Tarihin Garin Kudan 2

0
28

BABI NA HUƊU

Rana ta fara haskawa a sararin samaniyar garin Kudan, tamkar zinaren take  ɗauke da albarkatu. Mutane sun tashi suna jin wani sabon ɗumi a zuciyarsu, ɗumin da ake ji, idan aka ga alheri yana gab da farawa. Kamar yadda ake cewa:

“Idan gari ya fara motsi, ko tsuntsaye sukan san akwai abun da ake nema.”

A wannan rana an fara da al’amura guda  uku:  tsaro, haɗin kai, da bunƙasar arziki. Wannan shi ne ginshiƙan sabon ginin da aka fara a Kudan.

1. Dabarar tsaro (Jagorancin haziƙan mutane)

A ƙofar kasuwar Kudan, matasa sun taru ƙarƙashin jagorancin Salmanu Faris da Nuhu Baushe, Nawalmu da Garba Ode. Sun kafa Kudan Community Watch, wata ƙungiya da ta haɗa matasa masu kishin gari.

Salmanu ya tsai da kansa a gaban jama’a ya ce:

“Tsaro ba na gwamnati kaɗai ba ne. Tsaro tamkar alwala ne, kowa ya tsarkake nasa ɓangaren.”

Nuhu Baushe, fitaccen mafarauci mai hikima, ya ƙara da cewa:

“Mutum da ke iya bin sawu a daji, ba zai kasa gano matsala cikin gari ba.”

Sun rarraba matasa zuwa rukuni-rukuni:

1. Rukuni na dare, ‘yan sintiri masu bin layi har da mafarauta.

2. Rukuni na kasuwa,  waɗanda ke kula da kasuwar gari.

3. Rukuni na hanya, masu taimakon mata da yara wajen tsallaka tituna, musamman a lokacin cankuso.

Garba Ode, wanzamin gari, ya zama mai lura da lafiyar matasa. Kullum yana cewa:

“Idan ka so ka yi gudu mai nisa, to ka ci gaba lafiya.”

Mutane suka ji daɗi, suka fara hango kwanciyar hankali.

A farfajiyar babban masallacin Juma’a na Kudan, malamai suka fara gudanar da babban taron da ya tattara ɗalibai, matasa da manya. Malam Aliyu ya tashi ya fara magana cikin nutsuwa:

“Haɗin kai tamkar tukunya ce; ko an yi girki mai daɗi, ba za ku ci ba , dan tukunya ta karye.”

Daga nan malamai suka kafa shirin da suka kira “Tattalin Zumunci” , inda kowane gida zai ziyarci wani gida a kowane mako, domin sada zumunta. Wannan ya rage rigingimu da rashin fahimta. Sannan kuma duk Alhamis ɗin ƙarshen wata, malamai zasu dunga taru wa a masallacin Juma’a na cikin gari, don yin musaffa tare da addu’o’in zaman lafiya da ci gaban gari.

Mal. Auwal da Mal. Salim suka shigo da darussan boko, cewa matasa su koyi rubutu, fasaha, kimiyya da ilimin zamani. Suna yawan cewa:

“Karatu shi ne ido, idan ka rasa shi, koda kana da ƙafa za ka yi tafiya cikin duhu.”

Malam Abdulhafiz ya koyar da matasa dabarun tattaunawa da sauraro.

Malam Yasir ya koyar da “Tsarin gina gari ga matasa”.

Malam Salisu ya shigo da dabarun zama lafiya.

A hankali, mutane suka fara fahimtar cewa:

Haɗin kai ba maganar baki ba ce. Aiki ce.

BABI NA BIYAR

A kasuwar Kudan, ana ta hayaniya cikin nishaɗi. Abubakar mai kamfanin shinkafa ya kawo sabuwar na’urar tacewa. Ya ce:

“Shekara da yawa muna da fili, kuma muna samun amfanin gona mai yawa, amma ba mu da fasahar sarrafawa ta zaman, wacce za ta tace mana kayan amfanin gonan mu cikin sauƙi da kuma tsabta”.

