Tarihin Dr. Magaji Ahmad Gaya (PhD)

0
126

An haifi Magaji Ahmad Gaya a garin Gaya da ke cikin jihar Kano 17 watan Janairu a sherarar 1974. Ya yi karatun addinin Musulunci a makarantar gidansu, wato makarantar Alaramma Malam Shehu da kuma wasu makarantu a unguwar Matamawa da ke garin Gaya, a makaranta Malam Isah, sannan kuma da makarantar Malam Shu’aibu Zai da ke a ƙaramar hukumar Dutse ta jihar Jigawa.

Ya yi karatun Firamare a makarantar Dagara Firamare da ke garin Gaya, haka kuma ya yi karatu a makarantar horar da Malamai da ke dutse sannan ya kammala a makarantar horon Malamai ta Wudil a Shekarar 1990, inda ya kammala da takardar shedar malanta ta ɗaya (Grade II).

Da ga nan kuma, ya halarci kwalejin ilimi ta Kumbotso wadda aka fi sani da (Sa’adatu Rimi college of Education Kumbotso) a shekarar 1995 inda ya sami takardar shedar malanta ta ƙasa (NCE). Ya ci gaba da karatu a jami’ar Bayero, inda ya yi digirinsa na farko wato (B.A. Hausa Special) a shekarar 2004.

Ya sake komawa Jami’ar Bayero Kano inda ya yi karatun (PGD Hausa Studies) a shekarar 2008. Sannan ya koma Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sokoto ya yi karatun digirinsa na biyu (M.A. Hausa Ɓangaren Nazarin Al’adu) a shekarar 2018.

Bayan nan ya ci gaba da karatun digirinsa na uku (PhD Hausa Ɓangaren Nazarin Al’adu) a Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’adua da ke garin Katsina, ya kammala a shekarar 2024. Haka kuma ya yi aikin koyarwa a wasu makarantun firamare da sakandare da kuma Kwalejin Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kumbotso.

A halin yanzu yana koyarwa a Jami’ar Northwest, Kano Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya. Ya wallafa littattafai da maƙalu masu ɗimbin yawa. Yana da aure da ‘ya’ya masu albarka. Alhamdulillah.

Karanta Sakamakon Bincike A Kan Wasan Ƙunshi

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceWasu Laƙanin Sunayen Hausawa A Al’adun Gargajiya 2
Labarin na GabaMijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Ɗaya
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.