.
Game da taimakon yin magani da ayoyin Alƙur’ani kuwa, Mahiiru Sharif Bala ya rubuta Alƙur’ani don sha fiye da sau ɗari; Suratul Yusuf sau dubu ɗaya, Bisimilla da Wallahu ya ‘asimuka da Sanuƙ’ri’uka sama da miliyan guda.
Farin jinin rubutunsa da baiwar da Ubangiji yai masa ta sa an buga:-
i- Asshifar da ya rubuta da hannunsa sama da dubu talatin
ii- Dala ilul khairati sama da dubu ɗari
iii- Ishiriniya sama da dubu ɗari biyar
iv- Alƙur’ani ɗan izu ashirin sama da dubu ɗari biyar
v- Alƙur’ani ɗan izu goma sama da miliyan biyu
vi- Alƙur ‘ani ɗan izu biyar sama da miliyan biyu
vii- Ƙawa’idi sama da miliyan biyu
viii- Ashmawi sama da dubu ɗari biyar
ix- Risala sama da dubu goma
x- Iziyya sama da dubu goma
xi- Alburda sama da dubu goma
xii- Ira’atul biladi sama da dubu goma.
Har zuwa yanzu, Mahiru Sharif Bala bai gushe ba yana ba da karatu da ilimi a shahararriyar makarantarsa; tare da mataimaka sama da talatin da almajirai yara da manya, maza da mata sama da dubu biyar. Ubangiji Maɗaukaki Ya ƙara masa lafiya ya kuma sanya masa kyawawan ayyukansa a mizani.
Tsokaci
Akwai wasu malamai na Alƙur’ani fitattu a Kano da yawa – da ya kamata na gutsurawa mai karatu wani abu daga tarihin rayuwarsu, amma hakan ba ta samu ba.
Cikinsu akwai Malam Na Mai Ganji da Malam Giwar Takwasa da Malam Husaini Ɗangurai da Malam Ɗangidimoni; da Malam Ɗayyabu Mai Saje da Malam Yahaya Malammadori da Gwani Tata Bunkure da Malam Ɗan Ringim; da Malam Mai Hafizai da ma waɗanda ban ambata ba.
Domin karanta cikakken bayani a kan Wasu Daga Malamai a Katsina danna nan.
Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau danna nan.
Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.