Nan take sai ya ɗauki matasa 25 suka zama ma’aikatansa, mata 10 suka zama masu tace shinkafar da aka noma, sauran mutane 15 kuma masu noma kayan amfanin gona gami da samar da taki mai inganci.

Muzammil da Mas’ud suka haɗa ƙungiyar mazauna garin da ke noma.

Nafi’u da Isma’il suka fara shirin Noman Zamani da amfani da injina.

Mutane suka fara jin cewa tattalin arziki zai farka daga sumar da ya yi. Kasuwa ta zama wuri mai cike da motsi.

Mutum ya je kasuwa ya ji ana cewa:

“Kudan ta tashi, Wallahi Kudan ta tashi tamkar aure da ya zo da annuri.”

Ƙungiyar Mawaƙa

A gidan Labaran Adamu, aka yi zaman mawaƙa. Su Ashiru, Salahu, Ali Na Annabi da Rabilu sun rubuta sabuwar waƙa mai taken: “Uban arziki ”

Waƙar ta kama hankalin mutane sosai. A cikin baitocin waƙarsu akwai karin magana mai zurfi:

“Idan rana ta fito a gefenku, kada ku ce ba ku dace ba, ku tashi ku yi aiki.”

Wannan waƙa ta zama tamkar tutar motsa zuciyar al’umma.

Daga Ƙarshe

Yayin da rana ta doshi yamma, mutane suka tsaya a kan ƙaramin tudu suka kalli hasken rana tana faɗuwa. Kamar furen da ya buɗe, zukatan al’umma suka yi fari.

Farfesa Mu’azu ya tsaya ya ce: “Daurin mu a yau ya zama ginshiƙin gobe. Idan mu ka dage, Kudan zata zama abin koyi.”

Salmanu Faris ya ce: “Gari ba ya giɓi idan kowa ya ɗora nasa tubalin.”

Mutane suka ce gaba ɗaya: “Mu tashi, mu gina Kudan! Don tuƙa Tuwon gobe lafiya”.

Yayin da tashin hankali ya fara raguwa

A kwanakin da suka biyo baya, garin Kudan ya fara samun nutsuwa fiye da da. Ayyukan Salmanu Faris da tawagarsa: Nuhu Baushe, Nawalmu da Garba Ode, sun riga sun bazu a cikin gari kamar wutar daji a zukatan mutanen gari. Kowa ya fara kallon gaba, domin an fara ganin tabbas gari ya fara komawa bisa turba.”

A daren ranar Asabar, bayan taron tsare-tsare da suka gudanar a unguwar Kintonho , suka fito suna tafiya cikin farin wata mai haske. Kamar yadda Hausawa ke cewa:

“Idan dare ya yi tsawo, sai ya kai ga wayewar gari.”

Wannan kenan. Wayewar gari ta kusa.

Ginin Sabon Masallacin Juma’a

Washegari da safe, jama`a suka taru a babban fili yayin da ake ƙaddamar da ginin babban Masallacin Juma’a da Rt. Hon. Isa Ashir ya ɗauki nauyi. Ya yi wani jawabi wanda ya cika zukatan mutane:

“Garin da ya rasa tsaro, ya rasa komai. Amma garin da ya nemi ilimi, tarbiyya da haɗin kai, to ya kama sahun cigaba.”

Sadaukarwarsa ta ja hankalin kowa. Salmanu ya kalli masallacin yana murmushi. Ya ce a zuciyarsa:

“Ginin masallaci ba katanga ba ce kaɗai. Gina zuciyar al’umma ne.”

Makarantar Sana’o’i ta Tashi Tsaye

Ranar da suka fara shigar da kayan aiki makarantar koyon sana’o’i, sai yaran gari suka yi tsalle da murna. Wani yaro mai suna Zailani Sambo ya ce:

`Wallahi zan koyi gyaran waya in taimaka wa iyayena!”

Nawalmu ya yi murmushi yace:

`Ai haka ake so! Sana`a kamar garkuwa ce, mai shi baya jin yunwa.

Bisa ga dalilin haka,sai aka samar da wasu rassa kamar: gyaran lantarki, ɗinki, walda, girki da fasahar kwamfuta. Gari ya fara cika da hayaki na cigaba, ba na rikici ba.

Makarantar ƴan Sanda (Police Academy)

Garba Ode, wanda ke da ƙwarewa a ilimin ladabtarwa, shi ne aka ba alhakin tsara tsarin horo. Ya ce wa Salmanu:

“In an so zaman lafiya, dole a gina jami’an tsaro masu hankali, ba masu daga bindiga kawai ba.”

A can an samar da aji-ajin koyar da:

1. Magance rikici.

2. Dabarun tattaunawa.

3. Kare haƙƙin ɗan adam.

4. Sahihiyar bincike.

Ginin ya zama tamkar wuta da ake iya ganin hasken ta daga nesa.

Asibitin shakatafi (Primary health care)

Rt. Hon. Isa Ashir ya kuma aika injina da ma’aikata wurin gina sabon asibiti, domin ya ce:

“Ba tsaro ba tattali idan babu lafiya.”

An kafa sashen haihuwa, daakin tiyata, da ɗakin taimakon gaggawa. Dattawa suka yi addu’a, mata suka yi hawaye na farin ciki. A wurin ƙofar asibitin wani dattijo ya ce:

“ Turakun gari sun fara zama.”

BABI NA SHIDA

Matasa kuwa sun yi murna fiye da kowa da ginin filin ƙwallo na zamani. A ranar da aka fara dasa harsashin ginin wajen,ɗaruruwan mutane suka taro a wajen, don murna.

Nuhu Baushe ya ce:

“Matasa da ba su da abin yi, fitina na kiransu. Amma idan ka basu filin wasa,ka rage yawan ɓarna.”

Filin ya zama wajen taron matasa, wuri mai ɗauke da annashuwa maimakon hayaniyar rikici.

Sabon Tituna,

An fara shimfiɗa tituna masu faɗi a manyan lunguna. Hakan ya sauƙaƙa zirga-zirga, ya hana ‘yan fashi yin ƙwanton-bauna.

Salmanu ya ce lokacin da suka tsaya kallon injinan da ke aiki:

“Idan ka gyara hanya, ka gyara zuciya. Domin hanya ta haɗa ɗan Adam da ɗan Adam.”

Nawalmu ya ƙara da cewa:

“Hakika! In aka samu hanya, ko rikici na iya tserewa!”

Yayin da rana ta faɗi kan sabbin gine-ginen da suka ƙawata garin Kudan, Salmanu Faris ya kalli Nuhu Baushe, Nawalmu da Garba Ode, sai ya ce:

“Haɗuwar al’umma waje ɗaya, da shawo kan rikic, shi ne jigon abin da zamu sa a gaba. Mu ci gaba, kar mu tsaya.”

Gari ya yi shiru mai cike da salama. A cikin wannan shiru akwai wata magana ta gargajiya da ta dawo masa daga zuciya:

“Gari da alheri ya bunƙasa, ko tsuntsu na leƙen damar zama.”

Wɗancan dalilai sun sa garin Kudan ya samu cigaba fiye da shekarun baya. Saboda garin ya kafu shekaru ɗari biyu tun kafin jihadin Usman Ɗanfodiyo, wato a ƙarni na goma sha huɗu, wanda a yau (2025) garin ya samu shekaru ɗari shida da ashirin da biyar da kafuwa (625).

A makonnin da suka biyo baya, sabuwar duniyar Kudan ta fara bayyana a fili. Mutane suna yawo cikin kwanciyar hankali, yara na wasa a sabbin tituna, mata na fita kasuwa cikin kwanciyar hankali, dattawa na zama ƙarƙashin inuwa suna tattaunawa da nishaɗi.

A wani yammaci, Salmanu Faris ya tsaya a saman wani ɗan tudu yana kallon garin. Yana jin wani irin shauƙi da jin daɗi a zuciyarsa. Nuhu Baushe ya taho daga baya ya ce masa:

“Kai Salmanu, garin nan ya zama abin kallo! Haka ake so, idan rawani ya yi kyau, sai a yabawa mai ɗaure shi.”

Salmanu ya yi murmushi:

“Mu dai mun yi niyya ne, Allah ya daidaita. Kowa ya bada gudunmawa.”

A kwanakinnan, an ga wani sabon yanayi na haɗin kai wadda ba a saba gani ba.

Matasa suna taimakon juna wajen tsaftace titi. Mata suna koyon sana’o’i a makarantar horo. Dattawa na bada shawarwari a majalisa.

Kowane yanki na gari yana kama da sabon fure da ya fara buɗewa.

Ƙofar Arewa, Ƙofar Gabas, Ƙofar yamma (Kintonho), Ƙofar yamma ko Zaria.

Har’ila yau, kuma an kafa kwamiti na kowace unguwa, don tabbatar da tarbiyyar yaran unguwar gami da warware matsalolin zamantakewar auratayya. Waɗancan unguwannin sun haɗa da: Unguwar Makera (farfaru), unguwar Maƙera (babbaƙu), Ƙofar Arewa, Saidawa, Unguwar Zaɓi, Ƙofar Gabas, Unguwar Liman, Unguwar Bela, Juga (Kintonho), Yan Gishiri, Unguwar Malamai, Unguwar Ƴan Takalma, Tudun Wada, Ƙofar Fada, Sabon garin Kudan, Unguwar Malam Talatu, Rimin Baima, Kuka, Tartibu, Unguwar Tsauni, Unguwar Ma’aji, tsohuwar Kasuwa, Shagari Quarters da sauransu.

Garba Ode, wanzamin gari kuma ɗaya daga cikin shugabannin ci gaban al’umma, ya tsaya gaban jama’a a kasuwa ya yi magana cikin hikima:

“Idan mutum ya ceci mutum guda, tamkar ya ceci duniya ne. Mu ci gaba da taimakon juna ko kaɗan ne. Da kaɗan-kaɗan ne ake tara tsaba a rumbu.”

Kowa ya yi dariya, domin Garba Ode yana da hikima mai fara’a.

Ginin masallacin Juma’a, asibiti, makarantu da tituna sun ba mutanen Kudan sabon yanayi. Mutane suna yawan cewa:

“Ashe idan mutum mai hangen nesa yana mulki, gari ya kan yi kyau kamar hatsi a kwando!”

Rt. Hon. Isa Ashir ya sake ziyartar wuraren da ake gine-gine. Yara suka ruga suna ta murna suna kiran sunansa. Ya tsaya ya ce:

“Na gina gine-gine, amma ku kun gina haɗin kai. Ku ne jarumai.”

Kalmar nan ta sanya mata da maza yin kabbara da farin ciki.

A wata laraba, an gayyaci Salmanu Faris zuwa babban taron Majalisar ci gaban Kudan.

Duk jama’a suna jiran jin me za a ce masa.

Shugaban majalisa ya miƙe ya ce:

“Mutumin da ya jagoranci zaman lafiya, ya haɗa matasa, ya haɗa dattawa, ya ƙarfafa tsaro, ya samar da cigaba, ba wanda ya cancanci yabo kamar Salmanu Faris.”

Jama’a suka yi tsalle da tafi.

Salmanu ya miƙe cikin ladabi. Ya ce:

“Na yi abin da na iya ne kawai. Gari ba na mutum guda ba ne, gari tamkar tabarma ne, kowa zai iya samun zama.”

Jama’a suka amsa da cewa:

“Hakane! Gaskiya ka faɗa!”

Wannan dare, a ƙofar masallacin Juma’a, an shirya liyafar godiya. An kunna fitilu, yara suna murna, matasa suna ta kabbara.

An miƙa kyaututtuka ga jarumai uku na gari:

1. Nuhu Baushe, saboda tsayuwar tsayin dakan da ya nuna wajen kare jama’a.

2. Nawalmu, saboda hikimarsa gami da ƙwazon, wajen bincike gami da tabbatar da zaman lafiya.

3. Garba Ode, saboda basirarsa da kuma ƙwarewarsa wajen ladabtar da mutanen marasa jin magana.

Dukkaninsu sun yi jawabi ɗaya bayan ɗaya.

Nuhu Baushe ya ce:

“Rana ɗaya bata ƙona duka jirgi, haka rikici ba zai ɗauki gari gaba ɗaya ba idan muna tare.”

Nawalmu ya ce:

“Hikima tamkar haske ce; idan ka kunna ta, duhu ya gudu.”

Garba Ode ya yi dariya ya ƙara da :

“Ai ni Garba Ode, na saba da aiki da mutane. Idan kana so su nutsu, ka fara nutsuwa da kanka.”

Jama’a suka yi banƙwana da dariya.

Fitilu suna haske, tituna suna sababbi, masana’antu sun tashi, gidaje sun gyaru, kasuwa ta bunƙasa, matasa na neman ilimi da sana’a.

A hankali, mutane na ko’ina suna cewa:

“Kudan ta dawo.”

Salmanu ya tsaya gefe yana kallon wannan canji. Yana jin kamar an saka masa nauyin al’umma a kafaɗarsa, ba nauyi mai wahala ba, amma na alfahari.

Ya ce a zuciyarsa:

“Idan mutum bai yi wa gari ba, gari zai yi masa.”

Saboda haka ya yi addu`a:

“Allah ka saka da alheri, ka dauwamar da zaman lafiya.”

Fitilar gari ta haska fuskarsa, kamar wani sabon jarumi da zai ci gaba da jagorantar al`umma zuwa gobe mai haske.

Salmanu Faris, ya tashi tsaye cike da murna. Sannan yace ” al’ummar wannan gari mai albarka, na shirya wata waƙa, don taskance unguwanninmu da kuma wasu ayyuka na mu”. Ga waƙar nan kamar haka:

1.

A ƙasar Kudan mai daraja, mai farin taurari a samanta,

Tarihi ya haɗa ƙofofi huɗu, kowacce na ɗauke da alherinta,

Ƙofar Arewa mai kwanciyar hankali da nutsuwa babu tata,

Ƙofar Gabas mai mazan jiya, uwa ce ga arziki da rabonta.

2.

Ga Ƙofar Yamma, wurin jarumai tun kaka da kakanta,

Zaria ce ta gefe, mahaɗar ilimi da sadar da zumunta,

Duk mai shiga sai ya ji ƙamshi mai daɗi daga gadonta,

Kofofi mai tarihi, wanda ba ta gushewa har lokacinta.

3.

Makera farfaru,masu fasaha tun da, fitila ce ga sana’arta,

Makera babbaƙu, masu hikima wanda ba sa yin gorinta,

Saidawa da Zaɓi, unguwanni masu sana`a da himmata,

Unguwar Liman, Bela, da Juga,suna ɗauke da kamalarta.

4.

Yan Gishiri, unguwar arziki, mai ƙara armashi a miyarta,

Unguwar Malamai, maɓuɓɓuga ilimi, haske ke iliminta,

Unguwar Ƴan Takalma, ƙwararru ne masu zaratar fata,

Tudun Wada da Ƙofar Fada, wuraren mutunci da nagarta.

5.

Sabon Gari, sabuwar duniya mai ci gaba da inganta.

Rimin Baima, Kuka, Tartibu, kowacce tana da hikimarta,

Unguwar Tsauni da Ma’aji,wuraren tarihi masu basirarta,

Tsohuwar Kasuwa da Shagari Quarters, wurare masu limanta.

6.

An kafa kwamiti a kowanne yanki, don lafiya ta tabbata,

Tarbiyyar yara, warware matsalolin aure ban da salwanta,

Dattawa da dattijuwa na ba da shawara cikin tafiyarta,

Domin ƙauye ba na mutum ɗaya ba ne,” don cigabanta.

7.

Salmanu Faris ne ya tsara wannan waƙa mai nagarta,

Domin tunatar da sanin darajar unguwanni da ƙauyenta,

Duk inda ka juya, alheri yana haskawa tamkar alfijir a wajenta,

Allah Ya kare Kudan, Ya tsare ta da kwanciyar hankalinta.

Karanta Tarihin Garin Kudan

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceYadda Asalin Kishi Yake
Labarin na GabaTatsuniyar Jarumin Sarki